damuwa kan tafiyar nan taka, nayi istikhara na tsawon kwana huɗu kuma alhamdulillah naji kwanciyar hankali sosai dan da alama Saraki na yana Lafiya dan haka ka bar batun nan dan ina son ganin giccin ka a tare da ni Jamal".
"Amma Mami na riga na faɗawa takawa zan yi tafiyar nan har ya amince min, ba kya tunanin ya kawo wani tunani na daban kan fasawar tawa?
"Sam ba zaka fasa tafiya ba Jamal, kaje ƙasar da kace masa zaka kayi course ɗin wata biyun under your field daga nan ka dawo kayi aure dan Allah, ina son ganin grandchildren ɗina kafin lokaci na yayi".
Da sauri ya ruƙo hannun ta jin tana kawo batun mutuwa da sam baya san ji bawai dan be san dole zata mutun ba se dan yana fatan tayi tsawon rayuwar da zata ga dawowar gudan jinin ta mafi sayuwa a ranta cikin gidan uban sa da aka koreshi, cikin gatan sa kuma tunƙahon sa har ya taka matsayin da maƙiya suka ƙulla masa sharri domin shi.
"Insha Allah zan yi kamar yadda kika ce Mamina, ki taya ni da addu'a Allah ya bani Sa'a kinji alfahari na".
Hannu ta ɗora kan shi tayi masa addu'a kamar yadda ta saba yayinda cikin ranta ke ɗauke da kewar ɗan ta da yafi kowa kusanci da ita itama tafi kowa kusanci dashi, addu'a tayi masa a ranta kamar yadda ta saba duk ta tuno shi duk dama be taɓa barin ranta ba sedai ta danne kawai.
Sallama Jamal yayi mata ya tafi processing duk abinda ke haɗa na tafiyar ita kuma ta cigaba da duba litattafan addu'o'in da ya shigo ya same ta tana yi.
Ko da dare ta shirya tsaf dan zuwa turakar takawa kasancewar ita ke da kwana ranar, cikin haɗaɗɗen falon sa da ya kasance bame shiga se shi da matansa da ƴaƴansa ta same shi hannun sa riƙe da jarida yana dubawa, da sallama ta shiga ta zauna kusa dashi kafin ta miƙa gaisuwa.
Hannu ya ɗaga mata kasancewar karatun yasha kansa itama bata kuma ce masa komai ba ta shiga zuzzuba masa kayan abincin da ta ƙaraso dashi dan a falon farko ma'aikata ke ajiyewa me girki kuma se ta ƙarasa dashi.
Seda ya gama karanta jaridar kafin ya ajiye ya juya gare ta, cikin sakin fuska da walwalar da yake tsintar kansa duk ya kasance tare da ita ya amsa mata gaisuwar da tayi masa ɗazu yana me tambayar ta ya ta wuni.
Abincin ta tura gabansa bayan ta amsa shi da lafiya lau, cikin kwanciyar hankali ya soma cin abincin sa yayinda gimbiya Haleematu ta kafe shi da ido dan ɗan ta Saraki take hangowa a tare dashi.
Yanayin nutsuwar shi, yadda yake riƙe spoon har zuwa yadda yake tauna abinci duk takawa ya gado hakan yasa yanzu take ganin kamar shine a gaban ta, a dabarance tasaka tafin hannun ta ta goge hawayen rashin ɗan ta da ya zubo mata dan bata so takawan ya lura da halin da take ciki sedai abinda bata sani ba tuni ya gane me take tunani tun sanda ta kafe shi da ido har hawayen da ta share.
Ya daɗe da sanin Haleematu macece me tsananin kawaici haka kuma yafi kowa sanin halin ta na haƙuri kuma yafi kowa shaida irin son da take yiwa gudan jinin nata.
Tissue ya zara ya goge bakin sa bayan ya gama cin abincin, tashi tayi zata janye kwanakin ya dakatar da ita ta hanyar nuna mata kusa dashi
"Zauna nan Haleematu".
Kamar yadda ya umarce ta haka ta zauna dab dashi suna fuskantar juna, a hankali cike da dattako ya ruƙo kyawawan yatsun hannunta ya shiga murzawa a hankali kafin cikin murya me taushi ya shiga mata magana
"Me yake damun Haleematu na da har yake sata hawaye da damuwa? Wace irin damuwa ce haka da har gimbiyar Giwa ta kasa daurewa har raunin ta yana bayyana a fili? Shin akwai matsalar da ta shafi gimbiya ta da zata gagara sanar da ni Sarkin ta?
Duk yadda taso daurewa kasawa tayi, tsawon watanni biyu na barin Saraki masarauta yau ne takawa ya nuna yasan tana da damuwa duk da ta daɗe da sanin ya fahimci hakan yana dai kawar da kai ne dan kar ya bata fuskar tunkarar sa da batun Sarakin ko yaya sedai abinda ya manta a cikin halayen ta shine tafi kowa sanin sa da iya karantar sa kamar yadda yafi kowa sanin ta da fahimtar ta, ya manta tunda har ya nuna baya son jin komai dangane da Sarakin ita ɗin bazata taɓa kawo masa batun ba saboda tsananin biyayyar ta.
Janyo ta yayi jikin sa yana bubbuga kafaɗar ta har tayi me isarta ta share hawayen ta kafin ya ɗago ta
"Faɗa min, menene damuwar gimbiya ta".
Murmushin da ya tsaya iya saman lips ɗin ta tayi kafin ta bashi amsa
"Ba wata babbar damuwa bace, kawai dai zuciya tace bata min daɗi haka ina ji na empty, shikenan"
Tsananin tausayin ta ne ya kama shi, dama ya sani ba zata kawo masa batun Saraki ba ko za'a shekara nawa ne kuwa, shi kansa yana kewar ɗan nasa sedai da ya tuno irin laifin da ya aikata se yaji baya ko san jin sunansa balle tunawa dashi, bare kuma ita da yana cikin wanda zasu bada labarin irin shaƙuwar dake tsakanin su, akan ce ƴa mace itace ta uwa mace sedai a ɓangaren Sarakin da gimbiya is different, komai nasa Mamin sa ce, itace abokiyar sa, malamar sa, Auntyn sa, yayar sa kuma mahaifiyar sa haka a gare ta Saraki ne ƙawarta, maman ta, yayar ta, kuma wanta, ya sani in yace kar ta damu ma be mata adalci ba dan haka be sake ɗaga maganar ba se nasiha da wa'azi da ya shiga yi mata har hankalin ta ya kwanta har tayi cikakken murmushin da ya fito tun daga zuciyar ta ba wai iya fatar baki ba. (Allah Sarki uwa, i love U so much my umma💞).
................................
Babbar macece sedai ba wai irin girma sosai ɗin nan ba a kishingiɗe kan tattausan gadon da yasha shimfiɗu na alfarma, a ƙalla bazata wuce shakara 48 ba , daga kishingiɗen da take ta ke girgiza ƙafafunta da suka sha zanen jan lalle irin na zamani fuskar ta ɗauke da ƙasaitaccen murmushi, daga gefen ta kuwa matashin saurayi ne zaune kan tuntun ƙafar sa ɗaya kan ɗaya yana dubanta
"Kar ka wani damu da wannan dan ni baya cikin lissafi na ko kaɗan, ko kana manta ka girme mashi ne kuma a halin yanzu kai ke amsa sunan YARIMA ME JIRAN GADO? kana tunanin zan yi sake da sarauta zata faɗa ɗakin Haleema ne bayan ina da ɗa babba? Ko kaɗan dan haka ka kwantar da hankalin ka ka cigaba da rayuwar ka ni mahaifiyar ka RUMANA na maka alƙawarin indai ina raye to sarautar Daular Noor taka ce".
Sosai farin ciki da murna suka wanzu kan fuskar sa
"Shiyasa nake matuƙar so da ƙaunar ki Ammi na, Allah ya bar min ke ya ƙara miki lafiya me inganci ki ganni zaune kan karaga matsayin sarkin daular Noor, Sarki UTHMAN MUHAMMAD HASHEEM". Ya ƙarasa faɗa sautin Muryar sa cike da tsananin buri da fata wanda itama gareta gimbiya RUMANA hakan ne a ranta.
***************
"Ke yanzu Laylah baza kiyi wa kanki karatun ta nutsu bane, shin baki san rayuwar mace nada limit bane, fidabilillah ace kin zauna jiran gawon shanu kin ƙi aure kin zauna jiran wanda baki san yaushe zai dawo gare ki ba, yanzu kin yiwa kanki adalci kenan? Ko kuwa kin manta har Yarima Saraki ya bar masarautar nan be taɓa son ki ba ne?".
Hawaye ne masu zafin gaske suka zubo daga idanun matashiyar dake duƙe ƙasan dattijuwar dake magana, kallo ɗaya zaka musu kasan uwa da ƴa ne saboda tsananin kamannin da suke yi, a hankali dattijuwar ta saka hannun ta ta ruƙo kafaɗar ƴar tata
"Bawai bana son ki da Saraki bane Laylah, hasalima se na fi kowa san tarayyar ku sedai dole in faɗa miki gaskiya, kin sani kaf masarautar nan ba da wanda na aminta sama da gimbiyar Giwa haka itama gare ta, dan Allah ki cire komai a ranki ki bawa maneman ki dama Laylah, wallahi zaman ki haka ba aure yana damu na".
Ruƙo hannun dattijuwar Laylah tayi cikin sakin murmushin da be kai zuci ba,
" Ki taya ni da addu'a Ummi na, insha Allah zan yi kamar yadda kika ce, nima ina so in manta dashi sedai har yau na kasa hakan, kullum gani nake kamar ze dawo gare ni amma insha Allah a wannan karon zan ƙoƙar ta".
Cikin tausayin autar tata Umma ta ce
"A yanzu kam ni Sameera bani da wadda nake wa addu'a kamar ke Laylah, dan haka kar ki damu kinji Allah na tare da ke".
Gyaɗa kai Laylah tayi kafin ta miƙa
"Bari in je in duba abincin can kar ya ƙone".
Ficewa tayi tana saƙa da warwara cikin ranta na yadda zata iya yakice Saraki cikin zuciyar ta....................✍️.
Hhhhhhh😂🤣🤣 su Mommy an yi laushi luɓuɓus😜😜.
Gimbiya RUMANA, ko ita kuma wacce haka🤔oho🤷
Toooooo faaaahhh😳 ke kuma Laylah daga ina, wata sabuwa inji ɗan caca, #team_saraki Ina tambaya 🤔
©️ Ouummey 📚✍️.
*☑️Ote, comment and share fidabilillah*
Ouummey 13 (8/6/2022 9:46 PM )
💠💠💠💠💠💠💠💠
*SARAKI (the Accused prince)*
💠💠💠💠💠💠💠💠
Daga Alƙalamin Ouummey
Wattpad @Ouummey
*Marubuciyar;*
*1; HAƘORIN DARIYA*
*2; ƘASAR MU A YAU*
*3; BA NI DA LAIFI*
*4; Loading......SARAKI (the Accused prince)*
______________________________
*PERFECT WRITER'S ASSOCIATION* 🌞
```( WE AIN'T PERFECT, BUT WE'RE ALWAYS TRYING OUR BEST TO MOTIVATED AND ENTERTAIN OUR REDERS💪)```
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A✍️*
_________________________________
Page 1️⃣3️⃣
_________________________📖ko da suka isa can suka tadda su Meenah and alhamdulillah jikin Surryn da sauƙi sosai dan ta ma farka har suna ta hira da Leekha, kamar yadda ta saba haka tayi wato just ta tura ƙofan ta shige without Salam yayinda Saraki dake bayanta riƙe da ledodin shopping be shiga ba se da yayi sallama ya jira izini tukunna dan ga dukkan alamu gareshi mata ne a ɗakin saboda tashin muryoyin su da ake ɗan ji daga waje.
Kujerar gefen gado Meedah ta turawa Kisnah ta zauna suka shiga gaisawa da tambayar ya me jiki kafin ta maida kanta wajen Surayya da tun da Kisnahn ta shigo take ta sakar mata murmushi.
"Ya jiki swee swee?
Ta tambayi Surry calling her with the name she used to,
"Alhamdulillah da sauƙi Kissy, Ina ta zuba ido amma shiru nace to akwai abinda ya tsaida ki, hope dai guy ɗin be miki komai ba ko?".
"Sure naso na fito da wuri sedai kuma i have to wait for my new driver da na bawa appointment ɗin ganawa dashi da safen, no kar ki tashi hankalin ki ba abin da yayi min, all thanks to you my swee swee".
"Masha Allah, that's what I wanna hear tun farkawana".
"And you'll heal faster insha Allah".
"We hope so my Kissy, so your new drive brought you here".
"Yesso, ai tare ma muke, here he is".
Ta faɗa tana juya wa dan nuna mata Saraki sedai wayam bata ganshi ba, miƙewa tayi ta nufi ƙofa tana faɗin
"A'ah, ina kuma ya tsaya, i thought tare muka zo kofar ɗakin".
Buɗe ƙofar tayi da niyyar fita duba shi se ta tadda shi tsaye hannayen sa riƙe da shopping bags ɗin har lokacin, zaro ido tayi cikin mamaki
"So all this while kana tsaye a bakin ƙafa still holding the bags ko ɗan ajiye wa ka huta ma baka yi ba kamar wani soja, tabɗi, okay let's enter".
Bece mata komai ba ya bi bayanta cikin ɗakin, be kalli kowacce ba cikin su dan ba wadda ta amsa sallamar da yayi ya ƙarasa gaban Kisnah ya ajiye bags ɗin ya juya ya fita, da ido duk suka raka shi banda Kisnah da hankalin ta ke kan waya tana duba messages a watsapp ɗin ta
"Lord of heaven, Ina kika samo cute and handsome guy ɗin nan Kisnah?".
Surayya ta tambaya a ɗan ruɗe dan ita fa Allah ya jarrabe ta ko ta ɗorawa kanta son maza zance, idon ta idon namiji me kyau se dai ƙarfin ikon Allah ya hana ta samun shi, hatsabibiyar kanta ce wajen sanin salo salo na kissa da kisisinar jan hankalin maza masu kyau shiyasa yanzu ma tana ganin Saraki taji ya fa yi mata.
"Shine sabon driver na".
"Driver!!!". Suka yi exclaiming in disbelief, gyaɗa musu Kai tayi in assurance ba tareda ta dube su ba.
"Amma gaskiya me kyau ne, Oh my Goddd!!
"Baki ƙarya ba Surayya yana da kyau kam sosai".
Leekha ta faɗa in support of Surayya's words.
Wani irin yatsuna fuska Hameedah tayi ganin yadda Surry da Leekha suka ruɗe da ganin wani banza wai shi driver
"Kyan banza kenan, kyan ɗan maciji da baya hana a kashe shi, duk wannan kyan nasa dai sunan sa driver, so disgusting, mtsww".
Ta ƙarashe tana tsartar da miyau in disguise, ɗan taɓe baki Meenah tayi tana ɗan jefawa Surry harara
"Kin San fa ita Surry anything related to men shine abun yabo a wajen ta, ni duk banga abin zuzutawa ba a guy ɗin dan ba yau muka fara ganin maza masu kyau ba ai".
Janyo bags ɗin Kisnah tayi batare da ta tankawa kowa daga cikin su ba ta tura gaban Surayya tana kallon ta
"Yau Aunty tazo ne?".
"Tazo amma bata daɗe ba ta tafi, dama zuwan nata bana Allah bane shiyasa tun da yaya yace mata ze Kai wata be dawo ba se ta tafiyar ta meaning ai dai kafin ya dawo na warke".
Jijjiga kai Kisnah tayi tana miƙewa ta fara tafiya
"Bari naje police station naga yadda zanyi da wancan ƙaramin ƙwaron, in na fito da wuri maybe na dawo akasin haka kuma se gobe insha Allah".
"Allah ya yarda, but what about test ɗin da zamu yi gobe ga kuma abinda ya faru kinga ba zan samu zuwa ba".
"Karki damu, I'll handle that".
"Goodluck then".
Yatsu biyu ta ɗaga musu ta ƙarasa ficewa daga ɗakin yayinda Meenah da Hameedah suka bi bayan ta dan mata rakiya zuwa wajen mota Leekha kuma ta zauna tareda Surry.
Zaune a cikin motar suka same shi yana sauraren karatun Alkur'ani da aka saka gidan radiyon Sa'a FM, buɗe mata ƙofar baya Hameedah tayi take kuwa ta girgiza mata kai ta saka hannu ta buɗe gidan gaba ta zauna tare da maida murfin ta rufe, sauke glass ɗin tayi tai waving ɗin su daidai lokacin ya tashi motar suka bar wajen.
"Durumi police station zamu je".
Ta faɗa tana lumshe ido saboda yadda karatun Alkur'anin cikin ƙira'ar Sheikh shureim ke ratsa jikin ta har tana jin kamar ta dawwama tana saurara, wani irin shauƙi da nishaɗi take jin yana shigar ta from nowhere da ya tilasta mata lumshe ido tare da kwanciya cikin kujerar, karon farko tana zaune cikin mota without her daily headphone a kunnen ta.
Cikin wannan yanayin suka ƙarasa gaban ƙaton ginin police station ɗin wanda bama ta san sun kawo ba seda ya ƙwanƙwasa glass ɗin kusa da shi kafin ta ɗago ta dube shi, ɗage mata gira yayi kafin ya nuna mata station ɗin da idon sa, saurin kau da kai tayi dan jin yadda jinin jikin ta ya tsinke da signal ɗin da ya mata.
Hannun ta na ɗan rawa ta buɗe ƙofar ta fice da sauri tare da mai da ƙofar ta rufe, ɗan jingina tayi jikin motar har ta samu ta daidaita nutsuwar ta kafin ta buɗe side ɗin da ta fito ta ɗau purse ɗin ta da ta manta, batare da ta dube shi ba tace ya fito su shiga.
Fitowar yayi kamar yadda tace yayi gaba tana bin shi a baya har cikin station ɗin, dogon baƙin kakkauran ɗan sandan dake kanta ya fito da sauri yana welcoming ɗin su dan polisawa kaɗan ne zasuce basu san fuskar Kisnah ba, ko ba domin tsiwar ta da yadda ake kawo report ko ita tasa a kama wani ba, ba wanda ke cikin garin Manya daze ce be san K&S drinks ba, K&S table water, K&S couture, K&S textiles, K&S Furnitures, K&S shopping Mall, K&S flour and food stuff Wanda duk itace mamallakiyar su a yanzu.
Da sauri police ɗin yayi leading ɗin ta to office ɗin D.P.O dan jin ƙorafin ta, kai tsaye ta shiga office ɗin without any knocking or neman izini, a fusace dpo ya miƙe dan ganin wane shegen ne ya shigo masa without excuse se kuma yai arangama da Kisnah, da sauri ya washe baki yana mata maraba
"Welcome Madam Kisnah, have a seat please". Ya faɗa yana tura mata ɗaya daga cikin kujerun dake gaban table ɗin sa, ɗan ɓata fuska tayi kafin kuma ta zauna tana ɗan sakin fuska, da sallama Saraki dake bayan ta ya shigo wanda dpo ne kaɗai ya amsa masa banda Madam ɗin da tayi kamar ma bata ji ba, shima kujera dpo ya nuna masa wadda ke kusa da Kisnah ya zauna.
Gyara zama Kisnah tayi tana ɗora hannayen ta kan table ɗin dpo
"Nazo ganin sheɗanin da ya nemi shiga hanya ta ne day before yesterday".
Da sauri dpo ya miƙe yana faɗin
"Bari a kawo shi Madam".
Ficewa yayi yana bawa wani kurtu umarnin kawo Sageer wajen sa, da sauri kurtun ya amsa yana wuce wa ciki inda aka rufe Sageer, ɗaɗɗaure cikin sarƙa hannu da ƙafa aka fito dashi kamar wani gawurtaccen ɗan fashi ko makashin jama'a dan da ƙyar ma yake iya tafiya, gaba ɗaya kamannin sa sun canja kai baka ce Sageer ɗin nan bane haɗaɗden gaye me ji da wanka.
Karɓar sarƙar dpo yayi ya iza ƙeyar sa cikin office ɗin sa wajen su Kisnah, jan kujerar ta baya tayi tana jefawa Sageer mugun kallo lokacin da dpo ya gurfanar dashi gaban ta.
Shiru tayi tana bin shi da kallo kafin ta daddage ta sheƙa masa kyakkyawan marin da se da ya hantsila saboda ƙarfin sa, ƙafar ta takai ta kuma shurin sa yayi baya ya bugu da bango, hakan be mata ba ta tashi ta bishi tana duka da ƙafa faɗi kawai take
"How dere you, I said how dere you".
Sosai baki da hancin Sageer suka fashe dan ya daku da takalmin Kisnah da ya kasance me tsini sosai, dukan sa kawai take dan duk ta tuno ƙazamin hannun sa ya taɓa jikin ta se taji kamar ana hura mata wuta a zuciyar ta, ga kuma raunin da yayi wa Surayya da take asibiti sanadin shi, dpo na zaune kan kujera ko pim bece mata kan dukan da take wa Sageer ɗin ba wanda a ƙa'ida hakan ya saɓawa doka, se ma aikin sa da ya cigaba da yi hankali kwance kai kace baya wajen.
"Stop it, I said stop it". Tsayawa tayi cak kamar wadda aka dannawa pause kafin a hankali ta juyo ta dubi Saraki dake tsaye bayan ta wanda shi ya daka mata tsawar, kafe shi tayi da ido kafin a hankali ta girgiza kanta
"Baka san me wannan annamimin yayi min ba that's why you're saying I should stop, had you know what he did cewa ma zaka yi in ƙara masa".
"Whatsoever, dukan yayi yawa, can't you see he's bleeding, don't you get a heart in your chest?".
Cikin ihun masifa ta shiga bashi amsa dan ranta ya kai maƙura wurin ɓacin cewa ta ƙyale Sageer da yayi, har yana wani faɗa mata whatsoever, kamar ita, lallai ma!
"I don't care, nace I don't bloody care if he'll loose all of his blood here, this stupid guy use his worthless dirty filthy hands to touch me with his dirty intention, he attempted to rape me after drugging me which without Surayya he would have succeed, can't you understand, nace can't you see Surayya is there laying on sick bed because of this stupid brat, he intends killing her if not Allah has saved her she would have been in her grave since yesterday, and you're here saying I should leave him, tell me how can I leave this devil".
Be kalle ta ba ya juya ga dpo da tuni shima ya miƙe tsaye yana rarraba ido tsakanin su a ransa yana ayyana
'this guy must be her brother or boyfriend' Dan if not one of the two baya tunani akwai someone that has the gut ya ma Kisnah tsawa like this giving her orders.
"Take him to hospital, he's unconscious".
Da sauri dpo ya ƙarasa gaban Sageer dake kwance ƙasa wanwar har lokacin hancin sa na fidda jini ya fara jansa kafin ya kira ƴan sanda ɗaya ya kama masa suka ɗauke shi, juyawa yayi ga Kisnah da ta kafe shi da idanu, kallo ɗaya yayi mata yasan ta kai maƙura gurin ɓacin rai, kujerar ta da ta ture garin dukan Sageer ya jawo mata
"Seat".
Banza tayi masa dan fa takai wuya, ɗan shiru yayi kafin ya ɗan rage kausasa Muryar da yai ya sake faɗa mata
"Saet Please".
Kamar bazata zauna ba se kuma ta zauna tare da kau da kanta daga gare shi tana huci, zama yayi a kujerar da ya tashi shima
"He attempted raping you saboda kin sa kayan da basu dace ba? Okay hakan is nothing, you live your life as you wish, Amma bakiyi tunanin ya mutu ba saboda dukan da kike masa bayan akwai harbi a ƙafar sa ga kuma dukan da police ɗin suka masa, ba kya tsoron ya mutu a hannun ki? Ko baki san duka zunuban sa zasu koma kanki bane, why not ki Kai shi court a yanke masa hukunci daidai laifin sa? Yes he's a devil for what he did but what if you decide to forgive him? Do you know the reward, ehm? The prophet said whoever forgive someone Allah will also forgive him, do you think you've no sin? No! We all sinned because we're bin Adams and we'll all like Allah to forgive us, didn't you want to be among?".
Ya ƙarashe cikin sigar tambaya, sosai taji jikin ta yayi sanyi with his speech, a hankali ta girgiza kanta alamun she want, ajiyar zuciya Saraki ya sauke a ɓoye ganin ta karɓi nasihar sa
"So forgive him please, leave him for the sake of Allah, in har halin sa ne hakan kuma be tuba ba se kiga Allah yayi punishing ɗin sa one way or the other, will you pls forgive him?".
"Na yafe masa". Ta faɗa so cool hoping Allah will forgive her also.
Sosai yaji daɗin yadda bata da taurin kai sosai, he pray Allah ya shirya ta dan ya fara yadda da abinda Inusa ya faɗa masa ɗazu, now he believed she's simple yadda be yi tsammani ba.
"Akwai abinda muke jira ne?".
"Yes, ka faɗawa dpo nace a sake shi".
Gyaɗa kai yayi ya fita daga office ɗin, bakin ƙofa suka yi kiciɓis da dpo so kawai se ya dawo ciki shima dpon ya shigo, cikin sauke ɗan numfashi saboda doguwar maganar da yayi ya kalli dpo
"You released him, ta yafe masa".
Da sauri dpo ya kalle ta daidai tana miƙewa tsaye, gyaɗa masa kai alamar hakane kafin ta fice daga office ɗin, fita shima Saraki yayi cos se ya buɗe zata shiga motar dan yayi locking motar.
Jingina jikin motar ya same ta dan haka tun kan ya ƙarasa yayi unlocking car ɗin using smart Lock na car ɗin, jin alamun yai unlocking yasa ta buɗe ta shiga ta zauna kalaman shi na sake yawo a kanta, shiga yayi shima ya zauna tare da rufe ƙofar ya tada motar suka hau kwalta, ƙwaƙƙwaran motsi bata yi ba har suka kusa isa gida traffic ya tsaida su, ɗan buɗe ido tayi ta kalli titin ganin yadda ababen hawa suka cika ko ina alamun an tashi kasuwa, daga can tsallaken titi ta hango wani tsoho tukuf duƙaƙƙe yana takawa a hankali hannun sa saƙale da buhu, ɗan sake buɗe ido tayi ganin kuɗaɗen sa da ya samo sadaka (not sure) na zubewa ta wata ƴar huda jikin buhun, kallon traffic ɗin gaban su tayi taga suna da sauran kusan 20 count downs kafin a sake su dan haka ta ɓalle murfin motar ta fita da sauri.
Ƙarar buɗe side ɗin ta ya sa ya juyo dan ganin ina zata, kan idon sa ta kukkurɗa tsakanin motocin har ta ƙarasa wajen tsohon da yake tafiya kamar yaron da yanzu yake koyon tafiyar,
"Sannu baba, kana ta zubar da kuɗin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 27