asusun suka irga kuɗin suka ga ₦21,000 ne sauran wajan ₦16,000 Umma ta numfasa ta ce
"Zanje gidan su Aziza anjima, koda rance ne zan karɓo, sai ku shirya ku tafi makarantar Azrah dan ba zan barki a gida ba balle ki cigaba da kukan nan"
Murmushi kawai Azrah tayi, ta tattara kuɗin tasa a fos ɗin Umma sannan ta kai cikin ɗakin Umma ta ajiye akan mirror.
Wajajen 12:20pm Abdul ya dawo gidan tun daga bakin kofar yake ta doka sallama amma yaji gidan shiru, ya shiga ya kalli direction ɗin Mama yasan cewa su Siyama suna can wajan tallansu Mama kuma yasan ta shiga wajan Naman asabe ɗakin Umma ya kalla kamar zai fita sai kuma ya karasa ya shiga
Kalle kallen cikin ɗakin su Azrah ya fara sai kuma ya shiga ɗakin Umma idon sa akan fos ɗin ya sauka da murmushi ya karasa ya buɗe fos ɗin ai kuwa yayi tozali da kuɗin dake ciki da sauri har hannunsa yana rawa ya ciro kuɗin ya saka a aljihun sa da sauri ya fito, Azrah da ta taso a makaranta ta shigo gidan da mamaki take kallon Abdul daya fito daga ɗakinsu ta sake baki tana kallonsa ko kallonta bai yarda yayi ba ya fice daga gidan gaba ɗaya
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
#Jiddatulkhayr
08110615256
*BEYOND THE VEIL* (LABULEN SIRRIN)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 9: The Missing Funds
Kamar wadda aka dasa ta a wajan haka ya tsaya tana bin inda ya fita da kallon mamaki kamar wadda take shirin sensing ɗin abinda ya kaisa ɗakinsu jiki ba ƙwari ta karasa cikin ɗakin tana bi da kallo, wanda ganin babu wani abu daya canza yasa ta cire hijabinta ta kwanta dan kanta ke mata ciwo, bata daɗe ba sai ga Umma da Zahra wanda a hanya suka haɗu bayan sun shiga da sallama Azrah ta miƙe zaune tana kallon Umma ta ce
"Umma an dace kuwa?" Umma ta zare Hijabin jikinta tana sauke ajiyar zuciya, Zahra ta Kalle Umma ganin kamar mata ji Azrah bane yasa ta ce
"Umma Yaya fah magana take miki wai an samu?" Umma ta girgiza kai ciƙe da lallashi kuma da kwanciyar da hankali ga ƴaƴanta ta ce
"Ba'a samu ba amma ta ce zuwa anjima idan ta samu kuɗin da take bin wata zata aiko min" Azrah taji hawaye ya fara taruwa mata ta ce
"Ina ga zan cire rai kawai Umma, kila bani da rabone a karatu" Zahra ta ce
"Balle ma za'a samu in shaa Allah" Umma na kallon Azrah amma ta kasa cewa komai dan gaskiyar maganar kenan bata samu ba, miƙewa Umma tayi ta wuce ɗakinta da niyyar kwanciya sai dai tun daga bakin kofar take kallon fos ɗinta dake buɗe a yashe a bakin kofar ta ɗinga kallo babu ko kiftawa zuciyarta na bugawa da ƙarfi sai kuma tabi ɗakin da kallo, Zahra dake kallon reaction ɗin Umma ta ce
"Umma menene? Wani abu ne?" Umma ta girgiza kai ta ce
"Ina ganin kamar wani ya shigo fa kalli fos ɗin nan a yashe a ƙasa" ai a saba'in Azrah ta miƙe Zahra ta karasa bakin kofar da wuri ta shige Umma ta karasa ta ɗauki fos dake ɓuɗe babu komai a ciki ta ce
"Kambala'iiii wani tsinannan ne ya shigo mana cikin gida harda sace mana kuɗi" ta karasa maganar tana riƙe ƙugu kamar tana gaban wanda ya sace kuɗin, Azrah tayi murmushin karfin hali ta koma ta zauna tayi tagumi dan bata masan me zata ce ba, she's just speechless
Zahra banda masifa da tsinewa wanda ya ɗauki kuɗin babu abinda take yi, Umma ma ta koma ta zauna tana kallon Azrah, Azrah ta ɗago kai tana kallon Umma, Umma ta ce
"Dan Allah waye zai mana wannan abu har haka ko tausaya mana ba zaiji ba" Azrah ta girgiza kanta tayi kasa da muryanta yadda Zahra ba zata iya ji ba ta ce
"Umma shigowa na naga Ya Abdul na fitowa daga ɗakin nan sannan kuma bai yarda ya haɗa ido dani ba kuma ko kara second baiyi ba a gidan ya bar gidan" Umma tayi shiru tana kallonta da mamaki
"Dan uwarshi shi ya ajiye kuɗin da zai ɗauka, sannan kuma kika kyalesa har ya fita baki yi wani abu ba?" Zahra ta karasa maganar da zafin rai, Azrah tayi shiru dan bata so taji ba
Fitowa tayi daga ɗakin tana kallon Azrah ta ce
"Just imagine shine kika tsaya kallonsa har ya fita halan?" Tana maganar ta mayar da kallonta ga Umma ta ce
"Wallahi sai ya biya kuɗin nan ko kuma wallahi zai sha mamakin abin da zan masa" Umma ta sake baki tana kallon Zahra da mamaki dan tana ga kamar Zahra ta manta wanene Abdul, wanda har Siyama ya girma amma take maganar zai sha mamaki, ta zauna tana huci ta ce
"Yanzu idan Mamansu Aziza ta kawo na wajan ta kuma ya za'ayi? Sannan yau fah saura kwana biyu kenan?" Ai Azrah bata san sanda ta mike ba tana kallon Umma wanda har sannan hawaye ya fara zuba a idon ta tana kallon Umma ta ce
"Umma ina zuwa bari naje makarantar mu na tambaya zan iya biyan zallan neco da kaina tunda ba yanzu za'ayi ba amma yanzu kam babu wani hope to Dan ba zamu samu wannan kuɗin daga yau zuwa gobe ba" kafin Umma tayi magana harta fice
Zahra ta fito compound ɗin tana bi da kallo ko zata ga wani abu mai amfaninsu sai dai bata gani ba ga kuma kofarsu a garkame dama sune basu kulle kofa sai dai su tura su kulle babu key
Azrah tana shiga cikin makarantar su ta wuce office ɗin principal ɗinsu wanda da alama yana da bako kuma suna magana ne, ta tsaya a bakin kofar tana jiran ya fito, tafi minti biyar sai can aka buɗe kofar wani mutum ya fito daga office ɗin ta ɗan matsa masa baya tana kallonsa ta gaishe sa ya amsa mata yana washe mata baki ya ce
"Ya aka yi ƴanmata?" Ta girgiza masa kai ta ce
"A'a wajan principal ɗinmu nazo" ya matsa mata da sauri yana
"Toh toh toh shiga mana, ashe Kema ƴar makarantar ne, ai shikenan" daga haka ya sauka akan dakali ita kuma ta tura kofar officen ɗin ta shiga da sallama principal ɗin ya ɗago kansa yana kallon Azrah yana murmushi ya ce
"Azrah ke ce?" Kai ta gƴaɗa masa ta ce
"Yes sir, good afternoon" ya ce
"Afternoon, have a seat mana" ta zauna tayi shiru tana kallon sa sai kuma ya ce
"What is it? Akwai matsala ne Azrah ?" Ta gƴaɗa masa kai ta ce
"Sir, regarding maganar candy ne, wallahi kuɗin da muka tara an sace kuma bamu san inda zamu samu kuɗi daga yau zuwa gobe ba" yayi shiru sai kuma ya ce
"SubhanAllah! A garin yaya kenan? Allah ya tsare" ta ce
"Amin, shine yanzu nake so naji koda an rufe zuwa nan da a fara maganar registration ɗin NECO zan iya ma kaina?" Ya girgiza kai ya ce
"A'a daga can ministry of education za'a muku amma gaskiya sai wanda suka zana candy suka ci sune za'a ɗauka sunan su a biya musu both SSCE Exams ɗin, Kinga ba zaiyu ba sai dai idan zaki je wata makarantar ne kawai kiyi amma sai private school" tayi shiru kamar mai nazari can ta ce
"But sir, ina neman favor please a ka taimaka min yadda Allah ya taimaka maka ka rufamin asiri ka biya min wallahi kafin mu gama candyn Zan mayar maka da kuɗin ka" kallonta yake babu ko kiftawa sai kuma yayi murmushi ya gyara zamansa yana shafa fuskarsa ya ce
"Ai Azrah baki san me ba, duk sunan da muka kai musu muka ce sune wanda suka ci candy toh za'a biya musu kuɗin WAEC da NECO sannan kuma the best student za'a biya musu Jamb harda sponsoring karatun su" Azrah ta fara jin wani hope da maganarsa ta gyara zaman ta fuskarta ya fara bayyana alamun murmushi ta ce
"Okay, kuma duk daga government house ɗin kenan, Allah sarki governor, toh dan Allah Sir ka taimaka min sai kasa harda sunana mana" yayi murmushi ya ce
"Yadda kike kyakkyawar gaske har sai kin bada hakuri wai? Toh uban waye bai san kokarin ki a makarantar nan ba, ko baki yi candy ba zan saka sunan ki" Azrah ta share hawayen fuskanta ta ce
"Nagode sosai sir, Allah maka fiye da yadda ka faranta min" wani kallo yake mata wanda yasa godiyan da take masa maƙalewa tana kallonsa da mamaki ganin inda yake kallo Shima yayi shiru yana kallonta, sai can ya ce
"Zan iya taimaka miki Azrah, Amma you know, not everything comes for free..." Gabanta ya faɗi ta ce
"Excuse me? Ban gane ba sir" yana murmushi ya ce
"You're a smart girl Azrah, A pretty one too, Think about it" ya kare maganar yana kashe mata ido ɗaya meanwhile yana kokarin kai hannun sa jikinta
Azrah ta miƙe da sauri, hawaye na taruwa a idonta ta ce
"Thank you Sir, But I didn't come here to sell myself" wani murmushi yayi yana nuna mata hanyar fita ya ce
"Then, out"
Ta juya ta fice, jikinta ba ƙarfi.
Amma zuciyarta cike da karfin hali da hope ta fita daga building ɗin kamar wanda ruwan sama ya mata duka
Tayi ta tsaye a waje, tana kallon gate, tana ma kanta magana
"Ko da nayi kuka… ko da na rasa wannan damar… ban rasa mutuncina ba" ta harari gate ɗin tana jin zafi a zuciyarta ta kama hanyar gida
Harta isa gida bata daina mamakin principal ɗinsu ba wato yanzu babu wanda zai yi taimako saboda Allah, bayan ta shiga gida ta wuce ɗakin su taga Umma na zaune ga Zahra gefenta suna jin wani program a radiyo Umma ta ce
"Ya akayi Azrah?" Azrah ta girgiza kai tace
"Babu wata mafita kawai Umma" daga haka ta wuce ɗakin su Zahra ta bita da sauri ganin mood dinta ta ce
"Ya ake ciki Anty? Ba zai taimaka miki ba?" Azrah tayi murmushin dole ta ce
"Babu wanda zaiyi taimako saboda Allah sai ya nema ya lalata ka" Zahra ta sake matsowa kusa da ita ta ce
"What do you mean? Wai ba iskanci zai yi da ke dan Ubansa?" kai kawai Azrah ta gyaɗa mata kai, Zahra tayi wani murmushi ta ce
"I wish Ina wajan wallahi sai ya raina kansa banza jaki kawai, ce masa akayi talauci hauka ne da har saboda shegiyar wata waec zaki tsaɓawa Allah" ta miƙe tana jan wani dogon tsaki ta bar ɗakin dan ita taji harta tsane mutumin.
Yamma ta gama lullube garin ga wani hadari mai ɗauke da iska garin yayi daɗi, daga nesa da kuma neighbors ɗin kana jin hayaniyar yaran unguwar da ihun su alamun wasa dai suke, mutane na gaisawa, wasu kuma na dawowa daga kasuwa da gajiya rubuce a fuskokinsu
Bappah ya dawo gida yana shigowa kamar yadda ya saba bai yarda yayi making any sounds ba ya danna ƙofar ɗakinsa ya shige ba tare da kowa ya lura da zuwansa ba, A can cikin dakin, ya cire hularsa ya aje ya kwanta dan baya son kowa yasan yana nan
Haka Umma ta wuni a gidan bata da wani sukuni ganin yadda Azrah ma ke cikin tashin hankali, tana jin shigowar Bappah ta miƙe da sauri ta nufe ɗakinsa gudun kar anjima Mama tazo ta makale dan yanzu ita da bappah take son magana ba wani third party
Ta tura kofar ta shiga da sallama fuskarta cike da damuwa bayan sun gaisa ta ce
"Malam... dan Allah ka sauraren Ni kuma ka duba lamarin nan" ta ce da sanyi muryarta kamar wacce ke buƙatar taimakon sa
Bappah ya ɗago kai daga inda yake zaune, yana gyara zamansa ya ce
"Lafiya Bitti?"
Umma ta tura ƙofar ta rufe, sannan ta matso kusa "Yau an ɗauke kuɗin candyn Azrah daga inda ta ajiye Malam, Kuma an ce Abdul an ganshi yana fitowa daga ɗakinta yau, Na san ba wani shaida, amma akwai ayar tambaya ai Malam, kuma kai ka fi kowa sanin halinsa"
Bappah ya lumshe idanu yana sauke numfashi da ƙarfi, ya furzar da Islam bakinsa Bai ce komai ba, sai ya miƙe tsaye da sauri, Ya fice zuwa filin sakar gida cike da fushi kamar wanda zai tashi sama Kuma yasan Abdul zai ai kata
"Ke Fatsuma?! Ina ɗanki yake ya za'ayi ya shiga ɗakinsu Zahra ya sami makuɗan kuɗi masu mugun yawa na candyn ta? Gidan nan ba na sata bane! Ki kiransa tun da wuri ya dawo da kuɗin nan kafin ya kashe! Kuma bana son jin wani abu makamancin haka, wallahi sai na ɗauki mataki!”
Zahra dake zaune a bakin ƙofar ɗakinsu ta miƙe da sauri, zuciyarta cike da takaici, sai ta fara zazzaga tsinuwa ga wanda ya ɗauke kuɗin "Wallahi duk wanda ya saci kuɗin nan Allah zai nuna masa, tun daga yau ba sai gobe ba, Sannan rayuwar sa ba zata taɓa kyau ba, zai kare a roko kuwa, Kudin da aka tara da hawaye da yunwa ya zo kawai ya ɗauka kamar ba komai ba ko kuma nace kamar shi ya ajiye?"
Kafin kowa ya yi wata magana, sai ga Mama ta fito daga ɗakinta cikin hanzari kamar wacce aka kork
"Sharrin banza da wofi! Duk faɗin gidan nan, sai ɗana kuke zargi? Abdul ba barawo bane! Wani irin rashin adalci ne haka Malam? Kaje ka biye wa banzar matarka" ta kare maganar da mugun karfi tana son tayi eye contact da Bappah ai kuwa suna haɗa ido Bappah ya zama mute, gashi ta cika gidan da surutun da kowa ya sani idan Mama ta fara sai ta gama take hakura
Bappah ya juya kamar zai ce wani abu amma sai ya ƙasa, Ya juya ya koma cikin ɗakinsa zuciyarsa na tafarfasa Haka ma Umma tayi shiru, ta dawo ɗakinta da zuciya mai rauni da shakku
Zahra kuwa ta cigaba da zama a bakin ƙofa, tana huci kamar tanderu ta ce a kaikaice
"Ni dai ban ce da kowa ba, amma duk wanda ya sace kuɗin nan shi da yin kuɗi sai a lahira idan ana yi amma shi da uwarsa da kannansa sai dai suga a maƙwafta, kuma Allah ya isa, dan barawo barawo ne!"
Mama ta juyo cikin hargowa "Dan Uwarki da ni kike yi Zahra? wani kike faɗar waɗannan maganganun?"
Zahra ta kalle ta da idonta da babu tsoro, ta ce
"Na ce wanda ya saci kudin, amma Kinga na kira suna? Ai Ni da wanda ya sace nake magana"
Mama tayi shiru tana Binta da wani banzan kallon, Zahra ta ɗauke kanta ta cigaba da addu'o'in ta daga karshe Mama ta koma ciki.
Da daddare har Azrah ta kwanta kawai ta sake tuno yadda suka yi da principal ɗan saki tayi ta gyara kwanciyar ta kawai wani magana daga maganar principal ya faɗi mata da sauri ta miƙe zaune tana tunanin ambatan gomnati da yayi, ai gwamma na kowa ne why not gobe kawai ta tafi government house idan har zaiyu, murmushi tayi ganin ga wani Alternative kuma jikin ta bai bata zata yi loosing wannan karan ba da wannan tunanin ta kwanta a ranta.
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL*(LABULEN SIRRIN)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 10: When fate opens the right door
Washe gari tun asuba'in fari Azrah ta farka, damuwa ce fal a zuciyar Azrah, Ba ta yi baccin kirki ba, she's just pretending saboda Zahra, sosai idanuwanta sun kumbura saboda rashin baccin kirki, salloli ta dinga yi har akayi sallah sannan itama ta daura, tana cikin sallah Zahra ta tashi ta fita itama dan ɗauro alwala, tana starring waje ɗaya tana ƙoƙarin gamsar da kanta cewa yau tana da mafita dan da tunanin Jiya ta kwana kuma da shi ta tashi kuma ta gama making mind ɗinta up
Dan bata da wani sauran lokacin and kuma ba zata hakura ba sai ta gwada trying luck ɗinta, zata rubuta candy, Kuma yau ita ce ranar da ta yanke shawarar tunkarar wajan no matter what zata je
Da ƙarfe takwas da rabi na safe, ta fito cikin tsaffin doguwar riga da mayafinta mai launin Maroon wanda ya sake bayyana tsantsan beautyn ta, amma fuskarta cike take da fargaba dan babu annurin amma hakan bai ɓoye kyaunta ba, ta ɗaura jakarta a kafaɗa, cike da takardun candy, da kuma result ɗinta tun daga JSS1 to SS2 da kuma many awards certificate data samu wasu na spellings wasu kuma na best student wasu kuma na debate ne, Zahra ta fito daga ɗaki tana kallonta da mamaki ta ce
"Ina kuma zuwa da sassafen nan Yaya?" Azrah ta mata murmushi ta ce
"Zan je wani waje ne Zahra... Idan na dawo zan baki labari" ta kare maganar da assurance da kuma murmushi karfin hali, Zahra ta ce
"Allah Ya tsare ki Yaya, ya kuma baki sa'a koma menene na san it's going to be best" Zahra ta karasa maganar amma zuciyarta cike take tambayoyi.
Azrah ta leƙa ɗakin Umma ganin tana bacci kawai ta fita ba tare da ta tashe ta ba
Haka ta dinga tafiya da ƙafa, wasu motar su tsareta amma taki tsayawa wasu kuma su biyo ta amma duk babu wanda ta tanka musu, idan sun gaji dan kansu suke kyaleta a haka harta isa....
A gaban Government House taga wani motar na tsaye amma bata ma kalli inda motar yake ba dan wannan bashi ne a gabanta ba
Securities na wajan suna zaune, sai ga wani a bakin gate yana dube-duben masu shigowa da fita Azrah tana tunkaran sa, tana takawa cikin nutsuwa, sai dai a zuciyarta damuwa da tsoro sun fi yawa
"Ke! Ina zaki?" daya daga cikin securities ɗin ya tsayar da ita da tsawa kamar ba dan adam ba
Azrah ta ɗan ja baya da tsoro amma bata bari yayi affecting ɗinta ba cos yanzu ba tsoro bane a gabanta, ta ce
"Don Allah ina son naga gwamna ko wani Babba a ciki" wani kallo ya mata alamar bai gane ba? Irin is she even Okay? Ta ce
"Dama na zo ne akan maganar taimako, ina son na gan..." Tuntsurewa suka yi da dariya dan ba kaɗan ba ta basu dariya ɗayan yana kallon abokin aikin sa ya ce
"Is she even Alright?" ɗayan ya Kalle sa dan shima abin da mamaki ya ce
"I doubt much" Azrah tayi saurin cewa "I'm much Alright sir, taimako zaku min fah, dama government house ba wajan taimako bane?" Ya ce
"Ke! Koma baya! Bamu da lokacin wannan rubbish ɗin naki"
Azrah ta kafe su da ido, idonta cike da ƙwalla Sai wani ɗayan security mai taushi ya kalle ta sai kuma yayi kasa da murya
"Ke! Wayarki akwai kati?"
Ta ɗaga kai da mamaki take kallon sa ta ce "Eh... me zaka yi da ita?"
"Ki kira wanda kika zo nema, idan har da izini kika zo, zai fito ya shiga dake ko kuma ya kira waya ya ce a barki ki shiga"
Azrah ta yi shiru, toh waya ai bata da ita, ace tana da waya ai ba zata ma tsaya a wajan ba da tuni ta sayar, kuma ko da akwai wayan wa zata kira a ciki? Wa ta sani? Sai kawai ta ce "Ban da waya, banzo da ita ba"
"Eh toh, idan baki da waya, kuma baki da wanda zai fito ya shigar dake ko ayi waya, ya kike so mu miki?, wannan ma ai raini ne"
Azrah ta saki ajiyar zuciya
"Wallahi ba raini bane, dama... na zo ne akan maganar candy jarabawar sakandire, Ina nema ne a taimaka min da kuɗin rijista, Ban da wanda zai taimaka min ne sai nayi tunanin nan zan samu mafita tunda ai nan kowa zai iya kawo kukansa kuma a share masa"
"Ke! Ki juya! Bamu da lokacin sauraran karatun novel ɗinnan naki"
Amma kafin ta juya, wannan motar da ta gani tun ɗazu a wajan mai plate no ɗin gwamnati ta kuso kai zata shiga ciki, Azrah ta matsa gefe da sauri tana gyara mayafinta. Da sauri security ya buɗe musu gate, Matar cikin motar ta hango Azrah tana kade hannunta kuma duk tayi abin tausayi, kuma taji Convo ɗinsu, sai ta leƙa ta ce
"Wannan yarinyar fa?"
"Wani matsiyaciya ce da take cewa wai tana son a taimaka mata da kuɗin jarabawa" Matar ta ce da sanyin muryarta
"Ku bari ta shigo, muna buƙatar jin irin waɗannan yaran and she looks serious and responsible"
Security ya harareta amma ya ce
"Ke! Shigo"
Azrah ta kafe shi da idanu na godiya amma bata ce komai ba Tayi shigarta ciki, zuciyarta cike da fargaba da fatan Alkhairi
A cikin ginin Government House...
An kaita wani ofis na musamman a sashin kula da harkokin jama'a wato Public affairs Unit, banda addu'a babu abinda take yi, fatan Allah bata Sa'a kawai take duk da yanzu taji hankalin ta ya kwanta
Bayan ta zauna na mintuna wani mutum mai kamala kuma alamar girma ya shigo Shine Honorable Ibrahim Yusuf ɗaya daga cikin ‘yan siyasan da suka fi riƙewa a jihar da taimako ga al'umma, kallo ɗaya yama Azrah ya ɗauke kansa, Yana magana in very calm way kamar ba wani Babba bane a jihar yana kallon matar dake kofa ya ce
"Who is this girl?" Ta ɗan risina ta ce
"She came for help concerning education, sir" ya ce
"Let me speak to her, bring her in" daga haka ya shige ofis ɗin dake cikin wannan, Matar ta shiga da ita ciki sai kuma ta fito
"Assalamu alaikum" ta faɗa kanta a kasa ya ce
"Wa’alaikumus Salam" ya amsa mata ya ce
"Have a seat" ta ce
"thank you sir" sai sannan ta zauna
"An ce kina da matsala ne akan candy right?"
"Eh ranka shi dade, Sun ce za'a rufe rijista saura kwanaki biyu yau, kuma kuɗin jarabawar wanda na tara da kuɗin sana'ata an sace kuma babu enough time it's already late balle na sake tarawa, kuma a gida ma bamu da su... Na zo ne don neman taimako"
Ya zauna yana kallonta da mamaki
"Kin zo Government House ke kaɗai? Ba tare da rubutaccen wasiƙa ba? Ko wakili ba?"
Azrah ta girgiza kai "Eh... I follow my heart ne na taho Ina ganin idan akwai inda zasu saurare ni to nan ne"
Honorable Ibrahim ya gyara zaman sa dan banda mamaki ta babu abinda yake yi, kuma iyakar gaskiyar ta yake gani a kwayar idonta, maganar kuma itake tara kuɗin sana'ar ya tsaya masa a rai ya ce
"You mena you hustle and still go to school? Sannan ke kika tara kuɗin registern da farko?"
Ta gƴaɗa masa kai ta ce
Yes sir, Ina sayar da kayan miya, ina ƙulla gawayi da daddare, Zahra kanwata tana taimaka min da kai kaya makarantar su, and other stuffs Mun kai rabin kuɗin da ake nema sai aka sace su"
Kawai ya tsaya kallon ta ita kuma ta ɗauka bai yarda bane yasa ta ciro file daga jakkanta ta miƙa masa ya karɓa yana mamakin ganin results dinta, ba kaɗanba ta basa tausayi yasan tasa karatunne a rai shiyasa ya ce
"Me yasa kika cigaba da ƙoƙari duk da wannan wahala?"
Sai Azrah ta kalle shi da idanuwa masu ɗauke da tarihi ta ce
"Saboda bana son zama kamar wasu mata da suka saida mutuncinsu saboda jarabawa Ina da burin zama likita Ina son taimakon mutane... kamar yadda bani da wanda ya taimake ni"
Ya lumshe idanu yana sauraren kalamanta kamar yana karanta littafi mai sutsar da zuciya ya buɗe idon yana kallon ta ya ce
"Ki ba ni tarihin rayuwarki... daga farko, Ina son jin wane irin yara ne ke fuskantar irin wannan rayuwar "
Azrah ta sauke ajiyar zuciya sannan ta fara... ta faɗa masa yadda rayuwa ta canza bayan lokacin da karayar arziki ta samu Bappah, Yadda take aikatau a gidan mutane da irin sana'ar data yi wanda ba zata iya irgasu ba, da yadda Umman ta take fama da lalura har yasa ta bata kuɗin data tara, yadda suke fama dan ita ke ɗaukan nawin kanta da mahaifiyarta sai kanwarta, Bata ɓoye komai ba
Ya ɗaga kansa cike da tausayi ya ce
"Alright... I will help you In Shaa Allah Amma before that give me your number"
Azrah ta kalli ƙasa ta ce
"I don't have a phone sir" ya ce
"No phone? Hmm… Okay, give me your mother's number then"
Ta fara furta masa numbern Umman yana typing a wayan sa ya ce
"Where do you live?"
Ta faɗa masa sunan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 12