cire mata rigar ta sake qanqame jikinta tana kuka tace “don....don Allah ja'....." Rufe Mata baki yayi ya dago kanta yace “ki roqeni wani abun Banda wannan tunda Ammi da Abba Basu Isa su saki kiyi ba ni na isa nayi miki"
Baijira cewarta ba ya faketa ya dagata cak tana kuka tana shure² yaqi sauketa Saida ya dangana da ita bathroom din dama ya shirya terming dinsa kawai ya tsomata cikin ruwan alqyabbar kawaiYa cire Mata nanfa suka Dora kokawa kowa naji da taurin kai takaici ne yasa baisan sanda ya keta riqar sabuwar atamfar sharratone din ba ta rintse idonta da qarfi jikinta na rawa ganin ta saki Masa tanata ajiyar zuciya yasashi kunce zanin ya zare Mata komai na jikinta pant da bra kawai yabar Mata ya fara wanketa tayi tayi ya qyaleta tayi yaqi.
Aikuwa ta Raina kanta ta dirzu miqewa yayi ya bare sabon towel ya miqa Mata fuskarsa kamar Bai taba dariya ba yace “ki tashi jiranmu akeyi ki fito banson sakarcin nan naki" yana fadin haka ya fice daga bathroom din yama fice daga bangaren gabadaya qarasa wankan tayi jikinta har yanzu rawa yakeyi tana jera masa Allah ya Isa dama Wanda ya fada mass batayi wanka ba, towel din ta dauro ta fito ta ishe wannan matar da taje yimata kwalliya taqi da wata me kamala a zaune a dakin tsoro ya cikata amma sai taga wannan kamilar ta matso ta kamo hannunta tace “na zaci can zaa kaiminke Ashe Baban Innah ya murda kambu to hakanma yayi Salamatu kiyi ki shiryata goma na dare zaa fara walimar naga yanzu har takwas kinsan Magaji ba hqr ya cika ba" zaunar da ita tayi Salamatu ta miqa Mata Mai ta fara shafawa har yanzu ta kasa tsayar da ruwan idonta bayan ta gama salamatu ta fara aikinta ana kwalliyar hawaye na gogewa daqyar Hajiya Innah ta rarrasheta tayi shiru akayi kwalliyar tabata wani arnen leshi tace tasa ta sanyashi yayi masifar yimata kyau kasancewarsa maroon daurin dankwalinta ma an dauki kusan 30 minutes sannan aka gama Hajiya Innah ta bata sabuwar alqabba milk da akayiwa ado da Marron tasa Mata takalmin alqabbar shima milk ne sai awarwaro na gold masu tsadar gaske dayan hannun Kuma agogo sai zobba da dankunne da sarqa habawa wannan rana ta musamman ce duk da bata cikin nutsuwar zuciya data kalli kanta a madubi Saida tayi hamdala tare da ajiyar zuciya.
Bude qofar sukaji anyi jakadiya ce tazo ta fadi gaban Fulani Innah tace “Allah ya qara Miki lfy Mai martaba Magaji ne yace ayi muku mgn taro fah yayi taro ku kadai ake jira" dago Rafi'ah tayi tace “mun gama yanzu zamu fito" turaruka ta fesa Mata ta Kama hannunta suka fito kicibis sukayi dashi a qofar shigowa bangaren ya kalli Rafi'ah ya kawar dakai yace da fulani Innah “sannu mun wahalar daku" murmushi tayi tace “nadai fada maka idan kun tashi yanda zakuyi" kallon Rafi'ah yayi yayi murmushi yace “natsani wannan kukan wlh ki daina babu abinda zai hana saima tunzurani da kikeyi"
Tsakaninsu da gurin zamansu babu nisa ya janyota jikinsa ya shaqi qamshin turarenta ya sauke ajiyar zuciya suka fara takawa a haka tanata qoqarin janyewa yaqi bata dama takan wani farin carpet sukabi wasu dogarai na takensu gaba da baya sunata kirari da ihu tuni sautin dake tashi a gurin ya canza akasa na gidan sarautar saida suka zauna sannan mutane suka rinqa tasowa suna zuwa suna kwasar gaisuwa suna zuba mawa amarya da ango kari Ni'imah na gda batasan wainar da ake toyawa ba.
Saida lkc yaja sosai ta samu labari aikuwa kishi da baqin ciki ya tunzurata ta dauko mota ta fito tana rayawa a ranta wato ita bata isaba shiyasa baiyi Prince's day a aurenta ba sai wannan auren cin amanar ya tarawa mutane, anacan anata shagali biki yayi biki taro yayi taro ango sai washe baki yake yana satar kallom Rafi'ah da tayi kicin² da fuska taketa jan zuciya shi hakanma nishadi yake bashi, batare da sunyi tsammani ba kawai saiji sukayi an wankesu da ruwan Sanyi qarara abinda yaja suka miqe gaba daya MC baisan me akeba yanata zuba babatu saiji yayi ance “ku dakata yaku taron tsinannanu Wanda kuka taru saboda auren tsinanne da tsinanniya to ku sani dukkanku kunyi kadan kuci mutunci na harni zaaci Amana a cuceni........
_Vote_
_Comments_
_Share_
_Please_
*_Ummuh Hairan_*
*_Ummuh Hairan_*
*_Wattpad-realfauzahtasiu_*
*_25-26_*
_____________________________
_____________________________
Tasowa dogarai sukayi da sauri sukayi Mata cahhh suna fadin “Saita kalami yar talakawa...." Saurin daga musu hannu yayi ya miqe ya taka cikin cikar Izzarsa ya Isa gabanta tanata huci tana cije lebe, dafa hannu yayi tsammaninta marinta zaiyi sai taji ya sauke hannunta a kafadarsa ya janyota jikinsa ta fara qoqarin fincikewa yasa dukkan qarfinsa ya mannata da qirjinsa ya karbi abin mgnr yayi gyaran murya cikin sauti me nuna asalin izzar sarauta yace “da farko inayiwa baqinmu barka da zuwa tare da baku hqr a bisa abinda wannan zautacciyar tayi muku akasi aka samu baasan ta fito ba tadan hadu da matsalar brain ne idan abin ya motsa tana fuzga so do Allah kowa yayi calm down komai zai wucce am Sarkin gda da Sarkin qofa ku mayar da ita bangarenta a qara Mata tsaro don gaba kadan duka zata fara"
Yana fadin haka ya dago sakar Mata murmushi ya daga Mata yatsa ya barta tsaye sororo kafin ta ankara taji an cafeta sama an fice da ita daga gurin aka cillata a wani killataccen bangare a gdan shikuma ya koma gurin amaryarsa yana zama ta miqe ta fice daga gurin a guje ya sa aka bita itama aka riqe masa ita ya taso ya iso gareta yasa hannu ya kamota ya fice da ita daga cikin taron bangaren da aka fara kaita nan ya nufa da ita ya cillata saman kujera ya fara bala'i yana cewa “kema mahaukaciyar ce irinta da zaki biyeta ku watsarmin da mutunci a bainan nasi?
Miqewa tayi tana huci tace “akanme zakace mata mahaukaciya bayan kafita hauka da kana tunanin zaka samu wannan damar ka gama shimfida son zuciyarka a banza ne kana tunanin ko ita ta qyaleka duniya zata qyaleka ne? Ja'afar Ka cutar damu Allah ya isa wlh bazamu yafe maka ba Kaine Ummul aba'isin kowacee masifa ta rayuwarmu da dadi da wuya mun jurewa juna har kawo lkcn daka riskemu Ashe Kaine qaddararmu Kaine bala'in da zai fado rayuwarmu ya rusa mu kacina son kanka da son zuciya Wanda na tabbata duk Wanda yabi son zuciya qarshensa nada......"
Wata fusga da yayi Mata ta hanata qarasa kalaminta ya cillata gadon yabita ta zulle a guje ta nufi bathroom yabita ya sake wartota ya hadata da bango yace “qarya kikeyi Rafi'ah bazan taba nadama ba a rayuwata giya nasha ko caca nayi kokuwa zina na nemeki da ita da zakice zanyi nadama? Oh God" ya fada tare da bude qofar a fusace ya fice daga dakin ta koma ta zauna tana wani irin kuka me ciwo tana tambayar kanta me hakan yake nufi kenan ya kawota bangare babu kowa ya ajiyeta babu kowa nata.
Tana wannan tunanin taji an bude qofar an shigo ta dago da sauri ganin qanwar Ammi Bushira da Aunty Murja da Aunty raziqa yasata miqewa da sauri qarasawa sukayi gabanta Aunty Bushira ta Kama hannunta ta zaunar da ita tace “bazaki daina kukannan ba ko gashinan kinjawa kanki Ja'afar ya rantse bazakibar gdannan ba kinzo kenan...." Dagowa tayi da razane tace “ban gane ba?" Aunty Raziqa ce ta harareta tace “wannan haukan da kukeyi Kuna gwara kan mijinku babu abinda zaija muku sai raini da wulaqanta ita idan kishi yasata ta haukace ke mene hujjarki na haukacewa to wlh Abba yace ki kiyayi fushinsa sarai zaku raba hanya indai akan aure ne kowa ma yasan mijinku bai kyautaba to Amma shima ya zaiyi da zanen qaddararsa tun kafin a haifeshi sukayi alqawari da Ubangiji na duk wani Abu dazai faru dashi tun daga ranar da ya fara shaqar iskar duniya har zuwa Rana ta qarshe a rayuwarsa haka kema haka Ni'imah to akanme zaku haukatashi ku mayar dashi ball a tsakaninku ita ta bugashi nan ke ki bugashi can ko kin dauka saboda ya aureki don yana mijin aminiyarki babu alqalami tsakaninku to wlh ki dawo hayyacinki nasan iyayenmu basu barmu da jahilci ba saidai kana sane ka take sani sakarya kawai da takeson wasa da damarta"
Durqushewa tayi a gurin sosai kalaman Aunty Raziqa suka ratsata Aunty Murja ta dora da nata itama me ratsa bargo kafin Aunty Bushira ta cafe da cewa “gashi Allah ya baki mijin da yake sonki duniya ta shaida hakan Amma kinason yin sakacin sane masa kibi a sannu duk abinda hqr Bai bada ba to tashin hankali ma baya badashi dole yace yau a gdansa zaki kwana Ammi da Abba basuda damar sake ganinki wannan dalilin yasa zamu ari bakinsu muci musu danyar albasa Rafi'ah gdan yawa kika shigo Kuma gdan sarauta akwai qalubale a gabanki musamman daya kasance surukarki bata maraba da zuwanki dama yan uwan mijinki da suke daki daya dayan dakin Kuma su bama asan inda suka dosa ba Fulani Innah ce kawau take maraba dake sai mijinki to aikine ja a gabanki ki nutsu ki gane masoyi da maqiyi ki Kama masoyanki shima maqiyin karki canza Masa kallo karbeshi ki riritashi idan ya zaqe kai qararsa gurin Allah zaiyi Miki maganinsa abokiyar zamanki ma yanzu cikin sahun maqiyanki take yanzu haka mun barota tana alwashin saita kasheki saboda haka itama iya zama da ita zauna da ita da kyakkyawar zuciya zakiga ribar hakan anan duniya da gidan qarshe"
Sosai nasihar ta rinqa shigarta hadi da tsoro wannan miyagun kalmomi na Ni'imah akanta sunfi komai gigita duniyarta sun jima sosai Saida Fulani Innah ta shigo ita da Karimah sannan suka fita tana kuka tana rirriqesu sukadai samu suka tsere Haj Karimah ya ce ga hajiya Kaltume Amma batayo halinta ba tanada sanyi da sauqin hali hakan tasa sukafi dasawa da Ja'afar komai daya shafeshi baya boye Mata tana gaba gaba a cikin kowanne lamari nasa yanzun ma shine ya tasosu takanas yace su shiryata su tafi da ita gdanta bikin ma an gamashi ayi dinner gobe.
Suma nasihar suka rinqa yi Mata hade da rarrashi shikenan dai da gaske ta tabbata matarsa duk wani tsuminta da dabararta ya qare batada wani katabus kowa kalmarsa daya ta cire mgnr aminci ya riga ya rusata itama Ni'imah tayi watsi dashi ta rungume mijinta su zauna lfy, shiri sukayi Mata sosai na amaren gaske Basu gama mataba sai goma da rabi suka kamo hannunta suka fito tuni mota tayi ready kawai shiga sukayi sukadau hanyar martaba Estate suna zuwa sukayi parking suka fito da ita tanata gunjin kukanta Ammi da Abba suna fado Mata shikenan ta rabu dasu ta dawo cikin wata rudaddiyar rayuwa mara tsarin bawa zuciya farin ciki shikenan qurunqus ta tabbata kishiyar aminiyarta aminiyar da take ganin duk abinda duniya zatace bazata iya rabuwa da itaba sai gashi cikin sauqi kaidin namiji ya farraqasu har tana neman rayuwarta wani sabon kuka ya sake qwace Mata lkcn da aka haura da ita saman aka bude wani daki aka shigar da ita tare da yimata matsugunni saman wani tattausan kilishi basuyi Mata sallama ba saboda sunsan sallamar qarin tashin hankalinta zasuyi suna fitowa motar su Ni'imah na shigowa ita da wata yar yayar hajiya Sahura da tun dacan ma batason alaqar Ni'imah da Rafi'ah sunayin parking sukuma suna fita shima motarsa tana shigowa Samiha ce taja Ni'imah suka shiga ciki tana ciccijewa tana cewa “yanzu fah gurinta zai tafi ko yanzu da ita zai kwana...."
Rufe Mata baki tayi tace “ke kincika zafafawa abinda bazaije ko inaba kwana nawane amaryar maye a gabanki fah Mom tayi waya da boka na gangare yace zaiyi iyakar yinss yaga wani abu bai shiga tsakaninsu ba kuma kinsan zaiyi" ajiyar zuciya ta sauke daidai lkcn daya shigo tabisa da kallo fuskarsa babu alamun fara'a ya ajiye Mata leda ya haura sama ya jima sosai sannan ya fito ya sake wucceta har yaje bakin qofa yace “good night" wani malolo taji ya taso Mata amma data tuna tsiyar da suka kitsa sai tayi murmushi kawai ta miqe ta haura saman.
Kwanciya tayi tana saqawa da warwara inda shikuma yana fita ya bude motarsa ya dauki kayan daya siyowa amarya ya nufi bangaren gabansa har faduwa yakeyi tujarar Ni'imah bata tsoratashi kamar ta Rafi'ah itan akwai mugun kwarjini budewa yayi da addu'a ya shigà ya tsaya yana qarewa parlourn kallo yayi wani kyau an qara qawatashi sosai yaja numfashi ya haura saman kamar bangaren Ni'imah shima daki biyune a saman sai parlour qasa Kuma daki daya da kitchen da dinning area dakina biyu ya bude ya shiga ya hangeta zaune ta hade Kai da gwiwa tanata shassheqar kuka ya jima akanta yana qare Mata kallo kafin ya ajiye kayan hannunsa ya sanya hannun nasa cikin faduwar gaba ya dago fuskarta gabadaya kwalliyar dake fuskarta ta dame da hawaye yaja ajiyar zuciya yace.
“Kiyiwa Allah ki daina kukannan haka hukuncin Allah ya riga ya tabbata Rafi'ah wai ya kukeso nayine nikam?" Jan zuciya tayi ya sake gyara zamansa ya qara tallafo kanta yana me share Mata hawayen da hannunsa yace “a qa'ida tashi zakiyi muje muyi sallah mu godewa Allah duk da nasan baki murna ni inayi Amma shi aure ko bakaso rahamane da yakamata ka godewa Allah idan ya nuna maka ranar"
Da dabara yajata ta miqe sukayo alwala yajasu sukayi sallah raka'a hudu ya miqa hannu zai Kama kanta ta janye Murmushi yayi ya sake matsarta ya Kama kan nata da qarfi ya farayi Mata addu'a ya jima yanayi kafin ya gyara zamansa ya janyota jikinsa qamshinta da dumin jikinta yana ratsa nashi yanajin wata nutsuwa me gudana tana shigarsa wata qaqqarfar ajiyar zuciya ta sauke ya dago fuskarta da sauri yana mamakin dalilin tata ajiyar zuciyar cikin sanyin muryar da bata taba sanin ya mallaka ba yace “nayi Miki tanadin farin ciki dimun da'iman dawa'un My Luv don Allah ki bani hadin Kai kada ki biyewa mutane masuja da hukuncin Ubangiji inasonki zanyi hqr da komai naki kema kiyi hqr da mijinki kinji?"
Lumshe idonta tayi tanajin zagawar hannunsa a bayanta ya sauke ajiyar zuciya ya janyeta yace tashi kije kitchen ki daukomin flat na baki abinci" sunkuyar da kanta tayi yayi murmushin gefen baki yace “af sorry fah Ashe yau aikin nawane karki damu zanyi Miki komai idan kinaso har bacci ma ni zansaki kedin special ce" yana wannan mgnr ya dawo bayan ya kulle bangaren gabadaya yazo ya juye abinda yazo dashi daqyar da takurawa ya matsa mata taci hanta Tasha lemo yace “kije kiyi wanka kiyi brush inajin bacci sosai yau kunbani ciwon kai?" Batayi Masa gardama ba saboda tuna abinda ya faru dazu ta shiga bathroom din tayi brush tayi wanka ta dauro towel ta zuro alqabbarta lkcn data fito a tsaye ta tarar dashi da wata matsiyaciyar rigar bacci a hannunsa yana juyawa.
Matsawa yayi ya ajiyeta ya sanya hannu ya cirenta alqabbar ya ajiye ya Kama towel din zai cire ta riqe da sauri yaja numfashi ya miqa Mata rigar ya nuna Mata mayukan da ya fito dasu da turaruka yace “ki tabbatar kin gama kafin nazo duk abinda bakiyi ba na fito to saidai a hadu gaba bana jira idan zan kwanta" bai tsumayi amss ba ya shige bathroom din ta dauki rigar ta juyata tayi Mata kyau Amma duk rashin kunyarta bazata sata ta kwanta a daki gata gashi ba mayukan ta shafa ta fesa turarukan ta Koma kawai ta zauna ya fito ya dubeta cike da takaici gata dai kamar wayayya Amma bulkuma ce.
Baice Mata qala ba ya shiga shiryawa bayan ya gama yakai hannu ya kashe hasken ya kunna qaramin haske ya matso gabanta batare da tajishi ba ita bacci ma takeyi a zaune kawai saiji tayi yayi sama da ita ta fara zillewa tare da bude baki zatayi Masa kuka yayi saurin dora bakinsa a natan ya rufeta ruf a gadon tare da zame towel din yaja musu bargo kuka ta rinqayi masa tana gunji tanayi masa magiya..........
_Vote_
_Comments_
_Share_
_Please_
*_Ummuh Hairan_*
*_Wattpad-realfauzahtasiu_*
*_27-28_*
_____________________________
_____________________________
Daqyar da dabara saboda bayason wahalar da ita ya samu ya cimma burinsa ya saki wata ajiyar zuciya tare da dakatawa duk da dama bai yarda da mgnr su Barebari ba Amma zuciyarsa ta danyi dar saboda yasan abokin damo guza tabbas idan ta kasance aminiyar Ni'imah to komai zata iya faruwa amma sai gashi ya sameta asalin Varging duk da itama Ni'imah ya sameta da budurcinta Amma baikai qualityn na Rafi'ah ba duk masifarsa bai iya shigarta gabadaya a wannan dare ba kamar yanda ya shigi Ni'imah a daren farko.
Wani tausayinta ne ya kamashi jin yanda take kuka tana jujjuya kai tana Kiran iyayenta, ji yayi bazai iya cigababa sarai ya fahimci ba qaramar wahala zasusha ba daga ita harshi gata itanma Masha Allah akwai dauriya amma wannan abun yafi gaban dauriya saidai dabara, janye jikinsa ya farayi a hankali ya koma ya kwanta a gefenta yanajin sinadirun qaunarta yana qara zagaye duk wani bangare na jikinsa a hankali ya janyota jikinsa lkcn da wasu hawaye suka zubo masa ya rungumeta tare da hura Mata iskar bakinsa a kunnenta da haka bacci yayi ram da ita.
Ya dade yana kallonta ita komanta me kyaune yana godewa Allah da yayisa cikin mutane masu saa yasan aurenshi da ita ba qarfinsa ko isarsa bace kawai lucky ne da yake dashi a rayuwarsa da wannan bacci ya daukeshi shima, Kiran farko ta farka tajita tsam a jikinsa ta rinqa motsawa har ya tashi bai bude idonsa ba sai sakarta da yayi ta zura qafafunta qasa ta taka saiji tayi wani zugi ya ratsa qasanta ta cije ta miqa hannu ta dauko kayanta ta daura zanin a qirjinta ta rinqabin bango ta samu ta shiga bathroom din tayi wanka ta tsaftace jikinta tanajin zafi idan takai hannunta gurin hakadai ta gama ta dauro alwala ta fito.
Wardrobe ta bude wani sanyin dadi ya shigeta ganin kayanta a jere a ciki ta zaro doguwar riga da hijjab tasa ta shimfida sallaya ta tayar da sallah raka'atainul fajri tayi ta zauna tana istigfari ta yarda cewa istigfari shine mabudin dukkan wani alkhairi na duniya saboda shine abunda yake goge maka duk wani zunubinka ya kusantaka da Allah salin alin.
Ta Jima tana roqon Allah sanyi zuciya da ikon yiwa mijinta biyayya kamar yanda kowa yake horonta domin ta haqiqance aikin gama ya riga ya gama bata fatan shiga haqqinsa ko zata cutu tanason tayi Masa biyayya kamar yanda Allah ya hukunta bai isheta hujja ba a ranar qiyama tace da Allah saboda batasonsa ko don ya kasance mijin aminiyarta ne yasa taqi bin dokokin sa taqi yin biyayyar aure ba.
Miqewa yayi cike da nishadi ya samu kalar matar da yake mafarkin mallaka shekara da shekaru batada ganda wajen bautar Ubangiji tabbas Allah yanasonta shiyasa ya sanya duk wani mumini yake sonta, shima tsaftace jikinsa yayi yazo yayi salatul Fajri sannan yajasu sukayi asuba bayan sun idar kowannensu yayi azkar ya miqa Mata hannu noqewa tayi yayi murmushi yace “mafi alkhairin gaisuwa itace musabaha tare da sallama My Bestie ki saba ni gaisuwata kenan"
Yana fadin haka ya miqe ya cire doguwar rigarsa ya rage dagashi sai boxes ya matso ya dagota ya cire Mata hijjab din ya fara qoqarin cire Mata rigar ta riqe hannunsa tare da dago manyan fararen idanunta ta zubasu a kansa cikin saar lillahi suka fada cikin nasa yaji wani tartsatsin wutar qauna da feels gami da kwarjini sun kashe Masa jiki yayi kamar ya saketa ya fasa yace “akwai zafi kada ki takurawa kanki ki jure zaki dace inason kasancewa da iyalina a kowacce asuba hakan yanasa na yini cikin farin ciki don Allah kada ki batamin yinina a hankali zanbiki kedin special ce Rafi'ah"
Sosai gabanta ya tsananta faduwa tsoro ya dirar Mata tana tuno irin wahalar data dandana daren jiya idan yace zai qara yimata haka tana tunanin mutuwa zatayi.... Bai bata damar gama tunanin ba ya dauketa ya azata a gadon ya kashe musu glove din yayi musu cover da duvet babu abinda ke tashi a dakin sai shassheqar kukanta da nishinsa yanata zuba Mata sannu duk wata gaba ta jikinta Babu inda bai galabaita ba kafin ta samu yayi release ya kwanta luf a jikinta itakam tuni takai China a sume ya rinqa kwarara Mata ruwan albarka yana yabawa da baiwar da ilahi yayi Mata Saida ya saitu sannan ya fahimci halin da take ciki ya zare jikinsa a hankali daga nata ya dauko ruwa me sanyi ya rinqa shafa Mata.
Yanajin tayi ajiyar zuciya shima yayi bata bude idonta ba sai kukanta da taci gaba dayi ya shafa fuskarta yace “Sorry please zaki saba kinji matata Allah yayi miki dawwamammiyar albarka kin jiyar dani dadi yau ke ta dabance komanki dabanne" tashi yayi ya nufi bathroom ya hadanta ruwa yazo zai dauketa taqi dole yana kallonta ta zura hijjab dinta ta nufi bandakin tana dafa bango tana cije lebe yana kallonta cike da tausayi tana zuwa ta gasa jikinta tana kuka saboda azaba tayi wanka ta fito ta zauna saman drees stool ta dauki doguwar rigarta ta haye gadon daya cire bad sheet din ya shimfida wani ta kwanta tana jin dacin abubuwa da yawa a ranta da haka bacci ya dauketa batasan sanda ya dawo ba shima yayi wanka ya kwanta ya janyota baccin ya daukesu tare basu suka farka ba sai 11 saboda sunji jiki daga ita harshi inda uwargida Ni'imah takecan ta hadiyi baqin ciki da tashin hankali da asubar Mom ta kirata cikin dimuwa tace.
“Ya akayi baki binne layar da boka Na gangare ya bayar aka kawo miki ba yanzu gashinan kin rusa Mana aikinmu komai da baaso ya faru ya faru tsakaninsu" cikin gigita tace “bam.... Bangane ba naga a gabanki na binneta" dafe kai Mom tayi tace “to ya haka yanzu boka ya kirani yake fadamin yanzu aljanin daya tura ya dawo masa a galabaice ya kasa isa ga Ja'afar din duk sanda yayi yunqurin tabashi sai yaji kamar ana yayyafa masa ruwan tafasau ita Kuma Rafi'ah itama lkcn da ta tashi da asuba tayi sallah tayi addu'a shiyasa ya kasa kaiwa gareta Kinga zamufi samun sauqin tabata akanshi shidai kinsani batun yau muke barnar kudi akansa mun kasa samun galaba ba kawai aikinmu ya karkata kanta ita daya shi mu qyaleshi boka na gangare yace tabbas idan muka cika matsawa akan Ja'afar to kwabarmu zatayi ruwa domin kuwa yanada dafa'i irin nasu na gdan sarauta da baya bari su tabu"
Tuni Ni'imah ta fita daga nutsuwarta ta Kama kuka kamar wata zautacciya tana cewa “ai Kuna sane kuka bari komai ya faru tunda kunada ikon hanawa kun hanani daukar mataki a hannuna sannan Kuma kunqi dauka wlh bazan iya zama inuwa daya da Rafi'ah ba duk muna amsa sunan Matan mutum daya ba dole sai ta fita tabarmin gidana...." Katseta Mom tayi da cewa “abinda boka ya kasayi shine ke zakice zakiyi ta yaya? To bari kiji kada ma ki fara kinji dai da kunnenki abinda bokayennan uku sukace idan kika matsa kece zaki tafi kibar mata gidan ke Kuma shegiyace ke da zaki bari kishi yasa kiyi asarar zamanki matar sarki me jiran gado to tun wuri ma ki nutsu da ace zaki iyama da kin daina wannan haukan kinbi komai a sannu kin shiga jikinsu ta yanda zakifi yimusu illah"
Cikin shassheqa tace “bazan iyaba Mom ni bazan iyaba kawai ayi duk wacce zaayi na tsani Rafi'ah wlh ganinta ma zai iya sawa na kashe kaina yanzu fah banida wata taqama da zanyi Mata tasanni tasan sirrina dama da mijin zanyi Mata balli to shima tasanshi tasan komai dana sani game dashi nikam Mom bazan iya hqr da wannan baqin cikin ba...." Takaicine yasa Hajiya Sahura kashe wayarta ta rasa wacce irin ya Allah yabata da batajin shawara ana nuna Mata annabi tana rintse ido koda suke taqama da asiri wani abin sai an hada da kirsa gashi Ni'iman taqi ganewa sai shirme takeyi
Tananan zaune tanata aikin kuka ya shigo da sallamarsa mamaki ne ya kamashi ganin da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 19