ban tava baki kwabo ba, da abokaina suka zo ganinki suka baki kuxi ma na karve, saboda dama ni zuciyata ba ta kwanta dake ba, na daxe ina ganin kamar za ki iya aikata abin da kika aikatan, shine kika gudu ashe ba kuskure na yi ba.
Wato ke kina nufin za ki iya yin dalilin da mahaifiyata za ta qara yin fushi dani? Kina nufin bayan duk abin da kika sani na tsakanina da ita za ki iya yin dalilin da zai fi haka rashin daxi?
In bakya sona ai ba zan tilasta ki zama dani ba, ni wani irin mutum ne da yake girmama abin da yake son shi. Ko da kika ga na bi hanyoyin da na bi wajen karvar auren ki na lura da quruciyar dake gareki ne, sai kuma na ga ni za a gwada min qarfi, amma in bakya sona ai zan iya yin haquri ba zan so kaina a kanki, zan mutunta al’amarinki in bi son zuciyarki tare da adalci a kai.
Amma ai babu wulaqanci ko tozartarwa a tsakanina dake, ki tashi daga nan ki je ki shiga cikin qartin maza ki nufi Misau ki je ki cewa iyayenmu me?”
Cikin matsanancin vacin rai yake jero kalaman nashi, don haka bai ko saurari kukan da take yi ba.
“Waye ya baki kuxin mota?”
Ta yi shiru.
“Ko shi wannan mutumin ne ya biya miki?”
Ta yi maza ta ce, “Eh”.
Ya zuba mata ido shi ba abin ya xauke ta da mari ba. Ya yi qarfin halin sake tambayar ta.
“A ina kika san shi?”
Ba tare da ta kalle shi ba ta ce, “Tare da shi muka zo daga Misau”.
“Ke da shi da Abu?”
Ta ce, “Eh”.
“Zancen banza kenan”.
Ya miqa hannu ya kamata, ya ce, “Ai duk inda mavoyar kuxin naki suke sai na gansu yau, tunda na ganeki”.
Ya soma cire kayan jikinta yana watsarwa, ita kuma tana kici-kicin hana shi da qoqarin rufe abin da take ganin shi ta fi qin ya gani. Ba tare da ya saurari kukan ta ba.
Lilita ya tarar xaure kan siket xin ta, ya zubawa likitar ido cikin sanyin jiki. Wannan ai lilitar Inna ce dake zuba cinikin kayan miyanta a ciki. Wato Inna ce ta baki kuxin da za ki gudu daga nan ki koma gida ke kaxai? Wai me na yi? Gaskiya ba zan bar maganar nan ba.
Ya miqa hannu ya ciro lilitar don ya cire kuxin dake ciki, har da qullin magani a xaure.
“TAFXIJAM! Har da magani ta baki ki rinqa saka min?”
Ya zuba mata ido yana kallon ta.
“To bari Kawu Gixe zan kai wa in yi mishi bayanin komai don ya ga irin abin da aka shirya min”.
Jin ya ce, “Zai kai wa Kawu Gixe maganar yasa Saddiqa buxe baki ta ce mishi, “Ba Gwaggona ta bani magani ba Abu ce ta bani”.
Ya ce, “A’a, babu ruwan Abu, ita za ta yarda a qwareni ne? Kuma in ma ita ta bakin na yarda ni gara min magani da a baki kuxin motar da za ki gudu ki bar gidana ba tare da izini ba, ko wannan xan fitan da kika yi kin san iyakacin mutanen da kika tayarwa da hankali? Ba gara a tara miki magunguna ba, za ki ba masu mota magani ne su xauke ki a motar haya?”
“Is any one at home?”
Wannan kalmar da Mus’ab ya jiwo ita ta katse shi, a lokaci guda kuma ta jefa shi cikin fargaba da faxuwar gaba mai tsanani saboda fahimtar muryar da ta yi maganar.
Jennifer ce, to me ya kawo ta? Ya fito falon da nufin fita waje inda take, sai kawai ya ganta cikin falon zaune kan kujera riqe da karan sigarinta a hannu tana zuqa, ga kuma kwalbar giyarta a gabanta.
Mamaki ya kama shi, ya ce, “Ya ya haka Jennifer? Ya ya za ki shigowa matata wuri ba tare da kin jira ta baki izinin yin hakan ba?”
Ta kalle shi a lalace kafin ta tambaye shi cewa, “Ina ne wurin nata?”
“Kar mu yi haka dake Jennifer, kashe sigarin muje can wurina sai in ji abin da ya kawo ki, mai nan xin ba ta son warin sigari”.
Ta yi dariya ta ce, “Ba zama da kai ta zo yi ba kenan, any way wannan ku ya shafa, ina fata ba kirana ka yi don ka gaya min abin da matarka take so da wanda ba ta so ba?”
“Ni na kiraki?”
Ya yi tambayar a yanayin dake bayyanar da rashin jin daxin shi, don bai son fitina da ita a lokacin.
“In baka kirani ba me zai kawo ni?”
Ta ja tsaki tare da tofar da yawu tuf! Nuna alamar tir bai isa ba. Hakan da ta yi ya qara fusata shi.
Ya ce, “To na ji na kira ki kin zo, na ji kuma bana son ganinki don haka tashi ki fita”.
Ta ce, “Ai kuma baka isa ba tunda ka kirani sai na huta, sai na shanye barasata”.
Ya yi maza ya ce, “Ba a nan ba”.
Ba ta saurare shi ba ta jawo ledar da kwalbar ke ciki za ta buxe.
“Ba a nan ba Jennifer, kar ki neme ni da magana”.
Ya yi maza ya nufo ta don ganin ba ta fasa ba, nufin shi ya hana ta yin abin da za ta yin ta hanyar fitar da ita daga falon, ta yi zumbur ta miqe, yana isowa gareta ta yi maza ta wanke mishi fuska da wani irin lafiyayyen mari mai qarfi tau!
Ya ja ya tsaya ya zuba mata ido yana kallon ta zuciyarshi cike da mamaki.
“Marina kika yi Jennifer?”
Ta ce, “An mara, kai da kake marin mutane fa?”
Ya ce, “Ai kuwa kin sayawa kanki wahala, don kuwa zan tabbatar da wannan hannun naki ya daxe baki more shi ba”.
Yana rufe baki ya cafke hannun da ta yi marin da shi, yana cafkewa ta soma kururuwa saboda wahala.
“Ka yi haquri Mus’ab”.
Ya ce, “Haba, ai gara kar ki ba da haquri Jennifer, ai kin daxe kina burin marina na kuma daxe ina yi miki kashedin hakan, don haka tunda baki ji ba nima bari in yi abin da na yi alqawari”.
“Na tuba Mus’ab”.
“A’a, ai gara kar ki tuba, in kika yi haka ai baki zama cikakkiyar ‘yar iska ba”.
Saddiqa ta gaji da leqen abin da ke faruwa ta koma gadonta ta hau ta zauna cikin rawar jiki da tsananin tsorata da abin da ke shirin faruwa da hannun Jennifer.
Ban da duk wani mugun halinshi da Gwaggo ta sani bai da tausayi ko na anini. Ta faxi hakan cikin zuciyarta.
A waje Mus’ab ya tari mai tasi ya jefa Jennifer a ciki ya miqawa mai tasin jakarta a hannunshi, ya ce, “Ku tafi ta gaya maka inda za ka kaita, in kun je ka xebi ladan aikin ka a ciki”.
Ya juya ya koma cikin gidanshi inda ya bar Saddiqa.
“Kukan me kike yi Aisha?”
Ya miqa hannu zai tava ta, ta yi maza ta maqure a jikin bango.
“Kar ka tava ni”.
Ta yi mishi kashedi.
“Bana son ganinka kusa dani tsoro kake bani, duk abin da Gwaggo ta gaya min game da kai haka abin yake, sa’a ma ka ci ba ta san rashin tausayinka ba da ta qara tsanarka.
Na sha jin tana cewa, halinka guda xaya da ta sani shine kai xin mai tausayi ne, ba ta sani ba shima tausayin ka daina shi. Abin da ya fi komai bani mamaki cikin lamarin shine, wai Gwaggo ce ta haifeka”.
Mus’ab ya miqe tsaye ya nufi toilet xin dake xakin ya barta tana kuka. Ruwan wanka ya haxa mata ya fito ya kalle ta a nutse qwarai ya ce mata.
“Shiga ki yi wanka tunda kin ce bakya so in rinqa tava ki zan kiyaye al’amarinki qwarai matuqa kika kiyaye nawa, ni wani irin mutum ne da na fi so inda hali in baiwa kowa haqqinshi, ina girmama mace, in kuma ji tausayinta har in yi mata adalci.
Amma kuma bana iya yiwa wacce ba ta san darajarta kanta ba, ko kuma wacce ta nemi shige iyaka”.
Ya juya zai fita tare da faxin, “Amma kin san in har na je na dawo baki yi ba zan yi miki”.
Ta yunqura ta tashi ta shiga toilet xin da nufin yin wankan, shi kuma ya fita waje ya kira qarti da za su tsabtace falon Saddiqa daga qazantar da ya samu na fitsarin da Jennifer ta yi ta sakewa a dalilin wahala da kuma barasar da ta zube.
Saddiqa tana zaune kan kujerar gaban madubi tamkar mai shirin yin kwalliya, sai dai zuciyarta kawai take sauraro. Ko me yasa Kawu Gixe xaukan aurenta ya baiwa Yaya Mus’ab? Anya kuwa Kawu Gixe yana sonta ma kuwa?
Ta zurfafa cikin tunani. Wani abin da Kawu Gixe ya tava yi mata da zai sa ta yarda eh, lallai yana yi mata so irin wanda uba ke yiwa ‘yar da ya haifa.
Shigowar da Mus’ab ya yi ya katse ta. Ya zauna a gefen gadon cikin wata lallausan jallabiya, ga qamshinshi mai daxi yana tashi, da alama shima wankan ya yi.
Tiren abinci da ‘ya’yan itace ya ajiye a gabanta.
“Fara da wannan kafin ki ci kazar”.
Yana maganar ba tare da ya kalle ta ba, bai kuma fasa yanka mata kazar ba duk da zafinta, haka nan yanayin fuskarshi bai sauya ba da alamar har lokacin ranshi a vace yake.
“Kar ki sake yunqurin gudu ki ce za ki tafi gida ke kaxai, ni kaina zan iya mayar dake gida gaban Gwaggonki tunda har yanzu kuna ganin bani aurenki da Kawu Gixe ya yi kuskure ne. To na ji na yarda, tunda ita Gwaggon nine wanda ba ta so, to na ji na yarda, tunda abin haka ne na ji na yarda zan kai ki gaban Gwaggon in baku zavi…..”
Kan ya qarasa ta katse shi ta hanyar hankaxa tiren abincin ya kife a qasa, ta yi maza ta miqe tsaye cikin kuka. Shima ya miqe yana kallon ta tare da mamakin abin da ya yi wanda ya jawo hakan.
“Bana so, ina jin kunyarka ina kuma girmamaka, ka barni in ci gaba da hakan. Muna magana da kai kana sa sunan Gwaggo a ciki, ita ce za ka kai ni gabanta ka bamu zavin auren ka? Ka bani ni da kai mana, ko kuma don ka ga an baka ni ba da yardar ta ba sai kuma ya zama…..”
Ta qara tsananta kukan da take yi.
“Ki yi haquri Aisha, ki yi haquri na yi kuskure da na ambaci sunanta, to amma me yasa da za a kawo ki ba za ta yi miki irin nasihar da take yiwa sauran ba? Sai ta ce in kinga ba daidai ba ki gudu, ba za ta qarfafeki a kan ki tsaya ki taimakeni in gyara halina da take ganin a kanshi ne take qina ba?”
Saddiqa ta galla mishi harara karo na farko da hakan ya tava faruwa a tsakaninsu.
“Nice ma zan taimakeka ka gyara halayenka? Lallai kam”.
Ya xan yi murmushi kaxan karo na farko shima tun bayan da ya neme ta ya rasa a gidan.
“To shi kenan na ji in ba za ki taimake ni gyara halina ba, ai kuma bai kamata ki yi dalilin da mu’amala tsakanina da Gwaggon taki zai qara lalacewa ba ko?
Kin tava tunanin inda kin yi nasarar isa gabanta ke kaxai da sunan gudu abin da zai biyo bayan hakan tsakanina da ita? Ke bakya sha’awar kyakkyawar mu’amala ta shiga tsakanina da ita? Ai har da kwaxayin hakan ya qara sani dagewa a kan auren ki Aisha, don na san tana sonki za ta yi mu’amala mai qarfi da gidana, ko ba don ni ba saboda ke.
Kina tsammanin ina jin daxin abin da ke tsakanina da ita ne? Ita ta haife ni fa, nine namiji guda xaya da take da shi, don me ba za ki gyara tsakanina da ita ba sai ki nemi ya qara lalacewa?”
Jikin Saddiqa ya xan yi sanyi, lura da hakan ya sa shi qara yi mata magana.
“Kawu Gixe da ya bani ke ba kuskure ya yi ba Aisha, ya san ina sonki ne, ya san ba zan iya zaluntarki ba, ya san zan yi miki adalci, ya san babu wani wanda ya fini cancantar aurenki ko da kuwa a ya ya halayen nawa suke, domin nine nake zaune ni da Innata mu biyu sai aka same ki kika shigo cikinmu.
Muna ta murna muna ta ina muka saka dake, muna ta sonki muna renonki cikin kulawa da tausayawa, duk da yawan kukan ki da yawan rikicinki, raina kan vaci in na ga yanda Inna ke wuni hidima da xawainiya, da daddare kuma ki hanata barci da yawan kukan ki, ta yi ta fama dake, ta yi jijjiga tana girgiza ki har sai asuba ta yi kafin ki yi barci, lokacin nan kuma ba lokacin barci bane a wurinta, za ta kwantar dake ne kawai ta miqe ta shiga wasu sabgogin.
Ran nan raina ya vaci haushinki ya yi matuqar kamani na fito na zo na sameta na ce Mama bani fitinanniyar yarinyar nan ki gani ki samu ki kwanta kema ki huta kamar kowa, zan je da ita xakina in rarrasheta, in kuma kin fi so a goyata, to goya min ita a bayana ki xaure min ita ta yanda zanin ba zai kwance ba.
Sai na ga ta yi murmushi ta ce min, kar ka ji haushinta komai ta yi kar ta vata maka rai yarinya ce ba ta da baki, bamu sani ba ko wani abu ke damun ta.
Kalamanta kan sanyani jin tausayinki, in zauna in yi ta taya ta rarrashinki ina tausayi, ina ganin ba laifinki bane damuwa ce tasa kika hana min Innata bacci.
Gari in ya waye in yi maza in yi mata ayykan da zan iya taimakonta dasu, wanki, wanke-wanke, shara, xiban ruwa duk babu abin da bana yi kafin in tafi makaranta, don ta xan samu lokacin kwantawa ta huta da rana, dana……”
Qwan! Qwan! Qwan! Xim! Xim! Xim! Xum! Xum! Xum!!!
Bugun qofa ake yi babu qaqqautawa. Mus’ab da Saddiqa suka zubawa juna ido saboda jin yanda ake bugun qofar. Gaba xaya suka kalli agogon dake xakin, tara saura kwata ne na dare.
“Iko sai Ubangiji, ko waye kuma yanzu?”
Mus’ab ya kalle ta jikinshi a sanyaye.
“Ki yi haquri Aisha bana nufin vata miki rai, ban kuma karvi aurenki don in saki ki yi baqin ciki ba”.
Ya miqe ya nufi inda ake bugun qofar, a zuciyarshi yana tunanin to ko dai Jennifer ce ta turo mishi ‘yan iska don su xaukar mata fansa kan abin da ya yi mata? Ubangiji dai yasa ba wata fitinar ce ta sake biyo shi har gida ba.
Mus’ab ya isa qofar ya xan saurara kaxan don tantance muryar dake magana.
“Anya Baba basu tashi daga gidan nan ba kuwa?”
“Kai tafi can kai ma sakarai dukan qofar ne baka iya ba, kana yi kamar kana tsoro”
“Zan ji tsoro kai Baba in na tarwatsa gilasan gidan nan ya ya zan yi? Masu tsada ne fa”.
Ta ce, “A hau! Babu abin da za ayi maka ai jikokina ne a gidan suna nan a ciki babu wani tashin da suka yi, sun hangame bakuna ne kawai sun kwanta suna bacci, ana bacci kamar na mutuwa to ba a tunanin komai balle a rage dare a xan yi nafilfili”.
“Abu ce”.
Zuciyar Mus’ab ta gaya mishi.
“Me ya sake dawo da Abu yanzu?”
Ya tambayi kanshi cikin tsananin faxuwar gaba.
“Yanzu haka Inna ce ta turo ta”.
Ya juya ya koma wurin Saddiqa ba tare da ya buxe qofar ba, duk da su ma basu daina dukan da suke yi mata ba.
“Aisha, Abu ce ta zo”.
“Abu?”
Ta yi tambayar a yanayi na tsananin mamaki tare da dirowa daga gadonta.
Mus’ab ya juya don komawa ya buxe musu qofar ta yi maza ta ce mishi, “Ka shigar da ita wurinka kar ka kawo ta nan”.
Ya ce mata, “To”.
Mus’ab ya isa jikin qofar yasa hannu yana buxewa tare da tambayar, “Waxanne baqi ne haka basa sallama sai dukan qofa?”
“Kai tafi can ka bani wuri, a ga qato kamar ka a ce wai shi ake bugawa qofa haka saboda yana bacci bai farka ba, ai kuwa dai ya ji kunya”.
Ya yi murmushi ya ce, “Abu kenan, to ba a gidana nake ba?”
Ya shigar dasu qayataccen falonshi daga ita har direban.
“Sannunku da zuwa”.
Ya sake yi musu gaisuwar bayan sun samu wuri sun zauna, shima ya koma wata kujerar ya zauna.
Saddiqa ta shigo falon cikin kwalliyar burgewa, ga shi ta yane jikinta da gyale sai qamshi take yi.
“Wa ya vata miki rai a hanya Abu na ji kamar kina faxa?”
Abu ta harareta ta ce, “Yanzu idonku biyu ake ta buga qofar nan baku fito kun buxe ba?”
Ta yi murmushi ta ce, “Hirar amarci fa muke yi”.
Ta ajiye tiren da ta shigo da shi a gaban Abu ta koma ta sake shiryowa direban nashi ta ajiye mishi, bayan ta gaishe shi ta koma kusa da Mus’ab ta zauna a gefen kujerarshi.
Mus’ab ya sallami direban da ya kawo Abu tare da alheri mai yawa, ya dawo ya sake zama kusa da Abun yana taya ta matsa qafafuwanta da take yi.
“Ai kin wahala da yawa ne Abu, kwanan nan kika tafi kin sake dawowa, wannan tafiyar ai ta yiwa jikinki tsanani. In ce ko dai lafiya?”
Abu ta ce, “Ina fa lafiya, fitinanniyar uwarku mana ta yi sanadin tasowata wai ita za ta zo ta ga halin da na baro mata ‘yarta a ciki saboda hankalinta bai kwanta. Ko da yake dai nima nawa hankalin ba kwanciyar ya yi ba, saboda yanayin da na barku a ciki”.
Ta basu labarin al’amuran duka. Saddiqa ta miqe ta nufi kicin tana cewa, “A’a, Abu ni bana son haka, in za ku yi maganarku ku yi amma ban da Gwaggona a ciki, Gwaggo ce za ta turoki ki zo ki ganan mata halin da nake ciki hankalinta bai kwanta ba, wa take yiwa haka a cikin surukanta? In kin ji marmarin ganina kin zo kawai ki ce kin ji marmarin ganina, amma ba ki ce Gwaggona ta turo ki ba”.
“Ka ji ta ko? Ka ji min ja’irar yarinya ko? Wani marmarin ganinki za a yi? Na sani da uwar taku ta ce za ta zo in barta ta zo da kanta tunda baki ga abin arzikin da na yi ba”.
“Qyale ta Abu mu yi zancenmu”.
“Kun zauna lafiya ne?”
Ta yi tambayar cikin raxa wai kar Saddiqa ta ji.
Ya xan kalle ta a yanayi na murmushi ya ce, “Me kika gani yasa kika tambaya?”
Kan ta sake gaya mishi abin da ta ganin Saddiqa ta fito riqe da kwanon farfesu ta ajiye mata, ta koma kusa da Mus’ab ta zauna.
“To kin ce Gwaggo ce ta turoki ki yi bincike in muna zaune lafiya mene ne? Ina ce dama don kin san zamu zauna lafiyan ne yasa kika gudu kika barni?”
Mus’ab ya ce, “Rabu da ita Abu ba ta so ne in gaya miki gaskiya, sai dai abin da nake so ki sani shine, ko na zauna lafiya da Aisha ko wane irin hali nake ciki ba zan sake daxewa ban zo Misau ba, ba zan barki ki ji marmarin ganina baki ganni ba Abu, saboda na san kina sona”.
Ta ji daxin maganar tashi, nan take ta yi ta sa mishi albarka.
Sun yi hira gaba xayansu har suka kai lokacin da Aisha ta ce mata dare ya yi Abu muje in rakaki ki yi wanka ki sha magani ki kwanta don ki huta gajiyarki”.
Ta ce mata, “To”.
Mus’ab yana zaune a falon cikin tunani za ta dawo ne ko za ta zauna a can, sai gata ta shigo. Kwanukan dake wurin ta kwashe za ta fita dasu.
“Ke nake jira fa Aisha”.
Ba ta yi magana ba ta tafi ta dawo.
“To zo daga nan mana ya ya za ki zauna kuma a can?”
Ta ce, “A’a, nan xin ma ya yi”.
Ya qara gane don Abu ta yi abubuwan da ta yin duka.
“Ina ce nan za ki zo mu kwana?”
Cikin nutsuwa ta kalle shi ta ce, “Saboda me?”
“Saboda shine abin da ya dace ki yi, kema kin sani ko ba a gaya miki ba abubuwan da kike yi min sun yi yawa, bai dace a ce kina yiwa mijinki haka ba”.
Ba ta kalle shi ba ta ce, “Ba ka ce za ka kaini gaban Gwaggona ka bamu zavi ba?”
Ya yi murmushi ya ce, “Wannan maganar ba ta wuce ba”.
Ya taso daga inda yake zaune ya zo wurinta yasa hannu ya sureta, ya ce, “Tunda kin riga kin kawo kanki falon bari kawai in qarasa dake cikin xakin kawai”.
Ya zaunar da ita a kan gadon ya koma gefe ya zauna.
“Ina ce wannan maganar mun gama ta, kuma in bakya so in rinqa sa sunanta a cikin maganarmu ke me yasa kike yi min abin da kika ga dama? Yanzu kina nufin inda kin san zan kai qararki wurinta ta yi hukunci a tsakaninmu za ki rinqa
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 24