ubangiji mutane da Aljanu
mai iko akan kowa da komai, masha Allahu ya rabbi.
Lokacin da Jarumi Umar ya karaso ya sauka daga kan
dokinsa kai tsaye ya nufi mahaifinsa, ya gaida dattijan fada sannan
ya matsa ga mahaifinsa, duk abin da ya faru ya sanar da shi, tun daga
bature
81 Page
kan tafiyasu zuwa Birnin SHamnun har zuwa lokacin da aka yi
kokarin rataye shi, har zuwa da Yarima Abbas ya zo ya kubutar da
shi har ma da yadda Abbas din ya gudanar da bincike har ya zartar da
hukuncin da yake da ikon yin.
Dukkanin jama'ar fadar sun jinjinawa Yarima Abbas kuma
sun yi murna da ya zamo aikinsa na farko na matsayin Yarima nuna
halin girma da kuma nuna cewarshi jagaba ne mai adalci.
Gimbiya Suhaila bin Ababakari na nesa tana hango Jarumi
Jarumi Umar jira take yi kawai ya baro fada ya zo wuce wa zai shiga
gidata tare shi ta yi masa Magana don jin abin da ke faruwa, aikuwa
cikin ikon Allah bisa mamakinta sai ta ga ya yi sallamada manyan
fadar Hakimi Abdullahi bin Sharjas ya nufo hanyar da zata sada shi
ga cikin gida. Dukkanin abokansa sun tafi na su sashin da sauri ta
nufe shi. Kwatsam ya ganta a gabansa tare da zakuwa a cikin ranta
Ya sakar mata murmushi mai taushi, hade da jin kwarin
gwiwa samar mata da farin ciki na bata daddan labari.
"Dan uwanki yayi nasara zama sarki”.
Nan take ta durkusa kasa ta yi sujjadar shukra ta dago tana
yiwa Allah kirari da sunayensa tsarkaka kallonta kawai ya tsaya yake
yii yana wannan murmushi wadda shi kansa bai san yana yinsu.
Sai da ta kamala sannan ta dago ta ce "Da me zan saka maka
ya kai Jarumi Umar".
Ji ya yi kamar yace wani abu amma sai ya dauke idanuwansa
da barin kallonta domin ya fara yi mata wani kallo wadda shi da
kansa ya fahimci ya wuce gona da iri ba wacce suka yi sabon da zai
mata wannan kallon bace domin a tsakaninsu kawai taimako ne”.
"Da ni da ke duk mu godewa Allah mu kuma godewa
masarautar Bahara, da yarima Abbas, ban da zuwan da yayi a kan
lokaci da tuni na rasa rayuwata".
bature
Ta kara fadada murmushinta "Kai ne kataimake ni daga
fadawa tarkon kafure, ka kubutar da ni daga hannunsu, ka tseratar da
rikicin da zai hadu tsakanin kasashen musulunci.
Kai ne ka sayar da rank aka tafi kasar da ake neman mai
goyan bayanmu, domin su hallaka shi, kai ne ka cancanci yabo da
godiya a gare ni, ina mai kara gode maka, kuma watarana zan rama
maka wannan halacci"
Bai san Gimbiya Suhaila bin Ababakari na da matukar kyau
irin na yau ba, sai da ta kasance cikin nishadi tana dariya, koda yake
murmushi shi ke tona asirin kyawun dan adam, saboda haka ya zama
wani saakarai wajen kallon kyawun fuskarta, har sai da ta tsayar da
kallonta a kanshi ta fuskanci yadda yake kallonta, ya dimauce ya
kasa samun yadda zai sarrafa kansa har sai da ta dan jima itama tana
kallonsa a ranta ta ce Jarumi Jarumi Umar shi ne namijin da take buri
ta samu a matsayin mijia gareta yana da zati irin na mazajen gaske
dirin jikinsa ya amsa, yanayin jarumtarsa abin burgewa, shine mijin
da zai iya kare iyalinsa daga dukkan karfinsa, yana da kirki da kunya
kamar yadda take da buri, shi kansa ya manta da yanayin da yake
ciki, kwakwalwarsa mai saurin kawomasa shawarwari ta fara
shawartarsa a game da wani abu dangane da gimbiya Suhaila bin
Ababakari, amma bangaren zuciya mara karfin gwiwa na bashi
labarin matsayinta da na sa matsayin wannan tunanin ya dawo masa
da mafarkin da yake kokarin dorawa ransa.
"Dan uwana rabin raina”.
Muryar Hamdiya ya karade kunnuwansu kuma ya dawo dasu
cikin hayyacinsu, cikin rashin gaskiyar da gimbiya take ciki na
tunani dole Hamdiya ta fuskanci abin da ke wakana don haka ta yi
sim-sim ta bar wajen. Ya dubi Hamdiya, da take kokari yi masa
Magana "Ban san me yasa kake son ka bada rayuwarka ga mutunen
da basu da amfani a gare k aba, dan uwa na sha kukan rashinka".
bature
82 Page
83 Page
Ya dube ta duba na mamaki "Ban fahimta ba,su waye basu da
marasa amfani a rayuwata?"
Ta juya ta dubi Gimbya da takekokarin shiga cikin gida shi
maya kalle ta tare da suka dawo da dubansu ga juna ya riga ta
Magana ya san abin da take son sanar da shi “Kin ga Hamdiya
rayuwarta ta kowane dan adamce matukar ya bada gaskiya ga
ubangijin talikai, babu wani dan adam da za a zalunta ina kallo
batare da na taimakeshi ba, ina so ki koyi hana kanki shiga cikin
lamurana, ki zauna a matsayinki na 'yar uwata, ki koya wa ranki
sanin cewa ban taba fita daga gida da saka san cewa lallai zan dawo
na same ku ba, saboda haka ban saka ki lalubamin mutanen da suke
da muhimmanci ko wadanda basu da shi a cikin lamurana".
Yana fadin haka ya bar wajen ya bata waje tana kallonsa
kamar ta fasa ihu don takaici.
**
Sarki Muhammad farsi Farsi shugaban kafatanin nahiyar
larabawa a zamaninsa, yana zaune cikin kulawar matarsa Siyama
tana shayar da shi kayan alatu a kyakkyawan lambon gidansa suna
taba hira sama sama, ta lura da akwai tarin damuwa ga Mijinta
Muhammad Farsi, don haka sai ta fara tunanin ta yadda za ta shawo
kansa ya sanar da ita damuwarsa, saboda ita ya nuna mata kaguwa da
son sanin damuwarsa zai iya share ta, ta kawo maganar barin
'ya'yansa birnin don zuwa cika aikinsa, ta fahimci damuwarsa ba ta
wannan bangaren bane, saboda haka sai ta tuna da zuwan Abdullahi
bin bin Sharjas da ya zo garin yau kwana uku da suka wuce don haka
sai ta fahimci lallai akwai wani abu dangane da zuwan nasa a cikin
bacin ran Sarki, ta yi nisa ta mika masa wani karamin kofi da yake
cike da tataccen ruwan inibi, bayan ya amsa ta ce "Zuwan Abdullahi
bature
841 Page
bin Sharjas birnin nan ya zo da batutuwa da dama, a game da zargin Waziri Ja'afar, ya sarkin duniya mai kake tunani game da lamarin?" Kamar ta sosa masa inda yake masa kaikayi, ya kurbi lemon ya mika mata kofin ta amsa ta ajiye a gefe sannan ya ce "Rashin
walwalar da nake ciki ta rashin jin dadin jikina a shekaru biyu baya
zuwa yanzu, na kasa katabus a harkokin mulki na ya fara taba min martaba da kima, da yawan mutane suna tunanin na gaza yin riko da
adalci, suna min ganin na gaza samar da ci gaban musulunci, ina damuwa matuka da wanzuwar lamarin da suke zuwa kunnuwana ina
takaici da abu guda, makusanta na basa iya fayyace min duk abin da
yake yawo a birnin bare koma sauran kasashen da muke mulka, har
sakacina ya kai ga mutuwar ga ‘ya'yan Sarki dan uwana suna kokarin kashe junansu a kan mulkin masarautar da muka danka musu
batare da sun zo don a yi musu sulhu ba, mene ne amfanin waziri
Ja'afar da ya zamo wakilina akan komai, mene ne amfani shugaban
dakarun na birni da kauyekan wannan birni har ace kafurai za su kafa
wata rashin gaskiya su aiwatar a cikin kasuwar da afarma mukayi
musu suke zuwa su yi saye hajojinmu, mun yi cece kuce da Hakiman Kauye akan basa bukatar shigowar kafurai amma mun danne su da karfin mulki saboda muna musu fatan samun tagomashi daga ababen
da suke sana'antarwa, kuma ga ni a raye ban mutu ba, mene ne yake
damuna ne? ba cuta nake yi kamar ajali ba, mene ne yake sakani na
zama kamar sakarai".
"Ranka ya dade".
Ta tare shi da murya mai cike da shagwaba, yanga jan hankali
da kuma kwantar da hankalin ma'abocin saurare, ya tsayar da kansa ^
a kanta a nutse yana son ta ce wani abu. "Ranka ya dade" ta kara
maimaita cikin sigar muryar jan hankali “Ka yanke wani hukunci
wadda ya yi min dadin ji a zaman fada na ranakun da suka gabata,
cewar ‘ya'yanka duka za su fara shiga sabgogin mulkinka kai tsaye
bature
85 Page
na tabbata jininka ba zai yaudare ka ko gaza wa da abin da ka umarce
sub a, batu akan Waziri shi ne karfinsa bai zamo kamar na Sarki ba,
amma karfin da ke hannu yaranka tamkar naka karfin don haka ka
yanke hukunci mai kyau, sannan kuma na san tun daga yau in sun iso
za mu samu kyakkyawan labari”.
Ya dan yadda da maganar ta, amma dai ya kalli kansa "Me na
rasa ni da ba zan yi da kaina ba mene ne damuwa ta, lallai zan canza
mai duba lafiyata".
Gabanta ya yanke ya fadi domin hakan na daf da tonowar
asirinta ta ce "Kana zargin wani abu ne?"
"Bana zargin Mustafha da komai face tsufa da kuma kamar
bai da kwarewa a game da abin da ke damuna tunda ba cuta nakeyi ta
rashin lafiya ba, cut ace ta rashin sukuni, karfin gwiwaa, karsashi
shiga kowane sha'ani batare da gajiyawa ba".
Jikinta yayi sanyi tabbas ta gaddame masa yana dab da zargin
wani abu, don haka sai ta karkace ta gyara zamanta ta kalle shi “Idan
dama taki sai koma hagu maganarka gaskiya ce, fatanmu ka kasance
cikin karsashi kamar koda yaushe?"
Tana fadin haka yayi shiru idanuwansa na kallon guri guda,
gaba daya hankalinta ya bar wajen jira take yi kawai Zulehat ko
Hauletu su karaso cikin lambu ta mike dan zuwa ta sa a yi mata kiran
Mustafa ta kuma gana da waziri.
'Yarsa ce Gimbiya Zahra, ta nufo lambon cikin ado barori
biyu na taki mata baya, tsawon nisan tafiya taku gomasha biyu da
inda Sarki yake barorin suka tsaya gami da sunkuyar da kawunansu
kar, don kada su kalli inda Sarki yake, daga nan ne Gimbiya Zahra ta
ci gaba da tafiya har ta iso wajen da ake tanadarwa mahaifinta dan
hutuwa da yammaci sakaliya. Gimbiya Zahra ta sunkuyar da kai kasa
ta yi gaisuwa ga mahaifinta, ya amsa mata cikin murmushi da nuna
mata waje kusa da shi ya ce "Zo ki zauna”.
bature
86 Page
Ta tafi cikin ladabi ta samu wajen zama ta zauna daf da ashi
ya dafa bayan "Ya Zahra ta, kyakkyawar diya ta, mene ne
damuwarki?"
Ta yi murmushi ta kalli Sarauniya Siyama dake a takure waje
guda duk hankalinta ya dagule ta rasa mene ne abin da zata yi don
magance matsalar da za a jefa su ciki.
Ta tuna wasu lokutan can baya a lokacin da Likitan Sarki
Mustafa ya fito daga sashin sarki yana kokarin duk damuwa ta dame
shi adai-dai lokaci Siyama ta biyo bayansa bayan ta fuskanci ya
fahimci abin da yake damun Sarki yaki yin Magana ne saboda bai
san yadda maganar zata zama a cikin gidan ka iya yiwuwa ya yi laifin da zai ja masa kisa, ko wani dauren saboda babu wani likita
amintacce da Sarki ya yadda da shi kamar Mustafa. ta yi sauri ta sha
gabansa a lokacin da ta lura da babu mai ganinsu, su ka yi ido biyu gege domin da Mustafa. Mustafa yana muzurai yana kallon gefe da
kadaice da matan Sarki matukar ba dakin gani ba haramun ne kuma
kisa ne a kanka saboda hakan sai hankalinsa ya tashi.
"Kwantar da hankalinka babu wani da zai gan mu”.
Ya dube ta da alamun tambaya ta riga shi kara wata maganar
"Akwai wani abu dangane da ciwon Sarki me yake faruwa?"
Ya fara nuku-nuku ta daka masa tsawa "Ka fada min me ka
fuskanta?"
Babu yadda zai yi yace "Aikin sihiri ne, da aka yi amfani da
shi a bargon da karkashin matashin kansa tsawon lokaci su ne suka
haifar masa da ciwonsa, daga kwakwala zuwa karfin jiki, sihiri ne
mai karfe da ya kashe masa karfin jiki ya kuma kashe masa karfin ^
nazari da hangen nesa".
R
Ta dube shi tana nazarinsa domin tana da sakon da zata bashi
"Me kake tunanin aikatawa yanzu ina nufin me za a yiwa Sarki da
zai samu lafiya”.
bature
87 Page
"Ina son sanar da likita kuma sirikinsa bin Abbas ne domin
shi ne likita mafi rinjaye kuma yana aikin sihiri don haka shi ne
kadai zai iya da wannan al'amari da izinin Allah".
"Ibn Abbas, to ahir, ka da ka kuskura ka kawo wani cikin
gidan nan domin kula da Mai martaba kai ne za ka ci gaba da kulawa
da shi".
Ya dubeta yana son yi mata cikakken bayani bayan ya hadiye
wani yawo ya ce “Bani da kwarewar da zan iya magance matsaalar
Sarki ranki ya dade, matukar ana son Sarki ya samu lafiya dole ne sai
mun yi amfani da jarraba malamai wadanda suke da ilimi wajen
yakar sihiri, wannan yana ci masa jiki zuciya da kwakwalwa za ta iya
kai Sarki ya rasa hankalinsa wata rana ko kuma ya karfin lakar
jikinsa ta daina amfani, hakan zai iya sawa a rasa Sarki".
Ta Harare shi "Matukar ka sanar da wani wannan al'amari
abin da kake tsoro shi zai faru gare ka, domin zan maka sharrin kai
ne ka hadawa Sarki wannan sihirin idan kuma ka hakura ka ci gaba
da bashi taimako zan saka maka da mafificin alkairi ko bayan babu
rayuwar Sarki z aka ci gaba da kulawa da na Yarima Yazid.
Cikin rudani da tashin
dade?"
hakali ya ce "Me kike nufi ranki ya
"Ba sauri nake yi ba, na baka lokacin yin nazari da tunani,
sakamakon bijirewa za a dauki rayuwarka kacokan daga duk ranar da
ka yi tunanin sanarwa wani, duk sahun da zaka taka mutanenmu na
bibiyar lamarinka dan haka tunaninka da yankewa hukuncinka a
hannunmu yake"
Tana fadin haka ta nuna masa hanya domin ya ci gaba da
tafiya, sannu a hankali da sanyin jiki ya bar wajen..
Ta dawo daga wannan tunanin da ta yi hakan ya sa ta yi
karfinhali mikewa domin fita daga lambon Sarki. “Ranka ya dade,
bari na barka ‘yarka”.
bature
88 | Page
Batare da yayi mata Magana kai kawai ya jinjina mata ta mike ta fita barorinta na bakin hanya suka bi bayanta don mata
rakiya cikin gida.
"Baba tun da ka zama babu lafiya horar dani a matsayin
jaruma ya tsaya, babu mai kula ni ko Yaya Yazid ko Abbas". “Uhmm shine damuwar, rabu da su kin ji farin cikin idanuwana, zan samo likita ingantacce domin kulamin da lafiyata, ko don na ci gaba da baki horo, ai na gaya miki za mu tafi yaki tare kina bisa doki da takobi a hannunki kina wulwalata sama kina cire kan
munafukan Allah ta Allah'
"Da gaske Baba?"
"Sosai".
Ta yi shiru tana wani tunani “Naji Mama ta ce ciwonka Sihiri
ne ba cuta ce daga Allah ba kirkirarta aka yi”.
"Me kika ce?"
Ta kalle shi "Na ji suna hira da Hindu, ta ce tana yi maka magani a boye batare da sanin kowa ba, tana addu'a tana tofa maka
duk ranar da ta kasance kana tare da ita, a turakarka".
Maganar ta dake zuciyarsa sai da har ya samu wani lokaci
sannan ya dawo hayyacinsa ya dubi Zahra ya ce "Na gaji da zama ki rike hannayena mu koma ciki, ga magriba nan ta karato”. Lokacin da sarauniya Siyama ta koma dakinta sai ta samu
kuyanganta abokiyar sirrinta ta kut da kut ta zauna ta rubuta sako
zuwa ga Waziri na bukatar son ganinsa cikin gaggawa da bayanin a
takaice abin da ya sa ta ke son haduwar ta su saboda kada yayi
kasala.
Da fitar wannan hadimar tata kuwa sai ga wata yar sako daga
shugaban masu aikin gidan zuwa gare ta. Ta shigo falon ta fadi ta yi
gaisuwar ban girma gami da cewa "Yarima Yazid ya dawo, yana
kwance a dakinsa".
bȧture
89 Page
Ta zaro ido cikin tsoro da fargaba "Me ya same shi me ya
faru da shi? Bata jira jin ba'asi ba ta riga wannan yar sakon fita daga
dakin ta fice zuwa sashin 'ya'yan Sarki maza ta wata karamar kofa
wacce ita take sadaka da bangarensu, kuma bisa al'ada babu wadda
yake shiga ta kofar sai Yarima shi ma sai yayi izini an kuma amshi
izinin nasa am bashi dama, iyayensu da 'yan uwansa mata na iya kai
musu ziyara duk lokacin da suka so, ta isa falonsa a lokacin yana
kishingide a kan gadonsa na alfarmababu riga a jikinsa ga hannunsa
an daure masa da wani farin kyalle" da sauri ta kara sa "Dana
Yarima, me ya faru da kai?"
Ta kama hannun tana kallo "Ba wani abu bane yanka ne kar
ki damu?"
"Me ya faru kagaya min wasu ne suka tare ku?"
"Shugaban dakarun Benjamin.. amma kar ki damu na bishi na
dasa masa ciwon da ya fi karfin wadda ya dasa min akwai katon
yanka a cikinsa?"
Tana kallonsa tana saurarensa cikin rashin fahimta "She
Benjamin ya iya yi maka wannan raunin a wane dalili kar ka bata
komai dana Sarki yana tura ku ne domin ku je ku gwada fasaharku ta
iya siyasa da da yadda za ku iya kwantar da kai ku samu nasara
wajen makiyanku, idan ya tura ku yaki, yana so ku je ku nuna
tsantsar jarumta ta damatsa, da karfintakobi, ammaa duk sanda ya
tura ku sulhu sulhun nan kadai yake bukata, ba yaki, me ka je ka
aikata ya kai dana".
Ya girgiza kai yana ciccije baki “Mama nasani, ki kwantar da
hankalinki, ba yaki nay i ba, Benjamin yayi haka ne domin ya turo
sako zuwa ga Sarki, don ganin sun shirya yaki Mama, sun daina
shakkar masarautarmu, saboda baba ya gaza tabuka komai, lokaci
yayi da Baba zai dauki kujerar mulkinsa ya dankamin domin kada
martabar kasarmu da Kalmar Allah ta yi kasa a wannan nahiyar
bature
90 Page
kasashen da suke tsoron koda inuwarmu yanzu suna iya fito na fito
da mu kaico"
"Ka tafka kuskure Yazid ka tafka kuskure wannan nakasu ne
wannan nakusu ne,me ya faru".
Duk abin da ya faru ya sanar da ita ta kama girgiza kai "Kayi
kuskure, wannan labarin ba zai je kunnen Sarki ba, dole a rufe baki a
kan maganar fadanka da Benjamin za mu basu labarin saranka da
yayi ne kadai a kafada".
"Ba ni da ko shakka ban yi wani abu a bisa kuskure ba, nay i
abu ne domin nuna karfin ran jinin musulmi Benjamin yana daukar
cewa shi zarra ne, na kuma ladaftar da shi na nuna masa ruwa ba
sa'an Kwando bane, ki kwantar da hankalinki babu wani abu da zai
sauya".
Ta ci gaba da girgiza kai “Baka san komai a kai ba Yazid,
baka san mene ne burin da manufar mahaifinka ba, tura ka gwaji da
yayi kai da dan uwanka yana son ya auna tunaninku da kuma
hikimarku ne, idan Abbas yayi nasara ba z aka taba zamowa Sarki
ba, domin Sarki zai bada sunan Yazid".
Yayi shiru yana kallonta "Mene ne idan Abbas ya zama Sarki
ni ban zama ba, me kike shakka da shayi, Abbas kani na ne, ina
alfahari da shi, idan har fi ni cancanta zamowa Sarki zan goya masa
baya kamar yadda shi ma na san idan na fishi cancanta zai goya min
baya".
"Baka da wayu baka san abin da kake yi ba Yazid, idan har
Abbas ya zama Sarki zai tarwatsa komai namu, zai salwantar da
ruhin duk wani dana a doron kasa?"
"A wacce hujjar, da dalili, waye ya gaya miki wannan Mama
ki guje maganganun irin wadannan domin rayuwarki zata zama
gajera, 'ya'ya Sarki Muhammad ne jikokin Farsi masu Sarauta daular
musulunci, tarbiya da kaunar juna a jinin jikinmu, take, matukar
bature
91 | Page
bamu zalunci dan uwanmu ko nuna masa rashin goyan baya, ko
fitowa mu yake shi ba na tabbata zai ba mu kariya zai kuma daga
darajarmu".
Ya koma ya kwanta tayi suroro tana dubansa wannan lamari
shi ke tayar mata da hankali bata da wata mafita illa ta fice daga
dakin zuwa ga jin ba'asi dangane da sakonta data aika.
Lokacin da Sarki Muhammad ya isa fadarsa sai ya yi wata
irin shiga ta irin attajirai ba sarakai ba, ba tare da kowa ya sani ba ya
fice ta kofar da ya saba fita in zai yi irin wannan fitar ta basaja. Kai
tsaye gidan Imam Muslim ya isa, tunda ya lura mutane na fitowa
daga dakin da yake bata karatu sai ya tunkari cikin dakin karatun.
Yana zaune a durksuhe da dalibai a gabansa sun tsirawa guri guda
ido inda yake musu bayanin game da addini, kai tsaye ya samu wajen
ya zauna a ka zagaye malam da shi batare da kowa ya fahimci wane
ne ba"
"Ilimi wajebi ne ga musulmi, domin da ilimi kadai ne zaka
fahimci wane ne addininka wane ne mahaliccinka, sannan zaka
fahimci wanene shugaban halitta, idan hark a bar kanka babu ilimi
lokaci zai zo da za a yi ta sabawa koyarwar ma'aiki domin kawo
rudu daga cikin addininmu, ga ka musulmi a riga amma kafuri a
zuciya, abin da zai kawo maka kariya daga wannan gubar ka san
Allah kuma ka san Manzanninsa, Annabi Isa (Alaihil salam) bawan
Allah ne, kuma manzon sa ne, wadda Allah ya turo domin isar da
sakonsa, ya isar sun kashe shi, daga bisani an sauya labarin me ya
faru, shine suke bautawa a matsayin Allah, wannan aikin shirka ne,
darasi ne a gare mu, da muka zamo a cikin al'ummar Annabi mafi
girman daraja a wajen Allah, akwai mushirikai da suka juya wancan
lamarin ya koma Allah, ba za su yi kasa a gwiwa ba za su yi ta kafa
siradi har duniya ta nade ba za su fasa ba, za su dinga danganta Allah
da Annabinsa, wasu za su yi kokarin canza labarin to amma ilimi
bature
kadai ne zai zame mana mafi amfani a rayuwarmu da ta al'ummar
nan gaba".
A nan ne malam ya dago kai yana duban dalibansa ya zurawa mutumin da ya zauna ido bai ganeshi ba har sai da ya dago kai sukayi ido biyu da Sarki Muhammad Sarki Muhammad ya yiwa
SHehul Islam alamun yayi shiru ya ci gaba.
Wani daga cikin dalibai ya ce "Ya shehul Islam an ce Ka
bautawa Allah shi kadai ka roke shi biyan dukkanin bukata ba za iya
rokon Annabin Allah ba kenan?”
“Shehul islam yayi murmushi ya ce "Allah da bakinsa ya
furta cewa (Ihdinalsiradalmustakin) babu wani wadda za ka roka
biyan bukata face Allah babu wani da zaka bautawa face Allah,
shirka ce ka hada Allah da wani. An je ma'aikin Allah yana fushi da
hani akan hakan, ya shaida mana cewa shi manzon Allah ne wato
dan aikin Allah ne, Allah mabuwayi yayi bayani a al'kur'ani game
da zuwan Annabi Muhammad,ya gaya mana fifikonsa da sauran
Annabawa, shi ne Annabi mafi daraja yi masa karya, kafirci ne, bare
kuma ka bauta masa ko ka hada shi da Allah".
Wannan mutumin yayi shiru ya ce "Malam ni daga Dusara
nake tafe yau kwana nan arba'in a Birnin Bahara, kuma ina yawaita
zuwa karatunka, duk inda na ji ana wa’azi na kan tsaya na saurara, na
ci karo da wani malami a dusara yana mai fadin “Idan har baka hada
rokon Allah da sunayen Annabi ba, to addu'arka ba za ta taba
karbuwa ba?"
Malam ya dube shi ya ce "Kamar yaya?"
"Ya ce Sai dole Annabi Muhammad (SAW) ya amsa sannan
Allah zai amsa."
"
?"
Malam ya furta kai tsaye ya ci gaba da cewa "Annabi
Muhammad (SAW) shi ne mafificin manzon a cikin Annabawan
bature
92 Page
93 Page
Allah kuma shi ne mafi daraja. Saba masa sabawa Allah ne, a cikin
saba masa kuma akwai masu yi masa kage, duk wadda ya yiwa
Annabi kagi ya kafirta, duk wadda ya bautawa wani ba Allah baya
kafirta, Ka so annabi mafi kololuwar soyayya ka bi dukkanin
umarninsa a cikin umarninsa ba za ka ci karo da shirya ko wani abu
da zai sabawa al'kur'ani saboda haka karya suke shi yasa nake sanar
da ku ku yi karatu, a cikin ilimi ne kadai za ku karkade wannan datti,
domin abubuwa suna da yawa wadanda suka nuna karya ce karara
ake yi masa wannan ya ta faruwa bayan wafatinsa, za mu samu
lokaci da daliban ilimi masu zuwa garuruwa don wa'azantarwa da
da'awa domin su fara yaki da irin wadannan muggun 'yan ta'adda
acikin addinin musulunci Insha" ya dan yi shiru yana duban jama'a
daga bisani ya ce "Za ku iya tafiya sai bayan magriba za mu dora”.
Bayan kowa ya watse a masallacin jikin gidan Shehul Islam,
Shehul Islam ya ce "Ranka ya dade kai ne da kanka cikin wannan
badda kama?"
Sarki Muhammad yayi shiru yana kallon Shehul Islam har
Shehul Islam yayi tsammanin akwai abin da Sarki yake nazari akansa
har yayi shirin yi masa Magana sai Sarki Muhammad ya ce "Ya kai
Shehul Islam, na zo gare ka ne domin ka gaya min gaskiya, ka kuma
gaya min laifukana da Hakimi Nur ne kadai ke iya tunkara ta ya
sanar da ni, a fadin duniya, na san ina da matsaloli da suke yawo a
cikin hakimai na, suna tattaunawa a junansu, talakawana suna
tattaunawa a junansu Sarakai suna tattaunawa a junansu, amma
matsalar da nake da ita ana tsoron tunkara ta da ita,wacce koma baya
nakai birnin Bahara, wane ci gaba na kai Birnin Bahara?"
Koda Shehul Islam ya ji wannan batu sai ya dago da kai ya
dubi Sarki ya ce "Ranka ya dade, na ganka cikin shiga ta badda
kama, ko zan iya mikewa mu tashi mu shiga gari mu zagaya majalisu
na talakawa, mu shiga kasuwa mu ji kukensu?"
bature
94 Page
Sarki Muhammad ya ce "Ba ni da karfin jiki domin yanayin
jikina amma zan jure ka shirya mu je?" Ba tare da bata lokaci ba Shehul Islam ya mike gami da zuwa cikin gida yayi shiri yadda ba kowa zai gane shi ba, ya fito ya samu sarki suka kama hanya a dawakai suna tafiya suna tattaunawa a cikin tafiyarsu ne aka zo wani majalisi inda wasu dattawa suke zaune suna hirarrakin yau da gobe da alamun makotan juna ne, Sai Shehul Islam
ya ce "Mu ziyarci wancan majalisi ko za mu iski wani labarin
sarautar birnin daga gare su
**
Lokacin da Umar bin Abdallah ya fito daga cikin gida domin
yin shirinsa na fita zagayen jeji kamar yadda suka saba shi da
abokansa a kowacce yammaci suna zuwa