kaiwa kunne ba tare da yayi magana ba, wanda ya kira sa ya ce
"Sir, mun samu information game da sender ɗin yanzu haka na tura maka everything a DM ɗinka" sai sannan ya sauke ajiyan zuciya ya ce
"Mind you, bana son jin wannan magana ya fito daga gare ka and ina son ganinsa, make sure kun kawo min shi but Everything should be done secretly please" Mutumin ya amsa da toh cike da ladabi, bayan ya katse kiran sai yanzu yaji wani kwanciyar hankali, a hankali ya miƙe ya fita.
Umma data shiga cikin gidan zuwanta kenan daga gidan Maman Azizah ta kalle Mama na zaune ta ce
"Barka da Rana Maman Abdul" wani kallo Mama ta mata cike da tsana ta ce
"Wani munafurcin ne kuma harda wani gaishe Ni? Dama magana kike min ? Ko kuma so kike ki gwaɗamin ƴarki zata shiga gidan daula ne? Toh ta shiga mu gani mana" Umma tayi murmushi ta girgiza kanta ta ce
"Allah ya baki hakuri, miji kuma wallahi duk ina musu addu'a Allah basu nagari wanda zai riƙe su da mutunci ban cire su siyama ba dan duk kallon 'ya'ya na nake musu" Mama ta ja wani dogon tsaki ta ce
"Aikin banza, Uban waya ce toh ki musu idan duniya da gaskiya ai sai kice tunda Siyama ta girme su a basa ita amma ai baki yi hakan ba, sannan kuma naga har wani tsiya kuka tsiro daga ke har 'ya'yan naki" Umma bata kara ko Uffan ba ta wuce ciki abinta
Zahra dake cin abinci ta ɗaga kai tana kallon Umma cike da takaici ta ce
"Allah Umma da baki kula wancan matar ba, bata da hankali bata iya magana ba, ji fah wata mugun fatan da take wai ayi auren a gani? Lallai ma wallahi" har ta karasa maganar Umma bata daina kallon ta cike da mamaki ba ta ce
"Sannu Zahra, ita ba Uwar ki bace da zaki ce wai wancar matan? Toh kar naji kar na gani kin sake faɗin haka, kinji?" Zahra ta ɗauke kai ta cigaba da cin abinci ta.
Honorable ya shiga ɗakin da aka ajiye Garba a ciki, fuskansa ba yabo ba fallasa ya shiga ciki ya zauna akan kujerar dake opposite da wanda Garba ke zaune amma kansa a kasa, Honorable yafi minti biyar yana kallon sa sannan yayi gyaran murya, Garba ya ɗan ɗaga kansa kaɗan ya ɗan kallesa dan yana avoiding eye contact da honorable
Honorable ya ce "Waye kai?" Garba ganin Honorable ba mutumin da zai ce zai kawo masa wasa bane yasa ya ce "Sunana Sadiq" wani murmushi honorable yayi ya ce
"Ina son sanin komai game da wanan videon da ka turomin" Garba ya ɗan kalle sa sai kuma ya sauke kansa ya ce
"Duk abinda yake ciki ba faking bane, ita ce" Honorable ya gyaɗa kai ya ce
"Are you sure?" Garba ya gyaɗa masa kai ya ce
"Eh babu tantama" Honorable ya ce
"Ina son pure gaskiyar abin nace maka? Zan iya baka kuɗin da baka yi expecting ba" Garba ya ce
"Gaskiyar kenan, yarinyar ce kowa ya santa da wannan halin" honorable ya ce
"Then Meyasa katuramin? Did I request?" Ya girgiza masa kai ya ce
"But I'm trying to protect you ne bana son ka faɗa tarkonta" wani murmushi mai wuyar fassarawa yayi sannan ya miƙe ya ce
"Good for you, Weldon" daga haka honorable ya fita a wajan a bakin kofar ga sojoji suna tsaye tare da wasu police, ganin Honorable suka ja baya cike da girmamawa, yana kallonsu ya ce
"Zaku iya aikin ku, make sure har sai ya faɗi komai, dan naga yana son playing ɗina" daga haka ya wuce motarsa yana kara jinjina alamarin a ransa, fuskan kam nata ne amma yadda yaga body ɗin ko kaɗan baiyi kama da nata ba dan wancan jikin fat ne hakan ya tabbatar masa ba ita bane dan yasan Azrah bata da wani kiɓa.
Duk yadda sojojin nan suko so ya faɗa musu gaskiya ki yayi daga karshe suka hau dukansa babu ji babu gani, ganin akan ɗan 50k ɗin da yayi aiki wanda karshe ma bashi kaɗai ya ci kuɗin ba har wanda ya haɗa masa videon suka raba amma gashi akan sa ana neman a halakasa yasa ya fara ihu yana zai faɗa, suka tsaya da dukansa suna kallon sa suka ce
"Waya sa ka? Kuma videon waye wannan" yana haki ya fara magana ga hawayen daya ke sintiri ya ce "Ba videon ta bane haɗawa aka yi" wani soja ya haɗe rai ya ce
"Who?" Garba ya fara girgiza kai alamar suyi hakuri, ganin zasu cigaba da jibgansa yasa ya fara ihuun zai yi magana, nan take ya faɗa musu plan ɗin wanda suka saka sa aiki, wani police ya fita waje nan ya sanar da Honorable, honorable ya ce ayi arresting ɗinsu suma
Police station suka wuce nan suka ɗebo rundunar polisawa wanda sai ka ɗauka yaki za'a tafi ganin su ma kaɗai sai ya tsinkar maka da zuciya, harda polisawa Mata suka ɗauka, duk suka shiga motar suka kama hanyar gidan su Mama..
Maman Asabe dake tsakar gidanta tana daka ga kuma Yaranta suna gefe suna wanki suka ji an baka kofar gidan da sauri ta ɗago kai tana kallon polisawan da bata san adadin su ba suka cuso kai kai tsaye, ta fara ja da baya Yaranta ma duk cike da tsoro suke kallonsu wani police yayi magana da tsawa ana tambayar waye Maman Asabe, nan duk matan gidan suka dinga fitowa daga dakin su abinka da gidan yawa, ana kallon abinda yake faruwa, wani police ya shigo da Garba wanda duk jikinsa a fashe bakinsa jini ganin haka zuciyarta ya tsinke, nuna musu ita yayi wanda take aka saka mata ankwa tana kuka tana rokon su ba ita bace wallahi Mama ne wata police ta ɗauke ta da mari wanda sai data ga stars ba shiri tayi shiru Yaranta suka fara kuka, cikin unguwarsu duk aka fito ana son ganin meke faruwa suka fito da ita suka wurga ta bayan motar cike da kaskanci kuma da rashin tausayi, Asabe ta fita da gudu tayi hanyar wajan sana'an Baban su, su kuma suka ja motarsu suka bar unguwar wanda tuni an fara magana kasa kasa, Maman Asabe banda kuka mai tsuma rai babu abinda take yi, ta tsinewa Mama yafi a kirga...
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL* (LABULEN SIRRI)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 16: The Weight of Shame
Motocin ƴan sanda ne suka faka a daidai kofar gidan Bappah, yaran unguwar duk suka fito harda manya dan ganin meke faruwa, haka ƴan sandan nan maza da mata suka sauka zuwa cikin gidan, banka kofar su da bata da karfi suka yi, Umma dake compound tana alwala ta ɗaga kai tana kallonsu gyara mayafinta tayi tana kallonsu ganin sun nufe ta...
Yara da har sun fesawa Mama cewa ƴan sanda sun cika layinsu kuma jin sun nufi sashin Umma yasa ta fito tana murmushin mugunta tana son taga komai da za'a yi ayi a gabanta
Babu rahama ko alamun wasa a fuskokinsu, ɗaya daga cikin su ya ce
"Wacece Uwani?" Umma da kalli Mama da fitowan ta kenan bata bata ma ji su ba, a hankali tana kallon polisawan ta ce
"Gaskiya ban santa ba" wani tsawa suka daka mata dan they're very sure gidan ne la'akari da cewa Maman Asabe ce ta kawo su, Zahra ce ta fito tana kallonsu sai kuma ta kalli Mama dake murmushin mugunta irin polisawa suna ma Umma tsawa, a hankali ta ce musu
"Sir, gata can wanda kuke neman, itace Uwani" juyawa suka yi, ita dai Umma ta zama speechless, Mama kuma ba jin Zahra ta yi ba kawai gani tayi ƴan sandan sun nufeta kamar ta gudu amma ta dake tsoron kar ace bata da gaskiya ko kuma a harɓe ta, wani kallo suke mata wani ya ce
"Ke ce Uwani?" Mama ta gyaɗa kai zuciyarta na bugawa ta ce
"Eh nice... Ohh A'a bani bace ashe.." wani kallo wata ɗaya daga cikin polisawan kawai ta kama hannun Mama ta dasa mata anƙo, Mama ta fara magana tana cewa
"Wannan wani irin wulakanci ne... Mutum ba tare da yasan laifin da yayi ba sai ku kama sa? To ku jira mana mijina ya dawo" wani kallo Wani police ya mata wanda yasa ta haɗiye maganganunsa janta matar take yi har ta fita da ita waje, ai nan da nan Mama taji wani zufar ya sake gangaro mata sakamakon ido huɗu da tayi da Maman Asabe, cike da kaskanci suka wurga ta cikin motar ga ƴan unguwar duk an taru ana kallonsu.....
Wurin da aka kai su Mama ba wurin da ake kai masu laifi bane kawai, amma wurin da ake ƙoƙarin murkushe mutumtaka ne, Su Mama suna zaune a cikin Naman Asabe harta gaji da tsinewa Mama tayi shiru, wajan banda zarni babu abinda yake yi, Wani ɗan sanda yana tsaye a gabansu da duk da akwai noise mask a fuskar sa amma ya daura hannunsa akan hancinsa kamar wanda yake jin warin, yana kallon su Mama da idanu masu cike da raini ya ce
"Ku ne kuke daukar hoton wata Hajiya ku saka mata fuskar karya, kuna tunanin zaku tsallake hakan ne? Lallai ba ku san waye Honorable ba ne yasa kuka fara wannan jahilcin naku, wannan ba a film bane ko littafi, it's reality ne"
Mama ta sunkuyar da kanta ba don tana jin kunya ba, sai don takaici, tana jin kamar ta tashi ta zazzaga masa zagi jin wai Hajiya ma yake kiran Azrah, amma ta san hakan ba zai kawo mata mafita ba sai ma ta karama kanta wani laifi
Daga nan aka fitar da su zuwa wani ɗakin na daban, can suka wuni. Ba abinci, ba ruwa. Maman Asabe tana tsaye akan Mama ta dinga tsinewa mata tana faɗin
"Ina zaman zamana gashi kun jefa ni cikin ukubar bala'i, yanzu na koma gida nace wa Naman Asabe mene? Yanda yasha zamini kunne da ke idan ya sake Ni ina zan shige Ni asu?"
Mama ba tace komai mata komai ba, tana jin yunwa amma yunwar ba ta tada mata hankali kamar kalmomin tsinuwa da wulakanci da Maman Asabe ke zuba mata ba
Meanwhile..... Umma tana tsaye da rashin natsuwa, Idanunta har jaa yayi saboda tashin hankali tana jin kamar zata yi kuka tana kallon Zahra ta ce
"Zahra je ki kira Bappahn ku" Zahra ta taɓe baki sannan ta ɗauki mayafinta ta nufi hanyar inda Bappah ke zama, tun kafin Zahra ta isa, ta ci karo da shi a hanya, yana dawowa gida, fuskarsa cike da damuwa.
"Bappah!" Zahra ta ce da sauri "An kama Mama da Maman Asabe an kaisu station!"
"Me?" Bappah ya tsaya cak yana kallon Zahra da idanu masu cike da tambaya
"Wace irin magana ce haka? Station? Ina ne? Dama da akace polisawa sun taru kofar gida kamasu kenan akayi ko ya? Sai kuma ya kama tafiya da sauri har haɗe kafa yake yi ya isa gida ga Zahra dake binsa a baya
Anan compound yaga Umma na tsaye har sannan ga kuma Azrah dake zaune itama tayi tagumi, anan Muna ta fara sanar da Bappah abinda idanunta suka sani
Suna cikin wannan ruɗanin ne sai ga sallamar wani mutum, Mijin Maman Asabe ne, sau kuma.da Asaben daga bayansa, ya karasa ya mikawa Bappah sannan ya fara masa magana
"Ai wallahi ni banga laifin matarka ba, amma nasan halin Maman Asabe, zata iya shiga rigima fiye da haka, ita dan haka kullum a garin tara mutane suke jefa ta cikin masifa" inji mijin nata
Asabe dai na gefe tana ji tana kallon su, ba ta ce uffan ba sai ga su Siyama da Habibah sun shigo gida da sauri, fuskokinsu cike da damuwa, Asabe ta watsa musu wani banzan kallo cike da tsana sannan ta juya zata koma gidan su
Bappah da Mijin Maman Asabe suka tashi suka kama hanyar station ɗin unguwar su domin su san inda aka kaisu, Amma ba'a kai su station na unguwar tasu ba, Sun zagaya kusan rabin stations ɗin garin amma basu same su a can ba
Daukar washegari da kyar suka samu inda suke da taimakon wani police ɗin, Su Mama suna cikin yanayi mai raɗaɗi ba duka aka musu ba, amma sun sha wahala ba kaɗan ba wulakanci, yunwa, rashin barci, da tsoro Lokacin da Bappah ya tambayi bail, aka ce masa
"Bailing ɗinsu? Haba ku kuwa duk girman laifin nan, toh honorable bai yarda a bada bailing dinsu ga kowa ba" with shock Bappah yake kallon sa ya ce
"Honorable kuma?" Police ɗin ya gyada masa kai yace "Eh shi, yarinyar da zai aura ne suka ɗaura hotonta akan na wata matan banza wanda sun tura masa hakan kuma zai iya ɓata masa kujerar takaransa...
Bayan fitowar Bappah da mijin Maman Asabe daga ofishin 'yan sanda, jikin su babu ƙwari, ya gama sanyi wanda duk basu yi sammanin haka bane abun ya faru, haka suka fito kowannensu na dauke da fuskarsu mai nauyin laifin da suka aikata, Suna ƙoƙarin danne kunya da takaici dan ba kaɗan ba sun dasu kunya...
Bayan su Mama sunyi laushi iya laushi ga abincin kuma kamar yadda kasa ma karamin yaro zaka bada haka suke sako musu, can kusa da Magrib sai ga Honorable da kansa ya iso ofishin 'yan sandan fuskar sa ɗauke da ƙiyayya da mamaki....
"Ina mamakin ku akan me zaku ɗauki hoton mutum ku ɗora masa karyar da bata da tushe? Wannan fa cin mutunci ne! Wannan kuma ɓata wa mutum sunane" Honorable ya faɗa da murya mai ƙarfi
Mama da sauri ta furta "Wallahi sharrin shaiɗan ne ya yi mana tasiri"
Maman Asabe kuwa cikin rawar murya tace
"Ni Mama Abdul ce ta saka ni, ita ce ta ja ni cikin wannan magana da masifar, amma a gafarta mana yallabai"
Garba kam ya zauna ne tamkar ba a kansa ake magana ba ko kallo bai yi ba balle awa ran zai ce wani abun
Honorable ya ce "Me dalilinku na hakan kawai nake so baki? Duk shiru suka yi sun gagara basa amsa
Honorable ya mike fuska a daure ya ce "Na tabbata koma da ƴaƴa kuma yanzu ace ma naku aka yi wa haka zaku ji daɗi?"
Suka fara basa hakuri da neman afuwa amma ko kallo bai sake yi musu ba, ya juya ya bar wurin cike da taimacinsu
Da yamma Bappah ya fito daga ɗakinsa yana bin compound ɗin da kallo wanda yana son tabbatar da babu kowa, bakin kofa ya nuna yayi dialing ana honorable yana sake kaka cikin gida to be sure babu wanda zaiji wyan, Honorable na ɗaukawa cikin sigar natsuwa da tawali’u, ya fara da bashi hakuri
"Alhaji ina neman Alfarman mana" Honorable ya ce
"Ina jin ka Baba, menene? Bqppah ya ce
"Wannan matan da kasa aka kama da ɗayan Mata ta ce ka tausaya mata ka sake su, in shaa Allah hakan ba zai kara faruwa ba"
Honorable ya yi shiru na ɗan wani lokaci sannan ya ce
"Shikenan Bqppah zan sa a sake su amma saboda kai, kuma ban yaɓa dauka ai ɗayan matar ka bace" bayan gama.wayansu har sannan honorable bai daina jinjina wannan labarin ba...
Bayan wayar Honorable ya kira ofishin ‘yan sanda, ya bada umarni da a sako su Mama da Maman Asabe, amma kafin hakan, sai da suka sha masifa da gargaɗi mai tsanani daga hannun jami'an tsaro, an sake su ne kawai saboda girmamawar da Honorable ke wa Bappah, ba don suna da wani cancanta ba.
Rayuwar da suka yi a ɗan wannan wajan banda faɗa babu abinda suke yi kamar basu san junansu ba haka suka koma
Da suka dawo gida, Bqppah ya ɗaga kai yana ma Mama wani kallon tsana ya fara mata masifa kamar zai dake ta, ga taikaicinsa su Habibah da Siyama da yanzu sun ma daina zaman gidan, yana kallon Mama wani one look ta masa wanda ba shiri yayi sitt
Bayan magariba, jama'a suka fara shiga yin ja je, wannan yana fita wani zai shigo kamar wanda suke zuwa karɓan sadaqa tsabar gulma
Habibah da Siyama ne suka kulle ƙofar gidan suna masiyan gadon
"Gulma za ta kashe m
su, kai Allah wadaran naka ya lalace"
A bangaren Maman Asabe kuwa tunda tasa kafarta a cikin gidan mijinta ya fusata ƙwarai, har sai da ya kusa duka ta saboda fadan da yake mata
"Sau nawa nake ce muku bana son kallon matar nan kuma mu'amala amma bakya ji ko? Ga irinta ai nan, Kin jawo mini kunya!" Cewar mijinta
A gidan honorable komai na tafiya lafiya a ido, amma a zuciyar uwargidan nasa kamar wacca ake hura wuta. Uwargidan Honorable Hajiya Maryam,
ta saba ganin Mijinta a cikin natsuwa da kamun kai, A.amma kwanan nan tana jin canji wani abu da bata iya fassara ba
A daren ranan, matarsa ta biyu, Hajiya Rabi, ta shigo dakin uwargida da fuskar da ke ɗauke da wani nauyin magana. Ta zauna a gefen katifa, tana kallon uwargida da murmushin karya
"Anty... wallahi ban san ko zan faɗa miki ba, amma zuciyata ba ta barni lafiya, sau na huta brain ɗina zai dawo
Hajiya Maryam ta ɗago kai
"Me ke damunki haka Rabi?"
Rabi ta saki ajiyar zuciya. "Wallahi naji wata magana ce da ban jin ya kamata ki zauna baki sani ba, Sun ce mijinmu yana shirin sake aure shi yasa kwana biyu yake diverting zama gida ga kuma changes da suke ganinsa da shi,
Maryam ta ɗan yi dariya mai taushi
"Wannan magana ba sabuwa bace Miji namiji ne, ai..."
Sai Rabi ta katseta da gaggawa. "A'a Anty ba kamar sauran zance ba Wannan karon gaskiya ne,.kuma yarinyar kamar ita tayi kanta
Fuskar Maryam ta sauya. Wannan karon zancen ya ɗan dame ta "Yanzu ke faɗin haka? Wato magana ce da har take da tushe?"
"Eh kuma yarinyar kamar ita tayi kanta, Ni wallahi duk na tsorata"
Daga nan Hajiya Maryam tasa masa ido sosai nan taga yadda maganar Rabi gaskiya ne
Ba tare da ɓata lokaci ba, sai ta kira wata amintacciyar kawarta da ke da alaƙa da wani jami’in bincike, ta roƙe ta da a taimaka a gano wacece wannan yarinyar da ake danganta da mijinta, tace a tantance komai: asali, danginta, makarantar ta, da inda take zuwa.
"Ni ba zan zauna a raina ni ba dole kuma kowa ya bani respect Dina kuma ya gama aure a duniya" cewar Hajiya Maryam,
"Ko aure zai yi, dole na san wa zai aura"
A haka aka fara bincike cikin sirri, aka sa ido, ana bibiyar yarinyar da aka ji ana ambata. Zancen ya fara ɗaukar zafi, yayinda masu bincike suna yara duk wata information suna adana musu
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.*BEYOND THE VEIL* (LABULEN SIRRI)
YOTA ID/025
Wattpad © Jiddatulkhayr writes
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 17: The Silent Thunder
Wani babban parlon ne wanda ke ɗauke da duk wata kayan more rayuwa ta duniya, wata mata ce ke zaune a kan wata sofa tana ƙaɗa kafa har sannan zuciyar ta bata daina tafarfasa ba, tana danna wayar hannunta ne ba tare data san me take yi ba, wata mata ce daga cikin wanda ta saka su mata aiki ne ta shigo cikin nutsuwa amma idonta na ɗauke da wani sirri mai nauyi tana murmushi dan tasan Hajiya zata ji daɗin wannan samo dukkanin bayanan akan wannan yarinyar amma kuma ba lallai ta iya jura jin menene ba
"Barka da zuwa" Hajiya ta faɗa cikin kulawa
"Nagode Uwargida a gidan honorable, na samo miki dukkannin bayanan amma... kuma sai kin daure zuciyarki" ta kare maganar tana avoiding eye contact da Hajiya
Hajiya ta ɗaga gira tana kallonta alamun sauraro
Sai matan ta miƙa mata wani envelope dake dauke da wasu pictures na wata yarinya da kuma rubuce da bayanai ta ce
"Sunanta Azrah Matar da aka cewa Honorable yana da niyyar aura kenan Hajiya, amma karyan su tasha karya, na tura ƴan leƙe-leƙe sun binciko min cikakken bayani akanta"
Hajiya ta karɓi takardun tana duba hoton Azrah, lokacin da tayi ido huɗu da hoton nan take jikinta ya ɗaura rawa, numfashinta ya fara seizing, zuciyarta na bugawa da ƙarfi,
Fuskarta ta cika da mamaki da kuma tsoro da lokaci guda ya kamata
"Wannan... irin wannan kyau... balarabiya ce ko?!" Hajiya Maryam tayi tambayar ba tare data san ta furta hakan ba
"A'a duk da dai ance kamar ita mahaifiyar yarinyar ba'a san assalinta ba amma tabbas mahaifinta ɗan nan Katsina ne, mazauniyar kofar Marusa a Ghetto area suke ma Hajiya"
Kusan saura kaɗan Hajiya ta sake fisari a jikinta, da kyar ta miƙe ta nufi ɗakinta ta kasa tsayuwa ta kasa kwanciya, ta kasa zaune zuciyarta na cike da ɓacin rai da mamaki da kuma kishi daya cika shi fam
Kamar wanda aka tsikara sai ta miƙe da sauri ta fara shiri, cikin fushi ta saka kaya ko ɗaura ɗankwali bata yi ba ta fita zuwa compound da sauri wajan motarta ta nufa ta shiga ciki har wani jiri take ji amma ta tada motar ta figa a mugun guje kai tsaye gidan co-wife ɗinta ta nufa
Tana parking ta nufa entrance ɗin ba tare data tsaya ta rufe motar ba ko ta dawo da nutsuwarta ba, tin daga balcony ta fara kwaila mata kira, da sauri Hajiya Rabi ta fito tana kallon kishiyarta da mamaki, tun kafin tayi magana ta katse ta ta ce
"Kin ga wacce Honorable ke shirin aura? Kin san daga ina take? Wallahi wannan ai tozarci ne!" Hajiya Rabi ta tsaya cak yana kallon ta da mamaki sai kuma ta ce
"Babban Macece kenan zai aura?" Hajiya Rabi ma ta mata wani kallo ta ce
"Take this and see" ta kare mata maganar tana miƙa mata hotunan Azrah,wani zaro ido tayi tana kallonta bayan ta karɓi hoton itama tana kallo, murmushin takaici tayi ta ce
"Ai bamu ga ta zama ba, ina mu ina bari ya auro mana wannan? Ai mun shiga uku idan har ya aureta mulakanci kuma sai wanda muka gani" Hajiya Maryam ta ce
"Ke duk ba wannan ba, tashi zakiyi mu je mu tabbatar da gaskiyar lamarin... sannan mu bawa yarinyar concrete warning tunda daga ghetto area take ba abinda zasu iya yi, shi kuma tunda har bazai tsayar da hankalinsa ba munsan wata idan bai sani ba, ita kuma zata gane tsakanin mata akwai ruwan zafi".
A haka Hajiya ta sake sa aka kawo mata wani info wanda yayi daidai dana farkon, tana gama karantawa ta mikawa co-wife dinta ta ce
"To yanzu kin ga da idonki ko? Nace miki komai haka ne ba wata tantama, ta shi mu je, yau zasu gane akwai banbanci tsakanin mai power da wanda bai san ma me powern ba"
Hajiya da co-wife ɗinta ba su yi wata-wata ba suka nufi unguwar Kofar Marusa, Motarsu mai tsadan gaske na karaya ƙasa a cikin layin ghetto, wanda ba kasafai ake ganin irinta ba a wannan unguwar, wanda tun shigowar su layin yara suka fara bin motar da gudu suna kallon motar
A bakin ƙofar gidansu Azrah suka parka motar, Hajiya ta fara sauka sannan Hajiya Rabi karewa layin suke da kallo, kallon ma kallon kƴama
Kamar wanda ba zasu taka kasa ba suka nufi kofar gidan da kakkausar murya Hajiya ta fara sallama
"Assalamu Alaikum!"
Zahra ce ta fito tana daure da darduma a kafaɗa, alamar ta idar da sallah kenan, ta zare ido ganin manyan mata biyu cikin shigar masu hali da izza, tana kallon su ta ce
"Wa'alaikumus Salam Ina wuni?" Duk kallon Zahra suke wanda itama ba maraba da Azrah sai dai Azrah ta fita haske sannan ta fi tsayi
"Yauwa, Ina ɗakin Maman Azrah?" Cewar Hajiya ba tare da murmushi ba saima wani kallo data ke bin compound ɗin da shi
Zahra ta nuna musu ɗakin da hannu, ba tare da wani jinkiri ba suka shiga
Umma ce ta tarbe su da murmushi duk da bata san su ba
"Sannu da zuwa, ga waje ku zauna" ta yi maganar tana shimfiɗa musu dadduma, Umma ta ɗago ganin ta basu wajan zama amma basu zauna ba, cike da wulakanci Hajiya ta ce
"Barkanmu dai, amma ba zaman lafiya ya kawo mu ba, mun zo ne kashedi ma ƴarki Azrah" Hajiya Rabi ta karɓe ta
"Mun samu labari cewa diyarki Azrah na da alaƙa da mijinmu Honorable, har Office ɗinsa take binsa, toh muna baki kashedi da gargaɗi ta rabu da shi tun kafin lamari ya lalace muku, Kuma ku gaya mata cewa mu
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 10 Chapter of 12