da dogon tsaki....
A babban hall da za'a yi taron, hall ɗin ta cika da jama'a Iyaye, malamai, manyan baki da kuma 'yan jarida, Azrah tana zaune a kujerar gaba tare da wasu colleagues ɗinta, zuciyarta a nutse amma bakinta bai bar ambaton Allah ba dan haka kawai take jin wani faɗuwar gaba
Aka cigaba da gudanar da taron cikin aminci da kwanciyar hankali tare da girmama duk wani baki da yake wajan, bayan 'ƴan ɗanyi wasu daga cikin programs ɗin aka fara bada gifts sannan commissioner da kansa ya fito yayi bayanin akan akwai wasu students guda biyu da gomnati ta basu scholarship zuwa India wanda yana rokon iyaye idan har 'ya'yan su ne karsu hana su fita dan duk kaf garin Katsina mutane biyu ne aka ɗauka, yana gama jawabi aka fara kiran suna....
Kawai aka kira sunanta a matsayin Best Graduating Student 2025, kuma Honourable da kansa ne ya tsaya akan hakan har sunanta ya shiga scholarship list, Scholarship ɗin kuma zuwa wata shahararriyar jami'a ce a kasar India wanda dai sai kana da ƙafa ƙake samu
Zahra ta miƙe tsimɓil tana zara ido sai kuma tayi wani ihu wanda tayi calling attention ɗin mutane, ta rungume Umma tana ihun cewa "Umma Yaya aka kira... Wallahi ita aka kira fah Umma" har sai da Umma ta nutsar da Zahra kafin ta nutsu
Azrah ta miƙe daga kan kujerar da take zaune hawaye ya cika idon ta dan she can't believe, she's still processing ita ɗince ce or not?" A hankali ta soma takawa har ta isa wajan
Yayin da take karɓar certificate da kyautar scholarship masu hotuna suka yi caaa akanta kowa yana faman ɗaukanta ga manyan bloggers ma duk suna fama tanada bayanan su
wani dan jarida ya karasa wajan da Azrah take ya ce
"Miss Azrah, how does it feel to be awarded the best student and chosen for international scholarship?"
Azrah ta gyara tsayuwarta cikin natsuwa ta ce
"It feels like hard work finally paid off, I'm grateful to Allah, my mother, and everyone who believed in me even when it wasn't easy"
Tafawa ta kaure a hall ɗin kowa yana kallon ta cike da sha'awa Sai kuma ya ce
"A special appreciation goes to her mother a woman of strength and humility"
Aka nema mahaifiyarta data fito, haka Umma ta fito ta haye kan stage, an bata kyauta da girmamawa a madadin iyaye mata na makarantar, Kamar ba ita ba, ta tsaya tana murmushi da hawaye a idonta try hard not to cry abu guda daya faɗo mata rai yasa ta tsunkuyar da kai kasa abubuwa suna dawo mata kai fresh nan da nan taji zuciyarta ya karye atimes ji take kamar ta gudu, dakyar ta ɗaga kai tana faking murmushi ta soma magana cike da ilimin sannan da nutsuwa
"Assalamu alaikum everyone, I'm Bitti, Azrah's proud mother, Alhamdulillah, today I'm overwhelmed with joy. As a parent, I want to advise everyone to be a guiding light to their children. Be their first teacher, and prioritize their education. With Allah's blessings, I'm confident they'll excel. I'm thrilled to see Azrah's hard work pay off, and I'm grateful for the scholarship to India. Thank you, and may Allah bless all our children"
Duk wajan kallon Umma ake da mugun mamaki, barin ma wanda suka santa dan basu san haka take da ilimi ba, wajan aka hau tafa mata cike da sha'awa, miƙa mic ɗin tayi sannan ta sauka, kiran Azrah da Zahra aka yi suka tsaya aka musu hoto sannan suka koma wajan zaman su, Maman Azizah ta ce
"Ma Shaa Allah Maman Azrah wlhi ki gode Allah, dan ya miki komai, and also kin sake ɗaga darajarki da yaranki wajan mutanen da suke muku kallon talauci yau kinyi proving ɗinsu wrong cewa babu ruwan talauci da jajircewa wajan neman ilimi"
Umma tayi murmushi ta ce "Alhamdulillah!"
Baby ta tashi ta nufi wajan da Azrah take da murmushi ɗauke a fuskarta
Honourable na daga cikin manyan baki da aka gayyata dan taron, yana zaune daga gefe yana kallon duk abin da ke faruwa, duk da yadda yake jin tsantsan tsanarta a zuciyarsa amma hakan bai sa ya fasa taimaka mata a bayanta ba
Principal kam bai tashi zama spaced out irin na wannan moment ɗinba, bai tashi sanin Azarh nada wanda suka tsaya mata irin na yau ba duk da yasan she deserves it Amma sai masu kafa ake bawa, ranan bai yi mamaki ganin an biya mata wancan kuɗin ba kamar yadda yaga sunanta ne ya fito.
Yayin da ceremony ta kare, kowa yana ta jin Azrah da mahaifiyarta cos ba kaɗan ba suka bama mutane sha'awa fiye da kima bs, lokacin kuwa har hotonta ya fara yawo a kafafen sada zumunta, tare da taken
"The girl from the ghetto now heading to India!"
Azrah sake baki tayi tana kallon Zahra da Baby da suka fara raba takeaway wa colleagues ɗin Azrah duk da ba wani friends gareta ba,Azrah ta ce
"Ina kuka samu wannan?" Zahra ta ce "You think zamu kyale ki haka ne kawai? Just imagine fah, your grad? You must be joking" Azrah ta rungume ƴar uwarta tana jin sonta har ranta
Azrah ta wuce office ɗin principal taje karɓan envelope ɗin da aka tanada dukkanin bayanan dake magana game da scholarship ɗinta and some awards certificate, tana cikin tafiya taji murya yarinya
"Hey girl" Azrah ta juya tana kallon yarinyar da akalla zata bata shekara 5, da murmushi ta ce
"Hey! Good afternoon" mayar mata da murmushin tayi ba tare data amsa ba ta ce
"Congratulations Azrah!" ta amsa da "Thank you" har zata tafi ta ce
"Please Amma are you Nigerian?" Azrah ta gƴaɗa mata kai, ta ce
"Ayyah thought ba ƴar nan kasan bane, ganin how beauty you are, ga kuma sunan ki da is rare" murmushi kawai tayi daga haka ta wuce zuwa office ɗin...
Bayan ta fito ta samu already su Umma har sunyi gaba, tana tafiya a hankali kanta a kasa bata son yadda ake ta kallonta yasa taki yarda ta kalli mutane, ji tayi an rungumeta ta baya ɗan juyawa tayu taga Fatima ce, ta sakar mata murmushi Fatima dake faman ihu tana taya ta murna ta ce
"God! Azrah ina nasan abinda ke faruwa? Ai ina gida ina kwance ina jin labari nace banga ta zama ba, Kai congratulations" murmushi tayi ta ce
"Thank you, 2days ban ganki ba da safe ma ina ta raba ido still ban ganki ba" Fatima ta harareta ta ce
"Dama ke kina damuwa da mutane ne Azrah? Ai saboda rashin kirkin ki yasa na gaji da zuwa gidan ku, tun last papern mu nake ce miki bana jin dadi baki ko leƙo Ni ba, toh ranan ina komawa gida akayi admitting ɗina" Azrah ta ɗan buɗe ido sai kuma ta ce
"I'm sorry please, Allah baki lafiya my friend" daga haka suka fara jerawa, Fatima sai faman maganar wannan scholarship ɗin take yi har Azrah ta gaji da jin maganar, duk kuma inda zasu wuce da wanda ta sani da wanda bata sani ba da manya da kananan hatta malamansu sai congratulations suke mata, a haka har ta tafi gida..
Direct ɗakin Umma ta shiga ta same Umma da wasu few neighbors ɗin su sun shigo taya su murna, Azrah ta zauna tana gaishe su, duk suka amsa mata, ɗaya daga cikin matan ne Matar ta ɗan manyanta ta ce
"Azrah wannan kaɗan ne daga lamarin Ubangiji, sannan Allah ya dube zuciyar ki ke da mahaifiyar ki yadda kika kama kanki kuka tsare mutuncinku sannan kuma yadda kika dage da neman na kanki shiyasa Allah ba zai barki ba, ina so nace miki ki cigaba da wannan kyawawan ɗabi'un naki zaki sha mamakin inda zai kai ki" Azrah ta gƴaɗa ma Matar kai ta ce
"In shaa Allah, Nagode" daga haka ta miƙe zuwa ɗakin su tana shiga Zahra ta rungume ta tana sake wani ihun ta ce
"Ohh Yaya walhi kin biya, God! Just imagine, ai jikina ya bani ne shiyasa na dage Umma sai taje and Umma too did well" Azrah ta ture ta daga jikinta ta ce
"Zahra kadani kasa zakiyi?" Zahra ta ce
"Ba zaki gane bane duk cikin murna ne aswrr, chap waya ga Aunt Azrah a India shikenan Kema sai a ɗauka daga can kike fa" Azrah bata san sanda tayi wani dariya ba ta ce
"Sai kuma su ɗauka Ni ƴar can ne saboda ai ina kama da su?" Zahra bata kulata ba ta zauna ta fara buɗe envelope ɗin tana kallo cike da farin ciki wa ƴar uwarta cos she deserves happiness and more.
Da yamma Umma na zaune da 'ya'yanta baya duk bakin sun tafi, suka share gidan suna cin abincin da Maman Asabe ta kawo musu, jin muryar Bappah suka yi
Tun daga bakin ƙofar gidan, ana jin muryar Bappah yana kiranta
"Azrah! Azrah!"
Azrah dake zaune tare da su Umma da sauri ta miƙe tana amsawa "Na'am Bappah!"
Fuskarta cike da annuri, ta fito ta tsaya bakin kofar ɗakin nasu tana kallon Bappah daya shigo shima fuskarsa cike da annuri
Bappah yana kallonta da murmushi yana jin zuciyarsa cike da alfahari da sonta ya ce
"Alhamdulillah daughter! Duk da i always failed you as a father amma baki taɓa jin ki karaya ba, Allah ya cika miki burinki ya ɗaukaka ki duniya da lahira, Azrah kin kawo wa wannan gidan daraja, Kin kawo min kwanciyar hankali Azrah" ya kare maganar yana ɗora hannunsa a kanta
Azrah ta sunkuyar da kai tana murmushi, zuciyarta cike da farin ciki ta ce
"Bappah you never failed us, bari na kawo maka abubuwan da aka bani"
Ta juya da sauri ta shige cikin ɗakin, Bappah ya bita da kallon tausayi, bayan ƴan mintuna ta fito da wasu envelope da kyaututtuka, award certificate da wasu gifts ne, sai takardu na scholarship da kuma wani dan envelope na kuɗi, ta durƙusa ta mikawa Bappah
"Ga waɗanda aka bani Bappah, ka duba su"
Bappah ya karɓa yana dubawa fuskarsa ta gagara ɓoye farin cikin da yake ciki, ya jinjina kai, sannan ya ce
"Wannan shine abinda ake kira tarbiyya, halacci, da kuma jajircewa Allah ya ƙara miki basira Azrah, Kin fi kowacce mace daraja a idona, Allah baki miji na gari ke da ƴar uwar ki"
Zuciyar Azrah ta cika da taushin ƙauna da farin cikin, rana ce da ba zata manta da ita ba ganin yadda Bappahnta ke mata magana.
Last Free page
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
Episode 20: Bitter Hearts, Brighter Futuresss
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 12