yanda ‘yan kwanakin nan ta kula kullum kafin ya kwanta sai yayi chatting. Ta mike taje ta yiwo fitsari, ta sha ruwa sannan ta dawo ta kwanta, zuwa lokacin ya gama chatting din ya ajiye wayar yana azkar. Ta kwanta ta gyara kwanciyarta, bayan da ta kula ya gama azkar din ta lalubo hannunsa ta rike cikin sanyin murya tace ‘Abban Afaf.’
‘Umm.’ Ya amsa yana kallonta duka da hasken da yake cikin dakin bai kai ya kawo ba.
‘Uhm, gaskiya ina son zuwa asibiti naga gynae doctor.’ Ta fada tana wasa da hannunsa wanda ta rike.
Ya rike hannunta a cikin nasa ya kara bata hankalinsa yace ‘Baki da lafiya ne?’
‘No ba wani specific issue. Ka san dai kwanaki nace maka ina son naje a duba aga abinda yasa har yanzu ban sake samun ciki ba, kada naje wata matsala ce nayi ta zama gara naje a duba.’
Ya gyara kwanciya ya kara matsowa kusa da ita ‘Kina dai so ki dorawa kanki damuwa, har yanzu fa ba a yi shekaru biyu da barin ba. Iya wannan ya isa ya sa ki san cewa lafiyarki kalau, kawai Allah ne bai kawo ba tunda wancan din ma ba asibiti kika je kika samo ba ko?’
‘Na sani, amma dai gaskiya ina so naje a duba ni din na sami nutsuwa. Tunda ka ga idan naje aka ce min lafiyata kalau ai dawowa zan yi kawai na cigaba da addua’a, idan kuma matsala ce sa na nemi maganinta.’
‘Babu wata matsala kina dai son tonowa kanki matsalar. Ke yanzu ma da kike neman ciki ido rufe ya zaki yi da karatun? Tunda gashi kin shiga level 3 kuma ke da kanki kina cewa ya fi wahala. Ya zaki yi da laulayi ga karatu? Ko har kin mata ne? ai zai fi sauki idan ma dolene sai kin je asibitin ki bari ki gama karatun kafin ki kwantar da kanki.’
Suka yi shiru na dan lokaci, kowa da abinda yake tunani.
PAGE 94
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Jimawa kadan tace ‘Ina son zuwa gaskiya, amma dai ina jin zan bari mu gama examsa din wannan semester in ya so kafin a koma hutu sai na samu naje.’
‘To Allah ya kaimu.’
Tana son ta haihu duk da dai Mommy ma tace mata lafiyarta kalau amma ita gaskiya tana so taje a duba ta. Kuma yanda Mustapha yake gwada mata halin ko in kula idan ana maganar haihuwa ya sa gaba daya ta fara tunanin ko bai damu da ta haihu ba; to ya ma za ayi ya so ta haihu tunda shi masoyiyarsa ta haifar masa yara har uku?
Haka tayi ta sake-sake tana juyi, sai gefin asuba sannan bacci ya dauketa.
______
kamar kullum yana shiga office din yau ma damuwarsa ta yaye; musamman yanda kamshin turarenta ya yiwa kofofin hancinsa maraba bayan da ya shiga office din nasa ya rufo kofar. Wannan ya tabbatar masa da cewa ta riga ta zo office din watakila wani office din taje. Ya ajiye jakarsa a kan table ya karasa ya zauna a kan kujerarsa cike da farin ciki.
Sabuwar sakatariyarsa Naja’atu Musa Bello; watanta uku da fara aiki amma soyayya mai karfi ta kullu a tsakanisu. Duk wata damuwa da Khadeeja zata dora masa da ya shigo office din ya ganta yake mantawa da ita, idan kuma an tashi daga office ko a ranakun da babu aiki ya kan je gidansu zance. Duk da dai manya basu riga sun shiga zancen ba amma dai yana ji a jikinsa Naja’atu tasa ce.
Bai dade da zama ba ta turo kofar ta shigo, daga tsaye ta sakar masa kyakkyawan murmushinta wanda baya gajiya da kalla.
‘Ranka ya dade barka da shigowa.’ Ta fada tana juya kwayar idonta.
‘Good Morning my dear.’ Ya amsa yana ta faman murmushin da yake barazanar karawa bakinsa fadi.
Ta karasa ta zauna a kujerar gabansa, sannan ta dauki file a kan teburin ta mika masa. Nan take ya buda ya fara karantawa yana mata tambayoyi tana yi masa bayani. Bayan sun gama ya ajiye file din a gefe ya dubeta yace ‘To meye labari?’
Tayi dariya ta sunkuyar da kai a kunyace tace ‘Komai normal.’
‘Good. So nayi mana order din lunch ko? Don na san ko ance kizo muje mu ci a waje ba kya son zuwa eateries, sai shopping ko?’
Tayi dariya tace ‘Gara dai ayi order din.’
PAGE 95
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tayi dariya tace ‘Gara dai ayi order din.’
‘Ba damuwa, kiyi mana order din sai ki turo min account number na tura kudin.’
‘Yes Boss, an gama.’
Suka yi dariya gaba daya.
Tana shirin tashi yace ‘Yauwa, gobe ana open daya a school din su Afaf, please idan kika shigo around 10am sai kije musu, ki jiyo min duk bayanasu da performances din su.’
Ta gyara zama tace ‘Uhm, ok. But Madam ba ta nan ne ko bata jin dadi?’
Ya gyara zama ya fara lilo a kujerar da yake kai yana kallonta sosai sanna yace ‘No, lafiyarta kalau but na dai fi son ke kije ki jiyo min komai.’
Cike da farin ciki ta sake fadada murmushinta tace ‘Yes Sir, Allah ya kai mu. Kuma Allah ya sa kada kasa yayata ta bani query saboda na shiga aikinta duk da dai nima ‘yayana ne.’
Yayi dariya ‘Kada ki damu, baki da matsala da ita.’
Suka sake dan taba hira sannan ta fice ta koma office dinta cike da farin cikin yanda alakarsu take tafiya ita da ogan nata.
Ba zata taba bari Mustapha ya kufce mata ba don ta ga mijin aure. Ta gama degree dinta har tayi masters, saurayinta na karshe har sun zo gaisuwa haka kawai ya daina zuwa sai ji kawai tayi ana bikinsa da ‘yar uwarsa. Duk da ta san ba wasu shekaru ne da ita masu yawa ba domin shekarunta 28 kacal, amma dai ta san an matsu tayi aure a gidansu; musammam ummanta wadda aikin ma so tayi ta hanata sai tayi aure. Sai gashi ahse mijin yana wajen aikin. A hankali suka saba, har suka kai yanzu da take jin zata iya cewa ta fi matarsa sanin halin da yake ciki da inda yake a kowanne lokaci; don haka ma take jin cewa kwaceshi a wajen Khadeeja kamar kwace goruba ne a hannun kuturu, domin tun yanzu tana jin ta fara samun nasara tunda kullum ita yake kawowa karar Khadeejan sai ta bashi hakuri, ta riga ta fahimci irin zaman da suke yi da Khadeejan don haka ta gama shirya musu; lokaci kawai take jira.
____
Karfe sha daya take da lecture don haka sai da ta gama shirya yaran dukansu suka fita makaranta sannan itama ta karasa ayyukanta ta shirya.
PAGE 96
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Karfe goma da minti biyar tana zaune a gaban mudubi tana gayar fuska ta tuna jiya da daddare Shukra ta ce mata Anty tace kowa ya zo da Mommy dinsa open day 9am to 11am sannan sai a zarce da sports, kuma idan dai ba ta manta ba ma Afaf ta gaya mata duk da section din su Afaf din da ban da na su Shukra. Sai dai basu yi maganar da Abbansu ba, bai gaya mata itace zata je ko shine zai je ba gaba daya ta manta bata tambaye shi ba. Ta mike ta dauko wayarta wadda take ajiye a gefen gado ta dannan masa kira; sai da ta kirawo sau uku duka wayar bata shiga ba, don haka ta yanke hukuncin idan ta fita sai ta fara tsayawa a makarantar tasu tukunna kada taje sai ta wuce makaranta ya bugo waya yace itace zata je ya jika mata aiki.
Nan da nan ta karasa shiryawa ta saka jilbab dinta me kalar lilac sanna ta saka bakin sneakers dinta ta sallami Rashida sannan ta wuce.
Tana zuwa makarantar kai tsaye ajinsu Shukra ta wuce, duk malaman nasu sun santa saboda zuwa daukansu don haka ba tare da bata lokaci ba aka bayanan Shukra da kuma results dinta na CA. tana gamawa ta ja hannun Shukra suka wuce ajinsu Nasreen inda nan ma aka hada mata komai, Nasreen tana cikin wadanda zasuyi wasan tsere don haka bata samu ta fita daga aji ba Khadeeja ta ja Shukra suka nufi secondary section don ta karbo sakamakon Afaf da Habib.
Tun kafin su karasa kofar secondary section din ta hango Afaf tare da wata mata sanye da bakar abaya da brown envelops a hannunta, suna tafe suna hira; ga dukkan alamu a dai malama ce a nan makarantar duk da ita Khadeeja bata taba ganinta ba. Da suka kara matsowa kusa Shukra ta zare hannunta daga na Khadeeja tana cewa ‘La, Anti Naja ce gasu nan ita da Yaya Afaf.’ Ta karasa wajensu da gudu.
Da fara’arta ta cimmusu, suna haduwa ta kara fadada murmushinta cike da girmamawa tace ‘Sannu Anti.’
Cike da mamaki itama ta dan yage baki mai kama da murmushi tace ‘Yauwa, sannunmu.’
‘Ya aiki ya yaran?’ ta kula da yanda ta ke magana kamar da kyara don haka kafin ma ta bata amsa ta mayar da hankalinta ga Afaf tace ‘Yaya Afafa muje na karbo muku CA report dinku ke da Habib na wuce don nima school zan je.’
PAGE 97
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ta dan daga gira cikin halin ko in kula tace ‘Anti Naja ta karbar mana ai, dama na su Shukra zata je ta karba yanzu.’
Ta kalli Afaf din sannan ta kalli malamar da aka kira Anti Naja tana mamaki tace ‘Me yasa? Anti ai da kin barshi na zo gashi sun saka ki aiki.’
Ta kawar da kai ta daga gira tana cewa ‘No ba wani aiki, ai Abbansu ne yace na karbar musu.’
Itama Khadeeja ta dan zaro ido tace ‘Oh, ya zo kenan ko yaushe yace a karbar musu?’
Afaf ta fahimci Khadeeja bata san Naja ba kuma bata ma san da zamanta ba, sabanin ita da kannenta wadanda a cikinsu zata iya cewa Shukra ce kawai bata san Naja ba ko kuma ta santa amma bata san wacece ita ba. Ta dan yi gyaran murya tace ‘Anti ba fa malamarmu bace, sakatariyar Abba ce kuma shine ya turota daga office ta zo mana open day din.’
Mamakin Khaddeja ya karu, ta sake karewa Naja kallo na dan takaitaccen lokaci sannan ta bude baki zata yi magana sai kuma ta fasa. Ta dan yi murmushi da gefen baki sannan ta kalli kasa ta dago suka hada ido da Najan wadda take mata kallon da ta kasa fassarawa sanna tace ‘Oh, ok, Umm.’
Kafin ta ce wani abu Habib ya karaso wajen yace ‘Yauwa Anti kin karaso? Dama ke nake jira; don Allah zo muje ki cewa uncle ni bana son basket ball team ya barni na shiga football team. Haka kawai wai saboda ni dogo ne sai nayi basketball.’
Kafin Khadeeja tayi magana Najan tace ‘Au shine baka gaya min ba Habib, ai da ka gaya min nayi masa magana.’
‘Dama Anti nake jira.’ Ya fada cikin halin ko in kula ya zari envelop guda daya daga hannun Najan ya mikawa Khadija yana dariya yace ‘Anti guess what?’
Ta dan yi murmushi yayinda suka bar Naja da baki bude, tace ‘What?’
Ya zaro takarda daya ya mika mata yana cewa 38 naci a Hausa yau don haka yau da shawarma zan yi dinner ko?’
Ta karba tana dariya sannan ta bashi hannu suka tafa tace ‘Iyye, ai dole kaci shawarma tunda yau ka wuce gori. Haba ko kai fa, kullum komai kaci A da B amma a Hasua ka dinga cin D da F.’
Ya mikawa Khaddeja envelop din yana cewa ‘To zaki ga Uncle din?’
PAGE 98
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tace ‘No, tunda yanzu ka ga kun riga kun fara games ina jin ka bari sai gobe sai na zo na ganshi. Kafin nan munyi tattauna a kan football da basketball din kuma mun yi magana da Abbanka ko?’
Ya gyada kai ‘Eh, hakane.’
Naja tayi sauri tace ‘Idan kina sauri ne ai sai naje naga Uncle din.’
Tace ‘No ba sauri nake ba, kamar dai goben zai fi dacewa kawai.’
Habib ya katsesu yana mikawa Khadeeja envelope din yana cewa ‘Anti sai mun dawo, goben kya zo kawai.’ Ya wuce ya barsu a nan.
Naja ta mikawa Khadeeja hannu tana cewa ‘Ki kawo na tafiwa da yallabai takardun tunda office zan koma.’
Ta dan yi murmushi tace ‘No ina ga gara ni na tafi masa dasu tunda a gidansa zan kwana.’
Ta bata rai tace ‘Um, sai an jima.’
Ta wuce rike da takardun Afaf da suke hannunta Afafa din tana biye da ita suna hira.
Khadeeja ta bi bayansu da kallo tana mamaki; to yaushe yayi sabuwar sakatariya? Tunda da dai ta san sakatarensa namiji ne. kuma har yaushe sakatariyar ta kai matsayin tazowa yara open day har tana wani cewa a bata takardu ta kai masa? Tukunna ma; kamar dai yaran nan sun sa wannan sakatariyar, itace bata santa ba. To kenan har yayi introducing dinta a wajen yaransa a matsayinta na wa? Me yasa suka kwana tare bai ce mata tazo open daya ba kuma bayan ya fita ma ya kasa kiranta? Wanda tunda ta aureshi duk wata harkar makarantar yara itace take zuwa kuma shi yake saka ta ta zo. To me yasa wannan ya sa sakatariya? Naja? Bata son ta yanke hukunci cewa akwai wani abu tsakanin Mustapha da Naja amma dai tabbas tana da tarin tambayin da zai amsa mata.
Sai da ta raka Shukra aji sannan ta nufi fita daga makarantar.
Tun kafin ta gama fitowa daga cikin ginin makarantar zuwa farfajiyar wajen da ake ajiye motoci ta hangosu, tana rike da hannun Afaf suna magana har suka karasa bakin motar gefen direba ta sa mukulli ta buda motar; ta dan ja baya ta labe. Me take gani ne? Motar Mustapha? To shine ya kawota ko me?
Tana nan a labe ta hangosu; Naja ta bude motar ta zauna a kujerar direba sannan ta yiwa Afaf sallama ta ja motar.
PAGE 99
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Sai da ta karanta lambar motar a fili domin kara tabbatarwa motar Mustapha ce; kanta ya daure gaba daya. To me hakan yake nufi? Ya aiko sakatariyarsa ta zo wa yara open day kuma a motarsa. To hada kudi sukayi suka sayi motar a tare? Ko kuwa dai tsabar kauna ce ko rashin hankali ya sa suke sharing motarsa da sakatariya? Me yasa bai aikota a motar haya ba ko a motar office? Wato motar da ita idan dai makaranta zata ko arage mata hanya bata isa yayi ba itace ya bawa sakatariya take yawo a gari.
Kai! Gaskiya Mustapha ya rainata.
Tayi sauri ta fito daga inda ta rabe lokacin da ta hango Afaf ta nufo wajen.
Tayi mata sallama sannan ta wuce ta fice daga harabar makarantar.
A bakin titi ta tsaya, motocin haya sai tsayawa suke ba tare da ta hau ba; gaba daya ma ta manta inda zata saboda yanda zuciyarta take zafi; me Mustapha yake nufi da ita?
Har ta juya zata koma gida saboda yanda take jin ba zata iya zuwa lecture din ba sai kuma ta tuna idan taje gidan me zata yi? Rufe kanta kawai zata yi a daki tayi kukan da ba zai mata maganin komai ba; don haka ta sake juyawa ta koma bakin titi ta hau motar BUK. Ta kalli waje ta tagar motar, tayi murmushi ita kadai; wai itace a motar haya yayinda ga wata can tana yawo a motar mijinta. Takawar da kai ta share kwalla.
Ko da ta karasa makarantar ta san an riga an yi nisa da lecture din kuma ko ta shiga ma ta san babu abinda zata gane, don haka kai tsaye ta wuce hostel dakinsu Rahma inda suka saba zuwa su huta; duk da dai ta san suna wajen lecture amma ta san inda suke ajiye mukullansu.
Tana shiga dakin tayi watsi da kayanta ta fada gadon Rahma ta kwanta ta fashe da kuka.
Sai wajen karfe daya da kwata sanna suka shigo dakin suka sameta a kwance ta ci kuka ta koshi. Suna shiga Farida tace ‘Haba Malama, tun dazu muke kiranki a waya kin ki dagawa ashe kina nan abunki.’
Suka karasa suka fada kanta Asiya tace ‘Ko dai abun ya zo ne a tanadi goro da ledar amai.’
Ta sake fashewa da sabon kuka.
Suka yi tsuru-tsuru. Rahma ta shafa bayanta tace ‘Kawata kina fadar mana da gaba fa, don Allah me ya faru? Ko Babe bashi da lafiya ne?’
PAGE 100
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Haka suka yita jero mata tambayoyi, ita kuwa tayi banza da su har suma suka gaji suka yi shiru, suka zauna kawai suna jiranta. Sai da tayi mai isarta sannan ta basu labarin abinda ya faru.
Rahma tace ‘kada fa nayi ashar kawata, kut! Wannan wanne kalar wulakancine mutumin nan yake miki?
Farida tace ‘Motar da yake kyashin daukanki yaje ya bawa budurwa ko ma karuwa take yawo a titi? Lallai an gaida uban Afaf.’
Rahma tace ‘Gaskiya idan ya dau yau ya kamata yayi miki bayani na ganewa, duk da babu wani explanatin da zai sa na yarda babu wani abu a tsakanishi da ita ba sakatariya ba ko DG ce wallahi. Yayi miki bayani kuma kema ki karanta masa; wannan ai zubar da mutunci ne kina yawi a motar haya wata sidechick tana yawo a motar mijinki? Mijinki na sunna fa, Haba! Gaskiya dai ya kamata ki san yanda zakiyi ki kwaci kanki a hannun mutumin nana tunda shi ga alama bai san mutunci ba.’
Amina tace ‘Don Allah ku barta ta bai abun a hankali.’
Ta kalleta rai a bace ‘A hankali Amina? Shi a hankali kika ga yana yi min? Ni budurwarsa take cewa wai na kawo takardun yara ta kai masa saboda tsabar samun waje? Haba mana!’
Farida tace ‘Toh shi dai na gani, aure ai ba hauka bane. Wallahi ya kamata ki dage ki gaya masa abinda yake ranki tunda dai an dade ana ruwa kasa tana shanyewa, ai ba siyoki yayi a bakin rimi ba da zai mayar dake kamar wata sokuwa.’
Amina tace ‘Don Allah ku bari a bi abun a hankali, miji fa ba kamar saurayi bane haba!’
Rahama ta ja hannun Amina tace ‘Taso ‘yar uwa mu nemo abinci wannan batun na masu aure ne ba namu ba kin ji.’
Haka ta wuni a makarantar nan Amina tana bata baki yainda Farida da Rahma suke kara jaddada mata ya kamata ta dauki mataki idan ba haka ba rainin zai wuce haka.
Sai bayan la’asar sannan ta kwaso kayanta ta dawo gidan.
……….
Wunin ranar haka ta karasashi cikin kunci, saida ta cewa yara bata da lafiya sannan suka kyaleta don kowa yana so ya bata labarin sports day. Rashidace ta karasa duk wata hidimar gida da ta yara, har abincin ma da baya so Rashidan ta girka yau cewa tayi ta girka don a yanda take jin ko ta dafa ba zai yi dadi ba.
PAGE 101
MIJIN MARIGAYIYA
A HAUSA NOVEL BY SAKINA YAZID (INNAR SU AMAL)
Sai bayan sallar magriba sannan ya dawo gidan, bayan ya gama hayaniya da yara ya wuce dakin ya sameta. Tana kwance bata ko juyo ta kalleshi ba don haka ya yi zaton bacci takeyi. Sai kawai ya kintsa ya fice daga dakin.
Bata son yiwa yaro alkawari ta karya don haka tun da ta dawo ta sa Rashida ta hada mata duk wasu kayan da take bukata na hada shawarma sanna ta kwaba mata fulawar, yanda idan ta fito bayan isha’i sai ta hada shawarma kamar yanda ta yiwa Habib alkawari idan yayi passing Hausa.
Suna zaune shi da yaran ta wucesu ta shiga kitchen, nana da nan ta fara koakrin dorawa.
Tana daga kitchen ta jiyo yana amsa waya yana kwatancen gida; ta ja tsaki a fili tana fatan Allah ya sa ba bako zai yi ba don ko me zai yi ba zata gaisa da wani bako ba balle ta bashi ko da ruwa. Sai dai yayi duk abinda zai yi. Kafin ta gama wannan tunanin ta jishi yana cewa yanzu zai fito, inda ba tare da bata lokaci ba ta ji fitarsa.
Jimawa kadan ya shigo da leda ya wuce ya sameta a kitchen tana yayyanka fulawa zata fara gasawa. Ya mika mata ledar yana cewa ‘Ga wannan shawarma ce; sakatariyata ce Naja ta aiko delivery man ya kawo a bawa yara. Sai ki duba ki zubo a tray mu ci don na ji kamar da yawa’
Ta kalleshi da jajayen idanuwanta wadanda suka kode saboda kuka da tsabar mamaki; tayi murmushi mai daci sannan ta kashe wutar abinda ta dora a wuta ta nufoshi yayinda ya mika ledar a zaton zata karba. Ta bigi kafadarsa ta wuce ta shige daki ta barshi a nan tsaye.
Ya bi bayanta da kallo cike da tsananin mamaki saboda Khadeeja bata taba yi masa irin wannan wulakancin ba; kuma a gabn yara don duk biyoshi suka yi da suka ji yana maganar a juye a ci.
Nan take ya ajiye ledar kan sink sanna ya bi bayanta daki; yana shiga ya sameta a tsaye a gaban mudubi tana cika tana batsewa kamar ma jiransa take yi.
‘Wannan wane irin wulakanci ne ina miki magana zaki yi min tsaki a gaban yara saboda raini.’ Ya tambaya cikin jin kai da isa.
Ta kalleshi ta dauke kai tana murmushin takaici tace ‘Ji nayi kamar zagina kayi.
PAGE 102
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kallon takaicin da yake mata ya koma na mamaki, ya tsareta da ido kuma itama ta ki dauke nata idon. Yace ‘Ni na zageki? Ko kuwa dai ke kika zageni?’
Ba tare da ta bashi amsa ba tace ‘Wacece Naja?’
‘Mtseww!’ ya ja tsaki sannan ya cigaba ‘Sakatariyata ce; shine kike nema ki zageni saboda nace ta kawowa yara abu?’
‘Baka gaya min ka mayar da ita wakiliyarka a makarantar yara ba, har sai da naje musu open day sannan sai na ganta wai kai ka turata. Har tana cewa wai na bata takardun yara ita kace ta karbo.’
‘Eh, ai ni nace ta karbo tunda na fita ban gaya miki ba.’
‘Kuma ka kasa yi mi waya kamar yanda kafin yau duk abinda kake so ayi na yaran kake min waya ko da ina sama jannati ne naje nayi?’
Ya fara hasala saboda yanda take maganar a tsiwace ga wani kallon raini da take masa.
‘Ba fa na son wulakanci khadeeja; ni na turata ta karbo ko ban isa bane? Na zata zaki yi murna tunda kullum cikin korafi kike da mitar hidimar yaran saboda kina gani ba ke kika haifesu ba, ke naki karatun ne a gabanki.
Tayi murmushi tace ‘Ka isa har ka yi yawa, kuma alhamdulillahi tunda an sami mai karbata yanzu kam zan huta da wasu abubuwan. Kuma na gane nice ban isa na shigar maka mota ba shi yasa ita da kake ganin mutuncinta ka koya mata mota har gashi nan ta kai ta dauki motarka ta fita yawo.’
Ta daga kafa zata shige bandaki sai kuma ta tsaya ta kalleshi suka hada ido sannan tace ‘Bayan hidimar yaran sai kuma wacce hidimar take maka? Ko ma dai ka aureta ne nice ban sani ba?’
‘Ba fa na son iskanci Khadeeja! Kina ji nace miki sakatariyata ce kike wannan maganar banzar. Na aiketa don haka na bata mota ta taje ta dawo, shine kike wannan rashin kunyar? Idan da kina hidimar yaran ba tare da kosawa ba ai babu wanda zan nema. Na san idan na gaya miki sai kinyi mita don haka na nemi wadda zata yi cikin walwala na sakata, sai dai duk abinda zaki yi kije kiyi amma idan kika zageni wallahi ba zaki ji da dadi ba.’
Tayi murmushi ‘Hmmm! Ka fi karfin zagi yallabai, amma tabbas kayi yanda kake so don haka nima zan yi yanda nake so.’
Ta juya ta shige bandaki ta turo kofar ta barshi nan tsaye.
PAGE 103
MIJIN MARIGAYIYA
A HAUSA NOVEL by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Haka ya gaji da tsayuwa ya juya ya fice daga dakin; tana jin fitarsa ta fito ta saka mukulli ta kulle dakin ta bar mukullin a jiki ta koma ta kwanta.
………..
Tun a office Naja’atu ta sanar da shi haduwarsu da Khadeeja, kuma ita kanta sai da ta nuna rashin jin dadinta a kan ya san Khadeeja zata je ya tura ta. Sai da yayi ta faman bata hakuri sannan ya samo kanta. Bai taba zaton Khadeeja zata bashi matsala, don ya zata idan yace mata sakatariyarsa ce zata fahimceshi, yanzu gashi itama
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 10 Chapter of 25