Share this page
koma da baya ya kwanta yana kallon sama. Ba san me zai yi tunani ba, bai san me zaiyi ba, bai kuma san tsahon lokacin da ya dauka a haka ba. Daga baya ya koma ya zauna sannan ya jawo wayarsa ya bude number ɗin Safina sannan ya kira. Ba'a jima ba aka dauka "alhamdulillah. Allah shine abin godiya. Tunda nayi sallah nake zaune akan sallaya ina gaya wa Allah bukatu na akan ka. Gashi kuma ban tashi ba sai da Allah ya amsa min ya juyo min da hankalinka gare ni". Yace "listen Safina. If we are going to do this, then we are going to do it the right way. I am really heartbroken right now. I am in love, deeply in love with someone else, someone that I cannot have. Wannan ne dalilin da yasa aka matsa min akan auren nan. Bana son shiga hakkin duk wacce zan aura, so I want you to know what you are getting yourself into. Babu rufa rufa. I will marry you saboda ina son in farantawa iyayena rai, but chances are I might never love you, or anyone else. Me kika ce? Kin amince?" Sai da tayi shiru na wasu lokuta, daga dukkan alamu maganar ta sa ta dake ta sosai. Sannan tace "I don't know what tomorrow will present to us. Babu wanda ya san gobe. Yanzu na sani, abinda na sani a yanzu kuma shine ina son ka, ina matukar son ka. Na kuma san cewa in na aure ka zan baka dukkanin kulawar da miji yake bukata daga gurin matarsa. Na kuma san cewa ita zuciya an halicce ta ne a bisa son mai kyautata mata, so chances are high that you will love me. Maybe one day in ka tuna da waccan har sai kaji haushin kan ka ma kana tunanin what made you love her. So yes, I am going to take my chances. Na amince, a bisa alkawari guda daya, cewa you will try your best akan sauke dukkan nauyin da addini zai gindaya a tsakanin mu. Kuma ba zaka wulakanta ko goranta min soyayya ta ba". A cikin sati biyu aka gama bincike, kuma a iyakacin abinda aka samu babu wani abu da zai hana aure a musulunci. An gano asalin ta, an kuma yi bincike akan tarbiyyar ta. Daga nan uncles din Gidado, Uncle Habib, Faruk da kuma mijin aunty dinsa Maimunatu suka je har Katsina suka nema masa aurenta, a take kuma kanin mahaifin ta ya basu auren ta. Aka saka rana sati shida yadda zai zo dai dai dana Mufida kamar yadda iyayen angon suka nema. Daga nan kuma sai aka cigaba da gudanar da shirye shirye a duk bangarorin biyu. ****.     ****.    ****.    ****.    ****     **** *Her🧕🏻* Sama sama muka yi magana da Mukhtar, nayi kuma iyakacin kokari na na ganin cewa banyi masa wulakanci ba tunda yanzu ni ce da kaina na neme shi, sai dai kuma na katse maganar da cewa akwai abinda nake yi amma zan kira shi idan na gama. Na mike ba tare da na kalli Abdul ba nace "zan shiga ciki, thank you for...... For listening" ya mike shima "amma da zaki ji shawara ta kar ki koma ciki yanzu, ki dan basu space ki bari su huce tukunna. Ke ma ki huce" na tsaya amma ban ce komai ba, ya mike shima "let me take you home" na juyo "ba gidan ku zamu koma ba, mun samu gurin zama for the time being" yace "I know, amma zaku dauko kayan ku daga gidan na mu ai ko? Let me take you there sai ki debo muku kayan ku". Ban cigaba da musu ba saboda nima bana son komawa gurin Mommy da Daddy a lokacin. Muka shiga motar sa muna tafiya a hankali na jingina kaina a jikin window tare da rufe idona, hoping ina ma dai mutum yana iya hana kansa tunani? Na jima a haka sannan naji yace "Fiyya. Wata tambaya nake son yi miki. Ban san yadda zaki dauke ta ba. Please kar ki ji haushi bana nufin komai sai alkhairi. I will only ask the question dan naga yau mun samu fahimtar juna. You can choose not to answer it if you will" na dago kaina tare da bude ido nace "ina jin ka" kamar ba zai yi magana ba sai kuma yace "akan wannan da kika gaya min kina so, shine baban babyn ki?" Nayi sauri na kalle shi. Ya daga hannu "am sorry. In ba kya son amsawa forget I ever asked it" na juya kaina na cigaba da kallon gefe, sai da na jima a haka sannan nace "ba nashi ba ne ba. But kasan wani abu? Sometimes in akayi min irin wannan tambayar I wish cewa nashi ɗin ne. It would have made everything easier for both of us. Da sai dai Daddy yayi fadan shi ya gama, maybe ma ranshi ba zai kai yanzu baci ba, shima nashi iyayen in suka ji ransu ya baci suyi fada, but duk kan su ba zasu iya disowning din mu ba saboda suna son mu, at the end zasu nema mana mafita ne, which would be to get us married, muyi aure mu rike babyn mu, and live happily ever after. The end". Ban jima a gidan Aunty Hajjo ba na gama hada mana kayan mu, tare muka tafi da ita zuwa gidan da Daddy ya kama mana muka danyi gyare gyare kafin su Daddy su zo. Ita ta kira Mommy ta gaya mata muna tare. Da furnitures da komai a gidan dan haka kayan sakawar mu kadai muka shiga dashi, sai yan few abubuwan da naga babu nayi mana order za'a kawo mana har gida. Tunda su Daddy suka zo daga shi har Mommy babu wanda ya kula ni, Mustapha ne ya kai shi dakin da aka shirya domin shi sannan ya shirya masa kayan sa da duk abubuwan bukatar sa. Ni dai da naga na gama abinda zan yi kuma babu wanda yake yi min magana sai na wuce na tafi dakin da yake a matsayin nawa nayi kwanciya ta. Sai dare sannan Mommy ta shigo. "Ki tashi ki ci abinci" tace min. Na mike zaune kawai bance komai ba, sai ta zauna a bakin gadon tana kallo na tace "Safiyya wannan ita ce magana ta karshe da zanyi miki a kan auren ki. Duk da cewa yanzun ma ba wai zanyi miki maganar bane ba dan ina saka ran zaki chanja ra'ayin ki ba, zanyi ne kawai dan in nuna miki irin yadda rai na ya baci akan maganar. Ba kiyi halacci ba Safiyya, daga ke har mahaifinki ba kuyi min halacci ba wallahi. Ai na san kin san komai, duk da dai ni ban taba zama na gaya miki ba dan bana son ki dauki maganar kamar gori amma na san duniya ta gaya miki, kin san irin halaccin da nayi wa Safiya, ni na dauke ta a matsayin yar aiki sannan na mayar da ita mutum, duk abinda Safiya ta zama a rayuwar ta wallahi ni ce sila. Haka kema kuma, tun kina zanin goyon ki na dauke ki na rike tamkar nina haife ki amma yanzu ni ce abin gudu a gurin ki. Shi kuma mahaifin ki ya goya miki baya as always. Babatun sa da fadansa na banza ne in dai a kanki ne baya iya juya ki sai abinda kike so shi kikeyi. Ba'a saka ki ba'a hana ki. Kuma kowa ya dan dalilin da yasa kika samu kanki a halin da kike ciki kenan. Amma har yanzu bai dauki darasi ba. Da wasu iyayen ne ma har wanni zaɓi za'a baki? Bayan abinda kika aikata kuma ace sai an baki zabin mijin da zaki aura? Da wasu iyayen ne da tuni baki fadi uban shegen cikin ki ba? Kuma na san abinda zakuyi nan gaba, tunanin ku yanzu shine in an haifi shegen a dauko shi a kawo min ace in rike shi saboda ni ce karkatacciyar kuka mai daɗin hawa ko?. To wallahi kar ku sake ku doso ni da shi ma. Na fada miki wannan ne dan ki sani, zan cigaba da sauke nauyin ku da Allah ya dora min daga ke har mahaifin ki amma na daina going extra for any of you. Na daina saka bukatun ki a saman na ƴaƴan da na haifa da cikina. Tunda kun tabbatar min da cewa bani na haife ki ba. Kun tabbatar min da matsayina na matar uba kuma na dauki matsayin nawa". Har ta gama bance komai ba, tana gamawa ta mike ta bar dakin ni ma kuma na koma na kwanta na cigaba da kallon ceiling. Shin da gaske na yiwa Mommy butulci? Haka rayuwa ta cigaba da tafiyar min, har tsahon sati uku, Mommy ta janye jikinta sosai daga gare ni haka Mustapha ko magana baya yi min, nima kuma dama ba so nake yayi min maganar ba, Daddy ma kamar ko da yaushe sama sama yake min magana in dai har munyi doguwar magana to faɗa ne. Kullum dakina ne gurin zama na akan sallaya ta, anan nake sallah ta, anan nake kuka na, anan kuma nake bacci na. Na cigaba da zuwa asibiti ganin likita, na tabbatar masa da ra'ayi na na bayar da ɗan cikina for a closed adoption idan na haife shi. A ranar da muka cika sati uku a gidan ne bayan na tashi da safe na fita da niyyar gaishe da Daddy da Mommy kamar yadda na saba kullum, ina fita parlor sai naga Daddy shi kadai a zaune akan electric wheelchair dinsa da kofin tea a hannunsa. Na karasa na gaishe shi ina lura da bacin ran da yake bayyane a fuskarsa, a raina har na fara lissafin ko nayi wani sabon laifin ne. Amma sai naji bai yi min faɗa ba bayan amsa gaisuwa ta da yayi. Na mike ina dube dube. Na shiga kitchen na fito na kuma shiga dakin su Daddy na fito amma ban ga Mommy ba. Daddy naji yace "she is gone" na juyo ina kallon sa. "Gone? Gone where?" Yana kallona shima yace "home. Sun tafi Nigeria ita da Mustapha. Wai auren Safina za'a yi. Safina ce wai aka bayar da ita ba tare da ko faɗa min anyi ba. Suka shirya tafiyar su ba tare da sun gaya min ba. Sai da safe kawai suka fito da akwati wai Nigeria zasu tafi bikin Safina. She said wai na nuna mata cewa ke ba yar ta bace ba shi yasa ita ma ta nuna min cewa Safina ba yata ba ce ba". Not edited. Forgive the typos please. [07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: *❤‍🩹 Safiyya ❤‍🩹* *By* *Maman Maama* *Episode Ten: Soul Mates* Free Episode Na zame na zauna akan kujera cikin mamaki "aure Daddy? Safina ce zata yi aure amma ni ban sani ba? How? Why? To wa zata aura ma?" Yace "ba ta gaya miki ba kema? Kuna magana kuma?" Na gyada kai. Na san mun dan samu falling out da Safina kwanan bayan nan, and must issue din mu na san laifi na ne saboda yadda na zama very rude to her a watannin nan, hakan kuma yan ada dangantaka da mood dina da kullum bashi da kyau. Amma ban dauka har zata iya yin aure ba tare da na sani ba. And ko shekaran jiya munyi chats da ita. We even talked about magana ta da Mukhtar. Nace "muna magana Daddy, amma ko alama bata nuna min ba. Wa zata aura kuma?" Ya girgiza kai "ban sani ba, they didn't tell me and I didn't ask tunda sun nuna ban isa ba. Ba ki san samarin ta ba?" Na yi shiru ina tunani "Safina bata da saurayi. Ni dai ban san wani saurayi da take kulawa ba" na tuno da yadda takan takan yi min kallon zautacciya duk sanda muke tare in taji muna waya da Gidado. Tace soyayya irritating dinta take yi. "How can she do that?" Na fada a fili. Daddy yace " ba laifin ta bane ba. Am sure Sa'adatu ce zata hana ta fada dan tana so ta bata min rai, tana so ta nuna min nata ikon" nayi ajjiyar zuciya "babu komai Daddy kar ranka ya baci, we don't need them. We can do this alone. Su je suyi mata aure, Allah ya sanya alkhairi. All we have to do now is hire someone, kamar a nurse haka that can take care of you, sai kuma mu nemi a house keeper da zata ke shigowa ko da twice a week ne tana kula da gidan, and I can drive, duk inda zamuje zan iya kai mu" yayi shiru yana kallo na da murmushi a fuskarsa, sai kuma ya girgiza kai "Safiyya kenan. Kin dauka damuwa ta kenan? Wanda zai kula da ni? Damuwa ta shine wanda zai kula da ke idan babu ni. I don't want any enmity between you and them saboda ko babu dangantaka ta jini su yan'uwanki ne, ba na son in babu ni ki rasa wanda zaki yi turning to. Ke ba yanuwan uwa ne da ke ba, and in akayi auren ki da Mukhtar yan uwans sun zama na mijin ki, ke ba older siblings ne da ke ba. In na mutu ya zaki yi?" Na koma na zauna ina jin wani kadaici yana lullube ni. Tamkar Ni kadai ce a duniya. Ya cigaba "shi yasa da farko naso auren ki da Mustapha, at least it will strengthen the bond between you kuma ba zasu yi spilling secrets dinki ba. And you will still have Ahmad a matsayin uba ba matsayin uban miji ba, zai kuma saka ido ya ga cewa basu cuce ki ba. But now, now I don't know what to do sai dai addu'ar Allah ya kara ara min lokaci" Na gyara zama "amma Daddy ba ka ganin wannan tafiyar da suka yi suka barmu ta nuna true intentions ɗin su? Ta nuna cewa ba soyayyar Allah da Annabi suke yi mana ba?" Yace "Allah kadai ya san abinda yake ran bayin sa. I don't know abinda ke ran Mustapha, amma na san Sa'adatu is not cruel, stupid but not cruel, she is just scared that she will loose everything" nayi kokarin gane maganar amma ban fahimta ba sai na chanja magana "I still have the twins" yayi murmushi "yes, and they are the more reasons why dole in gyara tsakanin ku kafin in bar duniya, if not, you will loose them too, dan babu yadda za'a yi su juya wa uwarsu baya saboda ke". Daga nan na tashi na shiga kitchen na hada wa kaina smoothie na zauna ina sha ina jimamin abinda ya faru, har lokacin na kasa yarda wai da gaske Safina ce zata yi aure amma wai daga ni har Daddy bamu sani ba, kuma naji a raina babu abinda nake son sani irin wanda zata aura ɗin, waye shi? Yaushe suka hadu? A ina suka haɗu? Nayi kokarin mantawa da abin in fuskanci abinda yake gaba na amma sai naji na kasa. Na koma daki na dauko waya ta na kira Hassan, dole ai na san twins zasu sani musamman tunda suna Nigeria. Hussein ne ya sauka da murna a muryarsa ya gaishe ni "yaya da ke za'a taho? Kun fasa zama acan din? Mun dauka ai cewa kuka yi sai kin haihu zaku dawo Nigeria" nace "no Hussein ba dani za'a taho ba, kun yi waya da Mommy kenan?" Yace "eh dazu ta kira mu tace gasu nan zasu taso. I thought gaba daya zaku taho ai" nace "a'a, ita da Mustapha ne ka dai, ni da Daddy muna nan" naji chanji a muryarsa "but why? Me yasa zasu taho su barku ku kadai? Gashi Daddy babu lafiya ke ma kuma haka?" Nace "Mommy tace bikin Safina za'a yi. Kun sani?" "Bikin yaya Safina?" Ya mayar min da tambaya ta, nayi ajjiyar zuciya, basu sani ba suma, ya sake tambaya "wa zata aura?" "I don't know Hussein. Actually abinda na kira ku in tambaya kenan, daga ni har Daddy bamu san komai akan auren ba, and it hurts ne that bamu sani ɗin ba" ina jin sa yana magana da Hassan a kusa da shi, sai Hassan ɗin ya karba ransa a bace "but this is not right. Kawai tace mana zata je Katsina tun last two weeks kuma har yanzu bata dawo ba. She didn't tell us anything" nace "babu komai. In sun karaso kwa tambaye su details din sai muji" ya cigaba da fada sai na kashe wayar dan nasan idan ya fara ba dainawa zai yi, shima yayo gadon zuciya irin ta su Daddy. Daga nan kuma sai na mayar da hankali na gurin sama mana solution ni da Daddy, na kira Abdul na nemi taimakon sa na gaya masa abinda nake bukata, ina son a samo wa Daddy nurse namiji da zai ke taimaka masa with his day to day activities, sannan kuma da house keeper macw da zata ke shigowa two times a week tana gyara gidan, ni zan iya girki da dan sauran kananan aiyuka. Shima yayi mamaki da yaji cewa su Mommy sun koma Nigeria. Zuwa yamma sai gashi nan shi da Uncle Lukman sunzo, suka zauna a gurin Daddy har dare sannan uncle Lukman ya tafi ya bar Abdul ya kwana da Daddy, sai da safe sannan nurse din da aka yi hiring yazo. Aunty Hajjo ta kira ni tace in koma gurinta amma sai na nuna mata nafi son zama anan tare da Daddy, ina son inyi spending as much time as I can with him. Kuma naji daɗin days that follows dan na samu ina dan motsa jikina wajen zirga zirgar kula da bukatun mahaifina, abinci sai inyi masa kala biyar a rana, mu kan ci tare sometimes, in kuma yan fadan sunzo ya balbaleni da fada sai in tashi in shiga daki, daga baya sai na fahimci ganin cikin jikina ne yake triggering fadan sa, sai na koma yin iyakaci kokari na wajen ganin na saka kayan da zasu boye cikin. Kwana hudu da tafiyar su Mommy Safina ta kira ni. Ni tunda su Mommy suka tafi ban kuma yi mata magana ba ko a chats ita ma haka. Ranar sai ga kiran ta. Kamar ba zan dauka ba dan in kara nuna mata bacin raina amma kuma curiosity ya saka na dauka. "Kinyi fushi ko kanwata?" Nace "ohh dama kina da kanwa a duniya? I thought yan Katsina ne kawai yan uwanki" tayi dariya "wallahi ba laifi na bane ba, Mommy tace kar in gaya miki dan kar ki gaya wa Daddy, tana fushi dan yaki yarda da auren ku da yaya Mustapha. Sai yanzu nace mata ni dai zan miki magana, tsakanin su daban tsakanin mu daban" cikin bacin rai nace "but how can you do that Safina. Ni ban damu da rashin gaya min da baki yi ba amma Daddy fa? Daddy fa Safina. Ace wai ba za'a gaya masa maganar auren ki ba?" Tace "na gaya miki ba laifi na bane ba" nace "but you can convince her otherwise, ko kuma kibi ta wata hanyar da za'a sanar da shi" tace "what do you want me to do? Yanzu sai kawai in kira Daddy in ce masa anzo neman aurena an saka rana?" Na girgiza kai "a gani na Daddy yafi karfin haka a gurin ki, a tunani na duk wanda zaki aura gurin Daddy zai zo ya nemi auren ki sai ya amince sannan shi zai kai shi gidan ku na Katsina" tace "to yanzu dai an riga an yi an gama. Ni dai ke zaki taya ni bawa Daddy hakuri dan Allah. Nasan in yayi fushin sa ke kadai kike sauko da shi" nace "ni ba zan shiga cikin wannan maganar ba, nima lallabawa nake yi dan laifuka na sun fi na kowa yawa a gurin Daddy". Daga baya dana tambaye ta game da wanda zata aura sai ta bani labarin cewa a waya suka haɗu, kawai friend request ya turo mata tayi accepting shikenan cikin kankanin lokaci suka fara soyayya, ashe dama a gidan su kuma an fara matsa masa ya fitar da mata, shine ya fitar da ita. Nayi mata murna tace "I can't wait for you to meet him. I am sure you will like him". Bayan mun gama wayar da ita na tashi na shiga wanka, bayan na fito sai na samu kaina da tsayawa a gaban mirror ina kallon kaina ina tunanin yaushe rabon da in kalli kaina a madubi? Zan iya cewa ma ni har na manta da kamanni na. Na lura da yadda nayi baki na rame sosai idunwana suka faɗa ciki, duk glow din fata ta yayi diminishing. Ga uban ciki na da sai kara girma yake yi abinsa. Na dora hannu akan cikin ina kallonsa a madubi, Allah ne kadai ya san irin azabar da cikin nan ya bani tun daga samun sa har zuwa wannan lokacin, laulayi babu irin wanda ban sha ba, ciwo babu irin wanda banyi ba, azaba ta duniya kam na ganta akan cikin nan. Na tuna da Fiyyan da da irin gatan ta da irin shagwabar ta, na hango ina ma ace da aure na samu wannan cikin, da auren Muhammad. Na lissafo irin shagwabar da zan zuba masa ina jin ko bandaki ma sai ya goya ni ya kaini, na hango irin son da Daddy zai yi wa abinda yake ciki na, watakila ma sai ya kwace min fada a gurin sa, na hango irin son da Muhammad zai yi wa cikin nan da ace nashi ne, nayi murmushi ina tuna kalamansa, kullum baya rasa aabinda zai fada da zai referring to auren mu ko yayan mu, kullum in yana so ya tsoka ne ni sai yace zai gaya wa yayan mu abinda nake yi masa. Na tuno sanda ya gane ina tsoron asibiti yace duk ranar da zan haihu za'a sha drama. I wondered idan da munyi aure da yaya haihuwa ta zata kasance a gidan sa, maybe tare zamuyi labor, ko kuma doctor ya kora shi waje dan in ina ganin sa a gurin kara rikicewa zanyi. "ai kuwa ba zai fita ba" na fada a fili, dan karamin hauka zaiyi musu. Nayi murmushi. Sai kuma na bata rai ina tuna reality ɗina, I lost everything. The person who raped me took away not only my virginity but my everything, bai barni da komai ba radadin zuciya marar misaltuwa. Ni yanzu ba komai bace ba sai fanko, an empty shell without hopes and dreams, without even a zeal to live, without hope for a future. Karar wayata ta dawo dani cikin hayyaci na, na goge hawayen da ya sauko kan kuncina sannan na kalli screen din, sunan Mukhtar na gani. Na dauke kaina gefe ina cigaba da kallon reflection ɗina a madubi. I hate breaking his heart every time amma shi ya kasa ganewa, ya kasa fahimtar cewa dan nace na zabe shi ba wai yana nufin ina sonsa ba ne ba, na zabe shi ne dan bani da wani option left. I sometimes wondered ya auren mu zai kasance da shi, dan ni bani da burin komawa Nigeria ko da na rabu da cikin nan, too many memories. Ya sake kira. Na dauka na saka a kunne na bance komai ba "Habibty" ya fada, nayi shiru ban ce komai ba "ko bacci kike ne na tashe ki" nace "uhm uhm" "ko ba kya jin dadi?" Nace "uhm" "okay bara in barki ki huta. I just want to check on you inji ya kuke, wallahi bana jin daɗin zaman ku ku kadai daga ke sai Daddy, so nake in taho amma Abba ya hana ni, yace in bari sai kin haihu tukunna sai in taho. And guess what? I think suna shirin zasu daura auren nan ne kina haihuwa, maybe shi yasa yace in bari, watakila sai a ango zan taho". Naji kamar in rushe da kuka amma na cigaba da rike wayar a kunne na. Ya cigaba "ke har yanzu baki gaya min plans dinki ba for the wedding.

Chapter 11 of 14