Share this page
kowa na garin balle kuma ƴaƴan gidan marayu. Ba'a ɓata lokaci ba aka yi bikin su bayan wata ɗaya dan haka ƙa'idar su take basa sa lokacin aure da tsawo, soyayya ce sosai tsakanin Safwan da Asma'u dan ba wanda ke tare dasu da besan wannan ba. Basu taɓa haihuwa ba har suka shekara biyar, zuwa lokacin duk hanaklin su a tashe yake sedai shi Safwan yana ƙoƙarin dannewa dan lallashin matar sa, asibitocin da suka je ba zasu ƙirgu ba sedai ko ina faɗa musu ake lafiyar dukkan su ƙalau lokaci ne kawai be yi ba, a shekarar ne kuma matar Sama'ila ta haifi ƴa mace bayan namijin da ta haifa ya rasu, ranar suna Sama'ila ya sanya wa yarinya sunan wata tsohuwar budurwar sa da yake tsananin so wato bilkisu, anyi ɗauki ba daɗi kafin matar sa Haleema ta haƙura da batun sunan ta shiga kiran yarinya da Maigado dan bata tunanin zata iya ambaton ta da sunan bilkisu. Se da Safwan da Asma'u suka cika shekara tara da aure kafin Allah ya azurtata da juna biyu, kwatanta yadda suka ɗauki cikin a ransu ɓata baki ne, sun yi kuka sun yi dariya sun yi murna sun yi sadaka sunyi kyauta at long last suka dira a ƙasa me tsarki dan nuna godiyar su wa ubangiji, ko da Safwan ya tashi dawowa can ya bar Asma'u bayan ya ajiye mata masu kula da ita har huɗu dan yace a ƙasa me tsarki zata haihu dan ɗan ko ƴar su Sami tubarakin ƙasar. Wata sha ɗaya sannan Asma'u ta haifi santaleliyar ƴar ta mace me matuƙar kamanni da duka iyayen ta biyun, dogon gashi da suffar jikin ta sak Asma'u ce yayinda tsayin ta da kamannin fuskar ya kasance na Safwan, murnar da wannan ahali suka yi a lokacin bame misaltuwa bace, nan suka shiga kula da ƴar su da taci sunan kakar ta wato Sakeena da suke kira da Kisnah cikin so da ƙauna bayan sun tarkato sun dawo garin Manya. Haihuwar Kisnah ya zowa Alh Safwan da matsanancin buɗi dan a shekarar ya samu nasarar buɗe manyan Companies ɗin sa har uku da tashi ɗaya ya sanya musu sunan ƴar sa wato K&S FURNITURES, K&,S CONSTRUCTION, K&S FLOUR AND FOOD STUFFS, haka kuma ya bi duk ragowar Companies ɗin ya canja musu suna zuwa K&S. Duk wani mazaunin garin manya ya sani ya kuma shaida irin soyayyar da Alh Safwan je wa gudar ƴar sa Kisnah dan tun da tayi wayo da ita yake zuwa ko ina in ka cire wajen aiki, a kuma lokacin ne ya haɗu da Alh Haladu wanda ya ɗauka ya bawa matsayin manager dan takardun sa sun kai, soyayyar da Alh Haladu ke nunawa Kisnah ce ta saka Alh Safwan sake masa har suka dawo abokai ya danƙa masa kula da K&S drinks and table water da K&S flour and food stuffs saboda aminci yayinda har lokacin suna tare da Alh Sulaiman. Wata rana da ta kasance baƙar rana wa ahalin, ranar da ta kafa baƙin tarihi a zuƙatan su da ma rayuwar su gaba ɗaya..........................✍️. Me ya faru a wannan ranar, wane tarihi ne baƙin tarihin......amsar ku na wajena😍. ©️ Ouummey 📚✍️. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. Ouummey 36 (8/26/2022 9:51 PM) 💠💠💠💠💠💠💠💠 *SARAKI (the Accused prince)* 💠💠💠💠💠💠💠💠 Daga Alƙalamin Ouummey Wattpad @Ouummey *Marubuciyar;* *1; HAƘORIN DARIYA* *2; ƘASAR MU A YAU* *3; BA NI DA LAIFI* *4; Loading......SARAKI (the Accused prince)* ______________________________ *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________________                           Page 3️⃣6️⃣ _________________________📖 ƙarfe tara na daren ranar they were sitting a falo having fun with her parents as always, she was just 5 a lokacin, ranar Abbu kamar yadda take kiran mahaifin nata be fita aiki ba yadda ya saba ko da Nana as she called her mom ta tambayi Abbu dalilin ƙin fitar he answered her with "Am going no where today sweetheart, will be spending the day with you and my cute, beautiful and charming princess". Ko da take yarinya lokacin ba ƙaramin daɗi ta ji ba da abinda Abbu yace, she really loves her Abbu as you loved her haka ma Nanan ta, kasancewar only daughter ɗin su yasa suke pampering ɗin fiye da zato sedai hakan be sa sun kasa tsawata mata ba, in har tayi ba daidai ba suna nuna mata sedai in a cool way da zata ji a ranta Yes she's wrong, bata yi daidai ba. Ranar they wore the same dress with there Nana, blue black Arabian gown that fits their complexion dan dukkan su farare ne sedai Kisnah tafi Nana dan ita Nana hasken ta me duhu ne ba irin na Kisnah ba da ta gado Abbu. Sun yi yawo gurare da ba zata iya tuna adadin su ba, sun ci from all they want, sun siyo duk abinda suka so daga me amfani har zuwa mara amfani, a ranar duk abinda tace yi mata kawai ake ko da wanda basu saba yi mata ko barin ta tayi ba a baya. Tjey spent the day together kamar yadda Abbu yayi alƙawari dan se after 7, ko da suka dawo wanka kawai sukai tare da Sallah sannan suka kuma biye mata suka cigaba da shiririta da kayan wasan ta har almost 9 Wanda ƙa'ida lokacin baccin ta nine ɗin ne, sedai ranar bata san me yasa Abbu keep saying Nana ta bar ta ba while Nana tayi insisting she should sleep saboda tana da school kasancewar gobe Monday. Abbu follows them to her room da suka shiga Nana zata yi mata shirin bacci, its not odd Abbu follow them Dan sometimes shi yake canja mata kayan ka but se jikin Nana yayi sanyi ganin ya karɓi ragamar shirya princess ɗin tasu as they called her majority of times, gefe Nana ta koma ta na kallon su kawai while he dress her happily suna dariya, she's having some kinda bad feelings and it's just recently, se take ganin kamar something is about to happen, kamar akwai wani obstacle da ze zo ya shiga tsakanin wannan father-daughter love ɗin, sedai ta danne wishing all that's about to happen ya canja zuwa khair. Ko da Abbu ya gama shirya ta be tafi ba se ma ya sami gefen bed ɗin ta ya zauna, bayan yayi mata addu'a se kuma ya shiga sake tsokanar ta suka shiga wasa da pillows ɗin bed ɗin maimakon ya sata tayi bacci, tears rolled down Nana's cheeks haka kawai, she keep staring at them tana jin wani abu a jikin ta, something me kama da kewa, kewa irin me cin ran nan, sincerely she's missing them while gasu a gaban ta, da ƙyar ta iya daurewa ta share hawayen ta tana sakin broad smile da ya kai har tsakiyar zuciyar ta ganin gaba ɗaya hankalin su baya kanta, they were busy playing and seeing them like this is all she have and want at the same time. So da yawa in ta kalli relation ɗin ƴar tasu da mahaifin ta mamaki kan kamata, tare take wuni da ita a gida in ba school amma a fili yake ƴar tasu ta fi shaƙuwa da mahaifin ta sama da ita sedai kuma mamakin baya zuwa ko ina yake ɓacewa dan tasan akwai manyan dalilan da zesa hakan faruwa. To Abbu Kisnah has always been his first priority and she's still har yanzu, kafin ta shiga school ko ina zashi da ita yake zuwa hatta da office, seda tayi da ƙyar sannan yake tafiya office ya barta, lokacin tashi nayi kuwa haka ne ajiye komai duk muhimmancin sa ya taho gare su kuma tun a compound ze Fara ƙwala Kiran princess yayind ita kuwa duk baccin da take kira ɗaya yake yi ta farka ta fice da sauri neman mahaifin nata, and one more thing baya taɓa shigowa gida be ruƙo mata wani abu ba, a rubuce yake kullum akwai abinda ze siyo ya kawo mata and that helped in bringing the level of shaƙuwar su so high. Weekend kuwa is never a leisure time wa Abbu tunda aka Kisnah ta fara wayo, he spent every of his weekends trying to pleases her and make her happy ta hanyar kaita gidajen wasa, adventure palaces, shoppings da ma gurare da dama. Yasha haɗa musu tafiya to outside Hawarya ƙasashe masu irin kayan tarihi na yara ɗin nan duk dan jin daɗin ƴar sa wannan ma ya taimaka sosai wajen samar da shaƙuwa da fahimta tsakanin ta da mahaifinta. For Nana kuwa daga baya ƙin bin su gurare ta dinga yi dan gajiyar da ita suke yi su kuwa ko a jikin su shiyasa tace ta dena binsu se wajen da itama take son gani, ko da yarinyar ta fara zuwa school majorityn lokuta Abbu ke dressing ɗin ta dan ko Nana ta zo haka ne persuading ɗin ta akan ta tafi ta yi girki ze taya ta shirya princess Shirin da sometimes har se ta gama girki su basu gama shi ba sun ɓige da wasa se ta shigo su kwakkwaɓe fuska suna bata haƙuri. Zaman sa me kuɗi be sa yace ya ɗau driver was ƴar sa ƙarama da bata san komai ba, da kansa yake kai ta ya ɗauko ta in Kuma aiki yayi masa yawa ya kira Nana taje ta ɗauko ta, wannan gatan yasa Kisnah zama very happy and active, a lokacin mutane da yawa na mata kallon ƴar turawa ne saboda ƙibar da tayi tana yarinya ga kuma kyau da fari kamar ka sace ta. Gyaran muryar da Nana tayi yasa ya kallo gefen ta daidai yana ɗaga pillow ze buga wa Kisnah da ta ke ɓuya, hararar wasa ta masoya Nana ta jefa masa hakan yasa ya sake pillown hannun sa da sauri ya riƙe kunnuwan sa dan se lokacin ya tuna ashe barci suka kawo Kisnah tayi, "Am sorry my life". Abbu ya faɗa while holding his two ears "Nana Abbu is sorry please". Kinsha ta faɗa itama tana riƙe da kunnuwan ta kamar yadda Abbun ta yayi, girgiza kanta kawai Nana tayi dan ta saba da irin wannan halin nasu, ba dama ɗaya yayi laifi se su haɗe mata kai su dinga bata haƙuri har se taji she have no option but to forgive them. "Oya bid her goodnight and move to our room". Nana ta faɗa in serious tone dan in ba haka tayi wa Abbu ba he won't mind spending the night with princess gobe kuma ya makara aiki haka itama princess din ta makara school. Be yi abinda ta ce ba se ya fice daga ɗakin, bin shi tayi da kallo tana sakin smile dan tasan yayi fushi kenan tun da ta kore shi daga wajen princess, ƙara sawa gadon yarinyar tayi ta zauna bakin gadon ta shiga tofa mata addu'a kamar yadda suka saba duk kuwa da cewa Abbu yayi mata amma ƙa'ida ne itama se tayi mata, tana gama ta saka yarinyar ta haɗe palms ɗin ta kafin ta saka ta ta karanta Suratul nas, Suratul falaq and Suratul Ahad da kanta tare da ayitul kursiyyu sanan ta umarce ta ta kwanta ta ja mata blanket kan cikin ta tare da mata offing light ta kunna mata qur'anic recitation a mp3 ɗin ta da aka siyo purposely sabida hakan da kuma ƙara koyan karatun da take yi. Seda ta jira tayi bacci kafin ta bi bayan Abbu ɗakin su inda ta same shi kwance kan gadon su har yayi wanka ya canja kaya zuwa na bacci sedai da alama yayi nisa a tunani dan be ko ji shigowar ta ba, bata ƙarasa gare shi ba seda ta yi wanka ta shirya sannan ta hau gadon har lokacin yana yadda ta same shi da farko, hannu ta miƙa ta cire masa tagumin kafin ta fara tambayar sa damuwar sa a tausashe. Shiru yayi kamar baze faɗa mata ba kafin kuma a hankali ya janyo ta jikin sa ya nufi baki yayi magana dan basa taɓa ɓoyewa junan su komai duk kuwa da ɓacin ran da maganar zata haifar sun gwammace su fuskanci hakan su kuma tare ko ma mene ke ƙoƙarin shiga tsakanin su. "I'm having some strange feelings Husna, Ina jin wani iri a jikina, yanayin kamar irin wani abu mara kyau na gab da faruwa, irin feeling ɗin da na ringa ji lokacin da zanyi rashin inna har ma da baffa na, bana son barin ku Asma'u but it's like something bad is about to happen sedai ban San akan wa ya ba, nidai fatana ko meye kar ya shafi princess, Husna I can't hold myself in wani abu ya taɓa min yarinya, bazan iya ɗauka ba, i pray koma meye ya tsaya a kaina dan............". Da sauri Nana ta rufe masa baki dan tuni ya daɗe da karya mata zuciya da kalaman sa, she too is experiencing the feelings sedai yanzu da ya alaƙanta yanayin da mutuwar Inna da baffa se abin yayi tasiri a rai da zuciyar ta gaba daya har take jin kamar zata rasa su ne, kamar...kamar.... bata fata! Kamar wanda ya dawo hayyacin sa yayi saurin gyara yanayin fuskar sa trying to hide something to her karo na farko tun fara rayuwar auren su 15years back, kumatun ta ya ja Yana sakin dariya lokacin da take faman sharar hawaye "See this woman, are you crying for good, tabɗi amma dai anji jiki dan dama gwada ku nake na ga extent to which kike son mu ni da princess ɗina nad thank God you love us this much". Ya ƙarashe yana mata cakulkuli, dariya take tana kai masa duka tare da magiyar ya bari amma yaƙi seda ya galabaitar da ita sannan ya kwanta gefen ta yana dariya ita kuma tana nishi, seda suka mutu kafin ya soma magana "Ko me kika ga ya faru da bawa rubutacce ne Husna, dan haka mu kwantar da hankalin mu muyi addu'a tunda ba zamu iya sauya ƙaddara ba, now let's pray and sleep ma'un safwanu". Ya ƙarashe in a joking tone dan yasan ta tsani ya kira ta ma'un nan, aikuwa seda ta mintsine shi kafin ta fara addu'a shima ya shiga yin tasa, tana gamawa ta shafawa kanta ta shafa masa shima yayi as she did sannan suka kwanta rungume da juna cikin blanket, shiru suka yi har ta fara gyangyaɗi kafin tai firgigit ta ce masa "I love You". "I love You more ma'u na". Ya faɗa kissing her forehead, and that's the end of their conversation bacci ya kwashe ta, seda ya tabbatar tayi bacci kafin ya zare jikin sa ya koma ɗakin princess, dim light ya kunna sannan ya kwanta a gefen ta yana staring at her face kamar wanda aka bawa aikin zana ta har bacci ya ɗauke shi. Ƙarfe biyu da rabi na dare Nana ta tashi fitsari, ko da ta je ta dawo bata ga Abbu ba ɗakin Kisnah ta nufa ta kunna wuta, kamar yadda tayi zato kuwa nan ta ganshi kwance kusa da princess ɗin tasa, kamar ta tashe shi se kuma ta ƙyale shi ta koma ɗakin su ta kwanta dan gadon baze ishe su su uku ba balle ta kwanta tare da su. Ko minti uku ba tayi ba ta fara jiyo ƙara kamar ana dukan glass ɗin upstairs ɗin su da yake daga stairs ɗin zuwa saman su akwai glass days zagaye gurin da dole se ya buɗe sannan mutum ze hawo. Da sauri ta sauka daga gadon ta koma ɗakin Kisnah kafin ta shiga tashin Abbu cikin firgici, a razane ya buɗe idon sa dan yana cikin wani mummunan mafarki ne ta tashe shi, bata ko lura da yanayin saba ta shiga sanar da shi abin da ke kan faruwa, shima cikin tashin hankali ya saka hannu biyu ya sunkuci Kisnah suka zagaya suka fice ta ƙofar baya, Nana daga ita se rigar baccin jikin ta inda Allah ya so ta ma me kauri ce kuma haɗe take da wando suma duka haka. Gudu ya shiga tsugawa a kan titi yayinda terrorist ɗin suka rufa musu baya dan wanda aka bari zagaye da gidan sun sanar da na ciki fitar su Abbu, haka suka dinga tsere da motar terrorist ɗin har daga ƙarshe suka kai ga harbin tayar motar, cikin ihu Abbu da yaji ƙarar da tayar tayi alamar fashe wa ya ke bawa Nana umarnin ficewa daga motar ita da Kisnah, cikin ruɗewa Nana ta sungumi Kisnah da ta farka tuni ta jefa ta window, cikin son tseratar da ƴar ta ta jefa ta gurin da bata san ina bane ita dai kawai fatan ta ta tsira. Tun daga wannan jefawar da Nana tayi mata ta suma yayinda su kuma su Abbu motar su ta shiga karantawa tana juyawa har ta shige cikin daji kafin ta tsaya sanadin bishiyar da ta tokare ta, mintuna kaɗan kuma ta tashi da wuta gaba ɗaya (abinda kawu yaso yiwa motar su Kisnah kenan da suka gudu se kuma ba sukai ga harbin ba suka daki wannan tankar). Duk da ƙananun shekarun ta a lokacin se da tayi kuka ba kaɗan ba domin a islamiyyar su ana faɗa musu in an mutu ba'a dawowa haka kullum Nana na faɗa mata in ta mutu ba zata sake ganin ta ba se gashi yanzu ana faɗa mata Abbu da Nanan ta sun mutu, a yadda taji labari daga baya ko gawar su ba'a samu ba wuta ta cinye komai. Bayan bakwai ne kuma kawu ya tarkato suka dawo gidan da zama, bayan sadakar arba'in ne kuma ya shiga batun ya kamata ta koma makaranta amma ba zata cigaba da karatu a ƙasar nan ba dan wai ta samu ta manta memoryn mutuwar su Abbu...................✍️. ©️ Ouummey 📚✍️. ☑️Ote, Comment and share fisabilillah. Ouummey 37 (8/27/2022 12:37 PM) 💠💠💠💠💠💠💠💠 *SARAKI (the Accused prince)* 💠💠💠💠💠💠💠💠 Daga Alƙalamin Ouummey Wattpad @Ouummey *Marubuciyar;* *1; HAƘORIN DARIYA* *2; ƘASAR MU A YAU* *3; BA NI DA LAIFI* *4; Loading......SARAKI (the Accused prince)* ______________________________ *PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞 ```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)``` /https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/ *P.W.A✍️* _________________________________                           Page 3️⃣7️⃣ __________________________📖 England kawu ya shirya kai ta batare da shawara da kowa ba dan tuni ya babbake kan dukiyar ta dan yace bata da wanda ya fishi a lokacin kuma ba wai ta mallaki hankalin ta bane so ze kular mata da komai zuwa ta girma, ko sati da karɓar ragamar Companies ɗin be yi ba ya sauke Alh Sulaiman daga kan duk abinda yake jagoranta ya canja manajojin da ya ga dama. Ana ya gobe ze kaita England Alh Sulaiman ya same shi har gida kan be dace ya kai yarinya ƙarama ba wata ƙasa ita kaɗai bayan bata da kowa a can, ƙasar da komai namu ya sha banban da nasu kama daga kan al'adu, addini zuwa wayewa sedai tuni kawu yasa ƙafa yayi fatali da maganganun Alh Sulaiman suka rabu baran baran bayan kawu yayi masa cin mutunci wanda wannan ne yasa Alh Sulaiman ɗin yin fushi be kuma magana ba akan duk abinda ya shafi Kisnah dan kawu ya faɗa masa ƴa dai tasa ce dan haka baya san shisshigi da kalan dangi. Haka kawu ya kaita makaranta yayi mata registration ɗin komai ya danƙa ta hannun shugaban makarantar da sunan ze dinga turo masa kuɗin komai na buƙatar karatu amma bazata dawo gida ba har se ta gama karatun ta zuwa matakin ƙaramar secondary. Haka kuwa akai kawu ya dawo gida manya ya bar Kisnah garin da bata da kowa a hannun baturen da be san Allah ba, kamar yadda yace bata dawo manya ba kuwa seda ta gama primary gaba ɗaya sedai batun ilimin addini kuwa babu shi dan tun da ta bar manya ba wanda ya kuma tuna mata akwai abin bautawa da gaskiya wato Allah balle kuma akai ga su karatun Alkur'ani da hukunce hukuncen addinin Islam sedai a karan kanta ta riƙe yin Sallah dan sallah ce abu ɗaya da Nana ta fi jaddada mata fiye da komai hakan yasa duk zamanta a can bata manta da yin ta ba sedai yadda zata yi tan ne bata iya ba so take yin duk yadda taso kawai. Dawowar ta da ƙyar kawu ya barta ta yi wata biyu a gida lokacin tana shekara goma ya kuma maida ta ƙasar Canada inda tayi karatun secondary gaba ɗaya har ta fara University kafin kuma tashi ɗaya ta gudo ta bar ƙasar shine haɗuwar su da Deeq a restaurant ɗin nan yake faɗar ta gudu  ba sanar wa sedai suka neme ta suka rasa. Dawowar ta ta nemi admission a nan manya state University department ɗin law inda kuma a nan ta haɗu da duk ƙawayen ta kamar yadda muka ji a baya .      *Wannan shine tarihin Kisnah*                  (Mun dawo labari). Shessheƙar kukan ta da yaji ya ƙara ƙarfi fiye da baya yasa ya juyo ya kai duban sa gare ta, daga zaunen da take ta ƙara takurewa kanta tsakankanin cinyoyin ta tana kukan ta da ya ɗan ƙara ƙarfi dan ta daɗe tana yin sa sedai be kai ƙarfin na yanzu ba. Mamaki ne ya kama shi ganin yadda jikin ta yake rawa sosai kamar wadda aka watsawa ruwan sanyi a tsakiyar hunturu, gaba ɗaya se yaji jikin sa yayi sanyi, me ya same ta da take kuka haka, bata da lafiya ne ko me? Kamar wanda aka tunawa haka kalmar mara hankalin da ya kira ta ya dawo kansa, to ko shi take wa kuka? Amma in ze tuna an kira ta da kalmar da tafi wannan muni kuma be ko ga ta damu ba balle har ayi batun yin kuka? To amma in ba hakan take wa kuka ba ai ba abinda aka yi mata haka kuma iya sanin sa lafiyar ta ƙalau. Kawar da kansa yayi daga kanta se kuma yaji baze iya ba, kiran sunan ta yayi a hankali sedai ko ɗagowa bata yi ba balle ta amsa hakan yasa ya sake kiran ta wannan karon cikin ɗan ɗaga murya, a hankali ta fara sassauta kukan har sautin ya dena fitowa gaba ɗaya sedai hawaye kafin kuma ta ɗago kanta gaba ɗaya ta sauke jajayen idon ta da kuka ya rina ya sauya musu kala. Seda ya ɗan firgita ganin yadda kyawawan fararen sexy eyes ɗin ta suka koma kala mara daɗin kallo, kafe shi tayi da su taƙi janye wa har lokacin kuma hawayen ta basu tsaya ba se shine yayi ƙarfin halin kau da nasa kafin ya shiga mata magana cikin sanyaya Murya "Lafiya?, me ya same ki?, Wani abun akayi miki?". Girgiza masa kai tayi alamar a'a dan tasan ko tace tayi masa magana ba iyawa zata yi ba yadda Muryar ta ya dishe haka kuma bata saba faɗawa kowa damuwar ta ba bata kuma jin zata fara yau, a kaf rayuwar ta tana barin damuwar ta a ranta ne dan ba wanda take dashi da zarai sharing dashi, a haka ta taso har girma shiyasa hakan ya zame mata ɗabi'a yayinda take samar wa kanta mafita irin wadda taga ta dace,  bata san me zata ce an yi mata ba tunda ba'a yi mata ɗin ba shiyasa kawai ta zaɓi girgaza masa kan. "In dan mara hankalin da na kira ki ne kiyi haƙuri raina ne ya ɓaci a lokacin amma na san be dace na faɗa miki hakan ba so na janye ta ki ɗauka ban ma faɗa ba, kinji?". Ya faɗa cikin sake sanyaya Murya, girgiza kanta ta sake yi a karo na biyu kafin ta buɗe baki tayi magana cikin dasasshiyar murya ganin yana ɗorawa kansa alhakin laifin da be aikata ba, tasan ta ji haushin sa akan kalmar haka har tayi fushi kuma ba wai ta janye ba ne sedai ita ba abinda ya sata kuka ba kenan, Allah ta tuba

Chapter 23 of 27