Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
Sharjas, mutumci da karamci kuma ga iyalansa". Koda sarauniya Hauletu ta ji wannan batu daga bakin Hindu sai ta yi shiru tana nazari a cikin ranta daga bisani ta ce "Akwai babban matsala a cikin gidan nan yake aminiyar sirrina, ki yi sani cewa dana na cikin barazana da rayuwarsa akowane lokaci har maina jin tsoron, tsoro yana kamani yana hanani sukuni a duk lokacin da na kasance cikin wannan yanayi nakan dage karanta (LAHAULA WALAKUWWATA ILLA BILLAHIL ALIYUL AZIM) domin danganta komai wajen ubangijin talikai, a kwana kusa zuciyata tana gaya min, dole na nemi taimako daga wasu manyan mutane da Sarki yake basu daraja, domin su kulamin da yaro na". Ta yi shiru a daidai wannan lokaci daga bisani ta dora "Babana yana cewa a duk halin da ka kasance ka da ka nemi taimakon kowa ka nemi taimakon Allah, amma kullum zuciya tana gaya min in nemi wani na bashi amanar dana Yarima Abbas da a yanzu ya kai kimanin shekaru a shirin da haihuwa tabbas zai zamo abokin gogaggayar Yarima Yazid na ganin yardarsu a wajen manyan kasa, a wannan lokacin, saboda makirci kina ganin yadda ba a bar Yarima Abbas ya saba da koda shugaban dakarun gidan nan ba, bare har ga ya saba ga Shugaban Dakarun kasa, bai taba kai ziyara Sansanin Dakaru ba, bare har a fara tunanin gwada shi a matsayin magajin Sarki, kamar yadda kika sani ni ma na sani, babu yadda za a yi a rashin adalcin da kirki irin na Abokan zamana Yarima Yazid ya zama sarki su kyale min dana a raye, dole sai sun kirkiri hanyar da za bature 13 Page Bahara, akwai dakaru a ko ina, sai dai duk tsaron bai hana birnin ya zama mahadar Kafurai wajen shirya tuggun yadda za su kawo karshen brnin da musulmai. A cikin kasuwa mafi daraja a kasar Bahara wacce ake mata lakabi SUKUL SA'A wasu gungun Kirista, shugabansu JARFIS na tafe yana duba kayan da aka kasa a kasuwa, yana duba wa wadanda suka yi masa yana siya tsawon lokaci yana cikin wannan lamari da dakaru a bayansa har suka isa wani babban shagon wani tsohon da ake kira Kirzalu, Kirzalu asalin dan kasar Bahara ne wadda jinin kasar ne shi wadda kuma ya rudu da dukiya saboda yana zaune ne domin ya zama idon Kafurai da duk wani abu dake faruwa, kuma a nan ne suke kitsa shirinsu na zalunci. Babban shago ne da shi. Dai-dai inda Jarfis ya iso sai ya fara kamar duba kaya da haka ya shige cikin shagon dakarunsa suka tsaitsaya a bakin shagon ko da shigarsa sai suka nufi wani guri da ba zaka taɓa tsammanin kofa bace amma Kirzalu yana dafa ta sai ya murza wani mabudi take kofar ta bude kawai sai suka shege ciki tare, koda shigar su ciki sai ga su a cikin wani kayataccen ɗaki mai dauke da kujerun zama da matasai a ɗaya cikin matasai wani hamshakin mutum ne zaune a gabansa akwai kayan marmari yana zaune yana dauka daya bayan daya yana tauna inibi, batare da ya daga kai ya kalli wadda yake shigowa ba. Har Jarfis ya nemi wajen zama zai zauna sai wannan hamshakin mutumin ya daka masa tsawa gami da dagowa ya dube shi "Waye kai da har zaka same ni a zaune ba tare da na yi maka izini ba ka nemi wajen zama, maza ta shi ko takobi na ta raba kanka da gangar jikinka" Jarfis ransa ya baci kamar yaki bin umarninsa amma dole tasa ya tsaya saboda a kowane lokaci ana koyar da su da su bi musulmi domin su samo lagon da za su kama su da sasari.' bature Data 28 Page su kashe shi shi ne ya sa a wannan lokacin ba ni da wani sukuni tun da Sarki ya fara ciwo yau gobe lafiya gabana ki faduwa". Hindu ta yi shiru cikin dan gajeren lokaci har sai da ta ji uwar dakin nata ta share hawayen ta ja shessheka sannan ta ce "Neman taimakon Hakimin Annur daidai ne a gare ki, domin shi mutum ne adali kuma mai matukar son gaskiya, idan Allah zai baka kariya ba da kansa zai zo ya baka kariya ba, amma shi ne zai zama sanadin haka, kin fi ni sani duk wani ilimi a wajen kin a samo shi, tsantsaini da tsoron fadawa halaka yake sawa kike wannan tunanin ai saka miki damuwar da kuma tunanin nemo wadda zai tsayawa danki ki dauka ubangiji ne yake haska miki, a da can ban da karfin gwiwa a game da Yarima Abbas amma wannan maganar take ta sa na fara jin karfin gwiwa, tabbas mu yi hanzari ka da mu yi kasa a gwiwa”. "Maganar ki gaskiya ce, wannan haka yake, to amma yake Hindu ya kike gani za mu yi wajen ganawa da Hakimi Abdullahi bin SHarjasllah, ki sani cewar matukar sun san wani shiri to za su gyara na su shirin, abin da nake tunani wani amintacce za ki nemo min wadda zai kai masa ziyara wadda shi da kansa Hakimi zai nemi yarima ni kuma zan gayawa yarima sakon da zai je masa da shi”. ** Lokacin da Jarumi Umar ya iso babban turakar mahaifinsa, a daidai lokacin Hakimi na nazari game da bakuwar Suhaila bin Ababakari da kuma tunanin sakon da Sarauniya Hauletu ta zo masa da shi na son haduwa da Yarima Abbas. A wannan lokacin ya yanke kai ziyara babban birnin domin ganawa ta musamman da Sarki a game da sabuwar masarautar da ake rigima a kai, sannan kuma zai yi amfani da wannan dama ya gana Yarima Abbas. da 29 | Page Ya dubi 'ya'yansa biyu da suke durkushea gabansa ya fara da cewa "Ya kai Ahmad ina son kasani za mu yi tafiya a safiyar yau zuwa birnin Bahara, kai za ka yi min rakiya zuwa can". Ya dubi Yarima Jarumi Umar da yake a tsorace daga furucin Hakimi, domin idan akwai abin da yaki jini ya ji ko gani mahaifinaa y acc zai yi tafiya ba tare da shi ba. "Ya mai martaba ka yi sani cewa zuciyata tana shiga rudani hankalina baya kwanciya a duk lokacin da na ji cewa za ka fita daga cikin wannan kauye, Ya mahaifina ka sani cewar makiyan da suke son ganin bayanka a kasar nan sun fi makiyan waje yawa, idan har za ka kai...." Hakimi ya dakatar da shi da cewa "Ka kwantar da hankalinka Jarumi Umar, ka sani cewa wani muhimmin aiki ne ya taso wadda kuma yana bukatar na motsa, kai ma kumana tura ka wani aiki na daban aikin suna bukatar a yi su a tare domin dole ne na je na gana da Sarki Muhammad farsi dangane da matsalar Salman da Hilal, dole kai ne zaka tafi izuwa kasar Shamnun domin ka gano mana halin da ake ciki" Ran Ahmad ya baci ya dubi Jarumi Umar ya cc "Akowane lokaci kana jin cewar kai kadai ne kariya ga ahalin gidan nan, idan har ba zan iya kare mahaifina ba, na tabbata ba zai yanke shawarar tafiya da ni ba". Jarumi Umar ya girgiza kai yace "Ba haka nake nufi ba dan uwana, babu mai kare wa face ubangijin musulunci, abin da nake tsoro da fargaba shi ne buguwar zuciya yayin da na tuno kuna halin tunkarar birnin da yake cushe da makiyanmu, masu son ganin bayan mahaifinmu da ahlinsa". Hakimi yayi murmushi ya dubi Ahmad y ace "Iya abin da dan uwanka ya fada shi ne kadai abin da yake gudu, amma ba ya nufin cewar kai ba zaka iya bani kariya ba." bature 30 Page Sannan ya dubi Yarima Jarumi Umar ya ce "Aikin dake gabanka ya fi wanda ke gaban mu hadari, dole sai kun yi kaffa kaffa domin na san za a zuba dakarun da zasu hana ku ganawa da Sarki Hilal, domin ba bukatarsu a yi sasanci ba bukatarsu ayi tashin hankali a tsakanin kasashen musulmai, amma a zarar kayi tozali da Sarki Hilal ka yi masa albishir da cewa na tafi zuwa babban Birni don tabbatar da cewar shin Sarki ya san da abin da yake faruwa a kasar Shamnun ko kuma bai sani ba, wannan kalamin shi ne kadai zai sa Sarki Hilalya barku ku dawo gida lafiya, kuma idan yana da hankali shi zai sa a barwa duniyar musulunci zabar Sarki mafi daraja a tsakaninsu shi da dan uwansa Salman, amma matukar basu gan ku kun gana ba, to ku yi kokari tsirar da rayuwarku domin sun shirya ayi duk abin da za a yi, ka ga ke nan za su fara da kai”. Jarumi Jarumi Umar ya jinjina kai ya kuma fuskanci lallai akwai babban aiki a gabansu,don haka ya jinjina kai ya ce “Insha Allahu komai zai tafi kamar yadda ka tsara Baba". Hakimiya jinjina kai gami da cewa "Masha Allahu, yanzu ka je ka yi shiri tun da har yanzu muna cikin duku-dukun safiya, don haka idan kun tafi yanzu kafin la'asar za ku isa birnin Shamnun, kuma lokacin mun fara neman hanyar dawowa daga Birni, duk ku tashi ku je ku yi shiri". Ahmad da Jarumi Umar suka fito daga babbar turakar mahaifinsu cikin fushi da Ahmad yake ciki da dan uwansa domin shi sam gani yake kanin nasa ya raina masa tunani jarumtakarsa gani yake shi ke sama da shi”. 9 Abin da Jarumi Jarumi Umar ya lura da shi ya dubi dan uwan nasa ya ce "Amanar mahaifina da kuma kai kanka tana hannunka, ka da ka yi wasarere da rayuwarku duniya ta yi mana kunci" Kalamansa suka sanyayyar da gwiwar Ahmad a dai-dai lokacin da Kubrat da su GImbiya Suhaila bin Ababakari suka bature B 31 Page tunkaro in da suke Jarumi Jarumi Umar ya ci gaba da cewa "Ya kake tsammanin idan wani abu ya same Baba, da kai kana tunanin tsohuwar nan tamu mai tsananin kaunarmu zata iya dauka, a kodayaushe ka tuna da ita ka kuma tuna da al'ummar da suka jingina da mahaifinmu" Jarumi Ahmad ya ji dadi sosai har ya jawo Jarumi Umar ya rungume shi suna masu murmushi so da kauna, Ahmad y ace "Ka ji abin da Baba ya ce tafiyarka tafi ta mu hadari da taka tsantsan, ya kamata a ce ka kula kuma ka dawo cikin koshin lafiya domin rashinka kamar ragewa masarautar annur karsashi ne, rayuwar mutanen Annur sun dogara da Allah da kuma kai, kai suke yiwa kallon mahaifinmu, don haka ka kula dau uwana". Dukkaninsu suna murmushi na jin dadi da kuma wata karyewar zuciya har ta sa suka zubar da kwalla,dai dai lokacin Kubrat ta karaso da ita da Suhaila bin Ababakari. Kowa yana saurin goge kwallar don kar mahaifiyarsu ta fuskanci kuka sukeyi, kallo daya tayi musu ta fahimci damuwa a tattare da su, da yake ta riga da ta san halin da ake ciki tun a daren jiya ta yi nata kukan, sai ta share ta kasance don karfafa musu zuciya. Jarumi Umar ya dubi Gimbiya Suhaila bin Ababakarit ta dukar da kai "Barka da safiya”. Ya yi mata murmushi cikin kallon cikin idonta ya ce "Dafatan kin tashi lafiya”. "Ku yi kokari ku shirya domin ku isa a kan lokaci,kamar yadda mai martaba ya fada, ina muku fatan alkairi yarana Allah na tare da ku❞ Duk su biyun suka rungume ta "Insha Allahu" Su ka furta tsoron da take ji shi ne ta fara kuka yasa ta sake su ta dubi Suhaila bin Ababakari “Zo mu je wajen maimartaba yana jiran ki”. bature 32 Page Gimbiya Suhaila bin Ababakari cikin jin nauyi ta ce "Idan babu damuwa zan gana da Jarumi Jarumi Umar na dakika daya kacal Jarumi Jarumi Umar ya kalle ta ya kalli mahaifiyarsa Kubrat ya kuma dubi dan uwansa, sannan ya dawo da kansa gare ta, yayi shiru gami da cewa "Mu je" Ya yi gaba ita ma ta dubi Kubrat gami da murmushi sannan ta bi bayansa a nutse sai da ya bada tazara mai yawa sannan ya tsaya, ya tsaya dai-dai inda abokansa suke zaune don haka suka tsira masa ido sanin halinsu yasa ya fara kame kame ya dube ta ya ce "Ko zaki bani dan lokaci zan Jarumi Umarci abokai na don su je su yi shiri domin tafiya Shamnun” Ba tare da ta ce komai ba ta jinjina kai alamar ta fahimci uzurinsa". Ta tsaya ta zuba wa bayansa idanu yana nufi wajensu kafin yana isa suka amsa masa sallamar da yayi musu cikin zolaya yakalle su daya bayan daya ganin idanuwansu suna kan Gimbiya Suhaila bin Ababakari sai ya juya ya dube ta itama idanuwanta a kansu yake tana mai mamakin kallon da suke yi mata. Ya dawo da dubansa gare su y ace “Wai me ye haka kukeyi, komai wane abu yana da gurbi kar ko dora giwa a kan dantsako". Dawan ne mutum mafi maida hankali a cikinsu don haka shi ko dariya ma bai fiya yi ba, babban burin Dawan ya ga ana batun tafiya don aikin Allah don haka shi ya fara dakatar da su da cewa "Me ke tafe da kai?" Nan ne ya daina harararsu ya dubi Dawan y ace "Mu na da babban aiki a gabanmu, ku je ku shirya yanzu za mu tashi zuwa Shamnun don fara ni ma zan gama da gimbiya ne na tafi nawa shirin watakilatana da sako ne yasa take son mu yi Magana" Mu'az ya ce "Kowane lokaci a shirye muke ka je ka gama muna jiranka a wajen dawakai" bature bature B 33 | Page Kubait kuma ya ce "A gaida gimbya" Bai saurare shi ba ya juya ya koma ga Gimbiya Suhaila bin Ababakari ya tsaya tana kallonsa sai da ya dan tsaya ya ga ta ki Magana sannan y ace "Ina sauraren ki❞ Ta gyara murya ta ce "Dama na so na sanar da kai ne inda yayana ya sanar da ni yana boye ko zaka taimaka ka ceto shi daga zalunci dan uwansa?” Ta fada cikin rudu da sunkui da kai kasa ya dan yi shiru ya dago ya kalle ta "Ki kwantar da hankalinki Gimbiya, babu wani abu da zai sami dan uwanki Salma, kuma da yaddar Allah Salman zai zama Sarki in dai shi ne zababben mahaifinku, wannan alkawarin Allah ne, domin na tabbata matukar mahaifina ya tattauna da Sarki Muhammad farsi, ni kuma isa birnin ku, na kuma kai sako na, babu wani taurin zuciya da zai saka Dan uwanki ya yiwa Sarki gardama domin ya san ba zai taba yin nasara ba, don haka ki kwantar da hankalin ki Gimbiya". Ta yi wani murmushi jin dadi ta ce "Insha Allah, kuma na gode bisa taimakon da ka yi min a jiya na kara gode maka bisa wannan taimakon da z aka kara yi min, ina maka fatan dawowa cikin koshin lafiya". Shi ma ya dan yi guntun murmushi gami da cewa "Amin, y ace za mu hau hanya Allah sa mu dawo da mu same ku lafiya”. Daga gama wannan maganar sai ya juya ya bi hanyar bangaren Maza na gida ya shiga turakarsa duk wani abin bukatarsa ya dauko ya fito, bai tsaya ko in aba sai wajen abokansa, da sun yi shiri tafiya. A dai-dai lokacin da suka haye dawakai sai suka rufarwa hanya babu ji babu gani. A daidai wannan Lokacin Shamsu bin Aujarbn Abdallahi ya na hangensa daga can saman gidansa koda ya bature (. > 34 Page ga sun fita sai yayi sauri ya sakko ya nufi cikin gidan dan sanin abin da yake faruwa. A lokacin da Sarki Abdullahi bin Sharjas ya gama kintsawa sun fito tare da matarsa da kuma Gimbiya Suhaila bin Ababakari da Jarumi Ahmad. A hankali ya matsa gare shi jiki a sanyaye. “Dan uwana naga Da na Jarumi Umar tare da abokan gumurzunsa sun sukwani dawakai, kai kuma ka fito cikin shiri shin akwai wani abu ne da ba mu sani ba”. Hakimi yayi murmushi ya ce "Kwantar da hankalinka yanzu nake shiri na shigo Bangarenka na zayyana maka abin da ke faruwa, sai kuma g aka, Amanar mutane na iyalina, da gari na na hannunka, domin wata tafiya ce wacce ba a kimtsa mata ba ta same mu, dole daga yanzu za mu wuce Bahara, zan gana da Sarki akan matsalar gimbiya Suhaila bin Ababakari, sannan Jarumi Umar da ka gani ya fita shi ma ya tafi Shamnun ne domin magance matsalar da ikon Allah zuwa yammaci za mu dawo" Koda Shamsu bin Aujarya ji wannan batu sai yayi shiru da ya fuskanci shirun nasa zai kawo wani tunani daga dan uwansa sai ya ce "To Allah ya dawo da ku lafiya, kuma za mu ci gaba da gudanar da tafiyar komai har Allah ya dawo da kai lafiya". ya Daga nan ya bi su da kallo suka dunguma kusan dakaru ashirin ne ke musu rakiya. Bai gushe ba yana kallonsu har sai da suka bace masa da gani sannan yayi sauri ya nufi gida, ya sa a kira wo masa babban yaron sa Alban koda zuwa Alban sai dube shi ya ce "Maza ka je ka tashi ka je ka isar da dan aikin Waziri cewar lallai dan uwana ya yi abin da yake zargi wato ya nufi Bahara, shi kuma Jarumi Umar ya nufi kasar SHamnun, ka yi maza ka da ka bata lokaci". Alban ya fita da hanzarinsa don kai sakon maigidansa abin sirrinsa gatan sa kuma. bature B 35 Page Shamsudden wani mashahurin tsoho ne wadda yake adawa da mulkin dan uwansa, bai yi amana da Abdullahi bin Sharjas ba domin gani yake shi ne mafi cancanta da sarautar Annur, don haka kullum cikin bakin ciki da zagon kasa yake yiwa Mulkin Abdullahi bin Sharjas tsawon shekaru bai taba samun nasara ba, Abdullahi bin Sharjas ya sha kama shi da hada baki da wasu maha'inta kasa amma yana masa afuwa, saboda son a zauna lafiya domin abin da Abdullahi bin Sharjas yake fadi kullum shi ne dukkaninsu sun zama dattijai lokacinsu kalilan ne a duniya, baya son dan uwansa ya mutu a matsayin mai ha’intar kasa, kullum yana gyara masa kurakurensa, amma ya gaza fahimta, don haka duk lokacin da ake so a cimma wata manufa a cikin kauyen Annur to da shi ake hada baki, don a jiya da waziri ya bar kauyen sai ya sa dan aike zuwa gareshi ya sanar da shi cewar yana bukatar jin duk wani motsi da ya ga dan uwansa yayi. Tun da Waziri Ja'afar ya bar Kauyen Annur bai tsaya ko ina ba sai gidansa a babban birni saboda ya san cewar za a samu wannan babbar matsalar, don haka washe gari da sassafe ya zo fada don ya yi tsarin da zai warware kansa daga cikin matsalar birnin Shamnun kafin a samu wata matsala Ana zaune a fada kowa ya iso isowa Sarki Muhammad farsi kawai ake yi. Wasu da dama a fadar sukan tattauna batutuwan da suka zo wa da Sarki shi na yadda za su sanar da shi, wasu kuma na kokarin gyara Kujerar Sarki wasu na gyatta tsayuwarsu, malamai wasu daga cikin Hakimai da aka gayyata, Sarkin Kasuwa, Sarkin gida, da na fada Shugaban Dakarun waje da na Gida duk sun hallara suna jiran Sarki. Kwatsam sai ga Busar Sarewa alamar Sarki ya taho, ‘ya'yansa biyu ne suka fara shigowa cikin takama da nuna izzar mulki wato Yazid da Abbas. A nan take kowa ya mike a fadar aka bature ミ 36 Page fara dukar da kai kasa ana gaida su. Sai da suka nemi wajen zama sannan ne kowa ya zauna kuma waje yayi shiru. Jim kadai sai ga Sarki nan shi ma nan aka kara tashi yana tafe wasu dakaru biyu suna biye da shi kansa a kasa yake har ya isa inda kujerar mulki take wadan an dakaru suka koma hagu da dama suka tsaya a bayan kujera sai ya dago kai ya dubi duk inda mutane suke sannan ya daga hannu ya fara addu'a domin fara zaman majalisa, a ka yi salati ga manzon rahma, aka yi kirari ga ubangijin talikai aka nemi taimakonsa da goyan bayansa a game da daukaka Kalmarsa. Sannan aka shafa da fatiha. A sannan ne ya nemi waje ya zauna. To fa babu mai zama a wannan wajen har a tashi taro a haka kowa zai tsaya. Mai rubutun kundin mulki da kuma gabatar da abin da za a fara jira yake Sarki ya daga masa hannu ya fara domin dole shi ne farko adaidai lokacin Sarki ya daga hannunsa sai wannan mutumin da ake cewa da shi Zarkifilu ya fito gaban Sarki da katon kundinsa a hannu ya fara da cewa "Allah ya ja zamani Sarki ya karawa Sarki lafiya kamar kullum da kodayaushe, batu daga Sarki Jarumun Jakub cewa a karo na biyu yana bukatar birnin nasa wadda aka kwace masa Birnin Hilayan, sanan yana bukatar diya ta rayuwakan da aka salwantar a birnin yayin gwabza yaki, ya kara tabbatarwa ba zai kara turo sako na hudu ba, kaifin takobi ne zai ci gaba da Magana. A bagaren Kauyen Dire Hakimi Suleman yayi batu a game da bullowar Hangalawa tsille tsille suna zuwa babbar kasuwar Kudu suna tare mutane suna kuma zuwa suna amsar haraji, lallai yana mai kira da babbar masarauta a dauki lamarin da gaske domin sun fara dawowa. A ziyarar da Waziri ya kai kasuwa jiya, ya ci karo da sabbin mutane wadda ya sa an yi bincike a kansu ya gano cewar lallai wasu bature 37 Page mutane ne da suke son haddasa husuma domin sun dauko 'yar marigayi Sarki Ababakari zuwa wannan birnin amma cikin ikon Allah Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya kwace ta daga hannunsu. yau". Wannan su ne bakin labarin da za mu fito da su a zauren mu Fada ta kara yin shiru bayan da Zirkifilu ya kammala kawo batutuwa kamar kullum. Sarki ya gyara zamansa kai tsaye idanuwansa ya dago ya dubi kafatannin ‘yan zaman fada kafın ya dora ya ce "Sako zuwa ga Kafiri Jarman Jakub a gaya masa cewar ba mu da lokacin mai kori, ba kuma da wata Magana da ta rage a tsakanin mu, idan har ya tabbatar Takobin ce kadai za ta yi Magana, to na mu kodayaushe cikin washi suke. Game da Hakimi Suleman lallai a tashi dakaru na gaske a je Kauyen a yi bincike na gaske. Kafin Sarki ya kara Magana ta gaba, sai ga Shugaban Fada ya shigo tun daga nesa ya duka yayi gaisuwa "Akwai sako na musamman ya Sarki mai daraja”. Tun da Waziri ya ga shigowar Sarkin Fada sai hankalinsa ya ta shi, ya shiga zare idanu amma tun da dai yay i aikin hankali tun a jiya ya shigar da batun kafurai a kasuwa karyar da zai yi za a iya gasgata ta, maganar Salman ce wajen binciko lamari wannan kuma ya san shi zai jagoranci zuwa birnin kuma ko ma waye a cikin fadar to maganarsa yake ji. Har Sarki Fada ya je kusa da Sarki yayi masa Magana da ba kowa ne ya ji ba. Ya bawa Sarkin Fada Jarumi Umarni ya fice "Batu a kan Yar Sarki Ababakari ga Hakimi Abdullahi bin Sharjas nan ya iso domin yi mana cikakken bayani". Kowa da ke wajen sai da gabansa ya fadi domin koda wasa aka furta sunan Abdullahi bin Sharjas sai mutane sun shiga hankalinsu sun fara tunanin wata badakalar ta su za ta iya ta shi, bature : | Page saboda tsoronsa da kuma, Sarki na rufe baki Abdullahi bin Sharjas ya bayyana cikin sallama bangaren ya tsaya cak yana kallon kowa cikin fara'a. "Bangaren Masarauta, Malamai, Hakimai 'yan uwana dakatai Wazirin ina muku sallama ta addini musulunci". Kowa ya amsa masa sannan ya nemi wajen tsayuwa ya tsaya a sahon Hakimai. Bayan yin shiru na dan lokaci sai Sarki yayi gyara murya ya ce "Abdullahi bin Sharjas, sako ya zo daga Wazirin Bahara cewa ka kubutar da 'yar Sarki Ababakari daga hannun kafura, z aka iya fitowa ka yi mana Karin bayani”. Abdullahi bin Sharjas ya fito daga inda yake tsaye ya tsaya y ace "Tabbas da na Jarumi Umar shi ne ya tare su ya kuma amso ta ita da wanda yake yi mata hidima, sannan bayan haka Waziri ya zo har Kauye nemanta da yunkurin a bashi ita. Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta sanar da mu cewar Dan Sarki Salman ya saye duk wani Dakare, da duk wani dan majalisar Sarki shi da mahaifiyarsa, na lalllai shi ne zai gaji Sarautar mahaifinsa, a yanzu haka ma ranar rantsuwa kadai ake jira domin shi yake gudanar da komai, sannan ta ce ya bazama nemo dan uwansa Hilal. Shi kuma Yarima Hilal shi ne yay i sako ga 'yar uwarsa cewar ta gudo daga birnin a kokarinta na guduwa suka kama ta kuma suka tilastata akan sai ta kai su ga inda Yarima yake, dakarun da suke tare da ita kafurai ne, kuma sun nufi, Birnin Bahara da ita, wannan dalilin yasa na ce ya dace na zo kada da kafa domin jin ba'asi ko sakacin da Sarki ya jima yana yi ya fara taba martabar Sarautar Bahara" x Wata tsawa Shugaban Dakaru da Waziri suka dakawa Abdullahi bin Sharjas, har da zare takubba. Sarki ya daga musu hannu alamun su dakata cikin tsawa. Shi kuwa ko gezau bai yi ba bature B 38 39 Page domin bait aba zuwa fada bai furta Kalmar sakacin nan ba, ba kuma su fasa kawo masa bar aba, sarki bai fasa dakatar da su ba "Muna bukatar ji daga gare ku, sannan kada ka manta Waziri Ja'far sa'a daya da kawo Suhaila bin Ababakari wajena ya biyo sahunta, shin me ya sani dangane da zuwanta, dole sai an sarewa maciji kai kafin a samu nutsuwa" Koda Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya zo nan a batunsa sai yayi shiru ya kuma koma ya tsaya jin ta bakin Sarki Muhammad farsi. Lokacin Sarki Muhammad farsi yayi dakika biyu yana nazari kafin ya ce wani abu, a wannan lokaci shi ma Waziri Ja'afar yana na shi nazarin da ya kwana yana maimaita amsar da zata fitar da shi daga zargi, don haka tun da dan aikin Shamsu bin Aujarya zo masa yayi tashi dan aiki zuwa masarautar Shamnun abu na farko ya gargadi 'yan majalisar masu zabar Sarki saboda su ne wadanda aka tilasta su, aka kuma cika musu aljihu da sulalla, sannan aka yi musu alkawarin ci gaba da zama a majalisa, batare da yi musu wani sharri da kagen da za a kore su daga kan karagarsu ba. A dai-dai wannan lokacin Sarki ya katse shi yana mai cewa "Ko Waziri ja'afar yana da wani sani dangane da Gimbiya Suhaila bin Ababakari?" Waziri Ja'afar ya amsa "Ina

Chapter 3 of 9