gaidata sannan na ajiye mata nata, dakin Hajiya Salamatu na shiga duk yaran na zaune, suna cin abinci na gaida ta. "Mutanen Abuja, har an iso kenan!" "Eh Hajiya, ga wannan tsaraba ce. Wannan kuma gudunmawa ta ce ayi hakuri babu yawa." Amsa tayi tana faɗin. "Ikon Allah me yawan kenan, Ummu ashe kina koyar da girki ne a can?" Cikin girmamawa na ce mata. "eh amma na kusan kammala dake na wa'adi ne idan na gama shi kenan." "Allah ya dafa miki, ya kuma baki sa'a." "Amin Hajiya bari na gaida Abba!" Na dauki na shi kayan na fitar da shi, "Gaye nan ya samu mace fa, amma yake biyewa duniya yana mata iskanci." Inji Alfah Kanin Sharif. "Eh ya samu mace ga Allah, kuma irin matan nan ne na rufin asiri, Allah ya sa nima tawa tana da wannan halin!" "Amin Ya Allah. Ai naso lokacin da Alhaji ya kawo batun wa kai ya nimawa yarinyar domin tana da tarbiyya da hankali, ku kalli bata dauke ni a matsayin da suka dauke ni ba, yadda take mutuntatta ni yafi min kome dad'i, Allah ya mata albarka!" Ta fada tana murmushi. Da naje parlour Abba nan aka zuba min abin karyawa, ina ci ina bashi labarin wurin aikina. "Ai na gaya miki, nan gaba sai wata jami'an ta dauke ki aikin girki kafin nan ki nimo min takardunki!" Zare idanun na fara ina sosa kai nace mishi"Abba ni fa na tsani karatun boko ne!" Ware idanu yayi yana rike baki ya ce min. "Yau naga wacce bata kaunar boko, idan Mijinki ya zama.wani fa?" "Sai ya auri yar boko, tunda ni gaskiya bani gane kome na bokon nan!" Dariya abin ya bashi bayan na tab'a abincin na dauki tsarabarshi na bashi ina cewa. "Ba yawa wannan kuma gudummawata ce!" Na mika mishi, kamar da wasa Sai gashi Abba yayi ta min addu'a, kwanakin da suka biyo baya, ana ta shiri ne sosai. Ranar da aka fara biki a gkdansu amarya nima na fara nawa shirin aikin, a daren ranar Tinah ta iso na kaita har parlour Alhaji da su Hajiya, sun ji dadi sosai. Washi gari na kaita gidanmu muka wuni, sannan muka dawo ita da Sa'adiyya wani gani-gani sukewa Juna, abokinta ta biyo, amma sai zuwan ya koma nawa. Ana gobe daurin aure Abba ya kira ni. A gabansu Hajiya ya ce musu. "Ku ji da naku aikin ku bawa Ummu nawa aikin!" Mutane masu matukar kirki da mutunci suka ce. "yawwa gara da ka hada Ummu da aiki mu.ma mu ji da namu!" Haka ya aka bani aikin na shiga kitchen na amso kome na wuce bangarena, sannan aka turo min Nabila da Na'ima da kawayensu. Da Tinah muka daura aikin pepper chick. Muka kuma hada miyar jollop, washi gari muka tashi aiki kamar ba gobe yan matan nan da su muka ci Uban aiki, abinci ya kusan sauka kawai sai ga Aunty Rukayya da flat. Zata bude tukunyar Tinah da bagwaren hausarta ta ce mata. "Look me kake so?" "Abinci zan diba!" "Ba zaka saka ba, ina kake lokacin da muke aiki sai kazo kai me cin abinci!" Jin maganar Tinah yasa ni fitowa a daki ganin rukayya yasa na fahimci inda zancen ya nufa na ce mata. "Ki je ki tambayi Abba kosu Hajiya abincin nan na Abba ne."
"Eh nasan na shine na zo diba, ko ban isa ba ne?" "Gaskiya kin isa amma.ba zaki diba ba." Na fada ina gyara wutar. Fita tayi fuuu, sai ga ta tare da Maryam da Safiya Matar Ya Umar. "Ke yar uban waye da zaki hana abincin? Na kira Tafida ma yazo ya diba mana. Dama ina cike da ke yar iska mara kunya!" Inji Maryam, ban tanka musu ba, Tinah zata shiga na rike hannunta ina girgiza mata kai. Shigowar Tafida da Deen yasa na dauke kai ina cigaba da gyara murhun. Nan suka gaya mishi abinda yake faruwa. Ba don Allah yasa yazo da Deen ba ban san me Tafida zai min ba. Domin shi da Tinah kamar zasu bugu yana gaya mata ita bakuwa ce kada tayi wani abu da zai saka mutuncinta ya zube nan ta.kara harzuka. "Zuba musu abincin!" Ya fada yana takowa gabana. "Ba zata zuba ba, abinci na Alhaji ne su je su same shi ko matanshi, ai gaskiya ta fada dake su masu dangi ne shine akazo cin mutuncinta! Ba zata zuba ba!" Inji Deen, "Kai ya ishe ku Ummu Matata ce! Babu Dan iskan da ya isa shiga tsakanin mu." "Ni kuma Ummu kanwata ce babu shegen da zai ci zarafinta na kyale dan kutumar." Ai ba sai ga Tafida da Deen zasu bawa hammata isa. Da gudu nabila da Na'ima suka kai labari cikin gidan, Alhaji da zai wuce wurin daurin aure ya shigo har cikin gidan yana kallon yadda na shiga tsakaninsu. "Wai ni don Allah ya kuke so nayi ne? Abotarku na.tsawon shekaru zaku lalata saboda ni? Idan abinci ne gashi can su diba yadda suke so abu daya na sani Allah zai kamani da hakkin cin amana, ba yau na fara hidimar abinci ba, amma ba zaku yi fada saboda ni ba don Allah!" "Allah ya maka albarka Safiyyudeen! Allah ya tsare bayanka da gabanka. Abinci ni nan na bawa Ummu tayi min domin gudun fitinarku na bata, Aniyarku zata bi ku abin da kuke mata Allah sai ya bi mata hakkinta. Inda ake zuga ku ." "Abba don Allah kayi hakuri!" Murmushi yayi ya kalli Tinah ya bata hakuri cikin harshen Ingilishi, daga nan ya fita ya ce a kwashe mishi abincinsa a kai mishi cikin gidan. Haka kuwa aka yi na dauki sabin kullolina na alfarma na zuba pepper chick din, sannan na koma daki muka shirya shiga aikin cake, muna gama kwabi na bar musu na buga donut, kafin wani lokaci har na gama na kai shi rana.
A can bangaren Shuwa kuwa daura su tayi akan keken bera, tai ta zuga su tana gaya musu abin da ba shi ba ne. Karfe hudu na yamma muka gama sannan muka shiga cikin gidan bayan mun yi wanka . Dakin Inna muka shiga naga dasu Rukayya ko minti goma bamu yi ba muka fita na cewa Tina. "Mu koma bangarenmu!" "Ok!" Muka dawo, ko minti ɗaya bamu yi ba sai ga mata yuiuuuu. Hayaniyarsu ta fito da ni daga cikin kitchen na je diban abinci. "Lafiya?" Wucewa dakina Rukayya tayi tana faɗin. "bincike zamu yi bari na fara da dakinta!" "Ban gane ba?" "Shigar ku dakin nan, aka nime kudi aka rasa kuma.a inda kika zauna kudin yake!" Dariya nayi nace musu. "Bismillah!" Na koma kitchen din ina diban. "Innalillahi na gaya muku ita ce haka zuwana Abuja ta hada ni da dan uwana wai ina mishi sata, bayan ita ce take shiga dakinsa. " ba tare da na fahimci me suke nufi ba, matan nan suka rufe ni da duka, wanda ihun Tinah ya janyo hankalin mutane cikin gidan har da Tafida da suke kofar gidan, suka shigo ni kan ai na suma. Abba babh takalmi a kafarshi ya shigo parlour lokacin kowaccensu ta gudu sun bar gidan bakiɗaya. Tinah sai kuka take tana rungume. "Abba ka saka Tafida ya sake Ummu, Abba don Allah ka ce ya sake Ummu ba matar shi ba ce kashe ta zasu yi shi da Yan uwansa. Abba Tafida bayan son Ummu don Allah ka ce ya sake ta ni xan aureta!" Inji Alfah da ya shigo hankalinsa a tashe, ruwa akayi ta watsa min, kafin na sauke ajiyar zuciya. "Wallahi ban dauka ba, wallahi ban tab'a sata ba, ban iya daukar abin wani ba." Na shiga fada ina ihu, durkusawa yayi a gabana, ya janyo Ni jikinshi. "Allah sai ya saka miki, Allah sai ya bi miki hakkinki, nayi kuskuren barwa dabba ke bayan ke ce kika dace da samun mutum na gari na bawa Dabba rikonki!" "Tina rikota zuwa bangaren Kaltuma!" Ya tashi yana me kallon Tafida. "Ina son takardanta nan da awa daya!" Mai da hannunshi baya yayi yana me sunkuyar da kanshi. "kayi hakuri amma ba xan iya sake ta ba, ina son Matata!" "Tass!" Ya kifa mishi mari, duk da bana cikin hayacina sai da na juya ina kallon shi yadda ya zube akan gwiwarshi. A farkon rayuwata da naji wani irin mahaukacin matsayinsa me hade da kaunarshi da ban san yaushe ya min bazata ba. Abba sai kara marinshi nace mishi. "Don soyayyarka da Annabi Muhammad, kayi hakuri." Na isa gabanshi ina me durkusawa. "Don Allah kayi hakuri, laifina ne da ban je dakin ba, haka ba zai faru ba." "Ya sake ki tow!" Daga ni har Tafida muka kalli Abban. "Abba ina son mijina!" A fusace ya fita daga ɓangaren bakiɗaya, Deen ma ya saka kai ya fita, Mahmoud da shima ranshi ya b'aci ya fita daga gidan bakiɗaya, cikin Motarshi ya shiga yayi da dukar motar yana ihu, Tina ma fita tayi tana share hawayen da yake zuba mata. "Idan haka matanku suke da kashe kansu tabbas Ummu ta cancanci farin ciki a rayuwarta." T fadawa Deen da yake kokarin fita a gidan, "ina zaki?" "Somewhere!" "Muje ki zaga gari!" Ta shiga motar tana me bude pose dinta. Ta ga kome nata tayi murmushi. "Muje ga wannan ka bawa Ummu Atm dinta ne jiya network ɗin bankin mu yaki bani hadinka, shine ta bani Atm dinta. Me irin wannan kudin ne zai dauki dubu biyu!" Ya fada tana murmushin takaici. "Ummu bata da matsala shine dai matsalar Ummu sannan ya sake yan uwanshi suna wulakantatta!""shi ya wulakantatta ba su ba, da ya girmama ta babu me mata iskancin nan!"
Bayan fitar kowa na koma gefe ina me hada kaina da gwiwata, wani irin kuka nake me cin rai a karon farko da na kara jefa rayuwata akan Tafida, "kiyi hakuri!" Naji muryanshi, "nayi hakuri? Kace nayi hakuri naji zan yi ko babu kome ka bani hakuri da kanka amma ka sani daga ranar da na gaji ne babu me tankwara Ni!" Na rarrafa na shiga ban daki nayi wanka da ruwan zafi zazzaɓi ya rufe ni, haka aka yi bikin nan ba dadi. Washi gari ranar budar kai, ban yarda na fita ba kayan abin da nayi na bada aka kai, ina kwance Tafida ya shigo ya zauna a bakin gadon. "Wai ba zaki iya fita ba ne?" Kallonshi nayi kafin na ce mishi. "ina tinah?" "Tana wurinsu Inna!" Haka na mike na gyara zaman dan kwalina, na fita ina me yafa mayafi. A hankali na nufi cikin gidan, na samu ana ta hidima. Wurin wucewa naji wasu kawayen Maryam suka ce. "Ita ce ta dauki dubu biyu aka mata duka!" "Eh ita ce fa! Anyi mugun hali ga baki kamar zunubi ga sata" Kallon Tafida nayi da yake murmushin mugunta. Zan yi ya rike hannuna. "Me yasa kayi min haka?" "Saboda kin cewa Abba kina sona, Ni kuma nayi alkawarin sai na cusa miki bakin ciki ta ko ina!" Ji nayi numfashina yana son fita daga gangan jikina. A hankali na durkusa a wurin ina jin kamar bakiɗaya mutanen ke fada min magana. Dafe kaina nayi da karfi nace. "Ni ba barauniya ba ce!" Na fashe da kuka kokari nake nayi numfashi, dafe kirjina nayi ina wani irin haki, kafin nan na zame akan kafata. Kokuwa nake da numfashi amma yaki bani hadinka. Iya abinda zan iya cewa naji shine. "Ka daukota ne ku kashe ta? Ka daukota ku tozartani? " rike hannun Abba nayi nace. "Ka kai ni gidanmu don....." daga nan bana ce na san me ya faru ba, wannan abin da ya faru yasa Abba yayiwa Rukayya da Maryam Allah ya isa, bai yafe musu ba, shi kuma Tafida Abba ya rantse sai ya mai da shi zero percent. Abin ba dad'i ita Hajiya Salamatu haushi ya hanata magana domin an lalata mata bikin danta. Kwana na biyu asibiti, na farka saboda yadda jinina ya haura sosai, likitan sai fada yaƙe. Akan an barni da damuwa lokacin da Mama tazo gaida ni tayi ta min nasiha nayi hakuri na rage damuwa a raina, hmm bata san me ake min ba, domin daga wannan lokacin na hadu da mugun hawan jini...........
500
8130269641 Abdulrahman Ramlat Manga Opay
Shaida biya a turo ta wannan numbers din.
+2347035133148
Or
+2348130269641
Yan uwa Yan Nijar ga na ku inda zaku yi payment din: +227 84 50 64 76YAR MACE....🌺
*Mai_Dambu*
*Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CShgPK2Dsi8GIrvd5njOML*
*Ina mata yan yayi shin ko kun san kayan da Ummu take amfani da shi, yana fitowa ne daga shahararren Shagon nan na R&U Exclusive Kitchen and More! Kayan kitchen ne na gani na fada ina iyayen Yan mata ina iyayen Kwailayen ga dama ta same ku, Uwargida da Amarya, Budurwa da bazawara maza ku fito ga kaya nan sayan na gari mai da kudi gida. Kayan mu daban da na shago!*
Paid book
19
Kallon Mama nake bakina kamar an daura min dutse, na lumshe idanu ina son yin kuka amma na kasa, na juya na kalleta kafin nace mata. "idan kika ji labarin mutuwata, ba dad'i ya kashe ni ba damuwa ce, idan na rayu kuma ki taimaka ki min Alfarma daya!" Jikinta ne yayi sanyi, kaina na dafe ina jin kamar zuciyata zata fita waje saboda bugawa. A hankali na juya na kalleta na ce mata. "Me yasa baki tab'a tambayata meke faruwa a gidan aurena ba?" Na sha mamaki da naji amsar da ta bani wanda ban yi mamakin fitar shi daga bakinta ba, "Idan na tambaye ki meye ribana? Na tambaye akan me? Kowa yasan kina zauna lafiya tow akan me zan tafi lafiyar aurenki, Ummu indai ba so kike a zage ni ace na kashe miki aure ba, ki rufa min asiri ki zauna lafiya wannan wacce irin rayuwa ce? Daga tambayarki kin ga kudi zaki yanki jiki ko fadi!" Ware idanu nayi akan Mama. "waye ya gaya miki haka? Sharrin sata suka daura min fa!" "A'a Ummu yayar Mijinki ta gaya min Ummu bakya son zaman lafiya." Kallon ta nayi kafin na fashe da kuka, ina yi ina yada kaina saboda yadda kirjina yake zafi da ciwo. "Ke kika haife ni kin san abinda xan yi da wanda ba zan yi ba, a tsawon rayuwata ban taba kawo miki kara ko nayi musu da wani ba, me yasa yau daya don an gaya miki abu kaina zaki amsa? Me yasa baki jira ki tambaye ni ba? Indai ke kika gagara min adalci a duniyan nan waye zai min adalci? Zan tafi wurin Babana na gaya mishi." Anan na ga ta ɗan yi jim kafin ta ce min. "Ai maganar ba sai ta kai wurin Malam ba,.akan abin da bai taka kara ya karya ba, kiyi hakuri tow zan cigaba da miki addu'a!" Da wannan tayi ta kwantar min da hankali, har nayi shiru na zuba mata idanu, kullum Tafida da Abbansu suna hanya, amma ni ko sau daya ban taba mishi magana ba, kwananmu goma aka sallame ni, gidana na dawo na cigaba da jinya duk da ana dawowa da ni Mama ta wuce gidanta, sannan wani abin da ya kara cin tuwo a kwarya yadda Tafida baya ganin girman Mama, har gara Deen yana girmamata. Shi yasa nima nake girmama Ammah. Sai da muka kwashe sati uku muka koma abuja, sai dai nayi mugun fita barkan Tafida, ban da aikin da aka dauke ni ba zan kara bin shi ba, haka a hankali nayi ta fuskantar kalubale daga danginsa, ana haka aka sake wani bikin ban je ba, sannan tun dawowarmu Tinah ta dauke kafarta ashe sun yi fada kaca-kaca da Tafida tun a Maiduguri, tayi mishi alkawarin sai ta saka ya bar inda yake samun kuɗi kamar hauka, da shi yake saka shi jin shi wani ne, lokacin da ta gaya min murmushi nayi na ce mata. "Ina kika yi sanadin da ya bar aikin bashi kika yiwa ba, ni kika yiwa ki barshi yayi aikinsa Allah ta bashi Sa'a duk abinda ya gadama yayi."tunda na hadu da laluran nake gudun abin da zai d'ago min shi,.sannan bana son tashin hankali bakiɗaya gani nake kamar xan mutu yadda nake fama da ciwon. A hankali lokaci yayi ta gudu ana haka har watan azumi ya cimma na, a lokacin na gama aikin da aka dauke ni, ai kuwa na ce sai Maiduguri, dake kusan wata bakwai babu me kula dan uwansa, don nayi kokarin koyawa kaina shanye iskancin, sai dai mafi girman kuskuren da zuciyata tayi min fadawa soyayyar Tafida. Wani irin mahaukacin sonshi nake kamar zan yi hauka, idan nace ban fada jarabawa ba nayi karya haka yasa nake rufe kaina a ban daki nayi ta kuka, tun ranar Monday na shiga tattara kayana, yana gani bai min magana ba, nima kuma ban ce mishi kome ba. Sai bayan Isha na same shi a parlour. "Barka da hutawa!" "Yawwa yar gajeruwa, au ashe likita ya ce zuciyarki zata buga!" Ya fada yana murmushi. "Dama ina son na koma gida!" "Ban yi niyyar ki koma ba!" "Shi kenan!" Na fada daga haka na koma na cigaba da zama abina, na zata maganar ta wuce tunda ya ce min bai yi niyya ba. Kawai sai ga kiran Mama tayi ta fada akan me zance zan dawo Maiduguri, fada kamar ta ari baki ta kara, Abba ma ya kiranki ya tambaye ni ko akwai matsala ne. Nace mishi kawai zan dawo ne, na gaji shiru yayi kafin ya ce min. "shi kenan ki hada kayanki Alfah zai zo ya dauke ki!" Ajiyar na sauke ina me jin kamar anyi min albishir da gidan Aljanna. Nayi ta mishi godiya, sati daya da maganar ya kirani yace na shirya gobe za a zo a dauke ni. Yadda muka mai da Tafida gefe ba karamin zafi yayi mishi, ina kwance ya fado dakina, tashi nayi xan zauna ya nufo ni. "Me yasa kika rena ni? Ni nake aurenki ko Abbana? Gaya min me yasa?" Ya hauro gadon ya da karfi ya fisgo ni na fara ƙoƙarin kwace kaina, "Tafida bana son tashin hankali, don Allah ka kyale ni!" "Akan me xan kyale ki bayan kina kallona lusari ban iska kiyi abu na yi magana ba, ace bani da kirki bani da mutunci!" "Tow don Allah meye nayi maka? Na gaji da fitinarka zan tafi inda nake da gata da galihu.." "ai nan baki da shi? Tow bari na gyara miki zama!" Kuka na saka mishi ina rokon shi don Allah kada ya min haka, amma bai ji ba cikin shashekar kuka na rike hannunshi domin bakiɗaya karfi yake son gwada min. "Don kaunarka da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, ban san me akan wannan lamarin ba kada ka illata min rayuwa bayan ba son zama da ni kake ba!" Ina bai jin kira, ni dai nasan irin yadda ya zuba min karfi kamar jikan ilaya dan mai karfi, babu yadda xan kwaci kaina amma tabbas abubuwa da suka biyo baya, ban san yadda zan fade su ba, domin.nafi girmama fyade Tafida yayi min cikin mugunta da zalunci irin na ranshi. Haka ya ci mutuncina son ranshi. Sannan ya tashi a kaina yana me jan tsaki. Ya saka wandon shi ya bar dakin, dakyar na rarrafa zuwa ban daki nayi wanka tare da gasa jikina da nake jin kamar ba jikina yake ba, fatana kawai gari ya waye na bar garin Abuja. Kwana nayi ban yi barci asuban fari na hada kayana na fitar parlour wurin karfe biyar Alfah ya shigo yayi ta buga kofa, zazzaɓin da ya rufe Ni na lallaba na fito na bude mishi. "Kayi hakuri Alfa!" "Ba kome ina kayanki!" Na nuna mishi, sai lokacin Tafida ya fito ranshi a bala'in haɗe. "Kai haka ake zaka wani shigo gidan mutane da tsakiyar dare haka!" Dake basu shiri shi da Yaran Hajiya Salamatu. "Ayi hakuri!" Ya fada yana daukar jakata yana me barin parlourn, fisgo ni yayi yana me kallon fuskana. "Ki ka sake wani reni ya kara shiga tsakaninmu, sai na bi ta wannan hanyar sau goma wannan sau daya nayi tow idan kika bari na waiwaye ki abin ba zai mana dad'i ba." Tabbas duk macen da aka yiwa fyade matukar bata gigice ba, tow ciwon yana iya zama har cikin kwal-kwalwarta abin da ya faru da ni kenan amma ban gigice ba, sai dai wani irin tsoron tafida ya dasu a zuciyata, wanda ya ja na fara kuka yana ce min "shiii!" Na hadiye kukan kamar ba ni ba. "Ki kama kanki, shi kanina ne kada wani ya gaya miki cewa akwai wasa a tsakaninku, ki mai da kanki wata sakarai! Kina ji na!" Ya daka min tsawa, k'amkame jikina nayi tare da gyada mishi kai. "Yayi kyau maza muje ki shiga motar!" A hankali nake tafiya saboda yadda nake gogan wurin har cikin raina nake jin zafi, hawaye ne yake zuba ina sauke ajiyar zuciya. "Kukan na uban me kike yi?" Share idanuna nayi da sauri ina faɗin. "na daina!" Burina kawai na bar ganinnshi. "Ya tafiyarki ya sauya!" Ji nayi kafaffuna na rawa kamar ba su dauke ni ba. Fisgo ni yayi ya saka Ni a bayan motar yana faɗin. "Ki kula da kanki!" Gyada kai nayi ina kallon kasa. Motar na barin kofar gidan ya sauke ajiyar zuciya, idan haka aure yake tabbas ya tabbata asararre wanda ya bar damarshi tun farko. Zai barta ne kawai ta tafi don Abba yayi magana amma ba don haka ba, idan ya sakata a gaba sai ya ga abinda yake dadi a jikinta..(Ji dan iska mugu 🙄😒)
Tunda muka dauki hanya nake sauke ajiyar zuciya, sai da muka bar Abuja zazzaɓi ya kuma rufe ni, yadda nake rawan sanyi yasa Alfah kashe ac motar, sannan ya yi parking ya ciro min panado ya bani na amsa ina godiya. Bayan na sha yace min. "Ki kwanta ki huta!" Haka na kwanta a bayan motar, tuni barci me nauyi yayi gaba da ni. Ban farka ba sai da ya tashe ni, wurin karfe daya na rana, a lokacin muna fataskum zare idanun nayi ina son nayi magana. "Ga abinci ki ci, zuwa anan da karfe hudu zamu shiga Maiduguri." "Tashi motr sama kayi?" Na tambaye shi ina bude abincin. "A'a gudu nayi kawai!" A hankali na fara cin abincin har muka bar fataskum, a yanxu na tabbatar da ba tashi yake sama ba, irin matasan nan ne masu mugun gudu, Alfah akwai wasa sa rayuwa kamar yadda ya fada karfe hudu cib yayi mana a garin Maiduguri. Wani wawan ajiyar zuciya na sauke ganina a gidan. Abba da kanshi ya tarbe mu, a nutse na gyara tafiya ta duk da ba karamin wahala nake sha ba, na gaida su . "Ummu baki da lafiya ne?" Yake nayi ina faɗin. "Bana jin dadi ne amma da sauki!" "Allah ya baki lafiya!" "Amin Ya Allah!!" Na wuce bangarena a hankali kamar kazar da kwai ya fashe mata, ina shiga ruwan zafi na daura na jira ya tafasa, na jure a flast na nufi dakina da shi, na zuba a bawo na a zauna sai lokacin kuka ya zo min ina yi ina karawa, sai da ruwan ya huce na fita, na kara wanka na sha magani nayi sallah, sannan na kwanta ban farka ba sai karfe bakwai ashe har Nabila sai da ta shigo yafi sau nawa, Alfah yake gayawa Mamansu ai bani da lafiya, haka yasa Alhaji ya saka lallai a kai ni asibiti, gudun abin kunya na ki yarda, haka nayi ta jinya a hankali na manta da wani Tafida can. Haka na bude sabon shafin rayuwa, satina biyu aka fara azumi na nutsu sosai nayi rabon kayan azumi har garin Babana na je da kaina a cikin azumin yana uku sai da nayi aka kai azumi goma na dawo na nutsu nayi kyau, na dawo da kwana uku sai ga Tafida, sai da naji kamar xan yi hauka, kome da nake
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 17