sai kawai aka masa warning cewa idan beyi hankali ba zai iya rasa aikinsa.
Da yamma Azrah na tsakar gida tana kulla gawayinta sai ga Siyama da Habibah sun shigo ko da wasa bata ɗaga kai ta lalle su ba, sai kawai taji dariyarsu Siyama ta ce
"Kin ji ‘yar masu baiwa ko?A yanzu ma ita ce first name a list ko?" Habibah ta ce
"Ƴar gayu mana, ai yanzu jin kanta take ita wata shegiyar ce"
Azrah ba ta ce musu komai ba, sai ga Zahra ta fito
"Eh mana, ai dole taji da kanta ko kunga tayi kama da kalarku ce? Ai duk wanda ya ganta yasan ba ƴar gidan wahala bane, balle ta tsaya biyewa jahilai" Azrah ta juya tana kallon Zahra
Siyama da Habibah suka yi kanta da gudu suna zaginta amma ina tuni ta wuce ɗakin su ta window ta sa bakinta tana zagin su
Siyama ta ce "idan ba tsoro ba ki fito mana" Zahra ta ce
"Idan ba girma ya faɗi ba ina ke ina faɗa da Kanwar bayan ki? Ai shine maraban jahili da mai ilimin kenan, yanzu kun taɓa ganin Anty Azrah na cacan baki da ku"
Saukan mari taji da sauri ta juya tana kallon Umma sai kuma ta fara kuka, Umma ta ce
"Zahra ki shiga hankalin ki, bana son Wannan neman maganar naki"
Har sannan su Siyama basu fasa zage zage da suke ba daga karshe Azrah ta koma ɗaki.
Da daddare Mama na zaune a ɗakinta ga yaranta kewaye da ita can ita kadai ta furta
"Auren nan dole sai an fasa dan ba zan yarda ina ganin ƴaƴan Bitti suji daɗin rayuwa ba"...
Few Free pages ya rage, better ku biya kafin labari ya fara ɗaukan zafi
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL*(LABULEN SIRRI)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 14: The Price of a Daughter
"Ke Maman Asabe, yau ba sai kin zauna ba, mu tafi yanzun nan kafin ya fita tunda kince baya zama" cewar Mama tana takawa da sauri cikin riga da zani da mayafi daya rufe mata har kunnenta.
Maman Asabe tayi wani murmushin mugunta "Toh ai ni dama a shirye nake na ɗauka sai kin huta zamu" ta miƙe ta fara bin bayan Mama Wanda har tayi gaba ta ce
"Wannan mutumin da ake kira Garba dai ba wasa bane, ya taɓa jefa wata ‘yar unguwarmu na can zango cikin matsala har iyayenta suka koreta"
Dukkansu suka nufi bakin titi cikin shigarsu na gaggawa dan babu waccan take cikin nutsuwarta, Mama na ta furzar da iskan baki ta ce
"Ni wallahi ba zan bar yarinyar kishiyata ta fi nawa ba, Ai na haifi ‘ya’ya mata har biyu, ko ɗaya cikinsu ba ta taɓa ganin arziki ba sai wannan Azrah ɗin, In banda isa da ɗabi'a irin tata koda wasa bata yarda tayi wanka da Omo Bansan aina take samun waɗannan kuɗin ba gata sai uban saka kaya sai ka rasa aina take samun waɗan nan"
Maman Asabe ta ce
"Ki kwantar da hankalinki, Idan wannan mutumin Garba ya haɗa video ɗin nan da muke so, wallahi Honourable sai ya gudu da ƙafarsa ko sake waiwayo ta ba zai yi ba, wannan fa har tsoronsa nake kamar ba mutum bane sai kace machine ne".....
Bayan sunje sun faɗa masa yadda suke so ya zama, lokacin da suke hanyar komawa gida, Mama sai murna take dan yanzu hankalinta ya gama kwanciya ta ce
"Wallahi na san wannan abun zai yi tasiri, Yanzu sauran kawai mu nemo hoton ta ko wani short video nata kamar yadda ya faɗa"....
Da daddare a ɗakin Bappah, Umma na zaune tare da shi, duk sunyi shiru ba mai magana a cikin su, sai can Bappah ya daga kai yana kallon Umma ya ce
"Bitti, Honourable ya kira, jibi ne zasu zo a saka ranar auren wai,
ya ce komai ya shirya yanzu"
Umma ta dinga kallonsa kamar wanda ya dawo hayyacinsa dan ita bata yarda da changes ɗin nan nasa gareta ba sai sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Allah ya nuna mana, sannan muma Allah ya bamu abinda zamu fita kunya da shi"
ya amsa da Amin, daga haka ta miƙe ta fice daga ɗakin nasa tana jin damuwarta yana dawowa sabo full bata san yaushe zata goge wannan zanen kaddarar ba? Ita yaushe ne zata samu nutsuwa ga ciwon daya sata a gaba tana tsoron ta mutu yanzu ba tare da ta sake waiwaye wannan......
Bappah ma ya miƙe ya nufa kofa yana haska compound ɗin yana dube dube sai ga Abdul ya shigo gidan yana fito kamar wanda bai san sallama ba
Bappah ya daka masa tsawa sannan yana masa wani banzan kallo ya ce
"Ni dai na gaji da halin ka Abdul, kullum baka taɓa abu kamar nagari, ina ka je bana ganin ka kwana biyu a gidan nan?"
Abdul ya ɗan taɓe baki, "Toh ai ba wani abu nake ba sannan ba wani wajan nake zuwa ba..." Bappah ya daka matsa tsawa
"Toh idan ba wani abu kake ba, sai kayi ta yawo? In baka daina ba wallahi zaka bar min gida na rantse dan bana son iskancin banza da shashanci"
Abdul ya wuce ɗakin Mama yana huci, Mama na zaune tana tsince wake ta ɗaga kai ta kalle shi
"Me ya faru kuma?" ta tambaye shi
"Wannan tsohon faɗa faɗa kamar shi kadai ya fi kowa ganin laifi? Ni dai gaskiya na gaji kija masa kunne, tahm" ya fadi yana zama akan wani ruɓeɓɓen kujera
Mama na kallon yaran nata ta ce
"Yauwa ga wani aiki ya samu, hoton Azrah nake so ko kuma video nata, duk wanda ya kawo min yana da dubu goma"
Siyama da Habibah suka haɗa baki wajan cewa "Ni zanyi" wani kallo Abdul ya musu wanda yasa Siyama ɗauke kai tana hararansa yana kallon Umma ya ce
"Umma ba wanda zai yi a cikin su, naga ba waya garesu ba taya zasu fara, kema kin san wannan aikin nawa ne kawai" Umma na Murmushi ta ce
"Toh ka samu ka kawo min zuwa gobe da safe" yan kallon Umma ya ce
"Zan kawo miki kamar yadda kika ce amma ina fatan kuɗi na ba zasu yi ciwon kai ba ko? Kinsan bana wasa da harkan kuɗi" Umma ta ce
"Kana kawo min zan dasa maka kuɗin ka" ya gƴaɗa kai daga haka ya miƙe zuwa ɗakinsa dan kwnaciya
Washe gari da safe, Zahra ta fito cikin sabuwar uniform ɗinta tsaf-tsaf! Farar rigar da Black skirt sun yi mata kyau fiye da zaton mai zato
Azrah dake wanke wanke a sakar gida ta ɗaga kai tana kallonta ta ce
"Zahra ina zaki haka da wuri?" Ta kare maganar cike da zaulaya
Zahra ta yi murmushi,ta ɗaga jaka "Sabuwar makaranta mana, Private school ma kike ji, Allah ya saka ma Honourable, Allah ya ƙara masa fiye da haka"
Azrah ta yi murmushi bata da buri fiye da ganin Zahra na Murmushi ita da Umma, amma Maganar honorable Ibrahim babu wanda ya san me ke cikin zuciyarta, Hope and pain suna fafatawa
Tana gama aikinta ta fara kulla gawayinta ba tare data kalli Mama da Maman Asabe da suke tsakar gidan suna haɗa kayan tallah, tana ji suna jefa mata magana amma sai tayi kamar bata ma fahimce su ba ma dan ta basu uzuri yau ta sake gaskata rashin ilini na haifar da komai but how iyn earth zaka na ma ƴar cikinka habaice
"Wasu suna jin cewa idan sun iya abinci da sana'a sannan sunyi candy, to sun gama rayuwar kunci fah, daɗi ne zai biyo baya, ai muma mun yi fiye da haka" inji Maman Asabe tana kallon Azrah kai tsaye
Azrah ta shige kitchen ba tare da ta ce komai ba, Ta ɗauki gawayi zata hura dan ɗaura wa Umma ruwan wanka
Abdul ne ya shigo kamar zai wuce, tuno deal dinsa da Mama yasa ya tsaya ya ciro wayarsa, ya ɗan juyar da camera
Azrah da bata san komai ba ta zauna tana kan ketta ashana ya ɗauketa ba tare data sani ba, su Mama ganin haka suka wuce ɗaki da sauri suna jiransa fuskokin su cike da murmushi
Yana shiga ɗaki ya ce da Mama
"Na gama nawa, miko min kuɗin"
Mama ta amshi wayar ta ciro dubu goma ta mika masa
"Gashi Allah ya saka"
Daga nan ita da Maman Asabe suka fita zuwa wata shago, suka kira Garba
"Garba! An samu, gashi nan a waya, amma ba ta nawa wayan bane zamu turo maka kafin yamma"
"Tura min kafin karfe biyu dai" Garba ya fada da murya mai sanyi amma mai cike da mugunta
Mama ta yanke kira tana kallon Maman Asabe ta ce
"Yanzu ya zamu yi gashi dai kuma kema wayar naki karama ce kuma yace kafin karfe biyu"
Maman Asabe ta ce
"Sai muyi amfani da wayar asabe na kawai"
Da daddare bayan Mama ta tura masa 50k yace zata kara masa ita bata san kuma ya zata yi ba amma damuwar ta ba anan yake ba tunda aiki za'a mata
Sake kiranta yayi ta ɗaga ya ce
"Na tura ma babban namu videon, yanzu zaki cika da sauran kuɗin ko?" Mama ta ce
"Naji wannan ba matsala bane, shi ogan naku me yace?" Ya ce
"Yace a basa 24 hours, zai gama aiwatar da komai"
Mama tamiƙe tana hamada ta ce
"Toh Ni yanzu damuwata gobe zasu kawo gaisuwar nan ne fah ina so tun kafin su zo ya kalli videon nan" Garba ya ce
"Kina da gaggawa ne matsala ta dake wannan harkan ba yanzu muka fara ba amma sai ki bi kiyi ta harzuka mu idan kuma ba'a yi daidai bafa" Mama zata yi magana ya katse kiran abin sa
Washe gari da yamma misalin 4:30pm
Unguwar Kofar Marusa ta cika da SUVs gwanin ban mamaki Black Prado, Range Rover, har da wasu manyan Hilux. Yara suka cika titi suna tsalle da dariya ganin motoci a arean su, mutane suna ta leƙowa ta window ganin meke faruwa
Bayan Abokin Bappah ya shigo dasu cikin compound ɗin da aka gyara ba zaka taba cewa gidan bane, duk suka zazzauna aka fara gaisawa cike da mutunta juna..
Mama daga cikin dakin ta ji hankalinta ya kasa samun sukuni ta tafi jikin labulen ta yaye labulen tana leƙansu... "Na shiga uku Ni Uwani!" Ta furta a hankali ganin manyan mutane da ke cikin gidan
Zahra ma leƙawan tayi ta ce
"Laaah! Wallahi manyan mutane ne Yaya... ga su can suna zazzaune" ko kallonta Azrah bata yi ba tana fama da zazzabin da take ji kamar zai rufeta ne
A tsakar gidan duk suka gama introducing kansu da kuma abun da yake tafe da su
"Munzo tambaye da kuma saka rana gaba ki ɗaya"
Bayan duk sun saka baki Bappah yace a bari sai bayan ta gama exams ɗin ta sannan da sati sai ayi bikin wanda duk sun tafi a akan hakan
Anan ake faɗawa Bappah Honorable Matan sa biyu
Bappah yayi shiru sannan ya ce Allah ya haɗa kansu shi kuma ya basa ikon yin adalci a tsakanin su
Sannan wani dattijo ya mika envelope yana cewa
"Ga Sadakin mu 1 million naira"
Gaba ɗaya wajen ya ɗauki silent gasp
Wani abokin Bappah ne yayi breaking silence ɗin da cewa
"Amma bai yi yawa ba? Kaɗan mai albarka ake so ai" wani dattijo ya ce
"Hakan ma ba laifi bane Babban fatan shine Allah ya basu zaman lafiya"
Da zasu tafi Bappah da abokansa suka raka su har bakin mota suna godiya
Bayan tafiyan su Bappah suka ɗanyi magana da abokansa sannan suma ya raka su kafin ya dawo cikin gida dakin Umma direct ya shiga
Bayan ya zauna ya gama musu bayanin abinda ya faru sannan ya miƙa ma Umma kuɗin ya ce
"Ga Sadakin ta nan sun bada" ya fada yana kallon Umma da Zahra
"Na wa ne?" Zahra ta tambaya da karamin muryan ta
"Million daya"
Umma da Zahra suka zaro ido, "Miliyan ɗaya!?" Bappah ya gƴaɗa masu kai
Bappah ya kuma cewa:
"Amma fa... akwai wata magana da suka faɗa min"
Umma ta dago da sauri ta ce
"Wace magana?"
"Wai Honorable yana da Mata, Mata biyu ma"
Zahra ta zaro ido ta ce "Ya Salam!" Umma kam ma ta gagara magana dan bata san me zata ce ba at this point, Mata bama Mata ɗaya ba har biyu? Hakan na nufin Azrah zata je ta uku Inaaa bata san sanda ta girgiza kai ba ta kalli kofar ɗakinsu Azrah, nan da nan fuskar ta ya cika da damuwa ta, rayuwarta ne yayi flashing a brain ɗinta nan da nan jikinta yayi sanyi tana kallon Bappah ta ce
"Allah ya zabar mata mafi alkhairi, amma wallahi jikina yayi sanyi da wannan maganar"
Bappah ya ce "Ni kaina sai da jikina yayi sanyi ba kaɗan ba" Zahra ta ce
"Gaskiya duk son hutuna ba zan so Yaya Azrah ta shiga kan kishiyoyi har biyu ba, dan Yaya ba magana take ba dama nice nasan yadda zan kwace ƴanci na" Umma ma tunanin da take kenan sai gashi Zahra na faɗa
Meanwhile... Mama
Mama tun lokacin data lekasu ɗin nan tana daki tana share zufa Tana jin tafiyarsu Bappah ya dawo, ta fito da sauri.
"Me ke faruwa a gida? Su waye su din ne?"
"Sun zo tambayar auren Azrah ne har sun bada sadaki" Bappah ya amsa mata a takaice, Umma ta zaro ido waje abinda bata son ji ke nan
"Sadaki?!" ta faɗa da karfi Bappah ya ce
"Eh" Mama a na kallonsa ta ce
"Na wa?"
Bappah ya ce cikin sanyi murya
"Million daya"
Mama ta durƙusa, ta dafe ƙirjinta, nan da nan idonta har ya cika da hawaye "Na shiga uku! Azrah zata shiga gidan hutu? Har an sayar da rana ga sadaki million daya?" Bappah ya ce
"Ki tashi ki gode wa Allah, ki kuma tsanya mata Albarka sai Kiga Allah ya kawo wa su Siyama ma" wani bad look ta masa ta ce
"To kuɗin fa?"
"Na bawa Ummanta itace uwarta ai"
Mama tayi shiru, sannan ta wuce daki tana gyara zaninta daya kusa faduwa, ba tare da bata lokaci ba ta sanya hijab ta fita waje, bata ko damu da cewa Maghrib ya kusa ba, gidan Maman Asabe ta nufa dan bata jin zata iya hakura dan yanzu ma ita kaɗai tasan me take ji
Da daddare.. Umma na zaune a ɗakin su tana yanka fruits, Azrah na kusa da ita tana gyara notes ɗinta wanda tun ɗazu take avoiding magana da Zahra dan bata son jin komai game da saka rananta Umma ta sauke ajiyar zuciya ta ce
"Azrah ina son ki bani hankalin wani abu zan fada miki... "
Azrah ta dago kanta, ta ajiye pen ɗin hannunta tana kallon Umman
"Sun zo tambayar aurenki ɗin sannan an basu... sun bada sadaki... million daya..."
Azrah ta janye hannunta daga Umma, ta rufe book ɗin gabanta Idonta ya yi jajir lokaci guda, Umma ta sake gyaran murya ta ce
"Amma... akwai wata magana, sun ce yana da mata har biyu fah Azrah" Azrah tayi shiru tana ta kallon Umma cike da mamaki kamar bata fahimci me take cewa ba
Sai kuma ta kalli kasa tana jin zuciyarta na bugawa kamar wanda ake controlling bugawan
Umma ta kalli yarinyar nata cike da tausayawa ta ce
"Allah ya zabar miki mafi alkhairi Azrah, Amma wallahi jikina yayi sanyi, sai dai ba hakan yake nufin bashi ne mafi Alkhairi ba, zan cigaba da miki addu'a" sai sannan Azrah taji hawayen idonta ya soma zuwa ta ɗan kalli Umma sai kuma ta sauke idon ta kasa dama tun farko taga ya mata kama da mai mata, kuma tun farko ya mata girma yanzu kuma ga wata maganar mata har biyu ta share hawayen daya gangaro mata ta miƙe ta fita ba tare data kalli Umma ba...
This book costs 500. Make the payment to Hauwa Jibrin, Wema Bank account 0421255553, and send proof of payment to 08110615256.
*BEYOND THE VEIL*(LABULEN SIRRI)
YOTA ID/026
Wattpad © Jiddatulkhayr
Instagram © Jiddatulkhayr writes
Free page
Episode 15: A Cry Beneath the Veil
Tafiya take cikin sauri kamar bata ganin gabanta ko kula yaran dake gaishe ta bata yi damuwarta ta ganta gidan Maman Asabe, zuciyarta banda bugawa babu abinda take kamar waccan ba zata isa gidan ba. Tana isa gidan Maman Asabe, ko kwakkwaran sallama bata yi ba ta shiga
Ta tarar da ita tana shirin yin Sallah, Maman Asabe ta ɗago tana kallonta da mamaki, Mama ta ce
"Maman Asabe wallahi abin da nake tsoro shi ya faru yau!" Ta karasa maganar tsantsan bakin ciki yana bayyana a fuskarta
A mugun razane Maman Asabe ta gwalo ido tana kallonta ta ce
"Ban gane ba? Sun zo kenan kike nufi ko kuma an saka rana ne?" Mama ta sake share zufanta na countless times ta ce
"Su dai sun iso, Motoci sun cika titin mu fah yadda kika san ƴar gidan gomna za'a zo tambaya, ashe sadaki suka kawo, Ni duk ba wannan ba Sadakin ne yafi tsaya min a rai Maman Asabe" ta kare maganar tana share hawayen bakin ciki da suka fara sauka kan kuncinta, Maman asabe ta dafe kirjinta ta ce
"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un!" Mama ta ce
"Mu shiga ciki tsayuwa anan bai kama mu ba, ki kira mana Garba muji me ake ciki yanzu"
Bayan Mama sun kira shi harya katse bai ɗauka ba sai can kuma gashi ya kira back, muryarsa da sauti mai ƙarfi cike da Mugunta ya ce
"Yanzu na karɓi confirmation, video ya tafi hannun sa, Kuma na sa anyi forward zuwa numbern sa kai tsaye"
"Ya ce me?" Mama ta tambaya
"Baice komai ba tukuna... ya karɓa ne kawai, Amma ya ƙara cewa za'a ji daga gare sa da daddare ko gobe da safe"
Mama ta kashe wayar, ta miƙe tana kallon Maman asabe tace zata koma gida. ta nufi gida a hankali kamar wacca kwai ya fashe mata a ciki. Bata karasa ɗaki ba kawai ta tsaya nan sakar gidan ta fara Alwala tana idarwa ta wuce ɗakinta ta kama sallah, tana idarwa ko addu'a bata fara ba sai ga su Siyama sun shigo kamar wanda aka wurgo su haka suka faɗa ɗakin, fuskokinsu kamar wanda basu taɓa sanin wani abu wai shi murmushi ba
"Mama... gaskiya ne wai motoci sun cika kofar gidan nan? Sunce har Governor ya zo? Kuma akan maganar Azrah ce ko?" Habibah tayi maganar cike da damuwar da ya bayyana ƙarara a fuskanta
Mama ta kalle su, idonta ya cika da hawaye, tayi ajiyar zuciya sannan tace
"Toh ku zauna mana zan gaya muku amma kun tsaya min a ka"
Duk zama sukayi Siyama so kawai take taji ance mata A'a, duk Idanu suka zuba mata, Mama ta ce
"Wannan abinda kuka ji gaskiya ne, sun zo, kuma sun bada sadaki Naira na dukan Naira har miliyoyin ɗaya fah, biki kuma tana gama jarabawa za'a yi"
Kafin ta ƙarasa Habibah ta fashe da kuka, Siyama ta rike kanta tana fadin
"Ya Allah! Amma meyasa haka? Me yasa Bappah zai yarda bayan yasan na girme ta, har Habibah ta girme ta amma sai ya fara aurar da ita kuma?"
Mama ta share hawayenta, ta dafe kirjinta
"Ku kyaleni mana... wallahi yau ɗin nan zuciyata ta yi nauyi, kar ku kara min wata damuwan kuma... Allah ya zabar mana mafita".
Daren ranar, Azrah bata iya rintsawa ba, ta juya daga hagu zuwa dama, daga dama zuwa hagu aikin kenan, zuciyarta cike da rikice-rikicen da basu da suna, ta rike pillow ɗinta kamar zai ba ta amsa, tana starring waje guda
"Yaya zan zauna a matsayin mata ta uku? Ni da ko fiye da 18 ban yi ba? Yaya makomata zata kasance a gidan cikin manyan Mata? Umma, Zahra, Bappah... duk suna mafarkin jin dadina, Amma me zai faru da ni?"
Zuciyarta tayi mata nawi sosai gashi bata son ko da wasa ta daga ma Umma ciwonta, A hankali ta miƙe, tsakar gidan nasu ta fita ta ɗauro alwala sannan ta koma daki ta shimfiɗa sallaya ta fara sallah tana faɗa wa Ubangijinta damuwarta.
Bayan ya dawo gida very late ɗakinsa ya wuce direct, ajiye expensive phones ɗinsa yayi a bed side sannan ya cire kayan jikinsa ya wuce toilet dan fresh up, yana fitowa ya ɗaura sleep wear ɗinsa, ya haɗa tea yana sha wayansa yayi kara alamar shigowan message kallon wayan yayi sai kuma ya ɗauke kansa baya son wani damuwa shiyasa kawai ya tsaya a bangarensa saboda yana bukatan rest and probably bazai wuce first wife ɗinsa bace ta turo da sakon, miƙewa yayi ya ajiye cup ɗin sannan ya koma kan gado yayi sliding wayan new number ya gani amma sai ya share ya shiga searching numbern Azrah magana ya mata a Whatsapp ganin bata online kawai sai ya sauka har zai fita a Whatsapp kuma sai ya danna ya shiga wannan numbern, videos ya gani haka kawai yaji gabansa ya faɗi saboda yadda message ɗin ya shigo ba sallama balle wani content kuma private line ɗinsa ne ya daure ya danna download na video ɗin, nan take ya buɗe, playing video din yayi bai san sanda ya tashi daga kan gadon ba ba shiri yana zaro ido meanwhile yana girgiza kai trying all positive kar ya yarda da wannan videon.
Fita yayi a Whatsapp ɗin ya zauna speechless ganin hakan ba mafita bane kawai ya ɗauki ɗayan wayansa wani number yayi dialing ana ɗaga wa ya ce
"Ka duba DM ɗinka na tura maka abu, Find out who sent the video, Get me everything, names, locations, the sender's intent, I want to know who is trying to ruin this.." Bai karasa ba kawai ya katse kiran jin wani tsarawan da kansa ke masa
Honorable ya sake kallon fuskar Azrah da ke cikin video ɗin, yana jin wani abu mai wuyar fassara, tsakanin so, ƙiyayya da rudani, amma abu guda ya bayyana a zuciyarsa "She will be mine. No matter what" but yanzu yana son ya san dalilin hakan da gaske ne ko kuma sharri ne.
Washe gari da safe Mama ta tashi da mugun zazzaɓi wanda har hakan yasa ta gagara ɗaura abincin tallah, Zahra tunda sassafe ta gama shirin school ɗinta ta tafi, Azrah da itama ta tashi da zazzaɓin ta ɗaura breakfast ta kama aikin gidan saboda in few days zasu fara waec yasa bata zuwa makaranta tana cikin wanke wanke sai ga Siyama ta shigo gidan ko kallon ta Azrah bata yi ba, Siyama ta ce
"Sannu Malama, ai yanzu kina ji da kanki shiyasa ko magana baki ma mutane saboda kina jin Yanzu kinfi karfin mu ko? Toh ki sani gwara ki daina murna dan wannan ba inda zai kai ki kina nan cikin gidan nan"
ko da wasa Azrah bata kalli direction dinta ba ta kwashe kayan data wanke ta kai kitchen ta fito zata share compound ɗin ta kalle ta har sannan tana tsaye rike da kugunta ta taɓe baki, wani ashar ta jefa mata, sai sannan Azrah ta kalleta ta ce
"Look! Ki kama kanki please, kiyi maintaining wannan respect bond ɗinda ke tsakanin mu, Kinga nace wani abun ne? Balle kiyi tunanin saboda gaisuwar da aka kawo har zai sa na canza?"
Wani shewa Siyama tayi duk da bata fahimci wasu daga cikin maganganun Azrahn ba, tayi kamar zata kamata da faɗa dama jira take ta tanka mata sai ga Bappah ya fito daga ɗakinsa ya ce
"Siyama Karki kuskura, ke yanzu ba abin kunya bane a gareki kina neman tsokanan Kanwar ki? Just imagine fah? Ke waya hana ki fito da mijin da har kike wasu maganganun" Siyama ta kalle Bappah sai kuma ta fashe da kuka ta wuce ɗakin su tana jin haushin abin da Bappah ya mata
Azrah na shiga ɗakin Umma ta ce
"Azrah no matter what kar ki ce zaki na biye musu, harda rashin ilimi ke damun su, amma mutum me ilimi ai ba zai yi haka ba" Azrah ta ce
"Umma I'm always avoiding their dirty words, always pretending banji ba, yi nake kamar bansan suna yi ba ɗazun ma banyi niyyar kulata ba amma yadda naga take juya maganar wani iri shiyasa nace tayi respecting kanta" Umma ta sauke ajiyar zuciya ba tare data sake magana ba.
Yau tunda honorable ya tashi Matansa basu gane kansa ba babu wannan murmushin da ya saba musu balle wasa da dariya, kuma sun tambaye sa bashi da lafiya ne yace Lafiyan sa kalau, haka kawai yake avoiding mutane dan jiya ya kasa ma baccin kirki shiyasa gaba ɗaya ya tashi moody ganin ba zasu kyalesa ba duk da baiyi niyyar fita office ba kawai ya shirya ya gwammace ya tafi can inda babu wanda zai takura sa.
Yana zaune a office yayi nisa cikin tunani yaji wayansa ya fara ringing ɗauka yayi tare da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 12