kula dasu ita da yau zata koma aiki.’
PAGE 155
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
‘Amma dai ba dasu na zo ba a nan na samesu ko? Kuma idan ban manta ba nima daga zuwana aka hada ni da su, kamar ma ita an daga mata kafa. Hidimarsu ta makaranta ma wadda ta riga ta saba yi tun ma kafin ta auri ubansu balle yanzu da ta aureka, ai inaga wannan ma karamin abune.’
Ya gama kulewa har wani huci yake, ya cije lebe sannan yace ‘Khadeeja bana son wulakancinki fa, yanzu me kike nufi da yaran nan?’
‘Alkhairi nake nufi da kowa, kawai dai duk wadda take da kwana ta hada duk har gidan da yaran ta kula da su. Shikenan.’
Har ya juya zai fita ya juyo ya nuna ta da yatsa yana cewa ‘Yanzu shikenan kintura mata yara har tsawon sati hudu?’
Ta dago ta kalleshi cikin halin ko in kula tana cewa ‘Na tura mata mijin ma?’
‘Mtsewww!’ ya ja dogon tsaki ya fice ya maka mata kofar.
Tayi ‘yar dariya ta cigaba da wasa da Hammad.
……..
Har ya koma dakin tana kwance tana baccinta domin office din da zata ta riga tace sai wajen sha daya zata tafi saboda an canza mata branch sakamakon aurensu da Mustapha; ta san tunda yau zata fara reporting tana da damar makara. A hankali ya bude kofar ya shiga saboda kada ya tasheta daga bacci, ya karasa ya zauna a gefen gadon. Ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yana shafa fuskar, gaba daya kansa ya kulle. Yayi zaton yaran nan tunda suna wajen Khadeeja shikenan a wajenta zasu cigaba da zamansu ko da ya kara aure. Gaba daya ma shi bai taba zama sun yi maganar yara da Naja ba, kawai dai yana sakata hidimarsu idan ta kama kuma yana nuna mata cewa yana so su sami kulawar da yake jin sun rasa daga wajenta. Baya jin zata bashi matsala saboda yanda yaga tana kulawa da su tun ma kafin ta aureshi balle yanzu da zata yi da hujja.
Ya juya ya dan tabata. Ta bude ido ta kalleshi tayi murmushi sannan tayi mika. Tace ‘Honey har ka dawo?’
Ya dan kawar da kai sanna yace ‘Daga ina?’
‘Umm! Na zata ‘yan makaranta ka kai.’
‘No, ban kaisu ba sun riga sun makara sosai sai gobe.’
‘Ok, Allah ya kaimu.’
Ta zuro kafafunta kasan gadon ta kwanta a kafadarsa tana cewa ‘Bari naje na yi wanka sai na fito na hada mana breakfast. Ina jin ma kawai sai na shirya ka bani lift.’
PAGE 156
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Yace ‘Ai kuwa sai kiyi sauri don ga yara can ma ke suke jira ki zo ki bamu abincin gaba daya.’
Ta daga kafadarsa ta dan kalli fuskarsa da mamaki ‘Antin bata nan ne?’
Ya kawar da kai daga kallon da ta kafeshi da shi, yace ‘Tana nan. To ai kin ga kece da kwana don haka kece zaki dinga yin baimcin duka gida kina kula da yara, in ya so idan ta karbi kwana sai ta cigaba. Duk wadda take da kwana itace da gida.’
Ta sake leka fuskarsa da mamaki a kan fuskarta tace ‘Ban gane ba, ai ni ban karbi girki ba, kwana ne kace ka tambayeta ta bamu har tayi arba’in. kuma yara ai na zata tunda a wajenta suke sai suyi zamansu duk abinda ya kama ai zan saka hannu.’
‘A’a, wadda take da kwana itace zata dinga hadawa tayi komai kawai. Kiyi sauri kiyi wankan ki zo ki bamu abinci.’
Shiru tayi kawai tana binshi da kallo. Jimawa kadan ya kalleta suka hada ido, ya gyara zama ya kama hannuwanta duka biyun ya rike sanna yace ‘Kin ga wannan fa ba wani abun damuwa bane, ai dama kin san duk inda ake da mace sama da daya ai dama duk wata hidima rabawa ake yi. Idan yanzu kika ki yin wani abu ai sai ki janyo kwanan amarcin ya kare tunda kin ga dole ne na koma kan tsarin kwana bibbiyu don tabbatarwa an yi adalci ko?’
Ta sunkuyar da kai tana kallon kasa don gaskiya ita bata zata haka ba; ba wai ba zata kular masa da yara ba amma dai ta sa rai zasu yi zamansu a wajen uwarsu itace zata dinga hidimarsu ta kullum in ya so ita duk wanda yazo inda take a cikinsu zata yi masa duk wani abu da ya kama.
Ta dago ta kalleshi tace ‘To yanzu kenan duk wadda take da kwana itace zata dinga tashi tana yiwa yara komai?’
Ya daga mata kai alamar e.
‘To idan zani aiki fa.’
Ya kama habarta ya dago fuskarta, suka hada ido yayi mata murmushi sannan yace ‘Ki bari wannan a hankali zamu ga yanda za ayi.’
Ta dan ja baya zata tashi, ya rike fukarta ya sake tsareta da ido har saida tayi murmushi, ya sumabi lebenta sannan ya mike yana cewa ‘Muna kasa muna jiranki ni da yara.’
‘Ok.’ Ta amsa sannan ta shige bandaki.
Ya tashi yafito daga dakin.
PAGE 157
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid Innar su Amal
A parlor ya tarar da yaran suna zaune suna shan shayi da burodi wanda Hafsa ta dafa musu ruwan zafin. Ya nemi waje ya zauna ya dauki remote ya canza channel.
Ya fi minti tallatin da zama shi da yaran suna ta hira sannan ta sauko, ta sha kwalliya sai kamshi takeyi. Bayan ta amsa gaisuwar yaran kai tsaye ta wuce part dinta, nan da nan ya tashi ya bi bayanta yayinda Nasreen da Shukra suka rufa masa baya. Nan da nan ta soya kwai ta hada musu da shayi suka zauna shi da ita a dining table suka karya.
Suna gama karyawa shima Mustaphan ya shirya suka fito tare. Har zasu sauka daga bena sai kuma ya bata mukullin motar yace ta fito ta jirashi zai yi sallama da Khadeeja.
A parlor dinta ya sameta tana kwance a kan doguwar kujera da remote a hannunta yayinda Hammad yake cikin baby rocker dinsa yana ta wutsil-wutsil. Tana daga kwance ta amsa sallamarsa, ya karasa kusa da kanta yace ‘Zamu fita ni da Naja, itama yau zata koma aiki.’
Tace ‘Ok, a dawo lafiya.’
Har ya juya zai fita tace ‘Ta dai barwa yara abincinsu ko? Ga shi zasu je islamiyya ko da yake na san sun yi wanka in lokacin yayi ko Hafsa sai ta tayasu shiryawa su wuce.’
Ya juyo ya tsaya ya zuba mata ido na dan lokaci; ya ma rasa ta ina zai fara. Ya kan rasa yaren da zai yiwa Khadeeja magana da shi idan ta fara wannan taurin kan nata, lokuta da dama ya kan dauka cewa tana jin tsoronsa amma fitnar da yake gani a kwayar idonta idan tana wannan taurin kan tana bashi tsoro. Ya cije lebensa sanna yace ‘Fita fa nace miki zamu yi, ya kike so tayi da abincin ranansu?’
Ta tashi zaune ta gyara zamanta sannan tace ‘Yanda nakeyi idan zan tafi makaranta ko?’
Ya jijjiga kai sanna yace ‘Khadeeja please kada ki saka min ciwon kai da safen nan, ga yara nan ki basu abinci in ya so idan mun dawo ta basu na dare. Idan kuma kin ga dama ki barsu da yunwa.’
Ta kalleshi suka hada ido tayi masa gajeran murmushin yake ta zame ta kwanta ba tare da ta ce masa komai. Haka shima ya juya ya fice zuciyarsa cike da wasi-wasi saboda ya san wannan murmushin nata ba wai yana nufin zata kula da su bane, amma dai ya tafi yana addu’ar Allah ya sa ta kula masa da su.
PAGE 158
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Sai bayan la’asar suka dawo tare kamar yanda suka fita, a lokacin yara suna islamiyya. Don haka cikin wallwala ya karas ciki don ya san Khadeeja ta kular masa da yaran. Sai da ya leka parlor dinta ya gaya mata ya dawo sannan ya wuce dakinsa.
Yara suna dawowa daga islamiyya suka wuce parlor din Naja inda suka jiyosu ita da Abbansu. Kafin wani yayi magana Shukra ta fada jikin Naja tace “Yauwa Anti kin dafa bana abinci ko? Wallahi yau gari muka sha mu da Anti, tace idan kin dawo zaki dafa mana abinci.’
Ta kalli Mustapha sanna ta sake kallon Shukran, kafin tace wani abu Mustaphan ya janyo Shukra jikinsa yace ‘Gari kuka ci Shukra?’
Ta daga masa kai. Nan take ragowar yara suka tabbatar masa da haka aka yi.
Ya kalli Afaf wadda shigowarta kenan tana kokarin zama yace ‘Ke ba sai ki dafa muku ko indomie bace?’
Ta zumbura baki ta kawar da kai ba tare da tace komai ba.
Yayi gajeren tsaki sannan ya dubi Nasreen yace ‘Ina Hafsa? Ita ba sai ta dafa muku ba?’
‘Itama garin tace ai, Anti bata ce ta dafa komai ba haka tace mu jira Anti Naja ta dawo itace da girki.’
Ya kalli Najan wadda take ta fama cika tana batsewa, ya mike a fusace ya fice daga parlor din.
Tana zaune a parlor dinta tana shan kunun alkama ya sameta, kafin ta gama amsa sallamarsa ya fara magana a fusace ‘Khadeeja wane irin raini da wulakanci ne zai saka ki bawa yara gari, ke ba zaki girka musu abinci ba kuma ba zaki saka yarinyarki ta girka musu ba.’
Ta ajiye kofin kununta ta kalle shi tana jijjiga kai sannan cikin halin ko in kula tace ‘To ai mai girkin bata bar musu abinci ba kuma bata barwa yarinyar tawa wani abu tace ta dafa musu ba, shi yasa da aka ji yunwa na hada mana gari duka muka sha. Ina laifi?’
Ya fesar da iska mai zafi saboda yanda takaici ya kamashi, baya son yanda idan Khadeeja zata yi masa fitna take zama da nutsuwarta shi kuma tana saka shi yana yin spark. ‘Khadeeja, don Allah me kike so ne kike min wanna wulakancin.’
PAGE 159
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
‘Ba wulakanci nake maka ba. Abu daya kawai nake so shine kayi adalci, yanda nake bukatar hutu daga kwana saboda jego haka nake bukatar hutu daga hidimar gida da ta yara, don dama wallahi dagewa nakeyi. Idan kuka gama arba’in din muka fara rabon kwan sai na dinga hadawa ina karba.’
Yaja dogon tsaki ya yarfar da hannu, har ya bude baki zai yi magana kuma sai ya fasa. Ya juya ya fice daga parlor din.
……..
Duk yanda yake tunanin Khadeeja zata saurara masa hakan bai samu ba. Yana so ya mayar mata da kwananta da ya karab ya bawa Naja amma kuma yana son karin lokaci don ya kara sabawa da Najan. Haka dole ya hakura ya zuba musu ido; sai dai duk wani jin dadi da yake sa ran zai samu daga wajen Najan baya samuwa saboda yanda take wuni a gajiye saboda hidima. Suna kwanciya bacci yake kwasheta; gashi kullum cikin yi masa mita take a kan ita ya mayar da hidimar yara wajen Khadeeja. Duk da kusan Khadeejan ta sallama musu Hafsa tana tayata.
Ita kuwa Khadeeja gaba daya haushinta yake ji don gaba daya ya daina kulata, a yanda yake ji yanzu ma baya jin zai kulata koda tayi arba’in din idan dai ba itace ta kawo kanta ta bashi hakuri ba.
PAGE 160
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Duk yanda Naja ta zata kula da yaran nan zai yi mata sauki abun ba haka bane, domin da kyara take kaiwa yamma saboda gajiya. Gashi Khadeeja ta sallama musu Hafsa kullum cikin taimaka mata take; abu daya da Khadeeja ta hana Hafsa yi mata shine girki. Ta so kwarai ace ta dinga barwa Hafsa tana yi musu girki idan ta fita, amma Khadeeja ta ki bari. Don haka kullum kafin ta fita aiki sai ta dafa musu abincin rana kuma idan ta dawo sai tayi na dare. Gashi duk da suna shiri da Afaf ta gane Afaf ta fita son jiki, don duk yanda take jin zasu tayata aiki hakan ma bai samu ba.
…….
Yau satinta biyu da tarewa; yana zaune a parlor dinta shi da yaransa kamar yanda suka saba suna kallon TV bayan sallar isha’i. Ita kadai ce a tsaye tana kokarin jera abincin dare a dining. Tana jerawa tana mita a ranta yanda yaran basa tayata aiki, ko da zata ce su tayata to fa idan dai yana nan ba zasu tayata ba; sai dai tayi aikinta ita kadai. Gashi kuma baya son Hafsa ta dinga yi masa girki. Bayan ta gama jera abincin suka taso gaba dayansu suka zauna harda ita suna cin abinci.
Jollof sphagetti ce da kifi; ana cikin cin abincin Shukra ta daga kifin da yake kwanonta tace ‘Abba a cire min kaya.’
Har ta bude baki zata ce Afaf ta cire mata yayi sari yace ‘Ki mikowa Antinki ta cire miki.’
Haka Afaf wadda take zaune a tsakanin Najan da Shukran ta dauki plate din da yake gaban Shukran ta mikawa Naja. Ba tare da ta ce komai ba ta sa hannu ta bara kifin gida biyu ta cire kayar sannan ta mikawa Afaf wadda ta sake mikawa Shukra.
Haka har suka gama cin abincinsu babu wanda Naja ta sake yiwa magana.
…….
Tana zaune a gefen gado tana shirin kwantaw bacci ya tura kofar ya shigo da sallama, da kyar ta amsa sallamarsa saboda yanda take jin haushinsa. Gani take kamar da gayya ya bari matarsa ta sallama mata yaran sannan kuma sun kai su kula da kansu amma komai sai yace sai tayi musu.
Ya karasa ya hau gadon ta bayanta ya kwanta, tana kwanciya ya janyota jikinsa. Ta dan tureshi tana cewa ‘Bacci fa nake ji Habibi, wallahi na gaji. Kuma ka ga gobe yara zasu makaranta kuma zan je aiki.’
PAGE 161
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya kara kankameta yana laluba jikinta yana cewa ‘Sannu, bari nayi miki massage yanzu gajiya zata sauka.’
Ta dage ta janye jikinta ta zauna a kan gadon, hakan ya sa shima ya tashi ya zauna a kusa da itayana kallon fuskarta kamar mai neman amsa a fuskar tata. Kafin yayi magana ta langabe kai tace ‘Habibi ni dai don Allah ka mayarwa da maman Hammad kwananta, in ya so mu cigaba da yi kwana bibbiyu yanda tsarin yake.’
Da mamaki ya kalleta suka hada ido sannan yace ‘Kin gai dani kenan Baby.’
Ta mika hannu ta shafi gefen fuskarsa tana murmushin yake sannan tace ‘Ya za ayi na gaji da kai, ni kama ai ban ki ba ace ni kadai ce matarka kullum muna tare. Amma ka ga aiki yana yi min yawa sosai, yiwa yara abinci kadai ya isheni da shiryasu makaranta. Kullum a gajiye nake kai kanka baka samun yanda kake so a wajena. Amma ka ga idan zan dinga samun kwana biyu a tsakani na huta ai ina ga hakan zai fi mana sauki ko? Tunda nace a daukar min mai aiki kace Hafsa ta ishemu; ita kuma wannan yarinyar wallahi karin aiki ce saboda ta fi su wasa da son jiki. Ni ban ma san yanda akayi Khadeejan take zama da ita ba. Kawai dai kace ta karbi kwananta.’
Har ta gama maganar yana binta da kallo ba tare da yace komai ba, sai da ta gama ta numfasa sannan yace ‘Um haka ne, amma dai ai kinga kula da yaran yanzu fa ba wani aiki bane tunda gaba dayansu kowa ya iya kula da kansa. Kusan za a iya cewa abinci ne kawai sai an dafa musu.’
Ta kalleshi suka hada ido. Har ta bude baki zata yi magana kuma sai ta fasa; ta kula ba so yake ya karbi uzurinta ba. Yaran da hatta kula da kan nasu ma da yake cewa sun iya idan dai bata tsaya a kansu ba babu wanda zai yi, idan kuma aka barsu haka yace zai yiwa mutane fada. Ta ja numfashi sannan tace ‘To ka dai mayar mata da kwananta don Allah, a fara rabon haka tunda ka ga yanzu saura kusan sati uku ta cika arba’in din.’
PAGE 162
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya numfasa ya zame sannan ya janyota jikinsa ta gyara mata kwanciya yana shafa bayanta sanna yace ‘Kada ki damu, in sha Allahu da safe zan yi mata magana. Ai na san kina kokari wajen kula da yaran nan kuma suma zaki ga suna jin dadin zama a wajenki, nagode sosai da kike kula min da su.’
A haka dai ya samu ya lallabata suka kwanta.
Ya san wulakancin Khadeeja, tabbas idan yaje yace mata za a fara rabon kwana yanzu ba lallai ta saurareshi ba. Baya jin ma zai iya tunkarata da wannan maganar idan dai ba so yake tayi masa dariya ba.
Haka ya cigaba da lallabar Naja don baya ma son ya tayar da maganar mayarwa da Khadeeja kwanata da ya kwace.
………..
Tunda ta kwana ashirin da bakwai da haihuwa ta yada wankan jego, kuma da yake ita din mace ce wadda ta damu ta fatarta sai ta mayar da hankali wajen gyaran fata da gahsin kanta wadanda ruwan zafi ya bata. A zaman da sukeyi da Mustapha ta san yana jin haushinta saboda ta ki ta cigaba da kula da yara shi da amarya suyi amarci, ta san ba lalli ya barta wasu kudi ba. Don haka ‘yan kudadenta da ta samu a barkan Hammad su ta fito da su ta nemi Baffanta ya kara mata dubu goma sannan ta hado kayan gayarn fata. Nan da nan cikin sati guda haske da santsin fatarta ya fara dawowa.
……….
Kamar yanda ya saba kullum da safe zai leka su gaisa kafin ya fita. Yau din ma haka ya shigo parlor din da sallama. Suna zaune a parlor din ita da Habib suna cin abinci; ita tana zaune ta mike kafa da Hammada a kan cinyarta yayinda shi kuma Habin yake zaune daga gefenta yana cin nasa abincin. Funkaso ne ta soya da zafinsa tare da parpesun kaza suke karyawa da shi; don kanta ta dafa farfesunta amma ta riga ta saba shi Habib idan dai tana nan baya cin abinci a wajen Naja. Don haka idan dai ya shigo bata hanashi, domin wani lokacin ma ajiyewa take yi don ta san zai zo nema.
Ya karasa ya zana a kan kujera daga kusa da Khadeejan, bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Nan kuka kule kuna cin dadi ashe shi yasa na ji shiru.’
PAGE 163
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tayi dariya kawai ba tare da tace komai ba, Habib ne yace ‘To ai Abba Anti Naja tuwo ta dafa jiya na san dumame za a ci shi yasa na gudo.’
Sukayi dariya gaba daya. Ta san so yke yace zai ci domin yana son funkaso, ita kuma bata so yace zai cib saboda dafawa tayi har abincin ran tunda so take ta fita idan ta dawo kawai sai taci abunta. Ya dubeta tana cinye funkason karshen yace ‘Idan akwai funkason ki zuba min na dan ci, duk da dai nayi breakfast amma ya bani sha’awa.’
Ji tayi kamar tace masa babu, amma Allah ya sa bata iya rowar abinci ba, musamman ga mutumin da shi ya kawo cefanen. Don haka bayan ta cinye nata ta mike ta kwashi kwanukan ta shige kitchen bayan ta mikawa Mustaphan Hammad; Habib shima ya kwashi nashi kwanukan ya bi bayanta. Jimawa kadan suka fito tare, ta kawo tray din da ta riko ta ajiye a gaban Mustaphan sanna ta sa hannu ta karbi Hammad; shi kuma Habib ya fice daga parlor din.
Ya sauka kasa ya fara cin abincin sannan ya dubeta yace ‘Shine kinyi funkaso ko ki kirawoni.’
Tayi ‘yar dariya tace ‘Ai na san ka riga ka ci better ka cika cikinka shi yasa na sa yarona a gaba muna ci mu kadai.’
Yayi dariya ya mayar da hankali wajen cin abincinsa.
Jimawa kadan ta tahsi ta shige daki, bata dade ba ta fito tana rike da takarda a hannunta. Sai da ta zauna sannan ta mika hannu ta ajiye takardar a gafensa tana cewa ‘Ga posting letter dina, jiya na karbo. Anyi posting dina gidan talabijin na ARTV.’
Nan da nan ya bata rai, bai ce mata komai ba sai da ya karasa cinye abincin sanna ya dubeta yace ‘Kin san dai bana son aikin jaridar nan ko, sai da mace ki saka ayi posting dinki makaranta amma shine kika je kika saka aka kai ki gidan talabijin don ki dinga fitowa a TV.’
Ta kawar da kai tana mamakin Mustapha. Tana karatunta na aikin jarida ya ganta ya aurota amma tunda yaga ta kusa gamawa yake ta faman gaya mata aiki daya zai bari tayi shine koyarwa. Watakila ma da ace bai kara aure ba da ta hakura tayi koyarwar amma yanzu kam babu yanda za ayi ya auro amaryarsa tana aikin office duk da dai ba na TV bane; sannan ita yace koyarwa zata yi.
PAGE 164
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Tace ‘Ni bani nace su kaini can ba, sun duba abinda na karanta ne kawai. Kuma idan nace a kaini makaranta naje na koyar dasu me? Ni da na karanci aikin jarida.’
Cikin halin ko in kula yave ‘Ko hausa ba sai ki koyar ba ko English, amma kin san babu yanda za ayi na barki kina fitowa a gidan TV duk duniya suna kallonki kina iya yi ko?’
‘To yanzu ya kake so ayi?’
‘Kije kawai su canza miki, idan kuma ba haka ba ni zan je a canza amma ba zakiyi aikin TV ba matukar da aurena a kanki bana so.’
Ta dan gyara zama tace ‘To ai ko naje gidan ARTV din ma ba lallai na dinga fitowa a TV ba tunda aiyukan suna da yawa kuma ba duk ma’aikatan ne suke fitowa a TV ba.’
‘Ni dai bana son kije wajen kwata-kwata tunda idan dai kana wajen wata rana za a sakaki a wani shirin kuma babu yanda zaka yi. Kawai kije su mayar dake makaranta ko kuma ki bani takardun ni naje.’ Ya fada yana mikewa tsaye.
Bata ce komai ba yace ‘Ni na tafi gidan Hajia.’
‘A dawo lafiya, ka gaishe min da su.’ Ta fada ba tare da ta kalleshi ba, kuma da yake shima ba kallon nata yekeyi ba bai ma san yanayin da tae ciki ba.
Ta bi bayansa da kallo bayan da ya fice daga parlor din; ta ma rasa me zata ce masa. Koyon aikin jarida ya ganta tana yi ya aurota, kuma sau da dama ta sha gaya masa cewa babu abinda take so take buri kamar ace yau gata a gidan talabijin tana karanta labarai ko kuma gabatar da wani shiri. Sai da ta kusan gama karatun sannan yake sanar da ita shi baya son matarsa ta dinga fitowa a TV, kuma duk lokacin da ya gaya mata ana gaya masa cewa ita kuma burinta daya kenan a duniya. Daga baya nema ta fahimci cewa da ba don ya auro Naja a ma’aikaciya ba to da tabbas ba zai barta tayi aiki ba ma gaba daya. Yanzu kam ma sai taga kamar yana dai so ya takurata ne saboda bata yi masa yanda yake so ba, amma zata san yanda zata bullowa lamarin.
……….
Sai da ta bari dare yayi lokacin ta san Baffa yana zaune a gida sannan ta kirawoshi, bayan sun gaisa ta sanar da shi abinda Mustapha din yace game da inda aka kaita bautar kasa.
PAGE 165
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Bayan a saurari bayaninta yace ‘To ke kije makarantar mana, ai ba shine aikinki ba tunda bautar kasa shekara daya ne kawai.’
Tace ‘To ai Baffa idan naje ina fatan ne su rikeni su bani permanent aiki, kuma ka ga Baffa gaskiya ba zan iya aikin koyarwa ba don za a dinga samun matsala dani.’
‘Um hakane, to bari mu gani. To ko gidan rediyo zaki je a mayar dake? In ya so sai na yiwa Mustaphan bayani.’
‘Baffa ni dai da ka yi masa magana ya barni naje gidan TV din.’
Yace ‘A’a, kiyi hakuri ki yi a gidan rediyo tunda dai yace baya son a dinga nuna matarsa a TV kinga kuma hakan ya nuna yana kishinki. Kije kiyi a gidan rediyo ta yanda ko da an saka ki a wani shiri to muryarki kawai za a ji ba za a ganki ba.’
Ta so kwarai ace Baffa ya goya mata baya ta tafi gidan TV domin shi ya san tun tana yarinya burinta kenan, amma ta san tunda yace haka ba zai goya mata baya ba; sai dai idan ta matsa ranta ya baci. Don haka sai kawai
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 25