Zahra ta ja tsaki.
Washe gari.... Tunda Ayrah ta tashi yau haka kawai take jinta so tense, idan ta tuna wai Honorable zai zo gidan kuma wajenta zaizo sai taji kamar tayi kuka, tana tunanin wai da kansa zai zo?, ba wai magana a waya ba, ba kuma ‘yan aike ba, at this point bata san ko haduwar ta dashi Alkhairi ne ko akasin hakan ba, Tunanin nan ya ishi Azrah tun tashin ta daga bacci..
Zaune take a bakin katifarsu ta jingina da bangon ɗakin, tana starring one place, Zahra na gefenta, tana kokarin goge mata hijabin da zata saka, domin Umma ta ce kada ta fita da gyalle tayi using hijab sbd idan mutum kamar Honorable zai zo cikin gidan at least tayi shigan mutunci
"Kina jin tsoro ne ko kunya?" Zahra ta tambaya tana kallon fuskarta
Azrah bata amsa ba, Kamar zata fashe da kuka, amma ta ɗan daure, ta kalli gugan da Zahra ke mata ta ce
"Zahra... bana son wannan attention ɗin"
"To me kike so?" Zahra ta ce da dariyar mugunta
"Karatu ne kike so ko? Toh Mango park uwar karatu sai kin shanye komai a bokon kenan? To ai Kuma ya ce ba zai hana ki karatu ba ai ma yafi Sadeeq ko Saif ne ma?"
Zancen Saif ya tsinka zuciyarta, tana mata wani banzan kallon ta ce
"Waye kuma Sadeeq?" Zahra ta buɗe hannayenta alamun bata sani ba sai ta fara dariya ta ce
"Toh Nima na san sa ne? Kawai naji sunan ne yafito min daga baki" Azrah taja tsaki ta ɗauki littafinta tana forcing kanta da karatu
Can yamma sai ga wasu yara biyu sun shigo gidan da gudu suka yi wajan dakin Umma suna wai wani a waje yace a kira masa Azrah, Zahra tayi saurin cewa
"Okay, je kuce gata nan fitowa" Sai kuma ta mayar da kallon ta kan Azrah tana Murmushin Mugunta, ko da wasa Azrah taki kallon direction dinta kuma bata tashi ba, dan ita tasan yadda zuciyarta yake bugawa da karfi
Ganin bata da niyyar tashi yasa Umma ta ce "Azrah ke baki ji ance ana miki magana bane a waje? Kuma ai kinsan dole honorable ne amma kikayi kamar baki ji ba, ko dan kina ganin yanzu Shikenan zaki iya masa abinda ranki ke so saboda yana son ki" jiki ba ƙwari ta tashi ta wuce ciki bata jima ba sai gata ta fito sanye da Hijabn da Azrah ta goge mata
Tunda ta fita kofar gidan bata gansa ba sai motarsa dake parke hakan ya tabbatar mata yana cikin motar ne amma sai kawai ta tsaya tana kallon wani waje
A wajan honorable kuwa tun fitowanta yake kallonta bai san sanda murmushi tayi escape daga fuskarsa ba, bayan ya kare mata kallo sanin ba zata karasa ba yasa ya buɗe motar ya sauka ya taka har inda take tsaye yayi ƙasa da muryansa ya ce
"Muje cikin motar ranki shi daɗe, cos nan duk wanda yazo wucewa sai ya Kalle mu" ta gagara ce masa A'a haka tabi sa har motar, ta shiga da sallama
"Assalamu alaikum" ta furta muryanta ya soma rawa
"Wa'alaikum salam" Honorable ya amsa da murmushi mai ɗaukan hankali
Yana kallon yadda ta takuren waje guda kana ganinta kasan she's not comfortable da spot ɗin, a hankali ya ce
"Hope kunyi magana da Bappah and kinsan me ya kawo ni wajan ki right?" Kai kawai ta gƴaɗa masa, tana Allah² ya gama maganarsa ta fita dan ji take numfashinta kamar yana seizing ya ce
"Well! Duk da nasan ke ya kamata na farawa magana amma magana da Balpahn ku shine ya fi, and I want you to relax please Karki sa komai a ranki nayi miki alkawarin ba zaki taɓa dana sani ba Azrah" ya kare magana yana kallon ta amma ko making any move da zai nuna zata iya basa amsa bata yi ba, ya kuma cewa
"Karatu Shine burinki?" Ta ɗan Kalle sa sai kuma ta ce a hankali
"Yes, sir" ya ce
"Zan taimaka miki ki cika wannan burin naki, amma bana so ki ji tsoro, wannan ba abu ne da zai hana miki karatu ba, Rather, I want to support you even if you want to become a professor ne Azrah"
Ta ɗan Kalle sa, sai kuma ta fara jin nutsuwa ta ce
"Amma aiki fah? Zaka barni nayi? Cos ina son taimakawa Umma na da kanwata" ya ce
"Bazan hana ki ba, In Shaa Allah" ta gƴaɗa masa kai ya ce
"Kince baki da waya ko?" Nan ma kai ta gƴaɗa masa ya ce
"Okay" wani ɗan karamin paper ya miƙa mata ya ce
"My private line, sai kiyi saving da shi zaki na kira na" ta karɓa daga haka ya sauka ya buɗe bayan motar ya Ciro wani laida sai kuma ya koma motar har sannan laidar na hannunsa
Siyama da Habibah da suka taso daga tallan su duk a gajiye suke kamar wanda aka musu duka lis, tafiyan ma dakyar suke yin ta, ko hirar da suka saba ma babu dan duk shiru suka yi suna tafiyar su, Sai kwatsam suka hangi wata mota mai haske da sheki 'black Lexus SUV', na tsaye a bakin ƙofar gidansu
Habibah ta tsaya cak tana karewa mota kallo, sannan ta runtse ido tana ƙoƙarin processing ɗin fuskar data hango duk da ta ganta amma bata son believing cewa ita ce
"Kai Habibah... kamar Azrah nake gani daga motar can fah!" Siyama ta faɗa a daƙile
"Wallahi nima dai kamar ita nake gani... ko da yake sai dai mu je ciki mu tambayi Mama ko kuma idan muka je kusa ai zamu gani wacece"
Da sauri suka nufo gida cike da ƙudurci, da kuma tabbatarwa idonsu cewa ba ita ɗin ba ce.
Honorable ya ɓata rai ganin yana miƙa mata laidan tana ce masa ta gode ya ce
"Ba zaki karɓa ba ko? Roƙa kika yi da zaki ce A'a ina kyauta na baki? So, babu kyau maida hannun kyauta baya" da kyar Azrah tasa hannu ta karɓa tana masa godiya
Lokacin da suka iso kofar gidan yayi daidai da sanda Azarh ta juyo tana kallon Honorable cike da kunya tana karban laidan tana masa godiya, suka kalli juna ai basu san sanda suka yi hanyar cikin gidan da gudu ba
Suna shiga gida, kai tsaye suka nufi dakin Mama da zuciyarsu ke ƙuna da tafarfasa cike da hassada
"Mama! Wallahi mun ga wata a mota a kofar gida, kuma kamar Azrah muka gani a ciki!" Mama ta tafe kirjinta ta miƙe tsaye a secs sannan ta zaro idanu ta ce
"Azrah? Wace mota? Me kuka gani?"
Siyama ta zayyano duk yadda suka gani, Habibah kuma na gyara mata inda ta kauce
Mama ta nufi kofar gida a hanzarce tana leƙa, amma tuni motar ta fice
Azrah tana ganin reactions ɗinsu taga sun shiga da gudu tasan definitely Gulma zasu kaiwa Mama shi yasa ta fara Allah² ya tafi bata son draman su Mama su fara nunawa a gaban bako, yana cewa
"Toh sai an jima, sai munyi waya ko?" Ai bata san sanda ta gƴaɗa kai ta sauka da sauri ba tana gyara laidar hannunta ta nufa cikin gidan da sauri
Ya bita da kallo harta shige cikin gidan sannan ya shafa fuskan sa ya tada motar ya bar unguwar nasu.
Mama ganin babu mota wajan wayam yasa ta koma ciki da sauri wanda a lokacin har siyama da Habibah suma sun fito ɗan su sake kallo ganin Mama na musu wani kallo yasa suka leka waje da sauri suka ga babu wata mota a wajan.
Azrah na shiga ɗakinsu Umma da Zahra suna zaune har lokacin suna jiran shigowanta duk kallon ta suke harta ajiye laidan hannunta a gaban Umma
"Wannan fa, daga ina?" Umma tayi tambayar
Azrah ta sunkuyar da kai "Honorable ne ya ce in karɓa, har da wannan..." ta miƙa wani envelope, sannan ta ɗaura
"Kuma wallahi Umma naki karɓa shine ya matsa min"
Zahra ta matso kusa tana buɗe laidar ta ce
"Toh a dalilin me ba zaki karba ba? Naga ai ba roka kika yi ba sannan kuma...." maganar ne ya maƙale a bakinta sakamakon ido huɗu da tayi da wani babban waya a cikin kwalinta ta saka wani ihuuu ta tashi tana tsalle sai kuma ta rungume Azrah tana
"Wallahi dalleliyar waya ya tsiyo miki Yaya duba ki gani, ai wallahi kin more, chap kuma shine zaki tsaya kina nuku nuku da irin wannan mutumin" Azrah ta turata daga jikinta tana hararan ta
Umma ta ce "Sannu Zahra, wato idan kene karɓa ma zakiyi har kike ce mata a dalilin me zai sa taki karɓa ko?" Tana dariya ta cigaba da buɗe laidar wasu haɗaɗɗun Abaya ta ciro tana zara ido
"Kalli Yaya! Egyptian Abaya ce wallahi" Azrah ta mike tayi hanyar ɗakin su, Zahra ta taɓe baki ta cigaba da buɗe laidan ganin ɗayan laidan, laidan chocolates ne yasa ta miƙe ta ce
"Nayi nan, dama anan nafi karfi" Umma ta ce
"A'a karki taɓa komai Zahra ki tsaya har Bappahn ku ya dawo ya gani tukun nan" Zahra taki kallon, Umma itama tayi ɗakin.
Zahra na shiga ciki ta ce
"Wayyo chocolate, lallai dan siyasan nan ya sha kwana, ya iya soyayya wallahi, yasa yadda zai sace zuciyar mutum" Azrah ta ɗauke kai kamar bata san tana wajan ba.
Siyama da Habibah dake tsaye a tsakar gida duk suna jin abin da ke faruwa and yadda Zahra ke magana da karfi da kuma ihun ta suka juya suka koma cikin ɗakin Mama suna faɗa mata
Mama data yi tagumi ta wurga musu wata ashar ɗin ta ce
"Yanzu sai ku ɗaga min hankali ai, ina zan samu nayi bacci yau kince min kunga Azrah a mota? Wato ma har saurayi tayi? Na shiga uku Ni Uwani" ta karasa maganar tana kuma sake wani tagumi
Siyama ta ce "kila wanda take yawo da sune fah Mama, amma Ni nasan ba zai so ta ba"
Mama ta ce "Ai ina fatan hakan kuwa, yadda ƴan unguwa zasu sako ta gaba, ace ma ciki tayi Shegiya sai naga idon Uwar tata ai"
Washegari wata babbar motar kaya ce ta sauke kaya a kofar gidansu Azrah, Mai motar ya ce kayan abinci ne daga Honorable buhunan su shinkafa, cartons ɗin spaghetti da macaroni, kaza frozen, indomie, sugar, da sauransu.
Gaba ɗaya layi ya cika da surutu.
Mama ta fito da sauri tana kallo zuciyarta na tafarfasa, ga kawarta Maman asabe ma data shigo tana taya ta aiki
Ta koma cikin gida ta kwalla wa Bappah kira, bayan Bappah ya dawo daga nuna musu ɗakin Umma suka fara shiga dashi dan shima ya rasa bakin magana, Mama na kallonsa ta ce
"Wannan wane irin abu ne? Me ke faruwa? Don Allah ka faɗa min gaskiya!"
Bappah ya cije lebensa, ya ɗan ɗago ido yana kallon ta, a hankali ya furta
"Honorable ne dai ya ce yana son tallafa musu... kuma yana da wani niyyar Alkhairi ne"
Mama ta goge zufa "bangane tallafa musu ba? Toh kai ba zaka ce musu ba'a bukata ba, tsayama Malam wani Alkhairin kake magana kuma akai?"
Yayi kasa da murya "Ina ji kamar dai Azrah yake so"
Mama tayi wani ashar da sai da Bappah yaja baya
"Wato ƴar kishiya ce za'a ce ana so? Kai ba zaka nuna musu Siyama ko Habibah ba? Amma sai kayi shiru?"
Magana da suke wa Bappah yasa yayi waje danjin me zasu ce, Mama ta wuce ɗakin ta hankali tashe, Maman Asabe na binta a baya danjin meke faruwa.
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL*( SIRRIN SIRRI)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 13: The List They Tried to Erase
Yau tunda garin Allah ya waye duniyar tama Mama zafi ta rasa me ke mata daɗi, abincin da take a gida yau kam hakura tayi dan bata jin zata iya, tunda taga irin Alkhairin da honorable yake da kuma ɗawainiyar shikenan ta rasa sukuni yau kuma da Bappah ke waya da honorable a gabanta cewa magabatan sa zasu zo tambaya da saka rana shikenan ta sake ruɗewa kuma duk yadda ta dinga ma Bappah da ido amma ya kasa bin maganarta balle yayi stopping Honourable, ita kaɗai ke zaune a ɗaki tana ta faman sakawa da warware wa da tunani, hannunta rike da hijab amma har yanzu bata sa ba, wata makwabciyarsu ne ta leƙo siyan Alale ganin ko murhu ba'a kunna ba yasa ta shiga ɗakin Mama da sallama, Mama na kallon ta cike da abin duniya ya mata yawa ta miƙe ta fara magana a zafafe
"Maman ladi wallahi tallahi, idan har aka ce ba za'a fasa zuwa tambaya ba wallahi ko nawa sai na kashe, sai na kashe ko nawa ne nace, dan ba zan iya zama in kwashi bakin ciki ba ina ji ina gani ƴar kishiya ta shiga gidan Hutu" Maman ladi ta sake baki tana kallon ta sai kuma ta ce
"Haba Maman Abdul, dama rabon da Allah ya bawa wani akwai wani mahalukin da zai hana ne? Ni dai shawara ta ki hakura idan ba mijin ta bane ba za'a taba yin aure ba amma muddun mijin ta ne wallahi duk kinki sai an ɗaura" Mama ta katse ta
"Kimin shiru! Kada ki sake min maganar kaddara anan! Me yasa rabon zai fara da Azrah toh? Me yasa Azrah ce kaɗai bayan ina da nawa yaran" Maman ladi kam abin ma mamaki yanzu ya fara bata tana kallon tsantsan kiyayer Umma a idon Mama
Mama ta miƙe tsaye ta fara zaga ɗakin tana huci kafin ta tsaya, har sannan Maman ladi bata daina kallon Mama cike da mamaki ba, Mama ta ce
"Ki barmin kofar ɗaki dama na daɗe da sanin cewa bakin ku ɗaya da ita ai shiyasa zaki zo kina kare ta naga kema ƴaƴa matan gare ki amma ai har yanzu suna zuɓe a gaban ki! Idan ma Ni kaɗai ce toh sai nasan yadda za'a yi a fasa wannan zuwa gaisuwar wlhi, Malamai kuma nawa ne a cikin garin nan"
Maman ladi ta sake labulen ɗakin Mama ta ce "Ni Kinga tafiya ta, Allah ya yaye miki" daga haka ta nufa kofa sai kuma ta tsaya ta juyo tana kallon kofar ɗakin Umma sai akwai ta fita abinta.
Bayan wasu kwanaki
Bayan sun gama candy har saura kwana biyar su fara WAEC, Azrah ta faɗa duniyar karatu sosai dan koda yaushe tana riƙe da littafin ta, tana kuma kokarin kula da kasuwancinta kamar yadda ta saba, sosai honorable ya bata space ganin ta ɗauki karatun first priority ɗinta sannan zuwan ma ya daina sai dai har sannan basu bukatar komai dan yakan kawo musu everything enough. Wata rana yazo kamar kullum ta same sa a motar sa ta gaishe sa dan har sannan bata iya kallonsa balle ta iya magana mai tsayi a gabansa sai dai a waya, nan ma bawai takan yi sosai bane, tana ta sauraronsa wanda rabin Maganan ma shi kaɗan sa yake yi, ya ɗan ja hankalinta da tambaya
"Azrah, please give me Zahra's full name and age da kuma wani aji take yanzu, I want to do something for her" Azrah ta kallesa cike da mamaki sai dai bata ce komai ba
"Sir... Her name is Zahra Muhammad Sulaiman, She's sixteen, she's in Jss3" honorable ya gƴaɗa kai ya ce
"Perfect! I like her courage... remind me to send someone" Azrah bata fahimce shi ba amma saboda bata iya masa magana yasa tayi shiru kawai
Mama tayi sallama a gidan Maman asabe, Maman asabe ta fito daga ɗakinta tana gyara zanin jikinta ta ce
"A'a Maman Siyama kece a gidan namu, toh karaso mana" Mama ta karasa ta zauna tayi tagumi tana kallon Maman asabe ta ce
"Kinga ba zama ya kawo ni ba, yanzu so nake ki taimaka min ki bani shawara mai zan aikata wanda zai sa a fasa auren yarinyar nan" Maman asabe tayi shiru dan ita bata san me zata ce ba can ta ce
"A'a ga shawara nan, ina kince mutumin ɗan siyasa ne ko? Kawai a ɗauki fuskarta a ɗaura akan video ƴan iskan mata sai a kai masa Kinga ba zai so ace zai haɗa iri da ita ba ko dan kar a ɓata masa kujerar mulkinsa" Umma tayi wani shewa harda miƙewa tsaye ba tare data san tayi hakan ba tana kallon Maman Asabe ta ce
"Toh ai har kin fini tunani, yanzu wa zamu samu su mana wannan aikin ne? Nifa a shirye nake dana kashe ko nawa ne?" Maman Asabe ta ce
"Zan kira Garba naji ya za'a yi dan nasan ba zai rasa sanin masu yi ba" Mama ta fara dariya ta ce
"Kinga kuwa yadda ƴa unguwar nan suke kallonsu kamar gold zasu fara kyamar su suma".....
Umma da yaranta suna zaune suna hirar su cike da sha'awa da ban sha'awa, sai ga wayan Azrah ya fara ringing, Azrah ta ce
"Dan Allah Zahra ɗauka kice ina bacci" Umma ta kalleta Zahra ta ɗauki wayan bayan sun gaisa ta isar masa da sakon da Azrah ta bata ya ce
"It's Okay, dama ke nake son gani Zahra, ki fito ina kofar gida" daga haka ya katse kiran Zahra na kallonsu ta ce
"Yace wai dama da Ni yake son magana" Umma ta ce
"Toh ki tafi" daga haka Zahra ta ɗauki hijab ɗinta ta fita
Tana isa jikin motarsa ya sauke glass ɗin yana kallonta, murmushi tayi ta ce
"Sannu da zuwa Sir" honorable Ibrahim ya ce
"Sannu Zahra, kin kammala homework ɗinki kenan?" Zahra tayi murmushi ta ce
"Na gama tun ɗazu Sir" Ya ce
"Ma Shaa Allah" wani envelope ya ɗauka a dashboard ɗinsa ya mika mata ya ce
"Take this, naki ne idan kin shiga ciki sai ki duba ko?" Ta karba tana masa godiya, daga haka ya tafi
Da sauri ta shiga dan tana son kallon menene a ciki, Umma da Azrah sai kallonta suke bayan ta Ciro da papers ɗin envelope ɗin Azrah ta karba da sauri dan ganin kamar admission letter ne, sake baki tayi tana kallon papers ɗin, One of the best school ya mayar da Zahra sannan ga receipt na biya mata school fees tun daga SS1 to 3, ga kuma sauran receipts na other stuff, sanin wane shi shiyasa ko maganar interview ba'a nema a mata ba aka gama mata komai, Azrah taji hawaye ta mikawa Umma takaddun ganin yan kashe wajan 1.5M, lokacin da Zahra tayi tozali da sunan makarantar bata san sanda ta miƙe tsaye tana ihu da salle salle...
Azrah na karbar notice daga wani student, dake itace headgirl sai ga wani student ya zo yana kallon ta ya ce
"Senior Azrah principal na kiran ki a office, wai kije" Azrah ta kafe sa da kallo kamar bata gane ba sai kuma ta ce
"Where is he kace?" Ya ce
"Yana office ɗinsa ne" kai ta gƴaɗa masa ta sallame ɗalibin gabanta, Kalle Kalle ta fara ko zata ga Fatima dan ita tun wancan maganar daya gwada mata taji ta tsane sa kuma bata son zuwa office ɗinsa ita kaɗai ganin bata ga Fatima ba kawai ta nufa jiki ba ƙwari
Da sallama ta shiga ta same tare da wani Malami ta ce
"Sir, gani" ko kallonta bai yi ba ya cigaba da magana da ɗayan Malamin har ya gama masa bayanan sannan ya fita, Azrah dake kallon wani waje taji muryan sa
"Azrah look I want to help you, But I can't fight government for a stubborn girl like you" Azrah cikin nutsuwa
"Thank you Sir, amma I'll be fine" Principal ya tsaya kallon ta da mamaki dan bai taɓa expecting haka daga gareta ba, ya ce
"Okay! Out of my office! Since you feel big!" Ta juya ta fita ba tare da taji ɗar ko wani tashin hankali ba dan hundred percent sure honorable ya gama saka sunanta and he has nothing to do sai ya karata da iskancinsa
Da kallo baki buɗe ya bita with lots astonishment, yafi some secs yana processing sai kuma yayi dariyar mugunta ya jawo wani long book da aka saka result ɗinsu na candy a ciki, cire sunanta daga cikin jerin sunayen da gwamnati zata biya musu WAEC yayi, yana dariyan mugunta ya ce "Zanga me tsaya miki kuwa, zanga karshen rashin kunya ai"
Azrah na fita ta duba bata ga Fatima ba kawai tayi tafiyarta tana mamakin hali irin nasa, tsaki tayi tana sake godewa Allah daya haɗata da honorable sai yanzu ma take sake ganin honorable Ibrahim a matsayin wani wall a gareta...
Zahra na wanke wanke while Azrah na kitchen tana tuka abincin dare, ta gama kwashe abincin a kula ta kai ɗakin Umma sannan ta kwashe waste dishes takai ma Zahra daga haka ta wuce ɗakin Umma ta zauna, Zahra dake wanke wanke kamar daga sama taji shigowan Abdul wanda da fito ma ya shigo gidan ɗan kallonsa tayi ta ɗauke kai ta cigaba da abinda take yi, ɗan tsayawa yayi ya Kalleta ya ce
"Ke dan Uwarki baki ganni bane da ba zaki gaishe Ni ba?" Tayi kamar bata jisa ba, ya gƴaɗa kansa ya ɗauki buta ya nufa hanyar banɗaki, ajiye kayansa yayi a wajan sannan ya shiga
Zahra ta kai sauran kayan data wanke ta fito tana kallon hanyar toilet inda ya ajiye kayan a kasa, taka wa tayi a hankali harta isa wajan kallon wayansa da tayi a ajiye tare da wasu stuff ɗinsa ne yasa bata san sanda murmushi ya ƙuɓuce mata ba ta ɗauka da gudu tayi ɗakin Umma ta shiga tana haki, Umma na kallonta ta ce
"Wani rashin gaskiyan kika aikata Zahra?" Azrah ta kalleta sai kuma ta cigaba da abinda take yi, Zahra ta zauna tana murmushi
Umma ta kalli wayan hannun Zarah ɗin ta ce
"Zahra wannan wayan waye kuma? Sannan Meyasa zaki shigo a guje?" Ta kare maganar tana tamke fuskan ta, Zahra ta ce
"Dama nayi rantsuwa ai Umma, wayan Abdul ne kuma nace sai ya biya kuɗin daya ɗauka, so yanzu ne right time, ya biya ba tare daya sani ba kamar yadda ya ɗauka ba tare daya tambaye mu ba" Umma ta ɓata rai ta ce
"Zahra bana son wannan halin naki, bana son kina ɗauke abun mutane da sunan kina rama abin da suka miki, how sure shi ya ɗauka" Zahra ta ɓata rai ta ce
"Bayan Yaya ta kama sa" Umma ta ce
"Ki mayar masa nace, obey before complain Zahra" Zahra ta turo baki tana kallon Azrah irin tasa bakin nan amma Azrah yi tayi kamar bata ma san meke faruwa a wajan ba, Zahra ta ce
"Ai naga shi ya fara sace kuɗin candy ɗin Yaya Azrah ranan, Da ba dan Allah ya turo Honorable ba, da ai har yanzu muna kuka"....
Abdul yana fitowa a banɗaki yazo kwashe kayansa sai baiga wayansa ba da sauri ya zazzaga kayan nan ma baiga komai ba, wani ashar ya yi, sake duba kayan yayi da bai gani ba ya fara ihu
"Mutum daga dawowansa sai sata! Wallahi idan ban ga waya ta ba yau za'a ga abinda zanyi a gidan nan ashe baku Sanni bama kenan" Umma tana kallon Zahra da suke jin ihun Abdul da zage zagensa ta ce
"Zahra bani wayan idan ba zaki maida masa ba" Zahra ta ja baya da sauri ta ce
"Umma nayi rantsuwa fah" wani kallo ta mata wanda yasa ta miƙe ba shiri.
Bayan kwana biyu..
An manna sunayen waɗanda gwamnati zata ɗauki nauyin WAEC dinsu, Principal ya ƙaraso da takarda a hannun sa zai manna a notice board saboda kowa ya gani, ya ɗaga hannunsa zai manna sai gani yayi...
"Azrah Muhammad... number one?" With shock written all over him yake kallo
Yayi shiru, ya tsaya, ya kasa motsi, while ga students duk shi suke jira ya manna ɗin su gani hankalin su ya kwanta amma principal ya kasa koda ce uffan ne, kamar me whispering ma kansa ya ce
"Amma.... I removed it myself"...
Bayan kwana biyu..
Zahra ta fara sabuwar rayuwa a private school da honorable ya maida ta, Azrah na cigaba da karatu da kasuwanci sannan har sannan bata barin ibada.
Wata rana ta shiga school saboda research Principal ya kirata bayan ta tafi office ɗinsa ya sassauta nuryansa ya ce
"Azrah..Kin cancanta everything and more, Sorry for before"
Ta kalle sa sai kuma ta rasa me zata ce masa ta ɗan kalle sa taga ita yake kallo sai kuma ta mike ta fita a office ɗin ba tare data ce masa kala ba, principal ya bita da kallo yana mamakin yaushe tazo tana masa kuka akan ya taimaka mata amma yanzu wai yaze a cire sunan ta akan mistake ne
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 12