Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 9
mu yi kasa a gwiwa”. "Maganar ki gaskiya ce, wannan haka yake, to amma yake Hindu ya kike gani za mu yi wajen ganawa da Hakimi Abdullahi bin SHarjasllah, ki sani cewar matukar sun san wani shiri to za su gyara na su shirin, abin da nake tunani wani amintacce za ki nemo min wadda zai kai masa ziyara wadda shi da kansa Hakimi zai nemi yarima ni kuma zan gayawa yarima sakon da zai je masa da shi". ** Lokacin da Jarumi Umar ya iso babban turakar mahaifinsa, a daidai lokacin Hakimi na nazari game da bakuwar Suhaila bin ✓ Ababakari da kuma tunanin sakon da Sarauniya Hauletu ta zo masa da shi na son haduwa da Yarima Abbas. A wannan lokacin ya yanke kai ziyara babban birnin domin ganawa ta musamman da Sarki a game da sabuwar masarautar da ake rigima a kai, sannan kuma zai yi amfani da wannan dama ya gana da Yarima Abbas. bature 14 Page Ya tsaya yana jiran umarni daga Waziri Jafar. Batare da Jafar ya ba shi umarni ba ya mike tsaye cikin izza da isa sai da ya yi taku biyu zuwa uku sannan ya dakata yana kallon Jarfis sannan ya ce “Ina sokon da kake tafe da shi?" Jarfis ya gyara tsayuwa ya ce "An taho da Gimbiya zuwa wannan birnin zuwa dan takin lokaci yarana za su iso da ita kamar yadda ka umarta za a kaita masaukin da ka umarci a a jiye ta a can”. Waziri Ja'afar ya ce "Ka tabbata ka zabi kwararrun kuma masana wajen aiwatar da wannan aikin kamar yadda muka yi da Sarki Jarmusu Jakub". Jarfis ya ce "Kamar yadda ya umarce mu haka komai ya gudana, daga nan zuwa kowane lokaci dan aike zai iya zuwa ya sanar damu cewar an kai ta masaukin da ka tanada don kai ta can". Waziri Ja'afar ya jinjina kai ya ce "Za mu ga ni, sauraro". kuma muna Har Jarfis ya bude baki zai yi Magana sai daya daga cikin yaron Kirzalu yayi sallama tare da cewa "Akwai bako daga Kiristoci ya kara so". Koda jin haka sai Waziri Ja'ffar ya dubi Jarfis ba tare da yace da shi komai ba. Jarfis y ace "Babu shakka 'yan sako sun iso don haka ya shigo ya gabatar da bayani a gaban Waziri Ja'afar". Jim kadan bako ya shigo cikin dakin yayi gaisu wa da Jarfis tun da Jarfis ya ga jikinsa duk rauni hannunsa na dama sai digar då jini yake sai ya zabura ya ce "Ya kai Sarkal, mene ne yake faruwa na ganka a haka ka tabbata kun iso da Gimbiya kun kaita inda aka Umarce ku?" Sarkal ya sunkuyar da kai kasa cikin nadama game da cewa "Ya shugabana ka dauki rayuwata domin ba ta da wani amfani a gare ka, mun yi rashin nasara gabatar da Gimbiya zuwa inda aka Umarce mu". bature 15 Page Har Jarfis ya zare takobi zai sare masa kai sai Waziri Ja'afar ya daka tsawa gami da cewa "Ni nake yanke hukunci a nan, saboda haka ni ne zan dauki mataki a kan ka da kuma dan sakon ka". Koda ya dakatar da Jarfis sai ya tako sannu a hankali zuwa ga Sarkal "Kisan ka ba shi da wani amfani a gare mu face bata kaifi takobi da bata waje, amfani daya ya rage maka a gare mu yanzu shi ne "A ina kuka yi shashancin sakaci da gimbiya?" Sarkal ya duka har kasa ya ce "Waziri nayi iya bakin kokari na na ganin na cika aikina kamar yadda na faro shi, amma na gaza a daidai madakatar Annur, inda wani Jarumi guda daya tal kamar shaidani ya baiyana a gare mu, duk ya bazar da yara na suna can cikin halin mutuwa ko rayuwa, dakyar na iya rarrafowa na kawo kai na nan domin na sanar da ku halin da ake ciki". Waziri ya jinjina kai game da cewa "Mutum daya kace kuma dai dai mararrabar Annur. To me ya hada ku da shi a wane dalili?”. Duk yadda ta faru Sarkal yay i bayani Waziri ya tafi nazari a ransa yana tunanin waye wannan mutum daya, ko ma waye zai kasance daga cikin jaruman Hakimi Abdullahi bin SHarjas. Koda gama wannan tunanin sai ya dubi Kirzalu y ace "Maza ka basu rawani da alkyabba mu isa Annur kafin faduwar rana, domin matukar ba mu tafi da Gimbiya ba Hakimi Abdullahi bin Sharjas zai yi wani abu maza ku shirya. ** Fadar Hakimi Abdullahi bin SHarjasl cike da jama'ar ana shirin bada umarni abi sahun Jarumi Jarumi Umar bayan da yayansa Abdullahi ya bi shi tare da dakaru goma. Ana wannan zaman ne sai ga Jarumi Abdallahi da mutum goma da ya tafi da su, gaba gare su ga Jarumi Umar nan da Gimbiya a bisa dawakai sun nufo kofar gidan Hakimi Abdullahi bin Sharjas. Kowa da ke wajen suka zuba wa bature 16 Page Jarumi Jarumi Umar da baki ido har suka iso bakin fada a inda Hakimi Abdullahi bin Sharjas ke zaune a bisa kujera ga dattawan gari suna zaune. Jarumi Umar Bin Abdullahi bin SHarjas ya karaso fuskarsa cike da annuri ya iso wajen mahaifinsa ya fadi yayi gaisuwa gami da yin gaisuwa ga dattijan majalisa suka amsa masa. Bayan Abdallah ya sauko daga dokinsa ya zo kusa da dan uwansa sai ya dubi Jarumi Umar ya ce "Ya mai girma Mun fita hanya don zuwa kaiwa Jarumi Umar dauki kamar yadda ka umarce mu,sai muka gan shi ya taho tare da wadan nan matan guda biyu, bai yi mana wani bayani ba, mu ka biyo bayansa har zuwa gida". Guri ya kara shiru mutane suka mayar da hankalinsu ga Gimbiya da abokiyar tafiyarta. Hakimin wato Abdullahi bin Sharjas Annur wato mahaifi ga Jarumi Umar ya kalle shi cikin alamun son Karin bayani Jarumi Umar ya gyara murya y ace “Ba wani abu da na sani dangane da su Baba, abin da nasani shi ne na kwace su daga Annabi hannun Kafirai ma'abota kaucewa daga koyarwa Muhammad farsi, sun so na bar su su ci gaba da tafiya a cewarsu zamowarsu a nan zai haifar mana da barazana gami da farmakin abokan gabarsu" Daga nan bai kara cewa komai ba. Hakimi ya dubi Gimbiya da suke tsaye suna neman izini. Ya jinjina kai ya ce ‘Yata matso kusa". Gimbiya na jin haka sai ta jinjina kai alamar amanna sannan ta taho ga tsoho Abdullahi bin Sharjas ta duka ta kai gaisuwa "Yata, wace ce ke, daga ina kike?" Gimbiya ta ce "Ranka ya dade Suna na SUHAILA BIN ABABAKARI, ni 'ya ce ga Sarki Abubakari wadda yake mulki a kasar Shamnun,an kamo ni ne a lokacin da nake kokarin tsarewa daga masarautar mu domin gujewa ballewar rikicin sarauta, wadda bature 17 Page tun daga mutuwar mahaifinmu magauta suke ta kokarin ganin sun hana kasar zaman lafiya, har yayan mu Yarima SALMAN ya gudu daga kasar saboda farautar rayuwarsa da ake yi, saboda da yawa a cikin kasar Yarima HALIL ne ya siye su don zama magajin mahaifin mu, yayana Yarima Salman ya turo min sako na gudu a cikin dare saboda matukar ya hau kan karagar mulki duk wasu ‘ya'yan mahaifiyarmu sai ya kashe su, mummunan kisa, wannan shi ne abin da ya baro ni daga kasar mu, sai kuma aka kamamu, aka kuma danka mu a hannun wadan nan kafuran za su danka mu wani hannu da ba mu san ko su waye ba a cikin Bahara shi ne Allah ya hada mu da wannan Jarumi ya kubutar damu, amma suna yawan zantawa za su kai mu wajen waziri Ja'afar don gabatar da ni ga Sarki Nasir Su ka hada ido da Jarumi Umar ta yi masa kallon tambaya, ya sunkuyar da kai kasa yana sauraren abin da mahaifinsa zai ce matsalarsa dama dan uwansa Abdullahi da ya tuna hakan su ka yi ido biyu da shi a dai-dai lokacin shi ma Abdullahi kallonsa yake irin kallon tuhuma. Hakimi ya ce "Duniya bata samu ba, sai da jini ya zuba, addinin musulunci bai kafu ba sai da jini ya zuba, sulhu baya yiwuwa sai an zubar da jini, taimakon ‘wata kasar da wata baya tabbata sai an kwantar da wasu, ki saka a ranki ke ‘ya ce a gare ni kika taho neman tallafi na, maza Shame'u zo a shiga da su ciki, koda duniya zata 3 tunkare ni, ba zan bari a tafi dake ba, Allah ya kawo ki ne gare mu domin ya san za mu iya ji da duk wata bakar guguwa da zata mamaye duniya.. Jarumi Umar ya jinjina lamarin yana wani murmushin jin dadin tarba da mahaifinsa ya yiwa su Gimbiya. Hakimi ya dubi Jarumi Umar ya ce “Abin da ka yi yayi dai-dai ɗana”. bature 18 Page Ba haka Abdallahi ya so ji ba,domin a zatonsa za a yi wa Jarumi Umar fada kamar yadda wasu lokutan yake debo ta da zafi azo a yi masa fada musamman fada da arnan daji. SHEMA'U ta zo cikin sauri ta talbe su, ta yi cikin fara’a da murmushi daya daga cikin kannen Jarumi Umar kenan. "Hakimi ya kara da cewa "Kowa ya zauna cikin shiri domin komai zai ya faruwa daganan zuwa gobe za mu iya yin baki" daga nan matasa da sauran wadanda babu su a zaman majalisar Hakimi duk suka koma bakin aik, dattawa da Hakimi suka ci gaba da tattauna a game da harkokin mulki na yau da gobe Jarumi Umar dubi abokansa su hudu da suka saka shi a tsakiya Daddar ya ce "Eh ba mu labari umi Umar dube shi duban tuhuma y ace “Labarin me ke nan?" "KUBAIT ya yi muurmushi tsolaya yace "Ka da ka yi mana rowa mana, na ga fa yadda kake kallon gimbiya, ita ma na ga yadda take kallon ka❞ Duk su hudu suka kwashe da dariya shi kuma ya hade rai "Wai me kuke nufi ne?" Kubait ya tsaya da dariya ya ce "Mafaraucin dabba ne yau yayo farautar mutum, shin akwai wadda ya isa ya kwace masa abin farautarsa”. Su duka suka kara kwashe da dariya Jarumi Umar ya kara hade rai "In kun gama nishadinku ku ne me ni, babu ni a cikin* wannan gayyar". SAKLAHUL ya ce "Ita fa ba kamar Jaruma bace, ko wani, dutse mai nauyin gaske da za a nuna mata mazantaka, idan ka tafi ma za ka dawo kana ba mu labarin, eh ita zuciya ba komai take iya jurewa ba, domin wani abin gubace sai an fesar ake samun sukuni”. 19 Page "Idan ku kun kuna da sararin da za ku na barin zuciyarku da duk wani abu da bai shafi tafarkin Allah da ma'aiki ba,ni ba ni da shi". “Tafarki da sunnar ma'aiki duk suna daga cikin abin da muke maka fatan kasancewa tare" MU"AZ yay i furucin duk suka kwashe da dariya har yayi nisa yana jin su. Wani tsaki ya kara yi a ransa ya ce “Shashashe, ko me suka ga ni har ya sa suke zargin na kamu da so". ** A nan take Waziri suka hau hanya don zuwa Kauyen ANnur wadda anan ne za su ji su tabbatar da inda su Gimbiya suke a hanyar ne Jarfis ya radawa Sarkal rada cikin hikima yadda babu wadda ya ji abin da ya sanar da shi ya ce “Lallai zabi wani a cikin mutanen mu, ka je ka labartawa Jagora Philiphis halin da a ke ciki domin ya san shirin da zai yi." "An gama ya shugaba na" Sarkal ya sulele a hankali ya je ya sanar da wani daga cikin dakarunsa sakon da Philiphs ya sanar da shi, ba tare da bata lokaci ba Mahayin ya sulele a dokinsa ya nufi wata hanya. Tun da suka fito daga babbar birni ba su kara yada zango ba sai a cikin kauyen Annur. A dai-dai lokacin da Hakimi zai shiga cikin gidansa sai ga tawagar Waziri nan cikin sauri sauri sun iso bakin fadar Hakimi". Koda Hakimi da sauran yan fadar da basu tafi ba suna niyar tafiya suka ga Waziri a halin sauri sai suka dakata domin za su iya tafiya Hakimi ya sa a kirawo su su dawo saboda ganin Waziri sau tari babu alkairi a ciki ziyararsa. Kowa dake wajen ya duka ya gaida Waziri amma banda Hakimi Abdullahi bin SHarjas, kamar yadda ya saba a kowane lokaci bature 9 20 Page matukar ba fadar wani ya je ba ba zai zube yayi maka gaisuwa irinta sarauta ba sai dai za ku gaisa kamar yadda shari'ar Allah ta ala ta tanadar. Waziri ba yau kadai ya san da wannan rashin girmamawa da Hakimi Annur yake yi masa, duk kuma yadda zai yi yayi domin a kwace hakimanci daga hannun Abdullahi bin Sharjas abawa dan uwansa SHAMSU BIN AUJAR amma sarki ya nemi dalili, ganin dalilin rashin girmamawa ba zai sa Sarki ya sa a sauke Hakima domin ko shi da kansa Hakimi baya masa gaisuwa da ta dace suna rayuwa ne tare kamar da da mahaifi, kuma Sarki bai taba jin wani abu a game da haka domin yana girmamawa Hakimi Abdullahi bin SHarjas. Bayan kowa ya nutsu Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya ce “Lafiya muka ganka da yammaci likis haka ya Waziri Birnin Bahara Allah ta Allah yasa dai lafiya". Waziri ya waiga gefe da gefansa ko zai ci karo da wani alamu na gimbiya, ganin bai hango komai ba ya sa ya dawo da hankalinsa ga Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya ce Ko ka ji labarin batan Yarima Salman ko 'yar uwarsa Suhaila bin Ababakari, ‘ya'yan marigayi Sarki Ababakari?" Kowa da ke wajen sai yayi shiru har sai da Waziri ya tabbatarwa zuciyarsa akwai Gimbiya Suhaila bin Ababakari a hannunsu, sannan ya kara da cewa "Ya kai Hakimi ka yi sani cewa Wannan Gimbiya Suhaila bin Ababakari da wannan yaro Salman lallai masu laifi ne kuma ababen nema ruwa a jallo, don haka matukar suna nan ka gaggauta bani su domin na kaisu Masarautar Shamnun domin gujewa afkawa yaki tsakanin kasashen musulunci"* Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya yi murmushi ya kara taku biyu zuwa gaban Waziri Ja'afar ya kare masa kallo sannan ya ce "Yaushe Bahara ta fara tsoron ‘ya'yanta da fada da darashin adalci, yaushe karamar kasa kamar Shamnun ta samu karfin gwiwar gwada bature 21 Page kwanjinta ga Bahara, har yaushe Bahara ta samu rashin kuzarin da za a aiwatar da wani abu a wannan yankin da take da mallakinsa batare da ita ce ta shugabantar da shi ba? Ya kai Waziri ina tare da Gimbiya Suhaila bin Ababakari a karkashin tsarona, amma bana tare da Yarima Salman, sannan ka sani babu mace a cikin rikicin rigimar mulkin domin haka zaka iya tafiya neman yarima Salman ka kuma gurfanar da shi a gaban Sarki Muhammad farsin, amma Gimbiya tana tare da iko na". Waziri ja'afar ya jinjina lamarin a zuciyarsa, domin ya san taurin kai irin na Annur gabaki dayansu wasu irin jajurtattun mutane ne marasa tsoro don haka dole ne ya sake sabon shiri don tunkarar daukar gimbiya Suhaila bin Ababakari daga gare su…….. Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya katse masa numfashi da cewa “Oh na manta, wai ma Sarki ne ya turo ka ko kuma zuwan kan ka ne?" Waziri yayi shiru,domin ya san cewar Sarki ba shi da sani a cikin wannan lamarin duk yadda zasu yi su boye kada ya sani sun yi, tabbas ya cika matsawa a cikin lamarin nan ya san cewar Hakimi zai jewa da Sarki maganar wadda haka kuma barazana ce ga Yarima Hilal don haka ya ce "A matsayina na mataimakin Sarki aka wakilta ni domin daidaita lamarin birnin Shamnun, na kuma amince da yadda Sarki, burina na hada kawunan Yarima Hilal da Salman". Hakimi Abdullahi bin Sharjas yadube shi yace "Amma me ya kawo kafurai suka tsare Gimbiya Suhaila bin Ababakari? Ko su ma suna cikin masu nemarwa musulmai zaman lafiya?" A rude Waziri Ja'afar "A'a bani da masani ya akan haka?” Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya ce "Me yasa baka nemi ta yadda aka samo gimbiya ba? An samo ta ne daga hannun kafurai suna kokarin shigar da ita birnin Bahara shin wajen ka za sukai ta dama ko kuma wajen Sarki?" bature (1) Waziri ya kara shiga rudu amma sai ya daure yayi murmushi gami da shafa gemu “Mene ne alakata da Kafurai da su kama gimbiya su kawo min ita, babu mamaki sun kwace ta ne a hannun mutanen da suka taho da ita, lallai mun godewa Allah da ta dawo hannun na gari ba ta fada hannun yahudu da nasara ba, ya kai Abdullahi bin Sharjas na barka lafiya ka kula da gimbiya Suhaila bin Ababakari" Koda fadin haka sai ya juya cikin sauri masu bi masa baya suka bi shi da baya. Hakimi murmushi yayi kawai ya dubi jama'arsa ya ce Za mu yanke shawarar abin da ya dace bayan Sallar Magriba ** Sarki Muhammad farsi mutum ne mai son addini da ci gaban al'ummar sa, yana da son addinin musulunci kuma yana bawa addinin gudunmawa da gasken gaske, ta waje daya ya samu tawaya, auratayya, ya hadu da mata mara sa kishin musulunci, da ci gaban sa, wannan dalilin ya haifar da yaduwar masu taimaka masa a bangaren sarauta suka zamo munafukai masu son duniya da abin da yake cikinta, duk da tsatson su musulunci amma sulallan Zinare ya mayar da su bayi, ba masu yiwa kasa hidima ba masu yiwa matan Sarki Hidima game da bukatunsu, wannan dalilin yasa birnin ya zama ba shi da wata kariya duk kokari da yake yaken da Kakaninsa suka yi don gujewa fadawa tarkon Yahudu da Nasara soyayyar matar tasa ya girbe dukkanin wannan nasara sun shiga tarkon Yahudu da nasara dumu dumu, ana aiwatar da abubuwa da dama a cikin gidansa bai sani ba, ana aiwatar da abubuwa a kasa bai sani ba, za a zartar da hukunci bisa saka hannunsa batare da ya san an yi hakan ba. Ba kowa ce Ummul aba 'isin wannan barnar ba face matarsa ta kuma Siyamal Ihud, Siyama kyakkyawa ce ta kwatantawa, bunkasa gidan Sarauta da haihuwar tanjamemen Saurayi wadda Sarki yake matukar kauna kasancewarsa babban dansa Yarima YAZID bature 22 Page 23 Page bayan shi tana da 'ya'ya uku dukkansu mata, sai matarsa ta biyu mai suna HAULE ibn Abbas 'yar babban wani shehin Malami ce a wadda yayi mamaya a dukkanin daulolin na musulunci wadda ya samar da litattafan addini, kwararre ne kuma wajen ba da magani don haka Likita ne kuma Malami ne, aboki ne ga tsohon Sarki Wato Junaid babban Muhammad farsi. ZULEHA ibn Abbas tana da yara biyu mace da Namiji ta haihuwarta biyar ragowar duk an salwantar musu da rayuwarsu,idan ta haihu yaro baya cika shekara biyu yake mutuwa, wadan nan biyun ne Allah ya tseran mata da su wato Yarima Abbas da kuma gimbiya Jauhariya. Sai mata ta uku wato HAULE ita ma kamar SIYAMAN ce har ta fi Siya ma iya makirci da tuggu, matsalar ita bata taba haihuwa ba, don haka ta koma ta kama kafa da Siyama, saboda SIYAMA duk ta fi su dukiya, saboda danta ana ganin shi nemagajin Sarki duk wata dukiya da za a bayar kyauta ga gidan Sarauta idan ta wuce Sarki to shi ita ake bawa, ko a al'adance itace Shugaban gidan ta fuskar fifikon Sarki,ta fuskar siye duk wani wadda yake da ruwa da tsaki a cikin gidan biyayya take yi mata, haka duk wani da ke wajen gidan da yake da alhakin kawo ma'aikatan gidan Sarauta to shi ma bauta yake mata, saboda haka sai abin da ta ce a gidan ake yi. A lokacin tana zaune a kan hamshakiyar kujerar mulki ta cikin gidan Zuleha na gefanta a zaune barori da 'yan aikin gidan Sarki na zagaye da ita, wasu mata na can wata da'ira ana busa da gara garaya suna dan rausayawa, ta na zaune idon ta kyam akansu tana murmushi, wasu in sun shigo sai sun je sun yi mata kamar sujjada su kuma sumbaci kafafuwanta sannan su nemi wajen zama su zauna. A wannan Lokaci Hauletu na bangarenta ‘yar ta yar kimanin goma sha biyar na gefanta a zaune da barori waje da cikin daki suna masu jiran wata bukata a isar mata da shi, kaf cikin masu mata bature 241Page hidima Siyama ce ta kawo su, mace daya ce aminiya kuma 'yar uwa, wacce ita ce kadai amintacciya a wajenta wato HINDU. Da ita take duk wani sirrinta a gidan. Hauletu ta dubi 'yar ta "ZAHRA ta ce "Ki je daki ki kwanta za mu yi Magana da Hindu". Zahra ta dubi mahaifiyarta cikin girmamawa ta ce mike tsaye gami da jinjina wa "Na barki lafiya". Ita ma Haulet ta jinjina kai ta ce "Sai na shigo duba ki a turaka ki yi addu'a sosai ki kuma yi karatunki kafin ki kwanta". Zahra ta fara tafiya ta na zuwa bakin kofa wasu mata biyu masu yi mata hidima suka bi bayanta doguwar rig ace a jikinta an yi mata dinki da na kawa rigar jikinta har jan kasa take yi kamar Dawisu yana tafiya. Sai da ta fice aka mayar da kofa a ka rufe sannan Haulet ta dubi Hindu ta ce "Yake 'yar amana ta, me kika sani dangane da Kauyen Annur,shin kin taba zuwa ko kuma kina da labara, ko akwai wani da kika sani a kauyen". Da Hindu ta ji wannan batu sai ta yi shiru tana nazari cikin dan lokaci ta dago da kanta ta dubi uwargidanta cikin nuna kulawa sosai ta ce "Amincin Allah ya tabbata a gare ki, ‘yar malamai jikar malamai, jinin malamai matar hamshakin Sarkin duniya Muhammad farsi, ina da sani a game da kauyen Annur, har ma ina da alaka da Hakimi Abdullahi bin Sharjas, ya sanni farin sani, domin tawagarsa ce ta samo ni, ta kuma musuluntar dani, kafin ta kawo ni gidan Sarauta, saboda haka na koyi abubuwan da yawa a cikin kwanaki goma da nayi a gidansa kafin daga bisani a kawo mu nan". Haulet ta jinjina kai “Yayi kyau, na kuma godewa Allah da na samu haka daga gare ki, abin da yasa nay i tunanin tambayarki a game da birnin Kauyen Annur na taba ji kina maganar Kirkin matarsa Kubra, a lokacin da kike bawa Hindu labarin jarumtar bature 25 | Page kauyen, ban kuma ta shi bukatuwa da son sanin ba sai yanzu da wani dalili da ya ta so". Hindu ta yi sunkuyar da kai domin jin daga bakinn Haulet, jin shiru yasa ta ce "Ranki shi dade me kike nema daga gare ni, in sanar dake dangane daga Kauyen Annur”. Sarauniya Haulet ta yi shiru daga bisani ta ce "Wani abu ke dauremin kai yake kuma sani tunani game da rayuwar kauyen, gashi karamin kauye ne amma yadda kowane munafuki yake tsoron kauyen abin yana daure min kai, hatta Sarki akwai shakkar Annur a ransa akwai girmamawa ta musamman, a bangaren Sarauniya Zulehat kuwa bata da wani tashin hankalida ya wuce ta ji an am baci kauyen Annur, mahaifina in har ya zo wannan yankin to zai ce da ni zai je Kauyen Annur ban taba tambayarsa wani abu da ke faruwa a kauyen ba, sai yau na tashi da son jin labarin kauyen shi yasa kika ji na fara da tambayarki, shin me yasa duk mai mutumci yake girmama kauyen, me yasa duk munafuki yake shakkar Kauyen?" Hindu ta yi shiru tana dan murmushi tana tuna wasu abubuwa da suka faru a kauyen kafin ta dawo gidan Sarauta ta ce "Zama ne ya kama mu a gidan a lokacin muna matsayin bayi. A lokacin da muka isa Kauyen Annur a matsayinmu bayi mun taho cikin kaskanci da yunwa kishirwa da wahala, amma kallo daya Hakimi Abdullahi bin Sharjas yayi mana ya fuskanci damuwarmu a cikin Babbar Kasuwar Birnin nan. A lokacin ya kawo abinci da dabbobi daga kauyensa don siyarwa ya same mu a kasuwa a cikin wannan halin mu biyar ne. maganar farko da ya yiwa mafarautar mutane "Ku basu abinci da ruwa su sha, idan kuka kyautata musu za su yi daraja maimakon ku bar su suna cikin yunwa ga wahala". bature Daya daga cikin Dakarun ruwan sai ya ce "Ba z aka koya mana yadda muke sana'ar mu ba, idan sun yi maka ka siye su ka basu abincin da ruwa". Bai ji haushin bakar magar da yayi masa cikin fara'a ya cc "Har nawa ne?" Daya bayan daya ya fadi farashin mu, duk da kudin sun yi ya kalli abokin tafiyarsa ya ce "Ka biya shi kudinsu” yawa saiWannan mutumin ya dubi Hakimi Abdullahi bin Sharjas a tsora ce ya ce "Ya kai dan uwana kana hauka ne, idan muka sayi bayin nan da wadanan nan kudin dukkanin kudin mu sun kare, ga shi ba za mu kara dawowa kasuwa mu sayar da amfanin mu ba, har sai bayan sati, wannan ba karamar barazana bace ga rayuwar mu da iyalin mu". “Ya dube shi ya ce “Ka biya su na ce da kai, Allah da ya halicce mu, shi ya hore mu da kyautatawa da abin da muke da shi, yayi alkawarin ninka mana, na ji tausayin matan nan kuma ina saka rai Allah zai ninka mana a nan gaba" Haka kuwa a ka yi ya saye mu ya kawo mu gidansa ya ba mu Kalmar shahada muka amsa matansa suka koyar da mu addini. In takaice miki a kwana biyu wani Sarki ya kawo ziyarsa a cikin mu Sarkin ya sayi bayi guda biyu, dukiyar da Hakimi ya samu duk da ya rangwantawa Sarkin akan yadda ya biya shi domin ba ciniki aka yi ba kawai y ace In an sayar masa zai bada ninkin biyar na yadda aka saye su, a su kadai sun dawo da dukiyar da Hakimi ya saye mu, kafin Sarki Muhammad farsi ya zo da tawagarsa don ziyarar Hakimi a halinsu na dawo daga tafiya ya biya kudin mu uku shi ma kuma ninkawar yayi kamar yadda waccan yayi,a duk da Hakimi ya so ya bada mu kyauta, amma Sarki Muhammad farsi ya ce ya kara ninka kudin. bature 26 Page 27 Page A zaman da nayi a cikin ahlinsa na so ace na ci gaba da zama da su, domin tun daga ranar da suka fahimci ya amshi addinin musulunci da gaske sai suka kasance da ni cikin kulawa a dan kwanaki da nayi mun saba sosai har sai da nayi kukan rabuwa da su. Yau shekara goma ke nan kin ji ta inda na san adalci da tausayi irin na Hakimi Abdullahi bin

Chapter 2 of 9