zanyi asalin angwanci zan huta iyakar hutawa ranar da Prince Ja'afar zai kwana yana wanzar da qauna me yado a zuciya a gurin daya dace"
Harara ta maka Masa tare da miqewa tace “idan Kuma ban amince bafa?" Murmushinsa na Isa yayi ya miqe ya zare doguwar rigarsa idanunta ya sauka a faffadan qirjinsa me yalwataccen gashj tayi saurin dauke idonta shikam bai damu ba ya dauki wandonsa na yadi yasa ya dauki rigar ya sanya yasa hula ya matso gabanta yanata zuba qamshi yace “kofa baki amince ba kin amince Rafi'ah dolene ki aureni domin nasani kowama yasani ni dake mun dace sosai"
Dagowa tayi tace “ban amince ba Amma zaka dawo da Bestie na Ja'afar inada Wanda nakeso wlh harma munyi alqawarin aure nifa bantaba sonka ba hasalima wlh natsani namiji irinka mara sanin darajar alaqa Ja'afar Wakil please kada kaja alaqar nan har kayi yanda duniya zata fahimta Allah yasani bazan taba iya wannan cin amanar qaunarba bestie ta aminta dani ta dauki amanar kanta da duk wani sirrinta tabani munyiwa kanmu alqawarin rayuwa tare mutuwa tare Amma kana neman kawo mana tasgaro cikin tafiyarmu munyiwa junanmu alqawarin hada yayanmu aure idan Allah yaja rayuwarmu Ja'afar kada ka zama makamin yanke kyakkyawar alaqarnan kaji?"
Ta qarashe mgnr tana durqushewa a gabansa inda idanunsa yake kanta yace “kinason farin cikinta?" Saurin daga masa Kai tayi ya sake cewa “meyesa kika yarda kizo gdana saboda ita?" Sunkuyar dakai tayi yace “talk mana" dagowa tayi idonta cike da qwallah tace “saboda inason ta dawwama cikin farin ciki tare da abinda takeso" murmushi yayi yace “to ita meyesa bazatayi Miki wannan sallamawar ba?" Dagowa tayi suka hada ido ya qanqance qananun idanunsa ya nunata da yatsa yace “duk da cewar zuciyarki taqi gasqata Miki cewar kinasona Amma ni inaji a jikina jikinki da ruhinki sun karbeni Ni'imah itace qaddarar da take wahalar damu babu wani abu naki da yake boyayye a gurina kinason namiji me irin siffata to kin samu nine Rafi'ah nine Ja'afar Wakil ki karbeni kawai a wucce gurin babu wanda ya usa canza qaddarar Allah fah dagani harke babu abinda muka isa mu canza dole mu karbi duk hukuncin da ubangiji yayi akanmu"
Numfashi ya sauke yace “kada ki damu muje a daren nan zanyi Miki abinda kikeso bazaki kwana da ciwon mutuwar auren Bestienki ba Amma kisani a gobe zan sanar da manyana halin da ake ciki dama rashin samun dama daga gareki ya hanani furta musu koma...." Wata tsawa ta daka mishi data sanya gabanss faduwa tace “karka kuskura kada ka fara wlh bazan taba yarda da wannan haukan ba kuma ma Ina katabajin anyi wannan sakarcin to nidai bada yawuna ba idan kuwa ka sanar Kaine da kunya na rantse da Allah saina kashe kaina na huta kowama ya hut...."
Wata fizga yayi Mata ya hadata da jikinsa ya matse yana lalubar bakinta ta fara tureshi ya sake daidaita qirjinta a nasa yanajin yanda dukiyar qirjinta take gugar nasa qirjin, jin yanda electric din jikinsa suke wani touching yasashi saurin sakinta ya zauna a hannun kujera yana cakuda numfashi inda itama tayi baya da sauri tanajin wani shorck a cikinta da bata tabajiba daqyar ta daidaita nutsuwarta yana kallonta yanajin wani sabon baqon yanayi miqewa yayi da sauri yana korar shaidan da a'uziyyah ya dauki key din motarsa yace “muje ko?" Babu musu tabishi tana fita ta fada tata motar baiso hakan ba amma Babu yanda ya iya da ita haka ya shiga taja suka fice jikinta har yanzu wani yammmm yakeyi Mata tanajin wani yanayi da bata tabajiba, gidansu Ni'imah suka nufa Kai tsaye suka shiga tayi parking ta fita ta shiga gdan shikam baima fito a motar ba tana shiga Hajiya Sahura ta washe mata baki tace “da daren nan Rafi'ah lfy" numfashi taja tayi qasa ta gaisar da Mama tace “bestie fah Mama" sama ta nuna Mata tace tanacan tanata aikin kuka kamar kanta ka fara yo bandama abinta mijin da ya sakeki har yana fads Miki Wai sabodakene burinsa bazai cikaba meye na damuwa basai ta qyaleshi ya cika burin ba mugani"
Itadai miqewa tayi tace “tare muke dashi yana waje yace ta fito su tafi ya wucce" miqewa Mama tayi tace “tabdi Amma yakai riqaqqen dan iska bama zai shigo ba...." Kafin ta rufe bakinta sai gashinan ya shigo sai Kuma tayi shiru harda washe masa baki suka gaisa Dad taje ta Kira a sama yazo suka zauna Rafi'ah ta Kira Ni'imah tana ganinta ta rungumeta tana dariya me hade da kuka tace “da gaske ya mayar dani Bestie wayyoh dadi kema Allah yakaimu ranar da zan saka Miki yana Ina?" Janyo hannunta tayi cike da tausayin qawar tata suka fito ya dubeta ya kawar dakai ita kuwa sai wata kwarkwasa takeyi Masa shi Kuma rabin hankalinsa nakan Rafi'ah Dad ne ya lura da satar kallon Rafi'ah da Ja'afar yakeyi inda yayi gyaran murya zai fara mgn tayi saurin daga wayar qarya tana cewa “ok Ammi ganinan zuwa ki basa hqr" miqewa tayi ta dubi Ni'imah tace “zan wucce Bestie ki kula da kanki don Allah Allah ya kiyaye gaba" zuruf Ja'afar ya miqe yace “bari na rakata ki shirya ki jirani Ina zuwa" kafin ma wani yayi mgn ya fice suka kalli juna ita da Ni'imah Ni'imah tayi Mata murmushi tace “na gde Allah yabar qauna kema ki kulamin da kanki"
Har bakin motar ta rakota ta shiga yaja suka fice suna fita ya dubeta yace “amaryata me kikeso" ko kallon tsiya bai samu ba balle na arziqi mgnr duniya taqi tankasa sai latsa wayarta da takeyi taji yayi parking batare da ya sake mgn ba ya fice taja dogon tsaki tare da cewa “shashasha kawai" Bai wani jima ba ya dawo ya zuba kayan daya siyo a kujerar baya ya sake zama yaja ya nufi hanyar unguwar tasu yana parking ko sallama bata tsaya sunyi ba ta fice ta nufi cikin gda yabi bayanta dake jujjuyawa da kallo ya sauke numfashi ya bude ya dauko kayan yabawa megadi ya shiga dashi shikuma ya fice ya samu sahu ya hau ya nufi gidansa ya bawa driver mota yace yaje ya dauko Ni'imah a gda.
Lkcn da ta shiga ta tarar da Abba suka gaisa yace “ya jikin bestie din" amsawa tayi a gajarce ta haye sama ta cire rigarta da taketa zuba qamshin turaren Mr Ja'afar Wakil ta daura towel ta fada wanka taji an shigo dakin koda ta fito sai taga anti Murja ds kaya ta dubeta tace “anya wannan mutumin ba maye bane Rafi'ah?" Tabe baki tayi tace “dan wahala ba wlh na tsaneshi" murmushi anti Murja tayi tace “ni bawai shi na tsana ba tashin hankalin da zaayi idan ya fadi qudirinsa nake tsoro" batace komai ba ta shafamai a lallausar fatarta ta zura rigar bacci ta kwanta bacci me dadi ya dauketa yauma mafarkinta irin dai wanda tasabane sai ta yanzu take fahimtar inda ya dosa watoar wannan mutumin da take yawan gani ba kowace bane Ja'afar Wakil ne.
Da safe da wurwuri ta tafi makaranta saboda batason damuwa wayarta ma kasheta tayi ta jefata a jaka ranar bata samu zama sai dare ta kunna wayar ta sake sata a silent ta shiga karatu tana ganin kiraye kiraye taqi dagawa sai saqonni sukayita tururuwar shigowa Suma bata budeba tayi kwanciyarta Saida safe ta duba wasu duk shirmen Ja'afar ne taja tsaki ta qara kashe wayar.
Suna garden suna dan tattaunawa wani abokin karatunsu yazo yace “kinada baqi fah Rafi'ah" dafe qirji tayi tace “waye?" Batare da yabata wani attention ba yace “naga motarsa ansa JMW" iska ta furzar tace “kacr bakaganni ba kawai" zaro ido yayi yace “tabdi wlh bazan iyaba wannan guy din yana mgn kamar anyi masa dole" harararsa tayi ta tashi ta koma wani bangaren can nesa ta zauna wata flower ta rufeta taci gaba da karatunta ya akayi ya akayi saiji tayi an qwace littafin ta dago a tsorace.
Numfashi taja tare da miqewa ya zuba Mata ido yace “kina wahalar dani Rafi'ah da wanne zanji ne abubuwa sunyimin yawa fah inason samun sauqi ta bangarenki Amma kinqi tausayamin ya zakiyi da haqqina ne meye laifina don nace inasonki ni bada wani abun banza nasoki ba da aure fah Rafi'atuh meye laifin masoyinki?"
Miqewa tayi tana tattare takardunta tace “meye laifina Nima don nace banasonka bakuma zan taba sonka ba nikam bantaba ganin mayen mutum irinka ba ka rabu dani ka fita a rayuwata kaqi bafa ayinso dole to me kake nema danine maci amanar qauna?" Sosai yaji dacin kalamanta Amma bashida meyi shine ya kawo kansa dole ya jure iyakar wuya watarana sai labari.
Murmushi yayi yace “albishir nazo nayi Miki yau naje na samu Dad mahaifin Ni'imah na sanar dashi inasonki da aure yaje ya sami Mai Martaba ya sanar dashi Kuma inason komai ayishi a game cikin one month kamar yanda akayi na aminiyarki saboda haka daga yanzu ma zaki iya fara shirye shiryenki Nima zan fara daga yau bansan ra'ayinki ba zaki zauna a gidan sarauta ko Kuma Zaki zauna da bestie dinki"........
_Vote_
_Comments_
_Share_
_Please_
*_Ummuh Hairan_*
[1/4, 10:07 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_*
*_Ummuh Hairan_*
*_Wattpad-realfauzahtasiu_*
*_13-14_*
_Ina mamakin mutane da basawa rayuwa uzuri, shin Ina tunaninmu yake tafiya da muke manta komai yana gudana ne bisa iko da sahalewar Ubangiji bawai ra'ayinmu da_ _iyawarmu ba? Am sorry to say sisters and brothers mgnr addini babu ra'ayi a cikinta, idan har kunya zata saki kibar halal to shakka babu aure shine Abu na farko daya kamata ki bari saboda babu abinda yafishi rashin_ _kunya a duniya Amma Kuma shi Ubangiji da kansa yake cewa_ _(WALLAHU LA YASTAHAYI MINAL HAQ) tabbas Allah bayajin kunyar gaskiya saboda haka mu cire son rai mu tunkari gaskiya komi dacinta da ciwonta, Oum hairan ba son rai take rubutawa ba gaskiya take rubutawa wannan karon🤗_
___________________________
___________________________
Miqewa tayi tsaye ta zuba masa manyan idanunta masu saukar masa da kasala a mamakance take kallonsa yayi murmushi ya juya yana tafiya yana cewa wani abune zaikaini Indonesia Amma dole zan bari sai angama komai na bikinmu saboda bazan ballo ruwa nabarki da tarewa ke kadai ba, tabbas bakida laifi a cikin wannan lamarin amma duniya bazatayi Miki adalci ba hakanne yasa na shirya sanya qafar wando daduk Wanda ya nemi uzzurawa rayuwarki"
Baijira cewarta ba ya fice daga garden din Nina dake zaune tanajinsu ta taso tace “tabdi nidai bantaba ganin nataccen mutum irin JMW ba shi ko tsoro bayaji baya ko tunanin me zaije yazo?"
Jinjina Kai tayi tace “so yake ya yankemin duk wata walwalar rayuwata Nina yacika son kansa da yawa duk wani Abu da zan nusar dashi ya kasa ganewa wai har takai ga yaje ya fadawa Dad mahaifin Ni'ima wannan haukan nasa...." Zaro ido Nina tayi tace “wht? Da gaske tabdi kina ruwa Dan kuwa duk juyin da duniya zatayi indai manya suka shiga mgnr nan to kuwa saikin aureshi Kinga aminta zata qara qarfi gaku aminai gaku kishiyoyin juna...."
Batason shirmen Nina don sosai zuciyarta take tuquqi har wani daci takeji a saman harshenta itakam ta gamu da alaqàqai ya zatayi ne Ja'afar ya gane Kuma ya yarda batasonsa zama tayi dabar bisa gado tana jin kanta na wani juyawa yau duk arhar hawayenta ya qafe qaf yaqi zubowa namiji hankaka tabbas namiji buhun qayane namiji ciwon yatsa, tama rasa da wacce kalma zata fassarashi tayi daidai dashi Ja'afar ko iya haka yabarta ya gama da ita ya rusa alaqarta da Bestie dinta, wayarta ce ta dauki ruri tayi firgigit ta duba saitaga number Bestie gabanta yabada wani rass tunaninta lbr yaje Mata aikuwa ta kasa daga wayar sai lkcn kuka ya qwace Mata ta rinqa kuka me shiga rai itakam tana ganin masifa a rayuwarta yanzu badan mutuwa data dauke Mata Yassar ba da tuni ba wannan zancen akeyi ba.
Ji tayi an dafata ta dago ganin Nina yasata sake rushewa da kuka tace “bansan me zance da Ni'imah ta yarda dani ba a lkcn da wannan qazamin lbrn yaje Mata Nina kaina ya kulle wlh narasa gane mafitar rayuwata sai nakejin kamar na kashe kaina na hut...." Rufe Mata baki tayi tace “subhanallahi wannan ba kalmace ta Muslumci ba Rafi'ah ki daina idan fah Allah ya qadarta aurenki dashi bakida tsimi bakida dabara idan Kuma bai qaddara ba ko kinaso bazai yuwuba to ki fawwala masa komai duk wani motsinki yana yuwuwane da amincewar lillahi"
Shiru tayi kafin daga baya ta dago tace “amma mijin aminiyata Nina haba abin ya wucce tunani yakasa saurarona ya fahimci nufina wlh Koda baya auren Ni'imah ni baimin ba bawai don baikai ba aa halinsa ne baiminba banasonsa Nina ya zanyi ya gane banasonsa" murmushi Nina tayi tace “aa fah qaryane wannan wlh duk inda namiji ke kaiwa asoshi JMW yakai kawai dai kice saboda Ni'imah ne bakiji kinasonsa ba kuma ma badan dai mu Mata bamuda lissafi wlh mijinta tunda yaji a ransa batakai masa ba har ya darsa aure aransa to kuwa sai yayi ni sainaga da a auro maka bare da bakasan halinta ba ai gara wacce kasani tasanka in zata iya cutar dakai kasani idanma bazata iyaba kasani namiji fah idan yasa kansa Abu idonsa rufewa yake kunnensa toshewa yakeyi,
Sannan nifa sai nake ganin kamar itama bazata tashi hankalinta ba tunda tasan ba haramun bane" dago idonta tayi tana share hawayenta tace “bakisan Ni'imah ba bantaba baki lbrnta ba Nina Ni'imah qawatace aminiyata tun bamusan kanmu ba tun muna qanana nasani tanada zafin kishi ni da ita Tasha fadamin tsaf zata iya kashe mijinta ta kashe kanta indai yace zai qara Mata kishiya saboda bazata iya sharing din miji ba da wata to balle ni da ni kaina nasan indai na yarda na auri mijinta to naci amanar qauna kuma qauna bazata yafemin ba Ina tayata kishin mijinta saboda nasan tanasonsa fiye da yanda kike zato, nifa dana auri mijinta gara na mutu babu aure yafimin sauqi wlh ko bansan Ni'imah ba lbrn kishinta aka bani zan guji mijinta domin dawwamar lfyta da kwanciyar hankali na balle ni nice me bada lbrn"
Numfashi Nina ta sauke tace “to ilahi ya kyauta Amma ki daina kukannan kiyi addu'a ki tashi muje muyi C.A dinnan mu fito sai ki tafi gida nima gda zan tafi tunda anbamu hutun qwaqwalwa hakan zaibaki damar samo bakin zaren domin wannan mutumin da gaske yake wlh" miqewa tayi suka fita sai yamma suka gama C.A din ko hostel bata koma ba ta nufi gida hakanan tunda ta sauka a mota ta tari adaidaita taji gabanta yana faduwa jikinta a mace ta shiga gidan tana jin faduwar gabanta na tsananta,
Ajiyar zuciya tayi ganin parlour babu kowa tayi hayewarta sama tayi wanka ta canza kaya sannan ta fito,
********
*_Waiwaye adon tafiya_*
Mahaifin Rafi'ah Alh Nuhu mutum me jan iyali a jiki da kyautata musu kwata² su ukune Allah yabashi Yaya Rashid Aunty Raziqa sai ita auta Rafi'atuh inda suka taso cikin gata saboda mahaifinsu dan bokone Kuma dan siyasa sannan dan kasuwa da arziqi a gdansu bakin gwargwado gashi dason taimakon talakawa.
Don asalin alaqarta ma da Ni'imah cikin taimakon mahaifinta ne shekaru 18 baya lkcn sunada 3 years a duniya mahaifin Ni'ima maqocin shagon Abba ne a kasuwa sai karayar arziqi ta sameshi dake harkar gold sukeyi barayi suka shigo kasuwar sukayi barna Abba ma an taba dukiyarsa sosai amma dake yafisu qarfi Kuma shi kayansa ne na kansa yasa bai tozarta ba inda Alh Sabo mahaifin Ni'ima ya kasance kayansa hadin gwiwa ne don kaso 70% ba nasa bane gashi yana cikin wadanda akafi yiwa barna.
To dake akwai fahimtar juna tsakanin Alh Sabo da Alh Nuhu yasa Alh Sabo yana kuka yake zayyanewa Nuhu halin da yake ciki yana fada masa yasai da gidansa ya rage bashin kudin mutane duk wata kadara tasa ya siyar Amma bai gama biyaba har yanzu da saura 14 million da ake binsa gashi ko abinda zasuci babu a gidansa gidanma sai gdan gado ya koma kuma mahaifiyarsa ta mutu tun yana qarami matar babansa Kuma basa shiri da matarsa don kullum ciki gori takeyi musu.
Sosai Alh Nuhu ya tausaya masa take yayi masa alqawarin bashi gurin zama a gdansa sannan zai biya Masa bashin Kuma zai zuba masa sabon kaya yake juyawa har Allah ya sake dagashi ranar Alh Sabo yayi kukan farin ciki hakance ta faru a ranar Sahura ta dawo gdansu Rafi'ah da zama duk wani alqawari da Abba yayiwa Dad ya cikashi ashe kudin na Sarki Muhammad Wakil ne mahaifin Ja'afar da aka Kai masa sai yace yabarshi kawai ya yafe masa wadanda ya karba na baya ma don banasa bane na abokinsa ne murna ta cika Dad suka taho abin mamaki Abba saiya miqa masa kudin yace yasai gda dasu Amma yaqi karba qarshe suka tsaya a tsakiya kan cewa saidai a sake zubasu a shago ya zamana shima da hannun jarinsa hakance ta faru iyayensu na juya kudinsu gidansu na zaune lfy Sahura irin matannan ne masu homa dajin su wasune sai fankama ta qaru sun samu ci gaba a aro domin ko a lkcn gdan Abba ba qarami bane sosai ta rinqa shigewa Ammi har suka zama qawaye inda aka samu akasi ita Sahura macece me yawo ita Kuma Ammi batada yawo hakance tasa Sahura tafita mutane gata tun a lkcn da bin malaman masifa itakuma Ammi komai akayi sai tace Allah zai iya mata.
Anan gdansu Rafi'ah aka haifi qanwar Ni'imah Yusrah sai sabon balli ya tashi musamman da Sarkin Wakil ya turo matarsa ta tsakiya wato Hajiya Fatsum barka habawa sai firita ita tazama babbar mace har matan sarakai ke zuwa Mata barka to dake hali yazo daya sai Sahura da Fatsum suka dinke duk da Fatsum ta girmi sahura don a lkcn ma yaronta autan ma yana Cairo yana karatu shikuma babban yana Uganda yana karatun Parmarcy matan Kuma biyu tayi musu aure Salma da Dija wanda sune manya.
Haduwarta da Hajiya Fatsum yasata qara kanainaye Dad duk abinda tace shi yakeyi gashi tun a wancan lkcn ba wata biyayya ta cikaba kwanciyar aure idan zaiyi da ita saiya biyata, Ni'imah kuwa da Rafi'ah Allah ya hada jininsu ko bacci baya rabasu dole duk inda sukayi bacci nan suke kwana tsakanin dakunan iyayen nasu sunada shekara biyar aka sasu makaranta tun a lkcn Rafi'ah tafi Ni'imah mayar da hankali a karatu ita wasane akanta sai fada da tsokanar masifa ga surutu ita Kuma Rafi'ah irin silent dinnan ce batada hayaniya duk da tsokanar Ni'imah batada qarfi idan tayo tsokana saita gudo gurin Rafi'ah to itamma ba qarfine da itaba Amma sai ta hana a daki Ni'imah tace a rama akanta.
Haka sukayita tafiya har secondary a jarabawa ne suka raba layi saboda Ni'imah bata samu abinda akesoba sai ta tafi Art ita Kuma Rafi'ah Science Ni'imah taso jan Rafi'ah ta koma art Amma taqi tace na marasa qoqarine a lkcn ne Kuma wata qauna ta qullu tsakanin Rafi'ah da dan wan babanta Yassar Amma fah soyayyar bada Rafi'an akeyi ba duk wani Abu saidai ya fadawa Ni'imah ita Kuma ta fada mata.
Daidai lkcn ne Dad yagama tamfatsa gdansa suka tashi suka koma ranar ansha daru dan Ni'imah qin tafiya tayi inda ita Kuma Hajiya Sahura ta nace saita tafi da yarta har wani cewa takeyi ga sabon gida mi zaayi da tsoho ta manta taohon yayi mata Rana na kusan shekara goma, dukkansu Saida sukayi rashin lfy aikuwa Basu rabuwa sai kwanciyar bacci musamman da Abba shima ya Gina wani gidan kusa da unguwar su Ni'imah duk da dadan nisa Amma yafi dayar unguwar kusa don Nan idan bakasa gandaba da qafama zakaje lkcn ne Abba ya qara aure aunty Murja itama me sanyin hali babu ruwanta, zamansu lfy Lau da Hajiya Amina wato ammi Kuma daidai lkcn ne akayi auren aunty Raziqa shima Yaya Rashid yayi aure gidan ya rage saura Rafi'ah kadai aikuwa itama guduwa tayi sai tayi sati bata gidan tana gdansu Ni'imah wannan aminta tana burge kowa don ko Yassar yasani idan zaisaiwa Rafi'ah Abu to dole saidai yasai biyu ita da Ni'imah inkuwa ba hakaba bama zata karba ba yasha tsokanar Rafi'ah yace “to waini ko ku biyu zan aurane?"
Dariya takanyi tace “nikam da nafi kowa murna gani ga Bestie na gidanmu daya mijinmu daya kaga shikenan aminta tayi Rana" duk lkcn da ta fadi haka sai Ni'imah ta harareta tace “Allah ya kiyaye nayi sharing miji ke nifa wlh Bestie yanda ban taso naga kishiya a gdanmu ba haka zan rayu babu kishiya don wlh yanda nakejin kishin mijina tun kafin nasanshi zan iya kasheshi ns kashe kaina akan batun qara aure" Rafi'ah takanyi murmushi tace “nikam banida matsala akan abinda ubangiji ya halalta Ni'imah kishi kafirci ne shiyasa nake roqon Allah kada ya jarabceni da zazzafan kishin da zai hanani yiwa mijina biyayya kishin da zaisani yin shirka kishin da zai hanani haduwa da Allah salin alin Ina roqon Allah indai yayoni a wannan sahun to ya qaddaramin mutuwa kafin nayi aure don bana fatan na zamewa mijina fitina masifa Kuma bala'in rayuwarsa"
Tsaki Ni'imah takanyi tace “ai saikiyi banza mara sanin ciwon Kai yo akanme zanyi addu'a Allah ya ragemin kishi bayan kishin adone ga ya mace nifa ko akan kishi da Yusrah ma bugawa zamuyi me qarfi ya kwaci kansa Kuma wlh don na kashe kishiya bazan taba nadama don nasan itama ba Sona takeyi ba da zata samu dama zata iya kasheni to da ka bari a kasheka gara Kai ka fara kashewa"
Yanayin Rafi'ah bata musu balle jayayya hakan yakansa da taja taga Ni'imah ta kafe akan ra'ayinta saita qyaleta abinda ta dauka wani abin halitta ce baka Isa canxa mutum ba haka watanni sukayita turawa tafi na tafiya har shekaru saura wata bakwai candynsu akasa auren Rafi'ah da Yassar murna gurinsu baa cewa komai Yassar kusan yanayinsu daya da Rafi'ah shima sanyine dashi yana nuna Mata madarar qauna me mantar da zuciya damuwa kullum suna tare babu abinda yake rabasu su uku sai bacci wani lkcn suna zaune sai kawai Ni'imah ta Kama kuka idan suka tambayeta sai tace tana tunanin ranar da Bestienta zata tafi ta barta ta kwana ta yini bata ganta ba, itama Rafi'ah saita Kama kuka abinka da quruciya tasha samun Yassar ita dashi ta roqeshi ya auresu su biyu yakanyi dariya yace.
“Bakida hankali yarinya ni ba mijin mace biyu bane Kuma ko zan qara aure Ni'imah batayimin ba banason farar mace sannan ta cika son jiki da rakin masifa ke nifah har tausayin mijinta nakeyi" akan haka Wai yana kushe Bestienta akwai lkcn da Saida sukayi sati uku basa mgn har saida manya suka shiga abin saboda ita Rafi'ah tata matsalar kafiyar masifa indai aka sake ta furta abu to komai wuyarsa sai tayi shiyasa iyayenta suke takatsantsan da furucinta dama Hausawa sunce muskilin mutum wuyar sha'ani gareshi shiyasa yawa yawan mutane suke cewa ta fiye jin izza kamar wata yar sarki wasu suce don tana dakyaune take wulaqanta mutane.
Wanda a zahirin rayuwa ma ta gaske tafi Ni'imah sanyi da sauqi hali kowa takaka da me kudi natane saidai in taku batazo daya ba Amma dake bata da magana sai aka fassarata baibai, lkcn da suka gama exams sukayi candy ansha shagali iyayensu suka shirya musu party sannan Yassar ya shirya musu wani lkcn bikinsu saura wata biyar.
Ita Rafi'ah ba ma'abociyar son zama babu bawa brain aiki bace hakanne yasata zaqula wata makarantar amare ana koyar da girke² da kwalliya da tarairayar miji, da murnarta tazo ta fadawa aminiyar tata aikuwa Ni'imah ta sheqe da dariya tace “cabb kina da aiki kice innayi auren ma wahala zanyi da har zantafi wani koyan kula da miji da girki wlh bazan iyaba kema ki zauna ki huta abinki girki ko kuku yayi ai tarairaya kuwa yanda ya koyan haka zanyi masa" Rafi'ah tosa jan hankalinta Amma taqi jikinta a sanyaye taje gida take fadawa Aunty Murja ta rinqa rarrashinta tace “ance sai hali yazo daya ake abota amma ku taku halin ya bambamta nisan yayi yawa kamar misalin sama da qasa Kuma kun kasa rabuwa bazaku rabuba abin daga Allah ne kawai ki bari zan fadawa Abbanki ya biya muku idan ya biya ai dole
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 19