da ta kasa magana ya ce, "Hafsat yau d'in nan daga katsina ni ke Mahaifin Muhmoud da kan shi ya zo ya d'auke ni ya kai ni asibitin da aka kwantar da Mahmoud.
Mahaifin Hafsat shiru ya yi kamar mai tunanin kafin ya ce "Hafsat dama shi yaron da ya saceki din ya fada Miki Yana sonki?." Shiru Hafsat ta yi ta kasa ko motsi. Mahaifin Hafsat Kuma ya ci gaba da cewa "Jiya mahaifinsa ya zo har nan Bakori ya daukeni ya kaini Katsina asibitin aka kwantar da Mahmoud din bashi da lafiya anan yake fadin mahmoud din ne ya saceki."
Hafsat shiru ta yi dan ta rasa abinda za ta ce, Mahaifin Hafsat kuwa kallan Hafsat ya yi ya ce, "Hafsat, zan tambayeki amma Ina so duk abin da zaki fadamin ki fadamin gaskiya."
Kai Hafsat ta daga ma mahaifinta shi kuma ya ci gaba da cewa "Hafsat yaron nan ya taba kimarki koko?." Kai Hafsat ta girgiza ma mahaifinta kanta kasa tana goge hawayan da ta ji yana zubar mata wanda ita kanta ba ta san dalilin zubarsu ba.
"Kai mahaifin Hafsat din ya jinjina ya ce "kin tabbata?."
"Wallahi Baba babu komai hasalima ba daga ni sai shi muka zauna ba ya kawo min wata shohuwa tare muka zauna daga baya Kuma mahaifinsa da ya ganni ya maidani gidansa da zama."
Mahaifin Hafsat shiru ya yi sannan zuwa can ya ce, "Hafsat yaron nan bashi da lafiya sosai har na je na dawo bai son wake kanshi ba, Mahaifinsa ya rok'eni da in bashi auranki, amma bani da ikon hakan, tabbas Hafsat da ace ni mai cikakkyan Iko ne akan ki tom Wallahi da na ba da auranki ga yaron nan, dan daga yaron har Mahaifin yaron ni dai sun kwanta min"
Hafsat da dai kanta na kasa tana mai ci gaba da goge hawayan da bata san dalilinsu ba, kallan mahaifinta ta yi ta ce "Baba zan je in kwanta." Hafsat tashi ta yi ta shiga d'akin Mahaifiyarta ta kwanta.
Hafsat cikin k'ank'anin lokaci zazzab'i ya rufeta sosai dama cikinsa take ta fita.
Hafsat na nan kwance Mahaifiyarta ta shigo d'akin, ganin mutum alillib'e ya sa Mahaifiyar Hafsat matsawa kusa da Hafsat ta ce, "Hafsat lafiya me ke damunki?" Hafsat shiru ba magana, sai rawar sanyi da ta ci gaba da yi, Mahaifiyar Hafsat cire a bun rufar Hafsar ta yi ta na kallan Hafsat d'in ganin kuka ta ke ga kuma rawar sanyi da ta ke alamun zazzab'i na damunta, Mahaifiyar Hafsat kallan Hafsat ta yi cikin damuwa ta ce "Hafsat me ke miki ciwo?." Hafsat kamo hannun Mahaifiyarta ta yi tana kuka ta ce "Mama, dan Allah ki kai ni in gaida shi Wallahi ya yi min kirki sosai" Mahaifiyar Hafsat cikin sanyi ta ce "Hafsat wa zan kai ki ki gaida?" Hafsat ta na mai ci gaba da kukan ta ta ce "Yallab'e dan Allah mama" Mahaifiyar Hafsat cikin mamaki ta ce "Hafsat wa ye kuma Yallab'e?." "Mama shine wanda ya taimakeni ya yi min kirki sosai har duka yake rama min." Mahaifin Hafsat da yake ya na daga bakin k'ofar d'akin ya ji duk abinda Hafsat ke cewa d'akin ya shigo ya kalli Mahaifiyar Hafsat ya ce, "Yaron da ya tsinceta Mahmoud da ya ke yau Mahaifin yaron ya zo ya tafi da ni har katsina dan ganin halin da yaron nasa ya ke ciki, nan mahaifin Hafsat ya yi ma Mahaifiyar Hafsat ba yanin komai da maganar auran Hafsat d'in da Mahaifin Mahmoud ya rok'e shi ya ba Mahmoud d'in amma ya b'oye mata cewa Mahmoud ne ya sace Hafsat.
Mahaifin Hafsat kallan Mahaifiyar Hafsat ya yi ya ce, "Tom kin ji dalilin Cewar za ta ta gaida shi saboda na ce ma ta Mahmoud d'in bai da lafiya sosai" Mahaifiyar Hafsat kallan Hafsat ta yi ta ce, "Hafsat kina son zuwa ki kai da Mahmoud d'in ne?." Hafsat da saurin ta ta ce, "Eh Mama dan Allah." Mahaifiyar Hafsat kallan-kallo su kai da Mahaifin Hafsat, sannan Mahaifin Hafsat d'in ya ce "Hafsat zuwanki gaido Mahmoud ba zai yuwu ba saboda sanin kanki ne saura sati d'aya auran ki kin ga ko ba zai yuwu ba ki je gaida Mahmoud" Sallamar Usaini ce k'anin Hafsat ta sa Mahaifin Hafsat ya yi shiru, Usaini kallan Hafsat ya yi ya ce, "Aunty Hafsat Yaya Usman na kiranki" Hafsat ko inda Usaini ya ke ba ta kalla ba ta ce, "ka ce mai banda lafiya" Mahaifin Hafsat kallan Usaini ya yi ya ce, "ka ce mai ya shigo ciki bata jin dad'i ne" Mahaifin Hafsat fita ya yi itama Mahaifiyar Hafsat bayanshi ta bi.
Hafsat guri d'aya ta rakub'e tana jiran shigowar Usman.
Usman daga ka ganshi ka ga wanda ke murnar shirin angwancewa. Da mamaki ya bi Hafsat da kallo ganin yadda ta rakube kamar wata maraimiya Usman kallan Hafsat ya yi ya ce, "Baby wai me ke damunki ne Usaini ya ce min baki da lafiya?" Hafsat ba tare da ta kalli Usman ba ta ce, "Yaya Usman zuciyata ce ke gab da bugawa." Usman cikin alamun rud'ewa da maganar Hafsat ya ce, "Haba Baby dan Allah ki bar maganar nan mana muna shirin aure kina irin wannan maganar kinga invitation card da na kawo miki na biki ki raba ma friends dinki"
Usman ya d'ora ma Hafsat katin gayyatar a jikinta.
Hafsat ko bata san sanda ta yi wurgi da ledar invitation card d'in ba duk ya watse atsakar d'akin tana mai fashewa da kuka.
Usman kallanta ya yi ya ce, "Baby me ki ke nufi da hakan? Ni fa yanzu kamar mijinki ne in da saura sati d'aya ki zama matata na biya sadaki saura shaidu kadai suka rage mana me ye dalilin yimin wurgi da abu?." Hafsat cikin rashin sanin abin da zata ce ta ce "Yaya Usman ni ba zan aureka ba na fasa auran." Hafsat ta idasa maganar tana kuka. Usman bai san sanda ya tashi tsaye ba ya ce, "Baby ko dai tabuwar kwakwalwa ke damunki ne? kin san ko abinda ki ke cewa?" Hafsat ma tashi tsayan ta yi ta ce tana mai ci gaba da kuka "Yaya Usman nasan abinda nake cewa, ka yi hakuri zuciyata ba kai take so ba yanzu na fasa auranka" Usman shak'e wuyan Hafsat ya yi cikin tsananin kishin jin wani take so ba shi ba ya ce, "Ubanwa ki ka canza fad'amin sunan shi? Ubanwa kika canza na ce?" Hafsat cikin haki ta ce "Wallahi bana sonka ni akwai Wanda nake so ka sakamin wuyana dan ko kasheni za kai ba zan aure ka ba, so tsuntsu ne tom ya tashi daga kanka ya koma ka... ". Usman tsabar kishin maganar Hafsat da zafin maganar da ya ji ya sa ya wanka mata mari" Hafsat dafe kuncinta ta yi tana kallan Usman ta ce, "Ni ka mara?" An mareki d'in, kuma bari ki ji ko kina so ko ba kya so baki da miji sai ni Usman na ga uban da zai d'aura auranki ba da ni ba" Usman na fad'in haka ya ingije Hafsat ya yi tafiyarsa.
Hafsat ta shi ta yi tana kuka ta ce, "Bana sonka kuma ba zan aure ka ba in sha Allahu"
Usman cikin jin zafin Kala man Hafsat ya fita daga d'akin ya bar Hafsat kwance agun tana kuka.
Usman direct gidansu ya je wajan Mahaifiyar shi.
Mahaifiyar Usman ko ganin yadda Usman ya shigo ya sata nufi Usman d'in tana tambayar shi lafiya.
Usman fashe ma mahaifiyarsa ya yi da kuka ya ce "MaMa Hafsat wai ta fasa aurena ki taimakamin Hafsar ta ce ba za ta aure ni ba kuma wallahi mama da gaske ta ke dan duk na lura da yanayin take-takenta tun da wowar ta"
Mahaifiyar Usman kallan Usman ta yi ta ce, "Usman ka kwantar da hankalinka, Hafsat haukar banza ta ke yi inda dai ba ita ke da kanta ba aure kuma ina ma saura sati d'aya fa ya rage, dan haka ka bari zan je gidansu Hafsat d'in yau din nan idan ma uwarta ke zugata zan hadasu duka har uban nata inci ubansu."
Usman sosai ya ji hankalinsa ya kwanta maganar Mahaifiyarshi.
Da daddare kamar yadda Mahaifiyar Usman ta ce, haka ko aka yi gidansu Hafsat ta je tana zuwa ta yi d'akin su Hafsat, zaune ta iske Hafsat Mahaifiyarta ta matsa mata ta cinye abincinta ta kuma sha maganin zazzab'in da ta ke bata. Mahaifiyar Usman ta na shiga ta ce, "Ina Hafsat d'in ta ke dan ubanta in ji inma uwarta ce ke d'aure ma ta gindin abinda ta ke yi" Mahaifiyar Usman wato gwaggon Hafsat kallan Hafsat ta yi ta ce, "Dan Ubanki me kika cema Usman?" Hafsat da gabanta ke dukan uku-uku tun shigowar gwaggonta, Hafsat shiru ta yi, ai ko Hafsat a ba zata ta ji an wanke ta da mari, Mahaifiyar Usman ta nuna Hafsat da hannu ta ce, "Dan'ubanki ba kya ji ne ina magana? Ubanwa kika kawo wanda ya fi d'an'uwanki?" Hafsat shiru ta yi tana kuka jikinta ko ina rawa ya ke dan dama ita arayuwata tsoran gwaggonta Uwani ta ke yi.
Mahaifiyar Usman ko wani Marin ta sake kai ma Hafsat ta ce, dan Uwarki ba da ke na ke magana ba, Ubanwa ki ke so Wanda ya fi d'an'uwanki?" Hafsat fashewa da kuka ta yi ta ce, "Dan Allah gwaggo ki Yi hak'uri" In yi hak'uri ba kya son Usman ko-ko ya ya?" "Gwaggo dan Allah bana son Yaya Usman Wallah..."
Ai Hafsat ba ta k'arasa fad'in abinda ta yi niyyar fad'a ba gwaggonta ta rufeta da duka, dukan Hafsat d'in ta ke sosai tana cewa "Uban wa kike so wanda ya fi d'an'uwanki? Mahaifiyar Hafsat na d'akin amma ta kauda kai gefe.
Ana ahaka Allah ya kawo Mahaifin Hafsat dakin da saurinsa yana cewa "Maman Hafsat me ya yi zafi yarinyar bata jin dadi zaki rufeta da duka haka?." Bisa ga alama mahaifin Hafsat ya yi tunanin mahaifiyar Hafsat ce ke bugun Hafsat hakan ya sa ya zo da saurinsa ransa bace. Saidai ganin babbar yayarsu ce ke bugun ya sa ya yi shiru.
Mahaifiyar Usman ko sai da ta tabbatar Hafsat ta bugu sannan ta dai na dukanta.
Mahaifiyar Hafsat ko kallan Mahaifin Hafsat ta yi da ya yi shiru shi ka d'ai yana kallan Yayar ta shi ta ce, "Baban Hafsat ka gafarceni da abinda zaka ji amma Wallahi ban yadda Hafsat ta auri Usman ba✍🏻
Fadila Sani Bakori ce
💓💞SO NE SILA💓
💫💫
*🅙︎ARUMAI 🅦︎ WRITERS 🅐︎SSOCIATION📚🖊️*
_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa💪*_
*💫(🅙︎.🅦︎.🅐︎)💫*
Page 25 & 26
Kafin Mahaifin Hafsat ya yi magana Uwani ta yi karaf ta ce, "Zainab idan har ke zaki d'aura auran Hafsat da Usman dan Allah kar ki d'aura, auran Usman da Hafsat kamar an yi an gama ne sai dai in bana numfashi" Mahaifiyar Usman na fad'in haka ta juya wajan mahaifin Hafsat dake tsaye ya kasa cewa komai ta ce "Kai Kuma shanyayye an wanke an baka kasha ka yi shiru kamar baka ji rashin kunyar da mataka da yarka ke min ba."
Mahaifin Hafsat cikin sanyinsa ya ce "Ki yi hakuri Yaya uwani, komai zai daidaita in sha Allah." Mahaifiyar Usman bata tanka ma mahaifin Hafsat ba dan da alama ba haka ta so ba so ta yi ya rufesu da duka ko fada, hakan ya sa ta juya ta tafi cikin fushi.
Bayan Mahaifiyar Usman ta tafi ne, Mahaifin Hafsat ya kalli Mahaifiyar Hafsat alamun ranshi ya b'ace da abinda Mahaifiyar Hafsat d'in ta yi ya ce "Zainab, me ki ke nufi da ba ki yarda da Hafsat ta auri Usman ba? Bacin kinsan ko ni ban isa in hana auran Hafsat da Usman ba ban da wannan ikon inda ina da na gaba dani. " Ni fa ka yi hakuri Ina kan bakar maganata sai dai in za a shiga hakina ne a yi mana dole, dama tun farko Hafsat bata son Usman biyayyace kawai ta yi ta amince, Kuma lokacin bata ma gama tantance meye son ba, sai yanzu dan ta fito da ra ayinta Yaya uwani ta kamata ta buga." Ran mahaifin Hafsat a bace ya ce "Ok, kina nufin Yaya uwani bata isa ta bugu Hafsat ba kenan kome kike nufi? To bari ki ji Yaya uwani ko yanka Hafsat ta yi ko ni bani da hurumin magana bare Kuma ke." Ni fa ba wai dan Yaya uwani ta bugi Hafsat bane na yi wannan maganar, kawai dai na duba rashin adalcin haka ne, hakan ya nuna ko bayan auran Hafsat da Usman ba zata iya tsayawa ta yi adalci a tsakaninsu ba, sannan Hafsat bata da lafiya amma bata duba damuwar Hafsat ba ta kama ta ta buga saboda damuwar Usman kadai, Sannan ko alokacin da aka tsaida maganar nan Hafsat ta amince ne kawai dan biyayya amma ba wai dan tana son Usman ba, dan ni da bakina da na Hafsat mu kai magana ta ce min ba ta son Usman, amma da kuka tambayeta ta ji nauyinku a matsayin ku na Iyayanta ta amsa muku amma ba wai dan tana son Usman ba"
Mahaifin Hafsat Shiru ya yi kafin ya ce "Tom wai yanzu me ki ke nufi da duk magan-ganun nan da ki ke yi? " Abinda na ke nufi d'a bai fi d'a ba, kamar yadda ta ke son farin cikin Usman har ta kasa kawaici agabana aga banka ta bigi Hafsat wai dan kawai ta ce ba ta son Usman tom nima haka nake son Hafsat Kuma nake son farin cikinta." Mahaifin Hafsat kallan mahaifiyar Hafsar ya yi ya ce "Zainab, kada in k'ara jin magana makamanciyar wannan da ki ka yi ki na jina ko? Idan ba so kike a yi auran Hafsat baki gidan nan ba ki yi mata fatan alkairi kawai amma kar in Kara jin bakinki akan maganar auran Hafsat da Usman dan kamar an yi an gama ne." Mahaifiyar Hafsat shiru ta yi bata Kuma cewa komai ba. Mahaifin Hafsat fita ya yi ya bar Mahaifiyar Hafsat a nan tsaye.
Mahaifiyar Usman kuwa cikin b'acin rai ta tafi gida, tana zuwa ta kira k'aninta mai bi mata wan Mahaifin Hafsat kenan ta sanar da shi Kar ya fita za ta zo da safe.
Da safe kamar yadda Mahaifiyar Usman ta ce Mazan gidan su jirata zata zo haka ya faru da sassafe ta yi sammako ta nufi gidansu Hafsat din da yake babban gida ne shashi-shashi.
Mazan gidan duk sun San da zuwa Yaya uwani hakan ya sa masu sammakon fitar ma duk suka hakura suka jirata, duk sun hallara amma babu mahaifin Hafsat. Mahaifiyar Usman da ta zo zama ta yi su ka gaggaisa sannan ta kalli Nasiru mai bima ta ta ce, "Nasiru, ya banga Kabiru ba fa?" Wato Mahaifin Hafsat. Wanda Mahaifiyar Usman ta kira da Nasiru cikin girmamawa dan sosai suke girmamata kasan cewarta babba acikinsu ya ce, "Bari in kira shi awaya" Suna nan zaune sai ga Mahaifin Hafsat ya shigo. Nasiru ne ya kalli Mahaifiyar Usman ya ce "Yaya Uwani kin ce kina son magana da mu tom gamu mun hallara muna sauraranki." Mahaifiyar Usman cikin nuna alamun jin zafin abinda za ta ce ta ce, "Tom dama akan maganar auran Usman ne da Hafsat shine na ke so ku kira Hafsat ta mai-mai ta mu ku abinda ta ce min" Jamilu da ya ke shine k'ara min su shine ya tashi da kanshi ya je ya kira Hafsat.
Hafsat na kwance cikin zazzab'i k'anin Mahaifinta Jamilu ya kirawota, Hafsat cikin dauriya da yadda ta ke ji ta taho, Hafsat cikin muryar mara lafiya ta zauna d'an nesa da Mahaifinta ta ce, "Baba sannin ku gani" Mahaifiyar Usman kallan Hafsat ta yi ta ce "Hafsat, mai-mai ta abinda ki ka ce min game da auranki da yayanki Usman?." Wata irin fad'uwar gaba ce ta ziyarci Hafsat jin abinda gwaggonta Uwani ta ce, Hafsat Shiru ta yi dan ta rasa abinda za ta ce. Nasiru ne cikin alamun tsawa ya ce, "Hafsat dan Ubanki ba da ke ake magana ba?" Hafsat cikin in da in da ta ce, "Baba dan Allah ku ya femin Wallahi Baba tun lokacin da ku kai min maganar Yaya Usman na amsa ne ka wai, amma Wallahi azuciyata ba haka ba ne ban san sanda na amince ba am....." Tsawa Nasiru ya yi ma Hafsat tun kafin ta karasa ya ce "Dan ubanki ki rufe ma mutane baki kafin in fasa miki baki, bari kiji ko da ace ba Usman zaki aura ba kin yi kadan ana gaf auranki ki zo Mana da maganar Wai ba kya son Usman Wallahi ba zamu dauki wannan iskancin ba."Uwani kallan Nasiru ta yi ta ce "Ka rabu da ita Nasiru ni na fi tunanin zugar Mahaifiyarta ce, ni yanzu gani nake me zai hana gobe kawai a daura auran a wuce wajan kafin zugar Mahaifiyarta ya Kara tasiri a zuciyarta." Kasan cewar duk ba sa iya yima uwani musu hakan ya sa Nasiru ya ce "Tom Yaya Uwani duk yadda kika ce, amma ni bana ganin Zainab zata zuga Hafsat iskancinta ne kawai, amma Aminu ku ya kuka gani?."
Wanda aka Kira da Aminu ya ce "Tom, ni dai a ganina kar mu yi gaggawa inda kwatakwata ma yau saura kwana shida bikin ai, gani nake kafin nan kafin ranar mulallashi Hafsat din Mana." Eh tom maganarka Kuma haka ne." Nan dai suka taru suka yi ta yi ma Hafsat nasika kafin taron ya watse.
Hafsat na shiga dakinsu ta rike Mahaifiyarta tana kuka sosai ana a haka ne mahaifin Hafsat din ya shigo zama ya yi ya yi shiru ya dade yana sauraran kukan Hafsat din kafin ya yi gyaran murya ya ce "Hafsat, kinsan dani da gwaggonki uwani dukkanmu ba mu isa mu yi abinda Allah bai yi ba ko, idan Allah ya kaddara Usman mijinki ne ko kukan jini za ki yi sai kin auresa, haka kuma idan Allah ya sa ba mijinki bane ko duniya za ta taru ba zaki aureshi ba, dan haka ki yi hakuri ki bar kukan nan ki ci gaba da addu'a." Yana fadin haka ya tashi ya fita.
Bayan ya fita ne mahaifiyar Hafsat cikin sanyi itama ganin yadda Hafsat ta tada hankalinta ta ce "Hafsat, kin ji dai abin da mahaifinki ya ce miki ko, ki yi hakuri ki kwantar da hankalinki idan har ki ka ga kin auri Usman tom shi ne alkairinki saboda tun sa ranarku nake addu'a har yau ban fasa ba." Mahaifiyar Hafsat ta dade tana lallashin Hafsat kafin ta je ta ci gaba da aikinta ta bar Hafsat nan kwance.
Hafsat na nan kwance Fadila ta shigo tana fada tana cewa "Wai ita dan Allah gwaggo uwani haka ake ta ce wani dole sai kin auri Yaya Usman, su Kuma su Baba ba me iya magana bacin dukansu babu Wanda baisan Yaya Usman na shaye-shaye bama." Mahaifiyar Hafsat dake kitchen lekowa ta yi ta yi ma Fadila dakuwa ta ce "Uwaki Fadila, wato ana lallashinta shi ne ke Kuma zaki zo ki zugata, Allah ya sa ki Kara magana Allah sai na fada ma babanku in ya shigo." Fadila jan bakinta ta yi shiru kafin itama ta ci gaba da lallashin Hafsat din.
Haka rayuwa ta ci gaba da tafiya duk yadda mahaifiyar Hafsat ta so Hafsat ta kwantar da hankalinta abun ya ci tura dan yanzu ko abinci sai ta yi ma Hafsat da gaske take ci.
Yauwa kwana biyu kenan da faruwar hakan wanda ya yi daidai da saura kwana hudu bikin Hafsat da Usman.
Yau dangin mahaifin Usman suka kawo lefan Hafsat, nan fa gida ya Kuma cika da mutane masu ganin lefe. Wannan lefan da aka kawo ba karamin tada ma Hafsat hankali ya yi ba wanda har hakan ya yi sadiyar saukar mata da zazzbi sosai jikinta, kwance take tana kuka sosai ga yunwa da ta azabtar da kanta da ita.
Mahaifiyar Hafsat Koda ta shigo dakin hankalinta na kan Hafsat dan ta lura kullum hankalinta atashe yake. Zama ta yi gefan gadon Hafsat din hannu ta sa ta yaye abun rufar Hafsat din wadda jikinta har rawa yake saboda da zazzabi ga Kuma kuke da take yi. Mahaifiyar Hafsat cikin fada ta ce "Ba dai an baki baki kinki yin hakuri ba idan kika kashe kanki ke kika sani, garama ki sama ranki hakuri dan ko suma kike iyayanki sai sun daura auran nan, mafi a'ala ki yi hakuri ki rungumi auranki inda Usman dai ni shaida ce yana sonki sosai idan Allah ya sa rabon ya shiryu ne sadaniyarki sai ki ga ya natsu ya bar shayeshayen da yake yi, Kuma tun farko da kika amince ai kinsan yana shayeye-shayan."
Hafsat ba ta ce komai ba, Kuma ba ta fasa kukan da take yi ba. Mahaifiyar Hafsat haka ta gama Mata nasiha mai tattare da fada-fada kafin ta tafi.
Ana saura kwana biyu biki Usman ya zo gidan, kasan cewar Hafsat ta maida kanta kamar mai jinta kullum akwance ya sa mahaifiyar Hafsat ta ce ace ya shigo.
Hafsat ko na jin haka ta fashe da kuka a haka ya shigo ya sameta tana kuka.
Usman zama ya yi cikin sanyin jiki kafin ya ce "Na Kira Fadila ai ta kawo miki wayar ta ce min baki da lafiya shi ya sa ma na zo, ya jikin naki?." Hafsat ko jin Usman ma ba ta yi bare ta amsa mai, Usman kamar zai yi kuka ya ce "Hafsat, nina san kina Sona shiga tsakaninmu ake so a yi, amma ki sani ni Usman na yi miki alƙawarin za ki ji dadin zama dani ba zaki taba da na sanin aurena ba." Hafsat dagowa ta yi tana kallan Usman din kafin ta tashi ta zauna ta ce cikin roko kamar za ta yi kuka "Yaya Usman, dan Allah dan annabi karka sa son zuciya ka zutar da zuciyar da ta riga ta ginu da soyayyar wani a ranta, Wallahi ko lokacin da na amsa maka Ina sonka bansan me ye so ba, na amince ne kawai na yadda zan aureka ba wai dan inajin sonka a raina ba, yaddar auran ce kawai ta shigan ta auranka ba so ba, sai yanzu da zuciyata ta hadu da mahadinta sannan nasan ainihin abinda ake nufi da kalmar so, Ashe kamar so da ban kamar zan aureka ma da ban, idan har ka aminta aka yi auran nan ka tabbar gangar jikina ka aura dan dama itace ta aminta da auranka dan ban furta maka kalmar so ba na san dai na aminta da maganar auran kamar yadda gangar jikina ta yadda bisa tursassata itama na zaman aure da Kai da aka yi, amma ruhina da zuciyata tuni sun yi bankwana dani sun tafi mahallinsu sun tafi mahadarsu sun barni Ina aiki da gangar jikana kadai. Yaya Usman dan Allah ka furta ma gwaggo uwani ka hakura da aurena kodan samun salamar rayuwarka kaima, meye amfanin rayuwa da matacce Yaya Usman? Idan har aka yi auran nan ka dauka kamar ka auri matacciya c..." Kuka ya ci karfin Hafsat ya sa ta yi shiru.
Usman tashi ya yi yana kallan Hafsat ya ka sa furta komai dan Allah ne kadai yasan irin son da yake ma Hafsat, hakan ya sa ba tare da ya ce komai ba ya fita da sauri.
Mahaifin Hafsat daga dakinsa ya hango yadda Usman ya fito