want kids food for him” hadomai abinci akayi daban daban, yasayamai sweet da cheese balls pack, juice da biscuit yabada card yabiya, ma’aikatan wajen na fitowa da kayan yazo yabude motan aka samai komi a back sit sannan ya shigo yazauna, Safeerah takalli su adan hankali tahada ido da Waleed dakecin cheese duk ya batama Salim rigansa kayansa masu haske amman duk orange orange na cheese ajiki, tama Waleed alamu da hannu dayazo yawani kankame Salim abun yabata mamaki, Salim ya rufo motan yadan kalleta maida kanta kasa tayi, ahankali yace “why were u at the company this night?” Dan shiru tayi sai chan murya chan kasa tace “bakomi” ijiyan zuciya yasauke yace “alright bari na maidake gidan na tambayi Baba meya faru aka miki duka haka a fuska basusan ke mace bace” ya kunna motan dasauri tace “ni……ni bazani gidan nan b…..” takasa karasa maganan sabida rawa da bakinta yafara kuka na neman kufcemata hawaye yazubo mata takai bayan hannunta ta goge fuskanta da sauri muryanta na breaking tace “ni….nidai kabani Waleed nayi tafiyata thank you for everything” takai bakin hijabinta ta daura kan fuskanta sabida bataso Waleed yasan she’s crying yahau kuka shima, dan ijiyan zuciya Salim ya sauke yaja motan dasauri tasauke hijabin takalleshi ahankali tace “ina zaka kaini” shiru yamata bai cemata kala ba takai hijabin tana goge idanunta, Silver garden estate taga sunje yana horn aka bude yashiga estate din yahadu sosai, parking yayi agaban wani gida number 17 dan gidajen duk iri dayane yabude motan rikeda Waleed batare daya kalleta ba yace “when you’re ready come inside” yazaga bayan motan yadauko ledan abincin yawuce yabude kofan yashiga tabisu da kallo a bude yabar mata kofan gidan yahadu na bala’i.
Takai kusan 10mins a motan kuka take, kawai yamata hijacking yaro yakawota wani gida an gayamai ita yar iska ce? She’s not even understanding wats happening, yanzu idan mutumin nan yamata wani abu fa? Dudda he doesn’t look like a bad person but yanzu yazatayi? Inane nan ya kawota ya shige da danta? Meyakema Waleed? Idan shi maye ne ya cinye mata kuruwan d’a fa? Ganin tana tunanin Waleed sosai yasa ta goge fuskanta tass idanunta harsun kumbura tabude kofa tafito tamaida kofan tarufe tashigo gidan, tsoro yahanata kulle kofa, babu kowa a hadadden falon, muryan Waleed taji ta around wajajen dinning datake kyautata kitchen ne hakan yasa tawuce wajen asanyaye jikinta yayi sanyi duka tabude kofan hakan yasa ta hangosu yadaura Waleed kan island na kitchen din shi yana tsaye yana basa abinci Waleed naci sosai yanamai murmushi tabi kitchen din da kallo garin abincin duk ya zube a kasa da kwalayen abincin, kitchen din looks so messy kana gani kasan bai saba yi ba maybe ma this is the first time yake bama yaro abinci, for the first time ta tsaresa da idanu tun shekaran jiya data fara ganinsa he’s so gentle with Waleed, kaman yasan Waleed from somewhere, you Waleed means something to him, is not easy kabama stranger this care, who is he? Bata taba ganin Waleed ya yarda da stranger easily ba sai shi, yana basa yana goge masa kumatu yana masa murmushi hakan yasa Waleed nata murmushi, fresh hawaye taji sun zo mata dasauri takai bayan hannu ta goge su, ruwa yadauka na gora yabude yabama Waleed ya sha ya ijiye komi yasa hannu yadaukesa yajuyo ganinta yayi tsaye jikin kofa tana share hawaye da bayan hannu bamata san yana kallonta ba, wani irin radadi yaji zuciyansa namasa ganin the happiest girl daya sani back then is the saddest girl today and someone dares hit her, there’s this thing he feels about Safeerah he feels kaman ya maida problems nata kansa and just solve everything for her, shafa bayan Waleed yashiga yi yaron yayi gyatsa tareda yin lamooo ajikinsa bacci yayi awon gaba da shi daman yunwa yasa ya farka, dagokai tayi ta kallesa suka hada ido dauke kanta tayi dasauri, tahowa ya shigayi hakan yasa ta matsa gefe wucewa yayi yafito tabiyosa yahau staircase saita kasa hawa kawai saita fashe da kuka dan at this junction takasa rikewa. “Please kabani d’ana mutafi, I’m not one of those girls dake kwana gidan maza, ni kabani Waleed natafi ni ba yar iska bace” dudda yaji all she said but ko alamun tsayawa baiyiba yakarasa hawa tafashe da kuka da kyau tabisu da kallo takasa hawa benen karya mata wani abu, kwantar da Waleed yayi kan lafiyayan gado yaja bargo yarufa masa sannan yafito tareda rufo kofa har lokacin tana tsaye awajen tana kuka, saiya shiga saukowa akarshen stairs din ya tsaya yadan kalleta yace “I’m going home you can stay here as long as you want” ahankali tadago kanta ta kallesa hada idanu sukayi kasa jurewa tayi ta maida kanta kasa, anatse yace “idan na fita kizo ki kulle kofa ki sa key da sakata” yazaro wani phone daga aljihun wandonsa yadan taka zuwa kujera ya ijiye wayan yace “my number na cikin wayan nan Salim call me if you need anything zan kiraki gobe da safe” yasake yin shiru saikuma ya kalleta yace “put ice a face dinki, don’t cry again is affecting Waleed” gently tadago kanta takalleshi hada ido, komar da kan kasa tayi ahankali tana goge fuskanta da bayan hannu, ataushashe cikin murya kasa kasa that’s so gentle and soothing yace “sorry!” There is something she felt, batasan sorryn lallashi ne ko na menene ba oho but she just felt d word kaman ya daura hannu saman kanta yana lallashinta saitaji hawaye sun cicciko idanunta, wucewa yayi wajen kofa yadan dakata saiya sauke ijiyan zuciya yace “good night Safeerah!”.
EPISODE 1️⃣9️⃣
Yafice yaja kofan da all this while yake abude yarufe, tana tsaye awajen taji ya kunna mota yaja yatafi, ijiyan zuciya Safeerah ta sauke tashiga dukawa a wajen kafin takarasa kaiwa kasa kawai ta zauna ta jingina bayanta da bango komi daya faru na dawo mata, jitake kaman an daura mata dutse a kirji, abun is too much for her, idan ita su Momma kema abinnan wlh wlh wlh she can take it but not her parents takasa bringing kanta tadanne zuciyanta, she’s not crying because of abubuwan data gayama Momma wlh she’s not regretting it, she is crying because of Mama da Baba data batama rai suke fushi da ita, ga Baba baida lpy, she is also crying tana tunanin inda zatayi yanzu cus she have only this night to make a decision dan ko sama da kasa zata hade bazata koma gidan nan ba kuma saita dauke Baba da Mama daga gidan, she can’t believe gidan wani zata kwana yau, da kyar ta lallashi kanta tamike tsaye tawuce wajen kofan ta murza key tasaka sakata nasama dana kasa, tazo wajen window tadan daga ta leka taga motanshi baya wajen dan bata yarda dashi ba kar a sace su ko ayi rituals dasu, sannan tasaki labule tadawo tai shiru tawuce sama, dakin da Waleed yake taga kofan abude ta hango ta gansa kan gado yana shakan bacci hakan yasa ta wuce dakin ta maida kofan tarufe ta murza key shima tazauna nan jikin kofa ta jingina bayanta tabuga tagumi tana kallon Waleed, wani irin tausayin Waleed take he doesn’t deserve this kawai tahau kuka wiwi saita daura hannu abaki cus yanzun nan Waleed zai tashi.
**
Jan motansa yayi zuciyansa cikeda damuwa baitabajin abu ya damesa kaman yau yanda yaga Safeerah, the way she was crying ba, he felt everything down to her born marrow cus Safeerah daya sani 5yrs back was the happiest and the brightest girl ever with love from both parents nata sabida from yanda tadingamai surutu he picked iyayenta really care about her and loved her, what happened? What changed a shekaru biyar dinnan da Safeerah tadawo haka, the way yakeji is even if it means going to karshen duniya ne he’s ready to go just to see that genuine and innocent wholehearted smile dinta, and he will stop at nothing indai kan yasamo mata farin cikinta back ne. Kwana yayi da motan kawai yawuce GRA har zuwa unguwansu dan nesa da gidansu yayi parking ya kashe motan yayi shiru yana kallon gidansu wasu guys yagani a kofar gidan about 5 yayi shiru kawai yana kallonsu wayansa ne yahau ringing dasauri yakalli wayan dake jikinsa, ganin KB ne yasa yadaga yakai kunnensa KB yace “daha bari kaje gida an change kazo shikenan baka dawo ba? Are you afraid na maka lilis ne an arena eh Zer……” “I’ve found her Kabir!” Hardly Salim ke kiran sunansa jin yakira sunansa yasa dasauri yace “wa? Who did you find?” Jingina yayi da kujeran ya lumshe idanunsa murya chan kasa yace “Safeerah! But I think I’ve destroy her life Kabir!” Yayi maganan sounding very hurt baitaba jin Salim hakaba cus Salim mutum ne da baka gane damuwar sa, farin cikin sa ko bakin ciki but yau muryan Salim sounds pretty hurt, dasauri yace “kaga Salim calm down, this girl helped you when you needed help the most I get it, I can clearly say Safeerah na part of the reason why you’re alive today together with us, but stop blaming yourself for abinda ke faruwa in her life yanzu” cikin dan fada sounding pissed yace “da ban fada gidansu make a little 15yrs old girl shoulder responsibility na boyeni ba da none of this would’ve happened, I am a coward say it! The least I could do shine danaga small girl ce agidan dana juya cus I know everything about security, I know by being there I am putting her and her parents at risk cus yan anguwan nan are thugs but I stayed regardless and nabar gidan without fadin ayi protecting nasu or akaisu somewhere safe” shiru duk sukayi KB yace “kasan sanda aka cireka daga gidan nan baka hayyacin ka? How would you have called all those shot? Banda haka you were in hospital for about 30days wat are you saying Salim, do everything you can to save her and help her if she’s in need right now she deserve it, but helping you, hiding you was all her choice blame her good innocent heart!” Shiru Salim yayi chan yace “I want to marry her KB!” Dasauri KB yace “wait wat! Mekace?” Calmly yace “inaso na auri Safeerah! Makes her my wife!” Dan rage murya KB yayi yace “are you sure of what you are saying? Cus yau duka duka is 14 or 13days ne ma to your wedding da Nanah” strictly yace “and I want to marry Safeerah tommorow or next max!” Sosai gaban KB yafadi yama kasa magana, ahankali yace “she’s not safe agidan da suke, dukanta ake that I can never ever and ever tolerate! An koreta this night and I believe the whole thing have to do with Yayar Babanta dasuke zaune agidanta she’s not telling, I will sort her life out, she will never be alone again as long as ina raye I am Safeerah’s Sheild” yana maganan kawai ya katse wayan ya kunna motan yabar unguwan.
EPISODE 2️⃣0️⃣
Har aka fara kiran sallan asuba bata runtsa ido ba inama damuwa zai barta ta runtsa, she’s extremely worried, takasa daina tunanin iyayenta, tayi kuka har hawaye sun dena fitowa, idanunta sun kumbura suntum bakindai yadan sabe but it’s still there, gashi takasa tashi tai salla gani take kaman ta shiga bayi za’azo a sace mata Waleed hankalinta yaki kwanciya agidan, ga kanta dake ciwo sosai yana sarawa, ganin dai an fara salla yasa ta tashi tawuce bayi shima abude tabar kofan tayi komi tafito daure da alwala batasan inane gabas ba bangare daya kawai ta kalla ta kabbarta salla ta idar tafara azkar kanta na sarawa, hakan yasa ta kwanta kan dadduman ance ba’a cheating nature bacci barawo ne yayi nasaran kwasheta.
Kadan kadan take bude idanunta dake cike da mugun bacci jin kara, bin saman dakin tayi da kallo kafin firgigit ta tashi zaune kanta na amsawa tuna inda take ya akayi tai bacci haka agidan mutane ta kalli gadon dasauri tuna danta, Waleed tagani yayi daidai agado abunsa yana bacci, jin ringing waya yasa tamike ahankali idanunta basama buduwa da kyau tafito da shiga sauka kasa da sauri ta taho falon inda ya ijiye wayan tasa hannu tadauki wayan da yana inda yabarta taga Major Salim a jiki hakan yasa takai wayan kunnenta cikin muryan bacci dakenan yar karama kaman tana whispering tace “Helloooo” shiru taji anyi kaman babu kowa adayan side din da sauri takai hannunta ta goge idanunta da bayan hannu tazare wayan daga kunnneta takalli screen din again ganin the call is still on yasa tamaida kunnenta ahankali tace “Assalamu Alaykum” cikin wani husky natsassiyan murya yace “I’m outside open the door” hakanan taji kirjinta na racing dagajin muryansa juyawa tayi tabi dakin da kallo, ganin basu bata komiba yasa ta ijiye mai wayansa back tai wajen kofan, sakatan tacire ta murza key tabude kofan ahankali hada ido sukayi yana tsaye gaban door sanye dawata yadi that looks soft and textures milk mai kyau dan yau Friday yana wani irin kamshi, he looks squeaky clean kaman ka lashesa, faduwa gabanta ya shigayi sosai, adan rude tasaki kofan takoma baya tadan tsuganna ahankali tace “ina kwana” kallo daya yama fuskanta yadauke kai ya shigo this time around ya maida kofan yarufe dawani irin sauri abirkice ta mike kaman zai cinyeta tana kallon kofan daya rufe, kaman baiga yanda ta tsorace ba wuceta yayi ya shiga falon ya ijiye ledan wani super market akan kujera da basket na kuloli that looks like abinci, sannan yajuyo yakalleta batare dayama zauna ba tana tsaye chan wajen dinning sabida tsoro tana wasa da yatsun ta kanta akasa kaman yace woop ta arce aguje, hannuwansa yazuba a aljihu rigansa ya sassauta murya yace “are you feeling better today?” Duk duniya ita kadai ne idan zaima magana saiya gyara muryansa, ya tankwara yakuma tausasa cus yaga tsoronsa takeji, gyadamai kai Safeerah tayi ahankali, yana kallonta still yace “Waleed fa”? Dan dagokai tayi ta kallesa suka hada ido dasauri ta maida kanta kasa, she felt wani iri dataji harya rike sunan danta sannan ya tambayesa kuka kawai taji yataso mata amman tadaure asanyaye tace “yana bacci” shiru falon yayi bai kara magana ba itama bata sake dago kanta ba banda wasa da yatsunta datakeyi, gently tadan dago kanta ta kallesa hada ido sukayi yana mata wani kallo da takasa sanin na menene da idanunshi dake tsorata mutum, cikin wani irin yanayi na girmama mutum dakuma jin nauyi ahankali tace “uhmm nagode! Thank you for everything! Dama uhmmm idan Waleed yatashi zamu tafi”? Idanunsa na kanta bayako kyaftasu har yanzu yace “ina zakuje?” Dago idanunta tayi ta kalleshi suka hada ido zata sauke idanunta strictly yace “don’t try it!” Kasa maida idanun kasa tayi ta tsaresa da kallo kirjinta nawani irin bugawa none stop his eyes are wild Ya Allah! Sai kawai lips nata yahau rawa takasa daina kallonsa takuma kasa magana this is the first eye contact dasuke having tunda ta sanshi dayakai na kusan 30seconds, he noticed saiya kara tausasa murya yace “I said ina zaku Safeerah!”? Wani irin blinking idanunta suka shiga yi he’s too much for her eyes kaman yamata asiri kasa karya tayi tace “nim…..ma ban sani ba!”idanunta suka cicciko da hawaye sai kawai ya dauke kansa, kaman yasaki kuruwanta wani ijiyan zuciya ta sauke itama ta sauke kanta kasa, ahankali yace “okay” yanuna mata table din yace “have breakfast, take drugs that are here sai ku shirya, call me when you’re ready to go” gyadamai kai tayi ahankali tace “thank you” wucewa yayi wajen kofa yasa hannu yabude yafice saikuma yajuyo hada ido sukayi dasauri ta sauke kanta kasa, ahankali yace “zanje wajen Baba and talk to him you need to go back to your parents” da sauri ta sake kallonsa sai kawai tafashe da kuka sosai tana goge fuskanta da bayan hannu batare datai magana ba, ya tsaya jimmm yana kallonta kafin yasa hannu yazare key tabaya yajawo kofan yasa key cus ya lura gidansu ne batason komawa something is definitely going on, yanda yace zaije yaga Babanta karyazo kafin yadawo tagudu tabar nan what if tafada in the wrong hands ga yaro karami tareda ita, dasauri tai wajen window tana kuka taga yaja mota yabar wajen.
Rolex din hannunsa ya kalla is 11AM, he needs to help his helper whatever it takes, yarinyar that helped him a death row he will go to the end of the world just to see that smile in her face not cry or sorrows. Cikin 20min yakai kofar gidansu yakashe motan wuraren 11:30, babu kowa a kofar gidan yayi jim sai yafito a natse yazo wajen yakai hannunsa ahankali yayi knocking ya dakata shiru, sake knocking yayi na biyu ya tsaya shima shiru, yakai hannunsa yasake knocking akaro na uku, karan bude kofa yaji hakan yasa yadan koma baya kadan sai yaga an dan daga wani marfin lekowa yaga idanu hakan yasa yace “Assalamu Alaykum” ganin ba yan gidansu bane yasa anatse Mama da duk tayi wani iri tabude kofa tafito kallo daya Salim yamata yagane itane mahaifiyar Safeerah, Safeerah really looks like her but tanada haske Baba though Baba yafita haske, Mama kuma baka ce, saisa Safeerah is not black she’s caramel, anatse yadan duka cikeda kunya dakuma girmamawa yace “ina kwana” calmly Mama tace “lafiya lau wa kake nema?” Dagowa yayi yakalli Mama dake kallonsa ganin bata sansa ba calmly yace “Abba nake nema, Baban Safeerah!” Dasauri Mama takara kallonsa tana tunani dan unguwan nan ne? Tasan Baba na gaisawa da yan layin ko zaman dayake awaje saisa ma yake dan samin kudi sukan masa kyauta once in a while, ahankali tace “bayajin dadi ne yana kwance, waza’a gayamasa”? Dasauri Salim yace “meke damunsa Mama”? Kallonsa Mama tayi da kyau jin yanda yakirata Mama, hakan yasa Mama tace “wayekai bawan Allah?” Dan shiru yayi kafin ahankali yace “sunana Salim nine Ogan Safeerah a inda take aiki, jiya tazo company mu da daddare da signs na duka toh daman maganan nazo yima Abba kenan, zan iya dubasa Mama in yaso sai nayi maganan dake” sosai Mama ke kallonsa tanajin wani natsuwa dashi especially natsuwansa sannan ba yaro bane irin su Shamsu, babba ne kuma kamili wanda yasan kansa, ganin batai magana ba yasa ahankali yace “Abba yasanni mun hadu so daya” dan ijiyan zuciya Mama ta sauke, sannin Momma bata nan hakama Shamsu Salma ce kadai agidan kuma tasan tana bacci war haka yasa tace “shigo Bismillah” tajuya yabi bayanta a natse, ga mamakinsa dakin dake gefen gate na masu gadi yaga sunyi a babban gida haka da base on the little info he daya samu jiya this house na yayar Abba ne cus ance Shamsu yakawota yaron sister kenan, and mahaifin Shamsu is tsohon gwamnan Jigawa he’s late, why will her own blood brother be living a side na masu gadi?
Bude kofan Mama tayi tashiga ciki saiya tsaya agaban dakin, juyowa Mama tayi tace “shigo” ahankali ya shiga dan karamin falo ne ga yar katifa awajen dake a gyare tsaf ga ganamasgo da jakan school din Safeerah ke kai, ga gwangwnayen abincin Waleed a wajen sai few kayan wasan yara da ball, babu komi falon, dadduma Mama takawo ta shimfidamai ya zauna ahankali tace “bari nafito dashi” tawuce ciki taduka gaban Baba da baya gane wanda ke kansa idanunsa ganin ya bace gaba daya, ahankali tace “Malam Malam” motsi yayi yace “na’am Mamana na dawo? Waleed fa”? Shiru Mama tayi tun jiya kawai Safeerah yake tambaya ahankali tace “kayi bako sunansa Salim, yace ka sansa shine Ogan Safeerah, kampaninsu Safeerah taje jiya” dasauri ya yunkura zai tashi yakasa kamasa Mama tayi suka fito tazaunar dashi Baba yace “ina Safeerah Salim”? Ruwa Mama tasa a plate mai kyau pure water ta ijiye masa ta zauna gefen Baba, anatse Salim yace “ina kwana Abba” da kyar Abba yace “lpy lau ina Mamana Salim”? Shiru Salim yayi he’s feeling very sad seeing how sick Baba is yace “she is safe Abba, namaso nataho tareda ita nadawo da ita amman taki yarda, meya faru, waya daki Safeerah haka?” One thing about Salim is bayida tsoro ko kadan kokuma irin kunyan nan da jin nauyi bai iyaba unless idan bai damu da abuba shi ba yaro bane he is here for something and he will sure do that.
Kafin Baba ya bada amsa Mama tace “rashin kunya tayi da dambe” da dan sauri Baba yace “Salim kasan kowani family nada one or two issues haka, yar matsala aka samu jiya, one thing da Safeerah shine dan banzan zuciya ne da ita inhar aka tabani ko mahaifiyarta bata daurewa” Baba yayi murmushin manya yace “Safeerah ta taso ita kadai bata da siblings so kwata kwata bata understanding cewa Yaya da kani can fight, that is basically abinda yafaru nasan nai magana da ita na lallabata zata dawo Mamana akwai rigima kam Masha Allahu” Mama data kasa daurewa tace “Malam kasan dai koka lallaba ta tadawo yan gidan ba barinta zasuyi ba ko, itama kuma rasakunyan bakinta ba mutuwa zaiyi ba kasan dai Safeerah” cikeda damuwa Baba yace “zan bawa Mama Kubra hakuri da yardan Allah zata barta ta…..ta…t….” Hannunsa yadaura akirji kawai yayi baya Mama tace “Malam Malam” dasauri Salim yatashi kama Baba yayi yarike yaji jikinsa zafi rau yace “he needs hospital Mama” daukan Baba yayi yace “muje asibiti” chak yadauki Baba, Mama da already tasa hijabi tabiyosa tasaka slippers fitowa sukayi daidai Salma na zuwa wajen tana sanye da Shedanun kayan bacci tawani kalli Salim dake dauke da Baba daga sama zuwa kasa tace “wa kuka kawo mana gida batare dakun nemi iznin Momma na ba? Wlh sainasa kuma takore ku kaman yanda takori Safeer……” wani black kallo da Salim yamata yana saukowa daga few staircase dake wajen yasa tahadiye maganan ganin bata taba ganin hadaden guy irinsa ba damn he smells incredibly good, duk yawonta duniya bata tabajin kamshi mai dadi irin nasa ba, wuceta yayi yay gate yabude Mama tabisa itama Salma tabisu da sauri wata jeep urus tagani kofar gidansu aranta tace “who is this Man! A ina suka sanshi?”Baba yasa abaya Mama ta zauna kusa dashi yazagayo ta gaba ya shiga yaja motan da gudu Baba yafara tari sosai tana wheezing yakama hannun Mama cikin wani kalan murya yace “ina Safeerah”? Cikin damuwa Mama tace “na shiga uku Malam meke damunka iyye? Malam why are you confuse, kaga calm down tana kampanin datake IT lafiyanta kalau Oganta ma shiyazo nemanka kunyi magana, Malam kadena magana kaji asibiti zamu” cikin wani irin murya yace “ki rikemin Safeerah amana, ta wahala wannan mutumin yakusan kashemin y’a! Mama Kubra ta cutarmin da yarinya amman bakomi akwai Allah akwai kuma rannan gobe kiyama, banso Safeerah takara wahala, agabana jiya an mari y’ata, an doketa, an fasamata baki duk agabana, da Safeerah ta zauna inda za’a cigaba da dukanta kaman jaka gwara na daukeku munje muyita bara a titi, kicemata nace tazo bazamu koma gidan ba, munbarsa, na yarda, bazan kara zama inda za’a dinga zagin mahaifinta agabanta ba kinji, kucemata tadawo” Mama na goge hawaye tace “zan gayamata kadena magana ya isa kaji, babu abinda zai sameka Malam” yana wani nishi yace “ku saida kaya duka asaima Waleed abinc da kudin” daidai sunkai wani military hospital nan da nan aka karbe Baba anan emergency akai ciki dashi nurse tace “Sir zoka cike form” yakalli Mama dake kuka yace “muje Mama”.
EPISODE 2️⃣1️⃣
Binsa Mama tayi jikinta yayi wani irin sanyi ganin condition na Baba, she’s regretting dama ta tsaya tabar Safeerah tai haukan nan data kwakkwadeta, yanzu ga jikin Baba ya birkice ta ina zata fara idan Baba ya rasu? How? Cike komi tayi tamike musu sannan takama bakin hijabinta takai saman idanunta tadaura awajen wani huci tafarayi sai kawai Salim ya sauke kansa kasa cikeda tausayin Mama kana ganinta kasan tayi bottling so many things aranta but yau takasa, ahankali Salim yace “he will be fine Mama, babu abinda zai sami Baba da izinin Allah” bakin hijabin tasa ta goge fuskanta tass tasaki hijabin she’s very sad da jijiyan goshinta harya fito takada kai tace
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 15