abu kashin ya kwace mata, dan kadan ya fado ya zame daga duwawunta ya bata tsawon kafarta sanna ya dire a kasan toilet din. Yayi wuf ya dauketa ya daka mata tsawa yana cewa ‘Ki zauna a nan kiyi kashin nace, kalli yanda kika bata jikinki kika bata toilet din da kashi.’
Ta sake fashewa da kuka tana yi tana shessheka, takaici ya sa ko magana ba zai iya yi mata ba don haka ya kyaleta kawai yana tsaye tana rungume da kafarsa yana jira ta gama. Ko minti daya bata yi ba tace masa ta gama kashin, ya leka toilet din shi bai ga komai ba. Yace ‘Idan fa kika yi min kashi a wando zaneki zan yi Shukra gara ki gama kashin nan a nan.’
‘Na gama.’
PAGE 63
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Ya dauketa cak ya ajiyeta a wajen wanka, ya dauki sprayer din yin tsarki ya fesa mata ruwan da karfi ta yanda ruwan ya wanke kashin jikinta, sannan ya sabi sabulu ya wanke mata da hannunsa. Ya dauketa ya fitar da ita ya shiryata ya kwantar da ita sannan ya koma bandakin; ya tsaya daga bakin kofa ya karewa bandakin kallo. Ga guntun kashin da ta jefar a kasa sannan gashi duk ta shafe na jikinta a jikin toilet din bandakin har ya fara wari. Ya yi tsaki ya juya ya fice, jimaw kadan ya dawo dauke da tissue paper, ya warware kusan rabinta sannan yayi amfani da ita ya dauke guntun kashin jefe a toilet din. Sannan ya sake warwarowa ya goge toilet din yayi flushin sannan ya fito ya dawo parlor ya zauna cike da takaici da gajiya.
A nan a parlor din bacci ya kwasheshi, watakila saboda tsabar gajiya domin bacci yayi mai nauyi sosai. Maganar Shukra ce ta farkar da shi wadda taje tashinsa tana sanar da shi zata sha shayi. Ya tashi zaune yana mittsike ido, ya lalubi waya ya duba lokaci; karfe ukun dare saura. Haka ya tashi ya hado mata shayin ya zo ya bata ta shanye sannan ya ja hannunta suka koma dakin. A nan ya tarar ita da Nasreen duk sun riga sun yi fitsarinsu a kwance; ya canzawa Shukra kaya ya lallaba ya kwantar da ita a gefen da bai jike ba kusa da Afaf. Ya dan tsaya ya karewa dakin kallo, sai kuma ya juya ya fice.
Gaba daya kansa ya kulle; wai dama haka yaran nan suke ko kuwa don sun ga mahaifiyarsu bata nan ne kuma Khadeeja bata nan suka saka shi a gaba suka hanashi sakat, domin wasu abubuwan da suke yi ma kamar da gayya musamman Shukra.
Har zai zauna a parlor din kuma ya tuna sai ya dafa abinda zai yi sahur don haka y wuce kitchen, ya janyo indomie ya debo park uku sannan ya nemi tukunya ya dora; Afaf da Habib sun yita fushi a kan jiya bai tashe su sahur ba don haka yau idan ya gama dafa abincin sai ya tashesu. Nan da nan ya dafa idomie din ya zubawa kowa a plate ya dora a dining table sannan ya hadawa kansa shayi. Bayan ya gama ya wuce dakinsu, ya kunna fitila sannan ya karasa ya tashi Afaf, ta zauna a kan gadon tana mittsike ido sanna ya wuce ciki ya tashi Habib.
PAGE 64
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Yana juyawa ya bude ido yace ‘Abba asuba tayi ne?’
‘No da saura, sahur zamuyi tukunna ga indomie can na dafa.’ Ya bashi amsa.
Ya gyara kwanciya yana janyo abun rufarsa yana cewa ‘Ni ba zan yi azumi ba Abba, sai gobe.’ Ya rufe ido ya cigaba da baccinsa ba tare da ya sake bi ta kan Abban nasa ba.
Afaf wadda take zaune a bakin gadonsu ta juyo tace ‘Abba wai sahur zamu yi.’
‘Eh.’
‘To Abba ai jiya ne ya kamata muyi azumi kuma baka tashemu ba, nima dai gaskiya yau ba zan yi azumin ba sai gobe. Dama haka mukeyi da Anti; muyi daya mu sha daya.’ Ta fada cikin halin ko in kula.
Bata ma tsaya ta saurari amsarshi ba ta koma ta kwanta ta rufe ido.
Nan ya tsaya yana kallonsu cike da mamaki; wai su yaran nan me yake damunsu ne? yanzu zasu ce zasu yi abu kafin wani lokaci sun canza ra’ayi. Gaskiya ya jinjinawa mata, ai idan ba mace ba babu wanda zai iya raino; jiya fa Afaf fushi tayi da shi saboda bai tasjeta ba amma yau kuma ita yake tashi tana ce masa wai yau bai kamata tayi azumi ba.
Yana fitowa daga dakin ya hada indomie din ya juye a tukunyar ya rufe ya ajiye musu a kan idan gari ya waye sa ci abincin safe, sannan ya dawo ya karasa sahur dinsa.
………
Kamar yanda suka saba yau din ma da tunasuba suka tasheshi a kan yunwa suke ji, haka ya shiga kitchen Afaf ta taimaka masa ya hadawa kowa cereal domin duk sunce ba zasu ci indomie ba don tayi sanyimkuma basa son dumame, da ya takura musu ma sai Nasree cewa tayi ‘Abba kai fa idan ka dafa indomie bata dadi, ka bari idan Anti ta dawo ta koya maka.’
Don haka kawai sai ya mayar da indomie din ya rufe.
………
Tun wajen goma na safe yake sa ran shigowar Ummi don ya riga ya gaya mata yau ma tazo, sai dai ga mamakinsa har wajen sha daya saura bata shigo ba; gashi har na fara yi masa korafin yunwa kuma ana bashi warning ba za aci indomie ba sai da taliya ko macaroni. Yana shirin fita ya je gidan su Ummin aka buga gate; kanwarta ce wadda suke kira Nana, wadda bata fi shekaru bakwai ba.
PAGE 65
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Bayan ta gaisheshi tace ‘baba yace na gaya maka Ummi ba zata sami zuwa wajen su Afaf ba yau don ta tashi da mura me zafi tana kwance, yace sai dai ko zuwa gobe idan ta sami sauki zata shigo.’
Jiki a sanyaye ya amsa ‘To, kice ina mata sannu kuma kice ina gaida Baban.’
Ya rufe komar ya koma cikin gidan gwiwarsa a sanyaye; ya zai yi da yaran ga gidan kace-kaca musamman kitchen din, ko ina kwanuka. Tukunna ma; mura fa aka ce Ummi take yi. Inna lillahi wa inna ialaihi raji’un! Allah ya sa yarinyar nan ba Covid-19 ta kwaso ba garin yawon tsiya, don tabbas idan ta kwaso to ta shafawa yaransa.
‘Subhanallah!’ ya fada a fili yana daf da karasawa cikin gidan.
Bayan ya shiga gidan yayi musu bayanin Ummi bata da lafiya.
Yana ji yana gani haka ya hakuri Afaf ta dafa musu jallof macaroni, bayan sun gama ci kuma ta kwaso wanke-wanke ta fice da shi waje ta wanko; duk da koakrinsa na hanata amma haka ta dage ta wankesu. Sannan ta umarci Halifa da ya share cikin gidan wanda shima nan da nan yayi, suka dawo suka zauna.
Wunin ranar haka yayi shi yana gyangyadi domin ko ya rufe ido da niyyar bacci haka wani zai rugo kai kara har Afaf din ma, ko kuma azo ace masa ana bukatar wabi abu; ita kam Shukra haka kawai ma da taga ya shiga daki binsa takeyi, idan kuam a parlor ne da ya rufe ido zata kirawo sunanshi tace ya bude ido ta nuna masa wani abu. Haka har aka kusan magriba sannan ya samu da taimakon Afaf ya soya musu dankalin bature kuma ya dafa musu indomie ta dan yi dadi.
Wuni yaran suka yi suna ciye-ciye amma ko da ka sha ruwa ma saka shi suka yi a gaba ana cin abinci suna masa surutu da rigingimu kala-kala; shi dai zai iya cewa ba a hayyacinsa ya ci abincin nan ba. Haka ya dinga ci yana kwarewa.
Ya cika bakinsa da dankali Shukra ta mike ta jefar da dankalin da yake hannunta tana dafe duwawu tana cewa ‘Kashi Abba.’
Ji yayi wani malolo ya taokare masa makogoro; wai ita Shukra bata tashi kashi ne sai mutum yana tsaka da wata sabga?
PAGE 66
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Lallai yanzu ya tabbatar Khadeeja tana da kokari don kusan tunda aka fara azumin nan sai ana tsaka da cin abinci sannan Shukra take cewa zata yi kashi kuma ta tashi ta sakata; idan ma tayi jinkiri shine yake nuna damwarsa.
Ya dubi Afaf wadda ya kula kamar ta bata rai me yace ‘Yaya Afaf ki saka kanwarki a toilet tayi kashi.’
Ta tashi a fusace ba tare da ta amsa ba ta dire kofin shayin da taje sha a kasa, tana daga kafa tayi fatali da kofin shayin ya zube ya fallatsa ya bata Habib wanda yake kusa da ita. Ya mike a fusace yana nunata ‘Dalla malama ji yanda zaki konani da shayi saboda kashin wata.’
Ita din ma a fusace tace ‘To ka matsa mana, ko baka gani ne?’
Abbansu ya bude baki zai yi magana Shukra tace ‘Kashi Abba.’
Ya tuna yanda suka yi cikin dare ya tabbatar bai shirya wanke kashi a parlor ba don haka ya mike ya wucesu ya ja Shukra ya nufi bandaki da ita. Saida ta gama kashin ya wanke mata ya fito sannan ya saka su a gaba yayi musu fada, ya sa Afaf ta gyara inda ta bara da shayi.
Ya kurbi shayinsa da ya bari yaji yayi sanyi, haka daiya hakura ya shanye ya dan kara cin abincin. Haka ya hakura ya nemi waje ya zauna yana tunani don zai iya cewa ba kkoshi yayi ba ya dai hakura da abincin ne kawai, haka ya dinga binsu da kallo sunata wasanninsu har loakcin kwanciyar bacci.
……..
A cikin wannan halin Mustapha ya karasa kwanaki biyu shi da yaran a jigace, gashi duk wanda yayi atishawa ko tari a cikin yaran sai ya firgita saboda gani yake kamar corona ce ta kwantar da Ummi kuma suma sun shafa a wajenta.
Kamar yanda aka sanar ranar asabar aka bude gari, ba karamin dadi wannan budewar ta yiwa Mustapha ba. Tun waje karfe takwas ya shirya sannan ya shirya yaran gaba daya, sai dai da ya duba lokaci yaga safiya ta yi da yawa ya bari zuwa wajen tara da rabi sai su fita; domin so yake su je su dauko Khadeeja sannan idan ya kawota gidan ya barsu ita da yaran ya wuce gidan hajia ya gaishesu.
Sai wajen goma saura sannan suka kama hanya.
PAGE 67
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid
Tun kafin ya gama tsayar da motar yaran suka balle kofofi suka fice suks shiga gidan da gudu, bayan sun gaida Mommy wadda take zaune a parlor tace su shiga dakin Anti Nabila su taso Antin tasu inda take barci.
Jinsu kawai tayi a kanta suna shewa, ba shiri itama ta mike. Nan take aka shiga bata labarin abubuwan da suke faruwa a gidan. Itama tayi kewar yaran kuma ta ji dadin ganinsu sosai. A farfajiyar gidan Mustapha ya tsaya sai da Mommy ta tura Nabila ta shigo da shi, ta bude parlor din baki tayi masa iso inda Baffa yake jiransa don shima fita zai yi jin isowarsu ya sa ya tsaya.
Bayan sun gaisa Baffa ya tambayeshi wajen su Alhaji sai yayi gyaran murya yace ‘Yauwa, ina ga zaka bar Khadeejan ta dan kara kwana biyu don mahaifiyarta tace akwai abubuwa suke yi na gyara wanda al’ada ta tanada. Don haka ina ga ka barta ta dan kara kwana biyu mu gani.’
‘Eh, kuma da zuwa mukayi mu tafi da ita Baffa.’
‘Allah sarki, ina ga a dan daga musu kafa su gama shirye-shiryensu, ba zasu dauki lokaci ba suma na sani in sha Allah.’
Babu yanda ya iya kwarjinin Baffa ya sa ba zai iya yi masa wani dogon musu ba, don haka sai kawai ya sunkuyar da kai. Baffa yayi masa sallama ya fice ya barshi a nan cike da takaici; yaya Baffa zai yi masa haka? Wannan din shawarar Mommy ce ko kuwa dai Khadeejan ce bata son ta koma? Amma dai bari Khadeejan ta fito ya ji daga bakinta. Ya gyara zama ya hadiye malolon da ya tokare masa makogoro ya dana saita fuskarsa da ya ji motsi ana taba kofar daga cikin gida, ya mike ya koma kan kujerar zaman mutum daya ya zauna.
Khadeeja ce ta shigo da sallama, bayan ya amsa ta nemi guri ta zauna a kan three seater ta gefen da ya fi kusa da shi, bayan sun gaisa tace ‘Ya kuke kai da yara? Sun ce min ku kadai ne a gida ko gidan Hajia baka kaisu ba.’
‘To ina zan kaisu gari yana kulle, dole haka muka zauna mu kadai; don ma dai Ummi tana taimakawa, jiya ne kawai da shekaranjiya aka ce bata da lafiya.’
‘Allah sarki ai iyayenta suna mana kirki gaskiya, Allah ne kawai zai biya su.’
PAGE 68
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Suka yi shiru na dan lokaci; idan ma da yana da niyyar gaya mata wasu kalamai masu dadi to Baffa ya goge masa haddarsu, yanzu haushin kowa ma yake ji. Sai dai fatansa daya ya ga ko zai iya tsaran Khadeejan ta canza wanna tsarin don yana jin idan tace tana son ta koma ba za a hanata komawa ba.
Yace ‘Uhm, da ni fa zuwa nayi mu tafi amma na ji Baffa yace kamar zakiyi wanka ne ko gyara wai sai an kwana biyu zaki dawo.’
Ta dan gyara zama ‘Eh, Mommy tace a barni sai nayi wankan jego kuma dai da ‘yan gyare-gyare na kara hutawa sai na komawa.’
‘Wai baki gayawa Mommy cikin bai karasa wata uku ba ma, na zata haihuwa ake wa wankan jego. Ke dai idan akwai wani dalili ki gaya min sai muga yanda za ayi.’
Tayi ‘yar dariya ‘Shine dai dalilin gashi na gaya maka, don kaga har yanzu ma ban gama jini ba kusan kwana biyar kenan.’
‘Uhm! To yanzu babu yanda za ayi mu koma yau, na san ai duk wani gyara ba zai gagare ki ba tunda kin sami lafiya ga laulayin ma yanzu babu.’
‘Gaskiya kayi hakuri kawai muyi yanda Baffa ya fada, kwana nawa ne zaka ga ma na dawo gidan.’
Ya sunkuiyar da kai; tabbas wannan tsarin na Khadeeja ne sai dai bai san laifin me yayi mata ba take son tayi purnishing dinsa haka. Muryarta ce ta katse masa tunani ‘Kada ka damu in sha Allahu zuwa bayan sallah zan dawo, ka ga kafin nan ma Mommy ta samo min mai aiki.’
‘Bayan sallah? Haba! Wajen sati uku fa kenan? Ai na zata duk inda aka kai nextweek kin gama hutawar. Kuma mai aiki ai Habi zata dawo bayan sallah ko?’
‘Ban sani ba, wai dai don kada ta bani mamaki gara a samo min wata runda ga aikin gida ga hidimar yara sannan ga makaranta zan koma idan an bude gari ka ga ina bukatar taimakon mai aiki ko.’
Sai a lokacin ma sannan ya tuna ashe tana zuwa jami’a; amma dai shi har yanzu bai gane dalilin da yasa ba zata koma yau din ba har sai nan da sati biyu. Ya dai fahimci so take kawai tace aikin gida da na yara ya mata yawa, kuma shi bai ga wani wahala a ciki ba tunda Ma’u ma ko sau daya bata taba daukan mai aiki ba haka take komai da kanta.
PAGE 69
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Kawai dai ya fahimci Mommyn Khadeeja tana da son zuciya da iko shine take son ta juya shi kamar yanda take juya Baffansu, kuma gaskiya shi ba zai dau wannan ba.
Haka dai ya gama kwana-kwanarsa ya tashi ya kwashi yaransa suka wuce gidan Hajia cike da takaicin Mommy Khadeeja wadda duk ita ya dorawa laifi, gani yake kamar itace take juya Khadeeja da Baffan gaba daya.
Tuni Mommy ta bada umarni a samo mata ‘yar aiki.
………
Ransa a bace ya shiga gidan Hajia.
Yana shiga ya tarar da Yaya Jidda a gidan ita da yaranta, suna zaune a parlor din Hajia suna hira. A gaggauce yaran suka gaisa da Hajia da Yaya Jidda suka shige wajen Baffa da gudu inda yake zaune yana jiran Kaman dan autan gidan ya dawo daga shan mai ya kai shi unguwa. A nan Mustapha ya zauna wajen Hajia da yaya Jidda, bayan sun gaggaisaya dubi Yaya Jidda yace ‘Ke Yaya sai kace jira kike a bude gari ki taho, har ma kin rigani zuwa.’
Tayi dariya tace ‘Ni dama babu ni a lockdown in dai gidan nan ne kullum sai na zo, Alhaji ma ya gaji ya barni.’
Hajia ta dubeshi tace ‘Ya jikin Khadeejan?’
Ya dan karkata kai yace ‘Da sauki.’
‘Jiya ma munyi waya da Mommyn tata ai, ta dawo gidan ko sai kun fita daga nan zaku daukota?’
‘Mtseww!’ Ya ja gajeran tsaki sannan ya cigaba ‘Daga can muke, wai Mommyn tace bata gama hutawa ba kuma sai an mata wanka da gyara za a dawo da ita zuwa bayan sallah.’
Hajia ta gyara zama ta kama haba ‘Ikon Allah, to kai kuma sai kace me?’
‘To Hajia ya zan yi da su; shima baban nata bayan tuni muka gama magana da shi yace nazo na dauketa ina zuwa kuma ya canza zance; yace wai na barta. Itama kuma Khadeejan kamar haka ta zaba, kin ga kenan babu yanda zan yi da ita. Da ace ma ta bani hadin kai ne da zata iya canzawa Mommyn ra’ayi don kula kamar wannan shirin duka nata ne.’
Kafin Hajia tace wani abu Yaya Jidda tace ‘Ai kuwa lallai shiri, barin ne sai an yi wani wanka da gyara? Lallai matan nan, nifa dama shi yasa yaran ‘yan bokon nan basa wani burgeni, ciki fal iyayin tsiya.’
PAGE 70
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Hajia tace ‘To me suke nufi? Wannan duk ranar da ta haihu ai sai ta shekara sun gyara sannan zasu baka ita. To yanzu ya suke so kayi da wadannan ‘yayan, ko kuwa don ba ita ta haifesu ba? Tunda ia da nata ne hadawa zasuyi da su ko kuma ita da kanta ma ba zata yarda ta tafi ta barsu ba. Wannan ai ba tsari bane ba ma, sai dai da yake dama an bar gidan a hannun mace ai dole a ga son zuciya irin wannan.’
Ya gayara zama yace ‘Hmmm! Su suka sani kuma.’
‘To yanzu ya zaka yi da yaran? Ko kuwa haka zaku hakura kuyi zamanku tunda dama babu fita? Ko kuma nan zaka bar mini su sai muyi zamanmu, ka ga na sha allura a wajen Dr. Nasreen.’
Ya dubi Yaya Jidda sannan yace ‘Da tunani nake na barsu wajen Yaya Jidda sai na koma na dauko musu kayansu, in ya so sai a barsu iyayen Khadeejan muga lokacin da zasu dawo da ita.’
Har hajia ta bude baki zata yi magan Yaya Jidda ta tari numfashinta ‘Eh to kuma ka ga da sai muyi zaman mu, sai dai ka san gidan namu karami ne wajen kwanan zai iya yi musu kadan gaba daya da nawa yaran. Ko nan din ma ka barsu wajen Hajiyan ai duk muna tare tunda kullum ni nake zuwa na tsaya a kan hidimar gidan.’
Suka yi shiru na dan lokaci kowa da abinda yake tunani, jiamwa kadan hajia tace ‘To hakan ma ai yayi, ka bar min su a nan tunda ga baito nan tana nan zata iya duk wata hidimarsu. Tunda ka ga ai ba ma tsari ace kana zaune a gida daga kai sai yaranka yaran ma mata.’
‘Ba damuwa, zan je na dauko kayansu kafin biyar din ta yi.’
Ya tashi ya fice wajen Alhaji.
Yaya Jidda tabi bayansa da kallo; ya bata tausayi amma gaskiya ba zata karbi su Afaf ba, gara dai a nan din. Can gidanta idama ga nata yaran wadanda iadna ta ga dama nan take turosu wajen Hajia suci abinci suyi koamia sannan kuma a kara mata wasu? Gaskiya ba zata iya ba.
…..
Sai da la’asar ta kusa sannan ya fita yaje gidan ya hado musu kayansu ya kawo sannan ya koma ya barsu a nan.
PAGE 71
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Karo na babu iyaka kenana da ta dauki wayarta ta budo whatsapp ta duba; har yanzu bai amsa messages dinta ba kuma bai biyo whatsapp call din da ta yi masa ba. To me yake faruwa ne? Allah dai yasa lafiya Mustapha yake da shi da yaran. Da farko da taga tayi magana ta whatsapp bai kulata ba kuma ta kirawoshi ta whatsapp din bai daga ba sai ta zata ko fushi yayi, amma dai zuwa yau kwana uku abun ya fara bata tsoro kada taje ko wani abu ne ya sameshi.
Ta riga ta san babuu credit a wyar don haka ko balance ma bata duba ba; shi din ba mutum ne mai son saka mata credita ba, idan ma tayi magana sai yace wa zata kirawo ko kuma me zata yi da data din. Idan aka yi albashi dai idan ta yi magana yana saka mata naira dari biyar, shine zata samu ta raba ta sa data sauran ta dan yi waya. Don haka yanzun ma babu na wayar sai dai data din da ta yi mata saura. Tayi tsaki sannan ta sauka daga kan gadon Nabila inda take kwance ta wuce dakin Mommy.
A parlor ta sami Mommy tana zaune tana kallon tafsiri a tashar Sunnah TV, ta zauna a kusa da ita bayan tayi sallama ta amsa. Sai da suka dan yi jim kadan ta kula dai Mommy babu abinda zata ce mata sannan tace ‘Mommy don Allah ki dan saka min 1k a waya mana.’
Ta kalleta tana dariya tace ‘1k kuma? Ina Mustaphan ko kuma yau ba nashi kike so ba tunda kina gidana nawa kike so?’
Itama dariyar tayi ta kara langabe kai ‘A’a Mommy, don Allah dai ki taimaka, wallahi ya saka min kararwa nayi kuma dai kin san bani da kudi.’
‘Ke kenan kullum baki da kudi?’
‘Mommy bari dai na fara aiki.’
‘Uhm, shi Mustaphan ko dan na kashewa baya yaga miki balle gaki ‘yar makaranta?’
Ta dan marairaice ‘To ai kin ga yanzu anyi hutu Mommy, duk ‘yan sauran canjin ma na kashe.’
‘Shi yasa kike maula kuma? To dauko min wayata a daki na saka miki a cikin wanda mijina ya bani.’
Ta mike tana dariya tace ‘Mommy.’
PAGE 72
MIJIN MARIGAYIYA
A Hausa Novel by Sakina Yazid (Innar su Amal)
Baffanta ba wai millionaire bane amma dai ta san yana da kyauta; duk da Mommy tana sayar da ‘yan kunnaye da sarkoki amma duk wata sai ya tura mata kudin kashewa account dinta sai dai ko ya tura babu yawa amma fa sai ya tura. Kuma idan dai ta bukaci wani abu bayan wannan to yana iya bakin kokarinsa wajen ganin yayi mata sai dai ko idan babu hali.
Tayi zaton haka zata je ta samu a wajen Mustapha, musamman da yake yana yawan yi mata kyaututtuka da saka credit a waya laokacin da yana neman aurenta. Sai dai bayan ta shiga gidan sai ta tarar ba haka bane; don wani lokacin a kan ya saka mata kati a waya ya gwammace ya bata aron wayarsa tayi waya. Ko da ta koma makaranta ma tayi zaton zai dan dinga bata kudin makaranta da kudin kashewa sai dai tun a ranar farko da gane ba zai jure ba. Domin da farko bayan ta gama shiryawa tayi zaton zai kaita ne, amma sai dai suna fitowa da aka zo inda zai dauke hanya ya wuce office dinsu sai yace ta sauka a nan ta hau motar haya. Da tayi maganar kudin mota kuma sai yace mata wai ya zata tana da kudi; ta dai samu ya bata naira dubu kamar ba da son ranshi ba. Tun daga ranar ma sai ya zama ta daina damuwa tayi saui ta shirya ta bishi, yawanci sai ta jira idan ya fita sai ta kama hanya a motar haya. Kudin motar ma tana shirin ta tambayi Baffa ya dinga bata aka shiga lockdown; kuma har yanzu tana da niyyar kafin ta koma gida ta sanar da Baffanta kawai ya dinga tura mata kudin mota. Tana ta wannan tunanin taje ta dauko wayar ta kawowa Momy; ba tare da bata lokaci ba ta tura mara katin naira dubu kamar yanda ta bukata.
Nan da nan ta koma daki ta sake hayewa kan gadon Nabila sannan ta danna masa kira.
Sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ya dauka, cike da isa yana magana da kyar ya amsa sallamarta, haka
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 25