Ta ce, “A’a, bani ba ce”.
Ta yi maza ta miqe ta nufi matattala inda za ta hango mijin nata a falo, “Na ce ba”. Ya ce, “Na’am”. Ta ce, “Ba wannan ce yarinyar nan ba?” Ya yi maza ya ce, “A’a, ba ita ba ce, wannan ai qanwarshi ce”. Ta juyo tana faxin “Ai ashe kuwa ba ke ba ce”.
Sai da suka yi sallar la’asar sannan suka yi sallama, Ishak ya kawo turamen holland guda biyu tare da wani rantsattsen leshi ya bai wa Saddiqa, ita ma Abu ya ba ta turame biyu tare da dubu biyar wai ta ci goro kafin ya zo. Suka yi godiya suka tafi.
Mus’ab yana barin gidan bai zarce ko’ina ba sai shagon Alhaji Ibrahim Umar a cikin kasuwar Sabon Garin Kano.
Saddiqa tana zaune kan kujerar da aka ba ta, mamaki take yi na yanda aka maqare shagon da zinare Gold qirar daban-daban, cikin fara’a da iya karvar baqi Alhaji Ibrahim ya ce, “Barka da zuwa ranki ya daxe, hala amare ne suka zo ziyara?”
Mus’ab ya ce, “Babbar ta fara zaven abin da take so”.
Alhaji Ibrahim ya bi Abu yana nuna mata don ya tayata zave, shi kuma ya yi amfani da hakan ya matsa kusa da Saddiqa ya ce, “Aisha misali a ce kece budurwar da nake shirin ki rakani wurinta taxi na kawo ki nan me da me za ki zava?”
Ta yi shiru cikin tunanin maganar tashi, sai ya yi maza ya ce, “Taimakeni ki tashi ki duba mata sarqoqi don ina ganin kamar ra’ayinku kusan xaya ne”.
Ta yi murmushi ta ce, “To”. Ta miqe ta soma duba sarqoqin dake rataye cikin kabet-kabet, ta nuna wasu guda biyu aka ciro su aka xora kan sikeli ana gwada nauyi.
Alhaji Ibrahim da kanshi ya jinjina zaven da ta yi, ya yiwa Mus’ab kuxin. Ya kalli Saddiqa ya ce, “In an haxa da abin hannu bai fi ba?”
Ta ce, “Ya fi”. Ya ce, “To zavo kamar na hannunki kala biyu”. Ta ce, “To”.
Nan ma ta zuba ido ta zavo abin da take ganin in ita ce abin da za ta xaukawa kanta kenan. Ya biya suka fito suka shiga mota suka xauki hanyar komawa Misau.
Abu tana kwance a baya barcinta take yi, ita kuwa tana jingine sai dai can cikin zuciyarta Yaya Mus’ab da budurwarshi take tunawa, irin sayayyar da ya yi mata bayan ko fara zuwa wurinta bai yi ba. Wannan ranar da ya fara zuwa ko me zai yi oho. Ta yi maza ta kawar da tunanin ta hanyar tunawa kanta shi xin mai alheri ne ga kowa.
Shi kuwa Mus’ab yana tuqi ne tare da tunanin abin da ke tsakanin shi da Saddiqa wanda ba ta ma sani ba, sai dai zuwa yanzu kam yana ganin Innar shi ta soma sansano wani abu.
Sai da suka isa qofar gidan Abu ya sauke ta ya rakata ta shiga ciki, sannan ya dawo da nufin kai Saddiqa gida.
Saddiqa ta buxe qofar motar ta fita tare da faxin “Yaya ka huta gajiya”. Ya ce, “Amin, to zo mana”. Ta juyo tana kallon shi.
“Ai kin yi mantuwa”.
Ya xauko ledar dake xauke da sarqoqin ya miqa mata. Ta yi saroro tana kallon shi.
“Karvi mana Aisha”.
Ta ce, “A’a, ai budurwarka ka sayawa”.
Ya zuba mata ido ya ce, “Kin tava ganinta ne? To karvi mana”. Ta sake cewa, “A’a”. Da sauri ta juya ta nufi gida za ta tafi ta barshi dasu.
Ya yi maza ya tare ta a zauren gidan ya ce, “Haba Aisha, ni dake ai abotarmu ta hana mu yiwa juna haka”.
Ta maqure kanta jikin bango, shima ya mamayeta ta ko’ina ta zama ba ta shaqan komai sai qamshin jikinshi.
“In kika qi karva wa zan kai wa? Ki karva ki yi kwalliya in na gani a jikinki zan ji daxi, bani da wata budurwa tunda na kasa yin jarumtakar gayawa wacce nake so xin. Karvi kawai ki yi amfani dasu”.
“Ni da Gwaggo dukanmu bama son kyaututtukan da kake yi min, in jita wai akwai abin da zai biyo baya, kuma in yi hankali da kai”.
Ta soma kuka ya rasa yanda zai yi da ita, shi ba abin ya sake ficewa da ita zuwa wani wurin ba, ya san Innar tana jin isowarsu.
“Ni bani da abin da zan ce miki a yanzu illa in roqe ki duk abin da za ki ji a kaina ki taimake ni ki yi min adalci, ki bani damar da zan yi magana dake kullum ina gaya miki kina ganin kamar wasa nake yi bani da wani gata, in har ba ke ce kika tsaya min ba to zan shiga matsalar da ban san qarshenta ba.
Na dogara dake ne saboda qarfin zumuncin dake tsakaninmu da mutumta juna da muke yi, ni dai na san ko baki yi hankali dani ba, ba zan iya cutar dake ba, ke ce baki san yanda kike ba a wurina, nine nake rayuwa ni kaxai a wurin Innata sai ga shi kin shigo cikinmu, ina murnar nima na samu qanwa wacce zan yi ta tarairaya, wacce zan yi ta so ina tausayawa kamar yanda Inna ta yi min, sai kuma ta tafi ta barmu, sai kuma in rasa wacce zan cutar sai ke.
Ke kaxai fa ta bari a duniya sai in cutar da ke? Ai ni tunanina da burina da sha’awata bai wuce mu dunqule ni dake mu zama abu xaya ba, da tana nan a raye kuma ina tabbatar miki da abin da za ta yi mana kenan”.
Saddiqa ta xago ta kalle shi cikin kuka mai yawa, ta ce mishi, “Ba na gane abin da kake nufi da irin maganganun da kake yi min ban san me kake nufi ba”.
Ya ce, “To ki yi huquri ki karvi waxannan sarqoqin tunda na riga na saya sai ki yi min ado da guda xayan zan ji daxi sosai, gobe ki zo gidana don mu warware al’amuran dake tsakanin mu”.
Ta ce mishi, “Inna ta yi min kashedin zuwa gidanka, sai dai ko gidan Abu”.
Ya zuba mata ido yana kallon ta ya ce, “Haka ne?”
Ta gyaxa kai nuna alamar eh. Ya ce, “To kin gani Aisha karvi sarqoqin ki kai mata, gaya mata kawai ni na sai miki ita ta san abin da nake nufi”.
Tana sa hannu ta karva ya yi maza ya fice daga zauren don ya ji motsin fitowar Innarshi tsakar gidan.
Saddiqa na tsaye a zauren ta shigo riqe da tochlight xinta tana haskata.
“Me ya faru Saddiqa? Kukan me kike yi? Ya tava ki ko? Ya yi miki wani abu ne?”
Ta shiga haskata ta ko’ina, ta ce, “Nifa dama can ban yarda da kusantar juna da kuke yi ba”.
Cikin kuka Saddiqa ta ce mata, “Haba Gwaggo, Yaya Mus’ab ba xan’uwana bane?”
Maganar ta zo mata a bazata, ta tsaya tana kallon Saddiqa, matsanancin kukan da take yi ya qara mata tausayinta. Cikin zuciyarta ta ce, “Uh-uhum! Shi kenan wannan yaron ya gama da Saddiqa, don kuwa matsanancin kukan da ta yi jiya da wannan da take yi a yau ba komai bane illa SO, wanda ya san shi ya san abin da yake sanya zubar hawaye”.
Tausayin ta ya sake kamata da ta qara taabbatarwa kanta da cewar, “Wanda bai kamata a so bane Saddiqa ta kamu da sonshi”. Ta miqa hannu ta riqo nata ta jata suka shiga gida tana rarrashinta.
Shi kuwa Mus’ab yana barin gidan bai nufi gidanshi ba wurin Abu ya koma, har ta kwanta ta ji shigar shi cikin xakin nata, ta fito tana haskashi da fitilarta.
“Lafiya? Me ya faru ka dawo cikin wannan tsohon daren?”
“Abu ki ji Inna wai Aisha ta yi hankali dani”.
“Hankali da kai kamar ya ya?”
Ya ce, “To ina na sani Abu? Tana son rabani da Aisha, za ta rabani da ita”. Cikin matsanancin yanayi yake maganar. Ya ba ta labarin yanda suka yi da Saddiqa duka.
Ta ce, “To bari kawai tunda abin nata ya zama haka tun ba a ce komai ba za ta fara tsoratar da yarinyar ba za ta tsame hannunta cikin lamarin ta barta ta yiwa kanta zavi ba, to za ni gidan nasu zan gaya mata komai don ta san gaske kake yi”.
Ya ce, “Yauwa Abu, nima na c Aishan ta zo nan ta same ni ta kuma yarda”.
Ta ce, “To Ubangiji ya zava mana mafi alheri”.
Ya ce, “Ameen Abu”.
Washegari da sassafe Abu tana idar da sallar asuba ko laziminta ba ta tsaya ta yi ba ta lakato man shafawarta ta muttsuka a hannayenta da qafafuwan ta, ta miqe ta xauki carbinta da mayafinta ta yafa, ta sagala murfin qofar xakinta ta nufi gidan Malam Abdullahi, a zuciyarta tana fatan ta same shi suyi wacce za suyi don ta riga ta yi nufin taimakon Mus’ab a kan auren Saddiqa da ya yi nufin yi.
A tsakar gida ta samu Saddiqan tana yawo cikin rigar barcinta, idanuwanta a kumbure alamar daren jiya kukan da ta yi ba kaxan bane, ta yi kamar ba ta ganta ba ta nufi xakin ‘yarta tana sallama.
Da sauri Innar ta leqo ta ce, “Inna lafiya kika fito da sassafen nan?”
Ta ce, “Lafiya qalau, wurinki na zo ke da mijinki”.
Ta ce, “Ayya! Ai kuma ya fita don an sanar da rasuwa a cikin gari”.
Ta ce, “Wayyo babba ne ko yaro?”
Ta ce, “A’a, ya xan manyanta”.
Abu ta ce, “To, Allah ya ji qan musulmi”. Ta shiga ta zana suna gaisawa.
Saddiqa ta biyota da abin karyawa.
“In ce ko dai lafiya kike son ganin Malam Inna?”
Ta sake cewa “Qalau, dama qarfin zuwan nawa naki ne, don na san komai a gidinki yake Malam kam ai ba zai hana Mus’abu aure ba”.
Nan take ta shiga yi mata bayanin saqon nashi. Sai da ta ji ta yi shiru ta tabbatar ta kai qarshe sai ta xan yi murmushi.
“Uhm! Ai dama na san za a rina wai an saci zanin mahaukaciya, kyautar rashin hankali da yake yiwa Saddiqa shi ya qara fahimtar dani akwai yaudara a cikin lamarinshi, ko kin san tun yaushe rabon Sadisu da ya ji daxin yarinyar nan ko maganarshi ba ta son ji? To haka ake yi ba zai yi neman shi ba kawai sai ya rabata da wanda ya same ta da shi?
Sannan sau nawa ya turaki wajen nemar mishi aure Inna? Ya fito ake cewa sai ya qi zuwa ya bar yaran suna ta shirmen sonshi, haka nima yake so ya yi min?”
Abu ta yi nufin yi mata dabara ta ce, “Yauwa, to tunda an san halinshi ba sai kawai in ce mishi ya fito ba? Kinga ai sai ya yi tafiyarshi kowa ya huta”.
Inna ta ce, “A’a, a kan wannan kam kar a ce mishi ya fito tunda ko ya fiton ba bashi ita zan yi ba. Saddiqa marainiya ce, Innar kar ki shiga cikin maganar yaron nan har ya samu damar da zai cutar da ita.
Ba mijinta bane, ni dake mun san komai in har qa’idar bayar da aurenmu za a bi ai ba tarin dukiya muke dubawa ba cancanta muke bi da asali da mutunci, da sanin ya kamata. Don haka ayi mishi kashedi kawai Inna ya fita hanyarta, in ba haka ba kuma zai gamu da vacin rai mai yawa, sai in yi mishi…….”
Abu ta yi maza ta soma salati tana tafa hannu, ta ce, “Ki yi mishi me? Lallai kuwa da kin yi hauka. A kan ya ce yana son Saddiqa? Ki ce min kin yi hauka ban sani ba. To yi maza ki yi mishi baki a gabana don nima in zama shaida in qara sanin kema kin haihu.
Zancen banza zancen wofi, xanki guda xaya kin yi qememe kin qi yarda ki shirya da shi, kin takura kanki kin hana kanki sakat, kullum tsakanin ki da shi muzurai da xaure ido. Yana iyakacin bakin qoqarinshi a kanki, yana yi yana iya yinshi kina shirmenki. Sakarwa kawai ki ce min kina shirin tonawa kanki asiri don shine ke”.
Ta miqe ta fita ta bar Inna tana kuka saboda ganin vacin ran mahaifiyarta.
“Zan dawo in samu Malam Abdullahi in ji ko shima bakinku xaya, Saddiqan me kuma? Shima Mus’abun maganinshi kenan ja’iri mai taurin kan tsiya, ai babu abin da ban gaya mishi ba”.
Saddiqa tana xakinta adon lalle take yiwa hannayenta ta hango ficewar Abu cikin sauri, ta tabbatarwa kanta akwai wani abin da ke faruwa. Sai dai ba ta san mene ne ba, koma mene ne kuma ba ta jin daxin yanda Gwaggonta ke yiwa Yaya Mus’ab, kullum mamakinta take ji yanda ta mallaki xa jan gwarzo irin Mus’ab amma lamarinshi baya gabanta, ko tausayi kuma ba ya ba ta, kullum a cikin qoqarin kyautata mata yake, a cikin yi mata alheri yake, kusan kullum sai an zowa mahaifiyarshi godiya kan wani alherin da ya yiwa wasu amma ita ko a jikinta.
Mus’ab yana zane a xakin Abu jiran dawowarta yake yi, yana kuma sauraron zuwan Saddiqa cikin zullumu da tunanin abin da ake ciki.
Abu ta yi sallama ta shiga, ya bita da kallo gabanshi ya faxi saboda ganin yanda fuskarta ke xaure.
“Ya ya dai Abu? Ta yarda kuwa?”
Ta balbale shi da faxa ta ce, “Ta yarda dame? Tun farko mene ne ban gaya maka ba? Ban ce maka ka fita hanyar yarinyar nan ba? Ba dai kaima kafiyar tsiya ce da kai ba, in ka so abu kamar xa ya so waje. To ba ta yarda ba sai ka san yanda za ka yi”.
Ya sunkuyar da kanshi qasa ya yi shiru cikin nazarin abin yi, zuwa can ya xago ya kalli agogon hannunshi ya ce, “Goma ta wuce”. Gabanshi ya sake faxuwa.
“Kar dai ita ma ba za ta zo ba?”
Ya yi maza ya xauko wayarshi ya dana lambobinta ya ji ta xauka.
“Za ki zo kuwa Aisha?”
Muryarta tana rawa ta ce, “Gwaggo ta hanani fita, ta kuma ce wai in ka yi waya in gaya maka tana son ganinka”.
Gabanshi ya ba da ras! Ya kalli Abu ya ce mata, “Inna tana son ganina bari in je in ji”. Ta ce mishi, “To”.
Mus’ab yana zaune a gaban mahaifiyarshi cikin ladabi yana sauraron abin da take gaya mishi.
“Na ji saqonka wurin Inna, shine na ce bari in kira ka muyi magana ni da kai, abin a ce kai ne waliyinta wanda amanar al’amuranta suke hannunka, za ka bai wa mai hali irin naka ita?”
Ta zuba mishi ido tana kallon shi. Shi kuwa yana kallon qasa cikin ladabi ya ce, “Ina sonta Inna ba zan iya kwatanta muku yanda nake jinta ba in ban da hakan da ban zo gabanku neman auren nata ba, ina cikin wani irin hali ne”.
Ta katse shi ta hanyar faxin “Ai ba dogon bayani na nema ba tambaya kawai na yi maka baka bani amsa ba, cewa na yi in kai ne waliyinta za ka bai wa mai hali irin naka ita? Eh, kawai nake son ji ko kuma a’a”.
Ya sunkuyar da kanshi qasa ya ce, “A’a”. ta ce, “To shi kenan magana ta qare tashi ka tafi”.
Ya ce, “Ki yi haquri ki saurareni Inna, ni da mai hali irin nawa ba xaya bane, in a kan maganar Aisha ne Inna zan riqe miki ita fiye da duk yanda ake zato, babu wani wanda za ki baiwa ita ya fini yi mata adalci ko ya fini ganin darajarta, don ni bayan son da nake yi mata ina kallon ta a matsayin wacce zan riqe in yiwa gata don in sakawa mahaifiyarta alherinta a gare ni.
A wurinta na soma xanxanar ‘yanci, ba ta yi yawan rai ba, ba ta mori komai a cikin wahalar da ta yi a kaaina ba sai dai kullum ina yi mata addu’a. Ki taimakeni kar ki hanani ‘yarta, da tana raye na san za ta bani ita ba tare da ta tsaya kallon munin halina ba, na yarda ki bani ita bisa sharuxa da shaidun da za ki saka, zan cika duk wani alqawari da zan xauka a gabansu”.
Ta kalle shi a lalace ta ce, “Saboda yanzu kana cikin natsuwarka ne yasa kake tuna alherin mahaifiyar Saddiqa, haka nan yanzu ne za ka iya shaida alqawari da cikawa, amma in ka shawo barasa ta yi maka karo fa? Kana nufin zan yarda Saddiqa ta zama matar mashayi ko manemin mata? Yarinya ce da ba ta san komai ba sai ladabi da biyayya.
Me kake so in ce mata randa ta gane na san komai game da halayenka amma na xauke ta na baka don kawai ka yi min alqawarin da na san ba za ka cika ba, ba zan fifita sonka a kan nata ba, in na yi haka ban yi mata adalci ba, alhakin zumunci kuma ba zai barni ba, don haka fita hanyarta kawai don ba zan baka ita ba”.
A kixime ya ce, “A’a, Inna kar ki hanani ita, na rantse miki ina sonta, ki taimaki rayuwata ba zan iya haqura da aurenta ba”.
Ta ce, “Za ka yaudari kanka ne kawai in ka yi mata irin wannan son, don babu gami tsakaninka da ita, in dai ka kuma in alhakin wasu da suka rinqa binka kana wulaqantawa ne ya kama ka”.
Mus’ab yasa hankicif ya share gumin dake feso masa a goshi.
“Ki taimakeni Inna na tuba kar ki kamani da laifukan da na yi miki a baya ki hukuntani ta hanyar hanani samun matar da nake so”.
Ta ce, “Ba ni na hanaka ita ba Shari’a ce ta hanaka ita, da ta ce mazinaci matarshi mazinaciya, don haka zan qara yi maka kashedi ka fita harkar yarinyar nan kar ka yarda ka ce mata kana sonta, in kuwa ka yi hakan to ni kuwa zan rabaka da ita ta hanyar gaya mata halayenka, sigari, giya, neman mata, babu abin da zan rage a ciki don ta san ban cuceta ba”.
Tsawon lokaci suna zaune shiru, da qyar Mus’ab ya iya yunqurawa saboda sarawa da kanshi yake yi ya ce, “Inna ni zan koma”. Ta ce, “To, Ubangiji ya kiyaye”. Ya ce, “To, amin”.
Mus’ab yana fita gidanshi ya nufa, kai tsaye ya wuce xakin kwanciyarshi. Wunin ranar bai yarda ya ga kowa ba, babu abin da yake yi in ban da nazarin hanyoyin da zai bi.
Ya riga ya san Innarshi za ta raba shi da Saddiqa ta hanyar gaya mata halayenshi, to in har ta yi hakan wace hanya shi kuma zai bi don ya mallaketa?
Abu kuwa tana gidanta hankalinta yana wajen sauraron dawowar Mus’ab don ta ji bayanin da zai yi mata, shiru babu shi babu dalilinshi har yamma, har dare.
Abu ta tabbatar babu lafiya, domin qa’idarshi ne in dai yana garin to zai ci abincin dare a wurinta.
Gari yana wayewa ta yi sammakon tafiya gidanshi don ta ga halin da yake ciki. Muryarta da ya jiyo tana qwala sallama cikin falon ne ya yi dalilin fitowar shi sanye da doguwar jallabiya,
Ta zuba mishi ido tana nazarin canzawar da ya yi a ‘yan awowin da ba ta ganshi ba.
“Ba ka zo ka ci abincin dare ba lafiya?”
Ya ce, “Inna ce ta ce in fitar hanyar Aisha, Abu ya ya zan yi? Tana da haqqin in yi mata biyayya ita ce ta haifeni ko ba shi kenan ba”.
Abu ta zuba mishi ido tana nazarinshi.
“Amma ai kin san Aisha matata ce ko? Ko baki sani ba?”
Bai jira amsarta ba ya ci gaba da cewa, “To na rantse miki zan yi ta’adi, zan yi varna”.
Abu ta katse shi da cewa, “Kai Mus’ab hala maye kake yi na ga alamar baka cikin hankalainka, ina jin jiya kwana ka yi kana sha, wato ba za ka daina wannan halin naka da yake ja maka tsana a wurin su ba ko?”
Ya ce, “A’a, Abu so nake in gaya miki gaskiya cikin biyu ki zavi xaya, wanne ya fi?”
Ya tsareta da idanuwanshi da suka riga suka kaxa.
“Da in vatar da Sadisu da in sato Aisha in kawota gadona in voye ayi ta nemanta ba a gani ba wanne ya fi miki? Ki faxa”.
Ta yi tsaki cikin takaici ta juya za ta bar falon, ta ce, “In ka wattsake dagaa shirmen naka sai ka zo gida ka same ni”. Tana tafiya cikin ranta tana addu’ar Ubangiji ka shiryar da wannan yaro. Ta fita ta barshi a zaune.
Malam Abdullahi yana zaune kan tabarma a xakinshi shi kaxai, karatun Alkur’ani mai girma yake yi, matarshi ta yi sallama a bakin qofa har sau uku kafin ya dakatar da karatun ya amsa sallamar.
Ta shiga ta tsuguna a gefe ta ce, “Ina kwana Malam?”
Ya amsa. Suka gaisa sannan ta ce mishi, “Inna ce ta zo tana son ganinka”.
Ya ce, “To gani nan zuwa”.
Ya mai da Alkur’ani wurin zaman shi ya ajiye, sannan ya shiga falon matarshi inda ya san a nan take jiran nashi.
“Lafiya dai ko Inna?”
Ta ce, “Lafiya wurinka na zo kai da matarka kan maganar Mus’abu”.
Da sauri ya kira matar tashi, “Ke Habiba!” Ta amsa ta shigo ta ce, “Gani”. Ya ce, “To zauna mana”. Ya ba ta umarni. Don haka ta koma gefe ta zauna cikin sauraro.
Abu taa gyara zama ta ce, “Wurinka na zo Malam in ji wai da gaske kuke yi ne ba za ku ba Mus’abu yarinyar nan ba?”
Malam Abdullahi ya sunkuyar da kai qasa ya ce, “Inna da baku shiga maganar nan ba, ai kun san komai, wani abin ma ni kun fini sani. Ba muna son yin jayayya daku bane a kan maganar maraicin yarinyar muke dubawa, nutsuwarta da irin halayenta da irin xabi’unta, kun santa kun san Mus’ab.
Inna kun
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 6 Chapter of 24