Shamnun na sani cewa akwai dana
Jarumi Umar da ya je domin ya gano min abin da yake faruwa don
tabbatar da gaskiya, ku yi aiki na gaskiya a birnin don wanzar da
zaman lafiya, sannan ka rike Jarumi Umar matsayin da kake son ka
rike ni domin shi ne abin kallo a yanzu a kabilar mu, mu tamu ta kare
muna kan gaba da ta kowacce fuska da makiya ta kowane fuska
neman rayuwar mu suke yi, shekaru, a sun saka mu a gaba a kowane
lokaci mutuwa na iya riskarmu, daga karshe ina mai sanar da kai ka
rike gaskiya da amana, ka kai kukanka wajen ubangijin da ya halicce
ka, duk rintsi duk tsanani, tabbas za kasamu babban rabo, zan wuce
ina maka fatan Nasara a inda zaka je domin sassancin".
"Nagode kwarai, na ji dadin maganarka, Allah ya daukaka
musulunci da kasarmu baki daya".
"Ameen, Allah ya dawo da kai lafiya, kuma ka bi a sannu, domin duk takunka daya bayansa makiyinka ne ke saka kafa".
Daga nan kowa ya juya yana mai jin dadin tattaunawar da
suka yi, Abbas ya haye dokinsa, shi ma Abdullahi bin Sharjas ya haye nashi dokins suka tasarwa hanya shi kuwa dan munafukin Waziri Ja'afar sai da ya tabbatar kowa ya baci da gani sannan ya zo ya hau nashi dokin ya sukwane shi bashi ya tsaya ba sai gidan Waziri Ja'afar, ai kuwa Waziri yayi matukar jin dadin hirar da ta wanzu a a tsakanin Yarima da Abdullahi bin Sharjas, ya zo kan gabar da zai ruru wutar gaba a tsakanin yarima da Sarki, ya kuma hada wutar gaba da Abdullahi bin Sharjas har ya ja a kashe Abdullahi bin Sharjas domin alaka da yayan Sarki ita hanya mafi sauki da zaka hallaka makiyinka. Don haka ya ci ka da farin ciki yayi kuma tura
bature
54 Page
wata Baiwarsa zuwa cikin gidan Sarki don ta kai labaringa Siyama
domin itama ta kwana tana farin ciki
Washe gari da safe gidan Sarautar Shamnun ta cika ta batse domin an yi sanarwa an kama daya daga cikin dan leken asiri za kuma a gurfanar da shi a rataye shi kamar yadda ake yiwa duk wani mai laifin cin amanar kasa. Saboda haka tun sassafe mutane suke
zuwa wannan filin.
Mu'az, Dawan, Kubait Saklahul dukkaninsu suna cikin wannan babban fili domin saka ido su ga waye maciyi amanar kasa, duk da zuciyarsa na dukan uku uku idan sun tuna cewar Jarumi Jarumi Umar ne da aka kama suka yank masa wannan hukuncin sai hankalunsu ya tashi har su rasa abin da za su yi, sun saka a ransa matukar Jarumi Jarumi Umar ne ba za su bari hakan ta faru ba, sai
sun yamutsa wannan waje yadda sai dai su gaba daya a kama su a
kashe su gabadaya.
Wajen awa guda ke nan suna tsaye suna jiran ganin abin da suke zargi, sai ga mahaifiyar Sarki ta fito a madadin Sarki wato Sarauniya Ruma, Waziri na beye da ita a baya da zabga zabgan karatan dakaru domin basu kariya, an tanadi wajen zamanta mai kawatarwa. A inda take zaune akwai raga raga yadda babu wani
mahaluki da zai iya cutar da ita.
Bata jima da zama ba aka fito da Jarumi Umar fuskarsa a rufe kuma an daddaure shi da sasari na bakin karfe ana tunkudo shi
dakaru ne suka baibaye shi.
**
A tsakiyar fili ga wajen rataya nan a bisa wani babban teburi
wadda sai mutane sun daga kawunansu sannan za su iya hango mutum an tsara wannan wajen tun shekaru dari uku da suka shude,
tun lokacin da kafurai ke mulkin kasar kafin kasar ta dawo hannun
musulmai.
bature
55 Page
Lokacin da aka gabatar da shi wajen ya rude har wasu da aka
biya kudade aka dauki nauyinsu suka fara jefansa da takalmansa
wasu da basu san hakikanin meke faruwa ba su ma suka dauki
duwatsu da wasu abubuwan kasazanta suna jefansu da shi
Tun kafin a cire masa abin fuskar da takalminsa da kafadarsa
suka shaida abokinsu ne kuma shugabansu, sai suka fara shiga
damuwa domin basu san hanyar da za su bi don yaki da wadanan
zaratan dakarun ba, nasihar Abdullahi bin Sharjas a kullum
kodayaushe, ka da ka yaki dan uwanka musulmi da takobi, ka yake
shi da zuciyarka, da kuma harshenka, iyaka iyawarka, idan kaga zai
cutar da kai ka guje shi. Babu abin da Hakimi ya tsana irin yakar
juna.
Tabbas suka zare makami sai an yi mutuwar kasko kafin su
kwaci Jarumi Jarumi Umar, to amma tunda har Jarumi Umar ya gaza
aiwatar da komai, dole su yi hakuri da shi dominn yin wani abu a
wannan wajen zasu tsinci kansu cikin rashin madafa, tabbas suka
kasha rayukan musulmi fushi zai tabbata ga Hakimi kuma za su mutu
a matsayin makiya musulunci.
Babu abin da ya fi musu a nan face addu'ar fadin
"LAHAULAWALA KUWWATA ILLA BILLAHILA ALIYUL
AZEEM.
Wasu majiya karfi suka tura Jarumi Umar izuwa wajen
igiyar, batare da sun bayyana fuskarsa ba suka saka masa igiyar
sannan suka tamke ta, suka koma da baya suna jiran Jarumi Umarni
Sarauniya Ruma. Duk abin da ake yi idonta na kai, tayi shiru tana
kallo bata bada damar a sake shi ba har sai da waziri ya ce "Ranki ya
dade muna kara bata lokaci".
Sannan ta dawo hayyacinta ta mike ta fuskanci jama'a
"Wannan da kuke gani, dan leken asiri ne, masu son haddasawa
kasarmu rikici, masu kaunar ganin jininmu na salwanta a banza, mun
bature
ค
kama shi ne da laifin kawo maganar karya da gaskiya akan abin da
ba zai haifar mana darashin zaman lafiya ba", saboda haka zamy
yanke masa hukunci na kisa bisa rataya".
Ta yi shiru mutanen gari suna nuna goyan bayansu da
amanna da abin da ta fadi, kai tsaye kuma sai ta daga hannunta sama
wadda ta ta sauke za a janye turbin da yake kai ya zama igiyar ta
shake wuyansa harya sheka barzaho cikin dakika daya".
Abokansa suka dora hannu a ka suka ci gaba da addu'a
neman dauki ubangiji a daidai lokacin da Sarauniya Ruma ta sauke
hannunta kasa, alamar Jarumi Umarni da cewar a aiwatar.
Jarumi Umar addu'o'I yake cikin zuciyarsa wadanda
koyowar Annabin Allah ce idan mutum na halin gamuwa da
azalumai da
A'AUZUBIKALIMATILLAHILTAMMAT
masharranta,
MINSHARRI
MAKALAKA
Aka ture wannan turmin Sadauki Jarumi Umar ya fara wutsil
wutsil bai fasa addu'a du'a'a a ba cikin zuciyarsa, jin an ture turmin
sai ya fara kalimatusshahada.
A lokacin da karfin wutsul-wutsul din ya fara ragowa,
idanuwansa, sun kunburo ya fara sakin wani kakari na mutuwa, gaba
daya idanuwansa sun saki, mutuwa na shawagi a ruhinsa, suma ya
gabato a gare shi. Kulli nafsin za'ikatulmaut.
Mutane da ke tsaitsaye suna dubansa wasu cikin tausayi wasu
cikin tsana abokan tafiyarsa a dai-dai lokacin Mu'az ya kasa jure wa
yayi kukan kura ya kwalla kabbar, dukkanin su uku suka zare
takubbansu suka dauki kan Jarumi Umar. Dakaru suka sha kanšu
suka tare su ana kokari fara dauki ba dadi. Wata kibibiya kamar
walkiya ta ta wuce ta saman kawunan mutane daidai igiyar da aka
daure Jarumi Umar ta shigar burgu ta yanke ta, kai kace takobi aka
saka aka yanke igiyar, Jarumi Umar ya fadi kasa ko shurawa baya yi.
bature
56 Page
57 Page
Sarauniya Ruma da Waziri suka mike da kallo cikin kaduwa
da tunanin waye ya zo ya katse wannan al'amari.
Idanuwansu akan Yarima Abbas yana tsaye da kwari a
hannunsa idanuwansa na kallon gangar jikin Jarumi Umar.
Koda ganin Yarima Abbas sai kowa dake wajen ya rissina kai
kasa alamar girmamawa, hatta Waziri da Sarauniya Ruma, sai da
suka sunkuyar da kai kasa, cikinsu ya duri ruwa.
A Wannan lokacin Mu'az da su Dawan suka yi sauri suka
ratsa mutane suka isa kan gawar Jarumi Umar suna masu ihu da
kururuwa.
Dawan ya fada kansa ya dago shi ya cire masa bakar hular
rufe fuska da take sanye akanshi, duk ya hada majina idanuwansa
sun yi tulu-tulu kamar zai zazzago.
Dawan ya saka hannunsa kan jijiyar wuyansa. Saklahu ya
saka a hannunsa, duk su biyu suka fara wata irin fara'a kamar wasu
ciwon hauka, "Yana raye yana raye yana raye, haka suka dinga
maimaita. Muaz ma hannunsa ya saka ya ji, yana tabbatarwa ya saba
shi, a kawo agaji yana daye yana raye.
Waziri ya karaso ga Yarima. Yarima bai dube shi ba,
idanuwansa na kan Jarumi Umar da ake kokarin ceton rayuwarsa.
"Yarima...."
دو
Yarima ya katse shi da cewa “Ka je ka yi kokarin ceton
rayuwar Jarumi Umar kafin ka zo mu yi Magana duk wani likitan da
ka san kwararre ne ka neme shi domin ku ceci rayuwarsa.
**
"Ki ta shi❞
Wata murya ta tashe ta, a cikin baccin da take cikin dare, ko
da ta mike zaune sai ta ga dakin babu kowa,tabbas kuma ta ji an
tashe wani haske ta hango daga bakin kofa tana tsayar da hankalina
wajen ta hango wata kyakkyawarmace sanye da fararin kaya sannan
bature
•
58 | Page
haske har daukar ido yake, ta mike tsaye budurwa ta ce "Ki zo in
sada ki da dan uwanki Salman".
Ta fada da daddar muryarta, kafin ta yi mata tambayar
budurwa ta yi gaba ita kuma sai ta ji tana mai bin bayanta har suka
fita daga cikin daki ta fito waje babu kowa a farfajiyar gidan Hakimi
Abdullahi bin Sharjas, abin da ya bata mamaki ke nan.
Babu masu tsaron dare bare na safe babu kowa sai kukan
tsuntsaye ta so ta gaza bin bayan budurwa amma tazarada ta bata ya
sa takeson ta ji me ke tafe da ita. Don haka ta kara sauri dan ta
cimma ta.
Koda ta ci gaba da binta a baya har suka yi nisa can nesa
kadan sai wannan budurwa ta kyakyace da dariyar mugunta. Jin
wannan dariya ya sa Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta dago da
kanta cikin mamaki sai ta ga wajen ya cika da mutane sannan ga
wani mutum a gaban rundunar dakaru sama da dubu sun sashi a gaba
daure yake da sassarin bakin karfe hannu da kafa, fuskarsa a rufe ba
a gane ko waye shi.
Tana tsaye ta zuba ido gabanta yana faduwa sai wani
mahayin doki mai suffar kafurci ya bayyana a bisa dokinsa yana
zagaye wannan mutum da yake a daure, har sai da ya zagaya shi sau
uku ana hudu ne ya tsaya ya saka kaifin takobin nasa ya cire wannan
hular da ta rufe wa mutumin fuska sai ga Jarumi Jarumi Umar ya
bayyana suka yi kallo kallo da shi idanuwansa na zubda hawaye.
Ta tawo da gudun don ta zo inda yake amma kafin ta zo
wannan Katon Sadauki ya saka takobinsa ya cirewa Jarumi Umar
kai, jinin yayi tsartuwa har ya bata mata fuska. Ta kwala wała
mahaukaciyar kara mai amsa kuwa da amon. Tana ji tana kallo
gangar jikinsa ta sulale kasa, haka kansa yayi katantanwa a gabanta,
da ta durkushe a kasa. Kafafuwanta sun kasa daukarta.
bature
59 Page
"Jarumi Umar Jarumi Umar! Jarumi Umar!! Ta kwala kiran
sunansa sau uku. Firgigit ta farka daga bacci mai nauyi ne ya dauke
Gimbiya Suhaila bin Ababakari bayan da ta idar da sallar asuba, ta yi
sa'ar gaske da ta samu wannan bacci tsawon lokaci da ta dauka bata
samu kanta a wannan halin ba, don haka babu ma wadda ya tashe ta
ko don ta je ta gana da Abdullahi bin Sharjas domin jiya ya dawo a
ciki dare.
Ta farka a razane a tunaninta abin da ya faru yana nan a zahiri
don hakada gudu ta fita, Kuyangarta Rumaisa, ta riko hannunta,
ammaina ta kwace tana za su kashe shi. Tana fita sararin tsakar gidan
taga ana ta aiki irin wanda aka saba yau da gobe batare da wani
tashin hankali ba. Addu'a ta fara yi tana sauke numfashi kasa kasa.
Kubrat dake bada Jarumi Umarni ta lura da ita. Gimbiya Suhaila bin
Ababakari tana ci gaba da addu'a har ta samu nutsuwa acikin ranta
ta tabbatar da ba gaskiya bane abin da ya faru da ita mafarki take yi.
Akwai wata budurwa da bata wuce sa'ar Suhaila bin
Ababakari ba, ana mata lakabi da Hamdiya, Hamdiya wato
kyakkyawar budurwa ce da ta zama ‘yar riko a hannun Kubra, tun
tana da kuruciyarta, yar aminin Abdullahi bin Sharjas ce da ya rasu
tun tana karamar yariya, a wata tafiya da suka yi, da shi da matarsa
aka farmusu aka kashe su akan hanyarsu ta zuwa Birnin Bahara, don
kasuwanci.
5
-
Tun daga wannan lokacin Hamdiya take rike a hannun
Hakimi Abdullahi bin Sharjas ta zama tamkar ya a wajensa,
Hamdiya ta kasance mai matukar kyau da biyayya ga Uwar rikonta
Kubra, kuma ta kamu da matsanancin son Jarumi Umar tun tana
karama, tana yawan nunawa Jarumi Umar kaunarsa da take yi amma
yana nuna mata bai fahimci indata dos aba, saboda shi kwatakwata
babu ita a cikin zuciyarsa a matsayin ya so ta da aure amma yana
bature
60 Page
matukar sonta yana tausayinta a matsayin da yake daukarta na
kanwarsa marainiya.
=
Hamdiya ta fahimci Jarumi Umar sosai sai dai soyayyarsa
kullum karuwa take a cikin zuciyarta, duk wacce mace da ta gani ta
fita kyau da tsari sai ta ji kishin ya kamata domin tana jin tsoro ace
Jarumi Umar ya kama da son wata,a ganinta gwanda a ce da ita da
Jarumi Umar sun tsufa a haka basu yi aure ba da dai ta gawata mace
ta auri Jarumi Umar, saboda haka tun da ta lura da Gimbiya Suhaila
bin Ababakari, ta ga ba tsaranta bace a fagen kyau, sai ta dauke ta
tamkar wata kishiyarta, duk da cewar bata ga wata alama da ta nuna
suna soyayya da Jarumi Umar ba, amma haka nan take jin haushinta
take ji kamar ta shake ta ta mutu.
Saboda haka Hamdiya a daidai lokacin da Gimbiya Suhaila
bin Ababakarita fito daga dakin da aka sauke su, ita ma tana zaune ta
hango fitowarta don haka da suka koma daki Uwar Gida Kubra ta bi
bayanta sai ita ma ta tashi ta bi su a baya.
Rumaisa ta kasance tana tambayar Gimbiya Suhaila bin
Ababakari abin daya faru, ta fara koro mata bayani “Mafarki nayi,
wai an kashe Jarumi Umar.....
Daidai lokacin da ta furta an kashe Jarumi Umar Kubra ta
karaso dakin ta kuma wannan Kalmar.
Jikin uwar gida Kubra yayi sanyi ta dubi Suhaila bin
Ababakari "Me kika ce?"
Suhaila bin Ababakari da Rumaisa suka dago da kai, da Sauri
Suhaila bin Ababakari ta kara sa inda take. "Ki gaya min gaskiya mai
ya faru, jiya mahaifinsa ya dawo ya min bayanin dangane da halin da
Jarumi Umar ke ciki haka dan uwansa, ki daure ki sanar da ni
gaskiya".
Rumaisa ta ce "Mafarki ta yi Mama".
batúre
1
61 Page
Ta sanar da ita jikinta a sanyaye Suhaila bin Ababakari ta
kama hannuwan Uwar gida Kubra ta ce "Wani mummunan mafarki
nayi akan Jarumi Umar?"
Nan take ta kwashe duk abin da ya faru ta sanar da ita.
Yanayin yadda hankalin Gimbiya Suhaila bin Ababakari yayi
matukar tashi ya sa Kubra take kokarin ta kwantar mata da hankali
"Yar ta hankalina ya kwanta da ji kin ce mafarki ne? mafarki ba
gaskiya bane, sai dai kuma wata alama ce ta nuni ga wani abun
amma akodayaushe muna fatan ganin alkairi akan yaranmu, ki
kwantar da hankalinki".
Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta fara zubar da hawaye ta ce
"Mama ina tsoro ace ni ce sanadiyar mutuwar danki, daga zuwa na".
Dai dai wannan Kalmar Hamdiya taji a lokacin da ta zo ta
labe a kofar dakin.
"Jarumi Umar ya mutu! Innalillahi wa inna ilahir raj'un wata
kara ta kwala mai firgitarwa wacce hankulansu ya dawo kofar dakin
'Jarumi Umar"
Ta kwalla kara mai karfi wacce duk maʼaikata da suke wajen
gidan sai da hankulansu ya dawo kanta.
Kubra da Rumaisa, gimbiya Suhaila bin Ababakari suka fito
suka tarar da ita a matukar rikice "Ke ba alkairi bace"
Ta fara nuna Suhaila bin Ababakari, ke masifa ce a cikin
birnin mu, Jarumi Umarya mutu ta kashe mana Jarumi Umar”.
Mama Kubra ta daka matsa tsawa ta ce "Waye ya gaya miki?,
ki nutsu ki shiga hankalinki" amma ina ta kara rikcewa ta na kokarin
riko Suhaila bin Ababakari, ai kuwa ta yi sa'ar cafar wuyanta ta
shake tana ihun ta kashe Jarumi Umar.da kyar matan da ke wajen
suka kwace ta, ta ci gaba da ihu da kururuwa har sai da Kubra ranta
yayi mummunan baci ta zabga mari, domin ta shiga hankalinta
bature
Ta rike kunci cikin tsananin takaici, Uwar gida Kubra ta cc da ita “Me yasa baki yin abu cikin hankalinki nc, waye ya sanar da ke Jarumi Umar ya rasu, a ina kika ji wannan maganar?” Haushi da fushi ya fusata tata ta bar harabar wajen, Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta rike wuyanta, Uwar gida Kubra ta ce "Shiga da ita ciki Rumaisa, sannan ta dubi ragowar jama'ar ta ce
"Rashin nutsuwa ne da rashin fahimtar Magana irin na Hamdiya,
tana gaya min ta yi mummunan mafarki ga Jarumi Umar ne kawai ta ji karshen maganar shi ne ta zo cikin rashin nutsuwa, babu abin da ya
faru da Jarumi Umar”.
A sannan ne nutsuwa ta zo wa kowa a gidan sannan kowa ya
koma ya ci gaba da al'amarin gabansa.
Hamdiya ta tafi dakinta ji take zuciyarta ta dauki zafi, ta kasa
saita nutsuwarta, a yau ta kara tabbatarwa akwai wata makarkashiya
da ke zuciyar Kubra so take ta bada auren Suhaila bin Ababakari gad
anta Jarumi Umar, lallai son zuciyar da ake sanar da ita na Uwa
Kubra ya tabbata sau tari matar SHAMSU BIN AUJARtana sanar da
ita, amma bata taba yadda cewar son zuciya da son abin duniya ne da
it aba sai yau.
Zuciyarta ta kara kumbura ji take kamar ana turo mata wuta
cikin tashin hankali ta yi watsi da wani karamin ma'adanin
abubuwanta komai dake kan abin ya waste ta kara rusa kuka mai
tsanani ta fada kan shimfidarta.
Babu wacce ta isa ta auri Jarumi Umar matukar tana raye, sai
ta yi sanadiyar kashe ta, it ace zata auri Jarumi Umar duk rintse idan
kuwa bata aure shi ba to kuwa sai dai su rayu a haka, babu wadda zai
yi aure.
A bangaren dakin da Suhaila bin Ababakari suke Uwar gida
Kubra na tsaye a kanta don kwantar mata da hankali "Kiyi hakuri ki
bature
62 Page
kwantar da hankalinki babu wani abu haka take bata da nutsuwa
akan komai kuma zan tsawatar mata".
Suhaila bin Ababakari ta dubi uwargida Kubra ta kuma
fahimci abin da take kokarin yi na son kwantar mata da hankali ta ce
"Ba wani abu Mama, ko ubangijinmu baya kama dan adam da laifin
cikin rashin sani, wannan ba komai bane, akwai damuwa sosai rasa
jarumi kamar Jarumi Umar a cikin al'umma, na fahimci damuwarta
sosai kuma na yafe mata".
Uwar gida Kubra ta ce "Kina da zuciya mai kyau, nagode da
fahimta, in kin kimtsa idan Hakimi ya fito fadar tsakar gida ki je ki
gaida shi".
Gimbiya Suhaila bin Ababakari ta jinjina kai alamar zata je.
Sannan ne uwa Kubra ta fita daga cikin dakin ta kuma nufi dakin
Hamdiya tana kwance tana garzar kuka ta zauna kusa da ita.
"Ban san me yake damun zuciyarki kike bijirewa koyarwar
mu ba, akodayaushe muna koyar da ku muhimmancin bako a
wannan masarauta amma bakya ji, duk ranar da za a yi bakuwa
komai girmanta ko matsayinta sai kin nuna mata halinki na rashin
kauna, ki saita zuciyarki ki iya mu'amalar kirki da mutane
musamman 'yan uwanki mata ace a duk fadin garin nan da wajensa
baki da wata kawa ko aminiya, ke kullum cikin rigima kike da 'yan
mata, dan Allah ki gyara halayenki ki guje abin da zai sa na kara
dora hannu akan fuskarki, kin san ina son ki, ina kaunar ki ko da ba
ni ce na tsuggunna na haife ki ba, ina jin matsananciyar damuwar da
kike ciki".
Idan kina jin damuwar da nake ji da tuni kin tilasta aurena da
Jarumi Umar tunda kin sani sarai babu wani mahaluki da nake so in
ba shi ba
Ta fada a cikin zuciyarta har Kubra ta gama yi mata nasihar
ta gaji ta fita ba tace mata ta tafasa ba, jira take ta fita ta bata guri
bature
631
64 | Page
domin ta fara shirin da zata yi domin kawar da Gimbiya Suhaila bin
Ababakari.
Aka dauki Jarumi Jarumi Umar zuwa cikin dakin magani
cikin sauri da gudu gudu, da fari aka fara da zuba masa ruwa domin
ya dawo hayyacinsa, cikin ikon Allah numfashinsa ya dawo a
hankali, suka dinga godewa Allah, a hankali ya fara budewa
idanuwansa ya ganshi tare da abokansa duk fuskarsu hawaye ne ke
kwaranya. Batare da sun lura da ya bude idanuwansa ba, daga can
suka ji muryarsa na amsa amo da cewar "Na gaya muku zuwan
mutuwa a gare ni ba sauki bace".
Suka dube shi cikin farin ciki da annushuwa murmushi yake
yana shafa wuyansa saboda zafin da wajen yake masa ga shati sosai
wajen yayi jawur.
"Su ka hada baki saboda duk wasu lokutan da ya kutsa hadari
ya samu ya kubuta irin Kalmar da ya kesanar da su kenan cewar
Zuwan mutuwa ba sauke ce a gare nib a, maʼana mutuwa ba za ta zo
ta dauke shi cikin sauki ba, sai an sha artabu, wannan addu'arsa ce ta
neman yaddar Allah akan yay i mutuwa a cikin abokan gaba yana
yaki domin daga Kalmar Allah".
Suka rungume shi, har sai da mai saka masa magani ya gama
hada maganin sannan suka rabu da jikinsa ya saka masa maganin a
wuyansa.
F
"Me ya faru?"
Ya yi musu tambayar a lokacin da ake saka masa magani.
Adai-dai wannan lokacin Yarima Abbas ya shigo cikin daki da
dakaru na biye da shi. Ya kara so duk suka zuba masa idanu, har ya
kara so kusa da Jarumi Umar ya zauna ya mika masa hannu domin su
bature
65 Page
yi musabaha Jarumi Umar ya dube shi da mamaki ya ce "Ranka ya
dade"
Bai dauki hannun ba ya kara jinjina kai ga Jarumi Umar
domin ya aminta su gaisa. Jarumi Umar ya mika masa hannu cikin
girmamawa shi ma yarima ya amsa yana mai cewa "Mahaifinka ya
sanar da ni cewar nayi kokari na kubutar da kai daga sarkakiyar dake
cikin kasar nan. Lallai Allah ya nufa da kwanan ka a gaba”.
Jarumi Umar ya dube abokansa alamun tambaya domin bai
san cewar yarima ne ya cece shi ba, suka daga masa kai alamar
tabbatarwa. Jarumi Jarumi Umar ya jinjina kai “Ina godiya ranka ya
dade, ya mahaifina yake dafatan yana cikin koshin lafiya?"
"Yanzu haka ya koma gida tun jiya mun rabu da shi, kuma ya
san da cewar kana cikin hadari tun da ya fuskanci Waziri Ja'afar ya
san cewar ka taho birnin don haka da zan zo nan ya bani amanarka,
nagode wa Allah da ya sa na riske ka a kan lokaci.
Yanzu abin da nake da bukata da kai ka kwanta ka samu
hutawa, duk wani abu da za a zartar da shi ko fahimta a birnnin
Shamnun yana gare ni, kuma zan aiwatar da shi bisa yaddar Allah,
wannan nauyin mahaifina ya dora min kuma shi ne gwaji na farko
daga samun nagartar sarauta ta”.
Yarima Abbas ya mike tsaye cikin sauri ya juya ya fita tare
da dakarunsa ya barsu a tsaye anan. Kai tsaye ya shiga bangaren
sarautar gidan. Bai tsaye ko ina ba sai karagar mulkin gasar
Shamnun.
Babbar fada da ce da aka kawatata da gini na alfarma waje ne
mai girman gaske, da yake mallaki ne na Rum, a shekaru masu yawa
kafin yaki sarkin wancan zamani a dawo da ita karkashin ikon
musulmi sun yi matuka batar da dukiya da basira wajen gina wannan
fadar can nesa kujerar mulki take, sannan daga hagu da dama akwai
kujerun alfarma na waziri dakuma Babban Dakaren birnin sannan ga
bature
66 Page
'yan majalisar sarki su ma kujerunsu da aka kerata da zallan zinare a
shimfide sahu sahu a gaban kujerar Sarki.
Kai tsaye Yarima ya je bakin kujerar mulki ya zagaye ta
wajen sau uku kafin ya samu wajen zama. Ya zauna sosai yana
kallon kofar shigowa wacce take kallon saitin kujera bai dauke
idanuwansa daga wajen ba har sai da Yarima Hilal da kuma Waziri
suka shigo cikin fadar.
Ganinsa a kan karagar mulki duk hankulansu ya ta shi ainun
suka tsorata matuka. Ba wani abin tsoro bane domin wani mai
babban matsayi ya zo karamar masarauta ya zauna a kujerar mulki
hakan dama yana faruwa, idan Sarki Muhammad farsi zai je kowacce
kasa da take karkashinsa shi ne zai gudanar da komai har ya bar
kasar, amma abin da yasa suka tsora a wannan lokaci suna jin cewar
Sarki Muhammad farsi ya aiko dansa Yarima Abbas ne domin ya
kwace masarauta a datseta, har sai an kamala bincike wadda hakan
idan ya faru, babu shakka sai sun rasa kujerar mulkinsu, domin za a
iya dauko wasu daga cikin jinin sarautar a basu tun da sun kasa
daidaita kansu.
Waziri Adnan ya kara so cikin sunkuyar da kai kasa shima
Yarima Hilal.
'Ranka dade ina mai maka maraba da zuwa birnin Shamnun".
Yarima ya kalle shi cikin nutsuwa. Ya mayar da kansa kan
Yarima Hilal Yarimaya dube shi a dari dari “Barka da zuwa dan
uwana Yarima Abbas".
Yarima Abba yace "Na zo takasanas daga Babban birnin
zuwa birnin Shamnur domin aiki mafi muhimmanci a gare ni, na zo
domin na fitar da gaskiya na kori karya, kuma nayi alkawari ba zan
bar birnin ban sai na tabbatar da adalci, na kuma danka mulki ga
wadda ya cancanta. Yanzu mene ne laifin Jarumi Umar da kuka yi
kokari kashe shi? Shin baku san waye shi bane?"
bature
67 Page
Waziri ya dago da kai a tsorace ya ce "Ranka ya dade ba mu
san wane ne shi ba".
"Shin bai sanar da ku ba?"
Waziri yayi shiru har sai da Yarima Abbas ya kara maimaita
tambayar, sannan ne Waziri Adnan ya ce "Ya sanar damu amma
saboda halin da muke ciki na bukatar Yarima Salman da tsoron
shirin da zai zo mana da shi ya sa muka yi tunanin karya ya shiryo
mana don ya samu ya kawo mana sharri cikin masarauta”.
Yarima Abbas ya jinjina kai “Wane bincike kukayi domin ku
tabbatar da hakikanin gaskiyarsa ko akasin haka?"
Waziri Adnan yayi shiru domin bai da tacewa "Mun