unguwarsu da kwatancin gidan su
Ya ɗan yi shiru sai can kuma ya ce
"You're brave Azrah, You could've ended up in something else, but you're still focused" ta ce
"Na zaɓi mutunci sir, Ko da wahala ta min yawa, nasan one day definitely zanji daɗin hakan" Ya murmusa
"I respect that! From today, I'll personally support your education in shaa Allah, But I also want you to report back after your exams kunji?" Idanunta cike da hawaye ta ce
"Nagode sosai sir, Allah ya saka da Alkhairi, ya kare ka"
Ya miƙa mata kuɗi
"This is for your Tp"
Ta karɓa da duka hannayenta biyu tana jin babu irin kalmomin da zata iya masa godiya da shi, tana share hawayenta
Ya miƙe tsaye yana kallonta "Ill call your mom, Take care"
Tunda Azrah ta fito daga ciki gani tayi kamar a mafarki ne dan she never expect this, bata taɓa kawo hakan ba balle harta shiga ciki, ta sake share hawayen ta for the countless times ta fito, tana fita ta kalli wani taxi ganin kuɗin da ya bata dayawa ne kawai ta tsare sa ta faɗa masa inda zai kaita sannan ta shiga, har suka isa unguwarsu bata san sun iso ba sbd yadda ta faɗa tunani.
Ko da kuwa bata samu kuɗin candy kai tsaye ba, amma yadda Honorable Ibrahim ya saurareta da mutunci da kuma yadda ya karɓi lambar Umma ya tabbatar mata da cewa akwai hope
Tana shiga cikin layin su Zahra ce ta fara ganinta daga bakin titi wacca ta fita mikawa wani yaro gawayin daya tsaya, da gudu ta nufe ta
"Yaya Azrah! Sannu da zuwa! Ya akayi? Ina kika je? Naga is like your happy" duk ta jero mata waɗannan tambayoyin lokaci guda
Azrah ta janye mayafinta ya ɗan koma kafaɗarta, tana sauke ajiyar zuciya ta ce
"Bari mu shiga cikin gida mana na huta kadan, sai na faɗa miki" Azrah na gaba Zahra na Binta a baya suka shiga
Zuciyar Umma cike da tuhuma da mamaki tana kallon Azrah daga jikin kofa data fito daga ban ɗaki, zuciyarta na bugawa ta wuce ɗaki alamar bata so suyi maganar a tsakar gidan hakan yasa su Azrah binta a baya tana shiga ta juyo tana kallon Azrah ta ce
"Ina kika je Azrah?" Azrah ta zauna tana sauke numfashi tana kallon Umma cike da nutsuwa ta gaishe da Umma ta amsa
"Azrah daga ina kike haka?" Umma ta kuma jefa mata tambayar, Azrah ta ce
"Umma daga Government house nake" ta karasa maganar tana ciro bunch of money da yana bata, a take Zahra da Umma suka haɗa bakin cewa
"Daga Government house kuma?" Abin yaso bata dariya ta ce "Eh daga can nake"
Azrah ta zauna, ta ajiye jakkanta sannan ta fara bayani, Cikakken bayani, tun daga shigarta Government House, drama da securities, zuwa taronta da Honorable Ibrahim, Sai da ta kai karshe sannan ta ce
"Shine ya tambaye ni tarihin rayuwata, ya karɓi lambar ki... ya ce zai kira, idan Allah Ya yarda, zai taimaka"
Umma ta zuba mata ido, tana mamakin yadda ‘yar cikin cikinta ke da wannan ƙarfin hali da hikima, Kafin tace komai Zahra ta ce
"Yaya Azrah... Gaskiya I salute ur courage, yanzu kenan zakiyi waec da necon cikin kwanciyar hankali, Allah saka masa"
Azrah ta ce "Ba mu tabbata ba har yanzu... amma ko bai bani ba ace ma bai kira ba ai kuɗin daya bani na mota dashi zan yi amfani dan wallahi nasan nan ya kusa 80k"
Umma ta zuba mata idanu, ba don tayi shakkar Honorable ɗin ba, sai dai fargabar yadda duniya take a lalalce ta ce
"Allah Ya kawo mafita, idan har da manufa ɗaya yake son taimaka miki Allah basa iko, Amma ina fatan babu wani abu da kikayi wanda zai kawo mana matsala...?
Azrah ta girgiza kai "Wallahi babu Umma"
Umma ta sauke ajiyar zuciya "To Allah Ya saka masa, ke kuma Allah miki Albarka"
A bangaren Honorable Faruq...
Bayan tafiyar Azrah da yamma Honorable ya kira lambar da aka bashi, Umma ce ta ɗauki wayan ta kai kunne
"Assalamu Alaikum, ni Honorable Ibrahim ne daga Government House. Ina magana ne akan ‘yar ku Azrah"
Umma ta ce cikin girmamawa "Wa'alaikumus Salam, eh ranka shi dade, Allah ya saka da Alkhairi, ta dawo gida ai tun ɗazu"
"Na kira ne in tabbatar muku da cewa za mu taimaka mata da kuɗin candy. Ba za mu bari irin azamar da take da ita ta tafi a banza ba, sannan zanyi kokarin ganin sunanta ya shiga cikin wanda zasu samu scholarship da yarda Ubangiji"
Umma ta ji kamar ta saki ihu dan murna, idonta ya fara tara kwalla, tana fara masa godiya ya katse ta da wuri
Ya ce "Ku ci gaba da tarbiyyarta yadda kuke yi, sannan ku barta akan dream ɗinta, Karku hanata tunda har ta iya neman na kanta kuma ta iya ɗaukan karatun ta"
Bayan sun gama magana yace su turo da acc details wanda ba ɓata lokaci suka tura amma sai da suka sha mamaki ganin ya turo 500k instead 50k da suke nema.
Da daddare... acikin ɗaki Zahra da Azrah suna zaune a saman katifar su, Azrah ta jingina da bango Zahra na kallonta kamar zata yi tambaya can ta kasa daurewa ta ce
"Yaya... kina tunanin yanzu rayuwarmu zata fara sauyawa ne?'
Azrah ta ce da sanyin muryarta
"Zahra wallahi ni ma haka nake tunani kuma nake fata, Amma ba zan sa rai sosai"
Zahra ta langwabar da kanta, tana murmushin da ke nuna kwanciyar hankali
Washegari da safe...
Duk suna zaune bayan sun gama breakfast suna lissafin yadda zasu yi, Azrah kuma tana so su gama ta shirya zuwa makaranta kawai wayan Umma yayi ringing, Zahra ta daga da sauri tana mikawa Umma ta ce "Umma honorable ne"
Umma ta ɗauka ta gashe sa ya amsa cike da girmamawa yace
"Mun tura details ɗinta zuwa Government Education Board. Zata iya zuwa ta cike form ɗinta da gaggawa idan waec ko neco ya fito zata kai musu anan ne scholarship dinta zasu bata, amma zata jana Jamb da farko"
Umma ta fashe da kukan, su Azrah suna jira ta gama ta basu bayani saboda su basu jin komai amma yanayin umma kuma sun san wani abunne
Wani mako bayan nan...
Azrah ta kammala rijistar candy da taimakon honorable Kamar mafarki, amma gaskiya ce Haka rayuwarta ta fara ɗan buɗewa as not expected.
#Jiddatulkhayr
08110615256
https://whatsapp.com/channel/0029Vaq17Di3WHTWv5ju0w3Z
*BEYOND THE VEIL*(LABULEN SIRRIN)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 11: A visit that stirred Hearts
Tun bayan kiran da Honorable Ibrahim ya yi wa Umma da cike da mutunci, zuciyarsa ta kasa samun nutsuwa, ya zauna a ofishinsa yana tunanin Azrah yadda take magana da nutsuwa, kyakkyawan tarbiyyarta, tausayin da ke cikin idonta duk da irin mawuyacin halin da take ciki. Ba kawai ya ji tausayinta ba ya fara jin wani abu fiye da haka.
Yana komawa gida daren nan, maimakon ya wuce kai tsaye ya shiga gida as usual, ya zauna a cikin motarsa yana kallon hoton daya ɗauka da camera ɗin CCTV lokacin da take zaune a office ɗin
"Wannan yarinya... me ke damunta har haka? Kuma me yasa na kasa mantawa da ita tun jiya?" Yayi maganarsa shi kaɗai kamar yana jiran jin amsan daga garesa kuma.
Zuciyarsa na masa tambayoyi da yawa, A daren ranar bai samu bacci ba cos duk lokacin da ya rufe ido, sai hoton Azrah ya bayyana a zuciyarsa. Yanzu kam ya sani ba iya tausayi ba, zuciyarsa ta fara jan shi zuwa wani sabon yanayi, Ya fara tunanin "Me zai hana in taimaka mata gaba ɗaya? Ko... ko kuwa aure... ?".
Washegari....
Azrah na zaune a kitchen tana girkin abincin rana da misalin karfe 10 na safe, tana so ta kammala ta taje gidansu Fatima dan karɓan wasu takaddun da zasu fara na jarabawar candy wanda yanzu tana hundred percent assurance zata zana both waec da neco saboda ko bata ci candy ba tana da kuɗin da zata biyawa kanta balle ma bata fatan hakan, muryan Maman asabe da Mama taji a compound ɗin suna magana Mama ta ce
"Ke Ni yanzu abin nasu ma ya fara tsorata ni, Ni fah kullum idan aka ga yarana sai ace yaran wancan matar ne masu tarbiyya amma banda nawa dan suna zuwa tallah, amma wallahi Naman Asabe ina faɗa miki lafiyayyan abinci suke ci kuma ba Malam bane ya tsaya musu" Naman asabe ta riƙe haɓa ta ce
"Iko sai Allah, toh daga ina kenan suke samun kuɗin da suke siyan kayan abinci ni Uwani?" Mama na kwashe abincin sana'arta ta ce
"Yanzu ke har sai nace muku gashi? Yarinyar da ake ganin tafi kowa kyau a unguwar mana ita yasan inda take zuwa suke bata kuɗi" Maman asabe ta riƙe haɓa ta ce
"Kice yanzu dai ker take kallon mu?" Mama ta ce
"Tun yaushe kuma, ranan fah haka wani ya kawo mata kaya cikin Ghana, gashi bata wanka sai da sabulun turawan nan, ke baki ganin yadda jikinta yake wani sheki Ni" Maman asabe ta ce
"Bariki, wato shi yasa take jin tafi karfin yaranmu siyasa ko magana bata musu" Mama tayi wani humming,
Zahra ta fito a zuciye ta karasa inda Azrah take zaune ta ce
"Anty Zahra tashi ki shiga ciki zan karasa" Azrah ta Kalleta ta ce
"Ki bari zan karasa kawai, though nagama ai" ta sauke stew ɗin kan wutan tana mikawa Zahra kulan abincin, ta karbi kulan ko kallon su Mama batayi ba balle su sa ran gaishe su, tana hanyar ɗakin Umma ta ce
"Kai jahilci ma bai yi ba, Yaya kiyi sauri kizo ki tafi kinsan baki da lokacin ɓatawa" daga Mama har Maman asabe suka ɗaga kai suna kallon Zahra da har ta shige ɗakin Umma, Mama ta miƙe ta wulwulo wani ashar ta jefa mata ba, ta fara banbamin masifa da ashar
Azrah ta wuce su ko kallon inda suke bata yi ba, dan ita tana mamakin hali irin na Zahra, harta shiga ɗakin Umma bata Kalle su ba, Umma ta ce
"Zahra nace ki fita ki basu hakuri, basu haife ki bane da zaki jefa musu magana?" Zahra ta ɓata fuska ta ce
"Umma kinji na zage su dan Allah? Ko kinji na kira sunan wani? Kawai fa ina magana da Yaya ne nace ta shigo ciki saboda jahilci beyi ba"
Azrah ta zauna ta ce "it's okay Umma, yanzu idan ta fita maganar kuma zai dawo sabo saboda kinsan ba zasu kyaleta ba"
Zahra ta miƙe ta wuce ciki, ba tare data kalli Umma ba dan wallahi Umma ne ke taka mata burki
Kamar yadda kwana biyu honorable ya kasa manta Azrah haka yau ma har ya isa ofis, amma ba zai iya aiki yadda ya saba ba, yana jinsa very weak, kawai ya ɗauki waya ya kira wani amininsa a Education Board, yana ɗaga wa bayan sun gaisa ya ce
"Please idan yarinyar nan ta sake zuwa akan cika scholarship ɗin da nace a bata pls a sanar dani, Kuma ku tabbatar bata shiga wata matsala ko cin mutunci a kowanne mataki, sannan bana bukatar wani daga cikin staff ya nema mata magana idan ba abinda ya shafi cika maganar scholarship ɗin bane"
Mutumin ya yi mamaki, sai dai baice komai ba a haka suka yi sallama.
Kwana biyu bayan haka...
Rayuwa na tafiya musu yadda suke so, Alhamdulillah yanzu ba zasu ce ga wani abu da suke bukata ba, sun bunƙasa sana'ar su ba tare da sun dogara da Bappah ba.
Azrah tana can jikin katifa tana gyara jaridun da suka tsufa na Bappah tare da wasu old books ɗinsa da sometimes take karantawa, Zahra ta shigo tana kallon Azrah ta ce
"Aunt Azrah! Umma na kiran ki"
Tayi saurin mike wa, zuciyarta na tafi ya fara bugu da karfi dan haka kawai taji wannan kiran bata yarda da shi ba
A cikin ɗakin Umma, ta tarar da Umma tana riƙe da wayarta a kunne, Azrah yanayin data ga Umma na waya ta fahimci da Honorable take waya, ta sake baki tana kallon Umma da zuciyata take jin yana kara sannanta bugawa, Umma ta miƙa mata hannu alamar ta zauna sai kuma tayi sallama da honorable, Umma na kallon Azrah ta ce
"Azrah mutumin nan ne Honorable, ya ce zai zo gidan nan gobe"
Azrah ta buɗe baki amma ta kasa cewa komai sai kallon Umma da take ba ko kiftawa, Umma ta cigaba
"Ya ce yana so ya zo ya gana da mahaifinki"
Kamar saukan a rasu haka Azrah taji a kunnuwanta, jikinta yayi sanyi, Me zai ce? Me zai nema? Ta rasa abin cewa sai kallon Umma kawai take yi.
Da yamma bayan Bappah ya dawo daga Majalisar sa, Umma ganin Mama bata nan yasa kawai ta miƙe ta nufa hanyar ɗakinsa da sallama ta shiga ya ɗaga kai yana kallon ta ya ce
"Allah sa lafiya dai, dan bana son tashin hankali Bitti" Umma ta dinga kallon sa sai kuma ta daure ta zauna tunda ba abinda ya kawota ba kenan ta ce
"Malam dama honorable Ibrahim ne yace zai zo gidan nan gobe, toh yace yana son magana da kai ne" Bappah ya dinga kallon ta kamar bai fahimci me take nufi ba ya ce
"Ban gane ba? Me kuma haɗi na dashi? Sannan ina kika sansa?" Umma ta ce
"Shine wanda ya biyawa ƴarka kuɗin candy, yanzu kuma yana bukatar haɗuwa da mahaifinta ya ce, shiyasa na maka magana" sai sannan Bappah ya sake fuskansa ya washe baki ya ce
'Toh..toh.. ai sai kiyi bayani tun farko, shikenan Allah kawo sa goben, Allah yasa kuma Alkhairi ne zai kawo sa" Umma ta taɓe baki ta miƙe ta fita daga ɗakin Bappah
Bayan ta koma ɗakinta a'a usual kamar yadda ko wani garin Allah ya waye rana ɗaɗɗaya ne bata ɓuya tayi kuka haka yanzu ma tana shiga ɗaki ta wuce ta zauna a bakin katifar ta ta zauna ta rufe fuskanta da ɗankwalin ta tana share hawayen daya fara gangaro mata, tana jin zuciyarta na kuna bata san yaushe zata daina wannan kukan nata ba, bata san yaushe zata jita at ease ba, sometimes takan yi dana sani amma it's already late balle ta gƴara, jin motsin Zahra yasa ta goge fuskarta ta kwanta kamar mai bacci....
Da daddare bayan Isha'i Zahra ta dawo daga aika, idonta akan roban sauran awara da ya rage a cikin roban da ake fita da shi talla, bin compound ɗin tayi da kallo ganin babu kowa yasa ta tafi da ɗan sauri amma tana yi dan karta making any sounds, buɗe robar tayi ta juye sauran awara da akalla zaiyi na 2k a kasar hannunta dan kamar zai zuɓe ma saboda laidar ya masa kaɗa, jin motsi daga bayi yasa tayi sauri ta shige ɗakinsu tana ɗan leka ta jikin labulen taga Siyama ce ta fito, karasa cikin ɗakin tayi tana dariyar mugunta ta zauna tana miƙawa Umma katin data tsiyo mata
Azrah dake kallon ta da mamaki ta ce
"Aina kika samu wannan uban awaran Zahra?" Zahra ta jawo plate da Azrah ta gama cin abinci ta juye a ciki tana cewa
"Gidan su kawata na biya na karba, kinsan dama jita muka haɗa kuɗi shine yau ta mana" Zariya ɗiba ta koma gefe ta fara ci, Umma ta ɗauki guda biyu ta kai baki, Zahra ta ce
"Umma kara mana" Umma ta girgiza kai ta ce
"A'a Zahra wannan ma ya min" wani ashar suka biyo daga can compound, Zahra ta fara jin awaran da sauri kamar wacca take da ciwon yunwa, jin kalmar da Siyama ta faɗa ga kuma Mama ta fito itama tana masifa yasa Umma da Azrah kallon Zahra data ki haɗa ido da su, Siyama ta ce
"Wallahi Mama na shigo da awarar nan, kawai daga shiga bayi shine fa aka ɗauke"
Umma na kallon Zahra ta ce
"Zahra mayasa zaki yi haka? Baki san sata bane hakan?" Zahra ta taɓe baki ta ce
"A cikin kuɗin Yaya da suka ɗauka ne na cira" Umma ta ce
"A'a bana son haka Zahra, wannan ba hali mai kyau bane, wanda ya maka mara kyau ka saka masa da Alkhairi haka rayuwa take sai Kiga rayuwar ka yana kyau" Zahra ta taɓe baki ta juya taki kallon su Umma, Azrah ta ce
"Umma ɓata bakin ki kike da Zahra, amma Zahra bata jin magana wallahi" Umma ta ce
"ɗauki awarar ki mayar musu, sannan sai ki biya su kuɗin wanda kika ci" Zahra ta miƙe a zuciye ta fita compound ɗin ko kallon su Siyasa da suke zabe zage da tsinuwa bata yi ba, direct waje ta nufa tayi ɗan gaba da gidan su ta tara almajirai tana musu sadaqa.
Washegari...
Tunda suka tashi suka gyara gidan, Umma take gidan Maman Aziza ta karɓi aron dadduma mai kyau wanda idan at least honorable yazo zai iya zama akai, suka gƴara gidan suka share tas.
Kusan ƙarfe huɗu na yamma, wata mota ce ɗalleliya ta shigo cikin unguwar ta su, Kowa sai kuskus ɗin magana ake yi, wata babbar mota ce me tinted glass ta tsaya a gaban gidan su Azrah wanda har yaran unguwar sun fara taruwa suna kallon motar
Zahra ce ta fara leƙa kofar gidan dan ganin menene bayan ta samu labari daga yaran unguwar da suka shiga suka shafa musu, tana leƙa wa ganin motar ta koma ciki da sauri ta ce
"Aunt Azrah Motar Honorable ce wallahi!"
Azrah ta kalli kanta a madubi Zuciyarta na cike da ruɗani, ta shafa ƙirjinta a hankali, tana jin kamar numfashinta yana tsayawa ta ce
"Ya aka yi kika san shine?" Zahra ta ce
"A kofar gidan nan fah naga ya tsaya, kuma waye yace zai zo idan bashi ba, hala ma sonki ya ke wallahi" Azrah ta wurga mata wani kallo daya sa ta zanye bakinta tayi shiru
Can sai ga wayan Umma ya fara ringing, bayan sunyi magana ta wuce ɗakin Bappah ta sanar da shi akan ya iso
Bappah ya fito cikin shadda mai kyau, ya karasa har kofar gidan ya shigo da shi, suka zauna anan compound akan dadduman da aka shimfiɗa, ko kaɗan bai nuna ma kyama ko wani abu ba
"Barka da yamma Honourable" Bappah ya ce cikin ladabi
"Lafiya lau Baba, Na gode da damar da ka bani"
Honorable ya sake gaishe da Sallah cike da girmamawa, ya kawo maganar yadda za'a duba lamarin su Azrah game da scholarship akan dan Allah Bappah ya barta idan ta samu, ya ce
"Na sha mamakin yarinyar nan, Tana da ilimi, nutsuwa, da burin rayuwa"
Bappah ya ɗago kai ya kalle shi.ya ce "Haka ne sun gado hakan ne daga mahaifiyar su" sai kuma Bappah yayi shiru jin wani bakon yanayi da lokaci guda ya ziyarci jikinsa
Honourable yayi shiru kamar mai nazari sai kuma ya dake ya ce
"Dama na zo neman Alfarma ne ina kuma fatan zaku taimaka min" Bappah ya dinga kallonsa toh me suke da shi da har zasu iya ba sa, can Bappah ya ce
"Allah yasa muna dashi ma tukun" Honorable ya numfasa ya ce
"Idan har ba'a ma Azrah miji ma ina neman Alfarman a bani aurenta dan Allah" Bappah yaji tambayar a ba zata dan this is the least da zai kawo ran sa, ganin shirun Bappah yasa ya ce
"Nayi maka alkawarin ba zan hanata karatu ba, sannan zan gina mata future mai kyau da yardan Allah, dan Allah ka taimaka min"
Bappah ya sake yin shiru, sai daga bisani ya ce
"Zan tambayi iyalina, Amma ba zan hana ƴata cika burinta ba... in har hakan ba zai rusa rayuwarta ba"
Honorable ya ce
"Nagode kwarai, Allah ya saka maka ya tabbatar mana da Alkhairin sa" daga haka Bappah ya raka honorable har waje wanda ƴaran unguwar sun taru jikin motar suna kallo
Bayan tafiyan honorable Bappah ya shiga ɗakin Umma direct inda ya tarar da su zaune duk suma sun kosa suji make faruwa
Bappah yayi gyaran murya ya ce
"Toh abinda ya kawo sa wai yana so a basa auren Azrah ne idan ba'a mata miji ba"
Daga Umma har Azrah da wani expression suke kallon Bappah wanda ba zaka iya tantance what exactly fuskar su ke nunawa ba, Azrah ta fara girgiza kai, Umma ta ce
"Amma Malam ai Azrah tayi karama, ko gama secondary school bata yi bafa"
Bappah ya ce "Toh ai ba yanzu bane Bitti, dole zamu ce amsa sai ta gama secondary school, kuma yace ba zai hana ta karatu ba, zai barta ta cika burinta"
Zahra ta ce "Ahtoh, dama nasan mutum irin honorable ba zai hanata karatu ba" Umma ta ɗauki pillon gefenta ta wurga mata ta ce "ta shi ki bani waje mara kunya" Zahra na dariya ta miƙe ta koma ɗaki
Azrah da har idonta ya cika da hawaye, umma ta riko hannunta cike da lallashi, Bappah yana kallon Azrah ya ce
"Na san wannan ba burinki bane Azrah, Amma idan har zai bar ki ki cigaba da karatu, ya dace mu karɓa, amma think first"
Zahra ta sake lekowa
"Ina ganin ki yarda wlh Yaya, Kema ai kin san irin wahalar da muke ciki, Kuma ya ce ba zai hana ki komai ba"
Azrah bata iya cewa komai ba sai hawaye, can ta ce
"Na yarda... amma fa... ban san me rayuwa zata bani gaba ba, I'm just scared" tunanin ciwon Umma data yi kawai yasa taji ta amince masa.
Daren ranar...
Azrah na kwance, idonta biyu tana kallon sama, tana jin zuciyarta ya mata nawi, tayi addu'a da fatan hakan ba zai zama kuskure ba a rayuwar ta, dukda tana jin tsoro, but duk sanda ta tuna Umma kuma sai tayi calming kanta down"
A bangaren honorable kuwa..
Honorable yana kwance a kan gadonsa, Hoton Azrah da ya ɗauka a government house yana kwance a fuskar wayar, kuma tun ɗazu yake kallo, Yayi murmushi
"She's different Ya Allah" ya faɗa a hankali.
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL* (LABULEN SIRRI)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 12: Whispers and Watchful Eyes
Tun bayan tafiyan honorable har bayan kwana biyu bata sake jin motsin sa ba, dama koda yake kira da wayan Umma ne, har taji hankalin ta ya kwanta dan ta mayar da hankalinta sosai akan karatunta da kuma jarabawar da suke yi...
Tana fitowa a exams hall ɗin, ta zauna a jikin wani wall tana maida numfashi saboda zafin da hall din yake da shi, fifita kanta take yi, kamar ance ta ɗaga kanta kawai idonta ya faɗa cikin na Sagir, tana processing ɗin inda ta taɓa kallon face ɗinsa amma ganin ta kasa tunawa kuma har sannan ita shi ma ita yake kallo yasa ta ɗauke kanta zuwa wani direction amma me? Idon ta ya sauka cikin na Sadeeq, nan take taji wani bugawar zuciya, ɗan yamutsa fuska tayi ta ɗauke kallonta daga gare sa, sai yanzu ta tuna inda ta taɓa kallon sa, wani tsaki ta ja ta miƙe daga zauna da take, sake haɗa ido tayi da Sagir wanda yana mata murmushi amma koda wasa bata mayar masa ba, gaba ta kara sai kuma ta jiyo murya Fatima
"Azrah!" Cak ta tsaya ba tare data juyo dan bata bukatar sake haɗa ido da su, Fatima ta karaso ta na cewa
"Okay.. da ban fito ba da tafiya zakiyi ki barni?" Azrah tayi murmushi ta ce
"Ke, I'm moody ne, kuma naji na bar wajan" daga haka suka kama hanyar gida..
Azrah tana isa kofar gidan su ta fara jin hayaniyar Zahra da Habiba, da sauri ta karasa shiga gidan tana kallon Zahra data sha ɗanmara tana zazzaga ma Habiba magana kamar yadda itama Habiban tayi da alama dambe suke shirin yi yasa taje da sauri ta riko Zahra tana cewa
"Zahra kina da hankali? Ki wuce mu shiga ciki" Zahra ta kwace kanta ta ce
"Kinsan me tamin ne Yaya? Daga ajiye kuɗin gawayin da wani ya tsiya a waje na fah ta ɗauke, ina kan zuba masa kayan miya a laidar fa, kuma ina ganin kuɗin a hannunta shine wai ba zata bayar ba, Mamanta kuma wai taci Uwa ta, ce mata aka yi Habiban ta isa min wani abun ne?" Azrah ta ce
"It's Okay, ki barta kawai tunda tace bata ɗauka ba, kina amfani da ilimi not all the times zaki tsaya faɗa" Habibah ta wawulo wani ashar ta jefa ma Azrah ta fara zazzaga mata magana, Zahra ta kwashe da dariya ta ce
"Wallahi sai kin biya wannan kuɗin ko kuma bashi kika ci" daga haka tabi bayan Azrah da sauri, bayan ta shiga ta samu already Azrah harta zauna tayi wani iri ta Zahra tw ce
"Yaya mene ne kuma?" Azrah ta ce
"Wallahi ban faɗi maganar dan nayi hurting dinta ba, sai dana faɗa kuma ya dame Ni"
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 12