Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels AN HUTU HAUSABООK.COM YAYAN BILKISU S. AHMED Harafi Publlshers KaAure Ni BILKISUHAMUHD GODIYA AISHA IBRAHIM MRS YUSUF BICH DIRECTOR na S.S jihar sokoto da AMINIYARTA MASU KAUNAN JUNA WATO HAWA.U MRS T. HUSAINI COMMISIONER OF POLICE NA JIHAR LEGOS YABO INA YABAWA YAR BAIWA BILKISU DR MUSTAPIHA BUNZA MRS SAHABI AHMAD BUNZA UMMI SALMAN DA SALMA TUKUICI TUKUIČI NE GA MASOYANA A SOKOTO KAMAR HADIZA ADAMU GWARANYO MRS ABDULLAIII YAKUBU NNPC ABUJA. ecura Legend ta dade (saye a kofar gidan da Aya zan na mahaifinsa ne, shima mai motar na cikin motar zaune, mai gadi har ya gaji da nkon get ya yı zuru yana kallon ikon Allah. Sahabi Ahmad shi ne zaune cikin motarsa yana rike da G.S.M din sa yana aikawa da mami text, abunda ya dame shi shi ne awa biyu kenan ya aikawa da mami text har sau biyar (No reply) tabbas kuma wayarsa ta ba shi tabbacin cewa sokonsa ya isa gare ta zuciyarsa ta Kulu kamar zai kuka me ke faruwa da mami ne don Allah! Ya yi jira a bakin get kimanin minti shidda babu dai bayani, ya yi aiyar zuciya ya dagawa Idi mai gadi hannu ya tuka motarsa a hankali ya shiga ya mayas da get ya rufe. Hajiya mahaifiyarsu Sahabi na zaune a falo tana faukar karatun ahalari wajen malamar ta malama lami, ganin haka sai Sahabi ya wuce kai tsaye zuwa kicina sami mai masu abinci yace akawo nai abincinsa falon baki, yana zaune yana cin abinci yana hararar wayarsa G.S.M shi dai jin dadinsa da kwanciyar hankalinsa mami ta amsa text din sa, gab da zai gama cin abinci malama lami ta shigo tare da kaurara sallamar ta, ya amsa a mutunce, ta ce Baba Sahabi ina yini ya ce lafiya lau malama ai ban yi zaton kun gama karatun ba, shi yasa ban zo na gaisheki ba, ta ce, "Kai haba babu komi ni na, saba ka sani ba, shi yasa na zo mu gaisa, to ni na koma gida", ya ce "To. to bari mana na zo na rage maki hanya", ta ce, A'ah Baba zauna ka huta, kai da ka 4 dawo daga wajen aiki yanzu, ga Hajiya can ma ta се Kaninka Umar ya fiddo motar ta ya kai ni", ya сс "To, shikenan sai da safe malama". Hajiya ta shigo falon a dai dai lokacin da ya daga G.S.M din sa ya kira mami cikin muryar nan ta ta mai tsinke lakka sannan mai raunana zuciya ta ce Hello! Ya ce "Mami" cikin sheshckar murya da sarkewa, ya yi kiran ta ce Na'am Ab kar" lokutta da yawa takan kirasa da real sunansa Abubakar wani lokaci kadan kadan take kiran sa Sahabi amma kowannce ta kirasa yana so domin yana jin dadi. ganin Hajiya ya mike tsam ya kutsa kai dakin bakl ya mayas da kofar ya rufe don ya yi zance da mami rabin ran sa cikin sirri, ita ko Hajiyar ta tsaya tana mamakin yadda Sahabi ke mutunta komi na mami bai iya hada ta da kowa komi na mami daban ne a wajen Sahabi, ta girgiza kai ta fita kawai abinta. Sahabi cikin dai damuwa kamar yadda ya saba nuna mata ya cc, mami na sha nemanki a layi ba service, kana na aiko da text ba amsa why? Ta daga kafadu tamkar yana ganin ta tace "haka nan", ya yi shiru alamun damuwa can ya amsa ya ce, shin mami da gaske ko kin matsu da ni kamar yadda na damu da ke? a A nan fa ta yi shiru saboda yau haka ta wuni tunanin matsalar aure shin an ya ko ya dace ta yi aurc yanzu yadda taga ana ta samun tangarda ta fannin auratayya ta yi ajiyar zuciya ta ce, Ab-kar don Allah in ka sami hali ina son ganin ka bayan sallar issha'e", gabansa ya bada dam, ya cc, Ba dai wani abu na yi ba ko mami? Та се, "Кo kadan, ina dai son mu warware 2 wasu 'yan matsalolin ne", ya ce, Babu matsala ina naržuw a" Su ka yi sallama ya rufe wayarsa, ya saka aljihu ya nuli falon Hajiya. Ta shirya mai manyan tangaraye fauke da nau'en abinci kala biyu domin sanin kanta ne duk cikin 'ya'yanta babu.mai son cin abinci irin Sahabi da Abba tun suna 'yan kanana don haka a kullun komi na su na fannin abinci Hajiya bata wasa tana bayas da mahainmanci. Ya bude tangaran na farko Spring rolls ne nan da nan ya soma ci ya na washe baki yayin da Hajiya ta rinka tsiyaya mai kunun zaki mai kyan gaske, kayan kanshi suka rinka yi mai dadl a makwaogoro, Hajiya ta ce, "Hala dazun da mami ku ke waya?, ya yi murmushi ya ce, "Ita ce Hajiya af na manta ta ce, tana gayasda ke", ta amsa Na gode, ya dace ku shirya mana lokaci haka nan, ko na huta da kullum zaman jiranka ka zo ka ci abinci, ka ga sai naji da kannanka ya ce, "Ai zan shawarci mami Hajiya kila ma yau. Suka shiga zantattuka na game da iyali, inda Hajiya ta shaida masa karshen watan nan take son za su sokoto su wuce Kebbi wajen dangin mahaifinsu Sahabi, akwai gaishe - gaishen rashin lafiya ga gaisuwar mutuwa, da dibo dangi. *** *** *** Mallam Ahmad Shu'aib haifaffan Sokoto ne uwa da uba. Ya yi ilmi mai zurifi domin nuna iya kiransa mai mukamin likitan ilmi wato Dr. Shu'aib-ya dade 3 yana bada lecture a rikakkar makarantar nan irin ta daga wane sai wane wato Kuru akwai zamanin da ya zan mukaddashin shugaba a makarantar N.I.T "dake zaune a hanyar Basawa cikin birnin Zaria aikin sa na Rarshe shi ne ya rike shugabancin ma'aikatar nan ta Kaduna wato N.1.Т. A nan ne Allah ya yi ma Dr. Ahmad Shu'aib rasuwa a sanadiyar hatsarin mota. Ya mutu ya bar matarsa daya tilo mace mai kamar maza kwari ne babu Hajiya Aishatau, sanin kowa ne mace mai suna Aishatu Indo A'i sukan zamanto jarumai masu gaskiya da rikon amana ga kamun kai da taurin rai a dalilin taurin ran su ne ma har iyalansu su kan sha wahalar rayuwa da su amma fa akwai kula ta hakika, ga tsauri. To itama haka Aishar Dr. Ahmad ta kasance masa, tana da tarin ilmi sosai na zamani da na islam, ta yi nisa a fannin aikin lafiya yanzu haka tana matsayin Senior metron ta asibitin nan nursing home da ke Kaduna ko da mijinta ya rasu bata daina aiki ba. Aisha ta haifawa Ahmad 'ya'ya takwas hudu maza hudu mata. Hadiza itace babba sai Abubakar shi ne ake kira Sahabi abun nufi Sahabin manzon Allah sayidina Abubakar, na uku itace Sa'adiya sannan sunan mahaifin Dr. wato Shu'aib sannan auta Aisha. Hadiza da Sa'adiya sun yi aure kowacce da 'ya'yanta biyu Hadiza ta yi karatun likita a jami'ar Amadu Bello da ke Zariya tana zaune da mijinta anan Kaduna gaba daya 'ya'yanta 'yan mata ne sai Sa'adiya diyan ta mace. da namiji Accounting and audit ta yi digiri kansa itama lecturing take yi a kaduna polytecnic shi ma mijin ta Dr. Bauchi Senior lecturer ne a polytecnic kaduna. Usman da umar suna matakin karshe a jami'ar fodiyo da ke Sokoto sai Hafsat ta na sakandire antrudu a Danbo international kaduna yayin da Aisha take yin primary a Dambo din. Dr. Ahmad ya ga auren Sa'adiya da na Hadiza hakan nan ya san 'ya'yan Hadiza amma Sa'adiya kamal kadai ya sani bai san Hanifa ba. Sai shi madugu uban tafiyar wato Abubakar Sadiq Sahabi. A jami'ar Amadu Bello ya karanci injiniya (petro chemical) yana karewa ya yi hidimar kasa sai Dr. Ahmad ya tura sa Canada ya biya masa ya yi digiri na biyu zuwa na uku a fanni daban daban sannan ya dawo. Dr. Ahmad ya samar mai aiki a Kaduna Refinary in da ya ke har zuwa yau. Hajiya Aisha a matsayinta na matar aure kuma uwar 'ya'ya da yawa sannan kuma mai kula da lafiyar al'uma ta zama abar koyi sannan kuma abun tutuya ga sauran mata macece mai iya bada tarbiya ta hori diyanta da son junansu da tsananin kaunar kansu, babu yadda za'ai Karami ya kawo ma babba raini, suna girmama junansu kamar zasu hurawa junan su rai. A koda yaushe suna shawartar junan' su har sai sun tabbata abunda suka kudurawa ransu ya zan dai dai amma kuma an hore su da adana sirrinsu azuci ba komi suke iya yin shawara akan sa ba misali kamar Hadiza da matsalolin dangin mijinta bata iya sanarwa a gida gudun kada ta kulla gaba tsakanin su, ta kan yi shawarar ne da mijinta kawai, kamar 5 lokacin da suka kulla Kauna ita da shi bata amince ta i snawara da kowa ba a gidansu don tsoron kada a canza mata shawara, wannan kenan. Sun sani kyakyawar tarbiyar dayaita Allah komi rintsi komi wahala komi dadi suna tare da Allah ako ina suke wannan shi ne jigon su a komi sun yi imani da hakan, saboda ko da cikin matsala dayan su ya kasance da wuya su yawaita yawan magana sai dai yawan addu'a har sai sun ga komi ya yi dai- dai. Duk da hajiya Aisha ta yi nisa wajen aikin asibiti amma wannan bai hanata zama ta shiryawa iyalinta abinci mai kyau ba haka nan duk 'ya'yanta 'yan mata tun suna shekara biyar take soma shiga da su kicin, tun daga kan mijinta har zuwa kan 'ya'yanta ta sangarta su ba sa iya cin abincin sayarwa bai birgesu sun fi jin dadin wanda za'a shirya mai rai da motsi a gida babu ma kamar mai gidan da runbu Sahabi, ko bata shiga don mijinta da Sahabi to a yau babu mijinta na ta amma don Sahabi dole take kula da komi tamkar kullum. Haduwar mami da Sahabi da marece likis amma yi sallar mangarib a lokacin. Sahabi na gidan. anti Hadiza ma'ana diyarta ta fari 'yar kimanin shekara hudu da kanwarta mami mai shekaru biyu da rabi suka matsa mai sai ya kai su shan ice cream. To a yau babu yadda zai yi domin yafi sati biyu yana sa masu rai a kullum kuma aiki ne ke mai yawa, a son ransa ya koma gidansu inda hajiyarsa take wato a Dawaki road ya dauki wani sako da ya bada a nemo masa, sannan ya doshi gidansa da ke sullubawa road ya 6 gabatas da wasu ayyuka cikin kunfutas sa wanda yasan a kalla zai dauke shi fiyc da awa uku, to amma baya. son ya bar wa'annan gimbiyoyin biyu cikin kuke wato maama da mami ya mike ya Dauki mami ya ce, "oya saka takalmi muje maama",, a mota maama na tsaye tana waka, suka isa DIZZA harabar ta haske da fitilu masu hasken gaske, kai kace muna cikin yinin rana ne, sai matasa 'yan zamani ke ta karakaina a wajen. A dai dai inda Sahabi ya aje motarsa nan ne mami Abduljalal ta faka ta ta, Sahabi na biye su maama na gaba suna tafiya gudu - gudu hamzari - hamzari. Mami Abduljalal na zaune bisa kujera tana jiran a sallami wasu cunkoson 'yan biki da suka zo shan ice cream, jikinta a zahiri sanye take da irin doguwar rigar nan jallabiya mai ruwan anta an yi mata ado da 'yan kananan duwatsu tun daga sama har kasa, ta yane kanta da gylen jallabiyar amma Kasan jallabiyar siket ne da riga irin matsastsun nan, Mami doguwa ce amma siririya fara sol 'yar kabilar shuwa - arab, mahaifiyarta shuwa-arab ce, mahaifinta kuma haifaffan Maiduguri, don haka mai karatu na bar ka ka fassarawa kan ka irin kyau na mami komi nata dai na innar ta ne, idannunta kawai sun isa daukar hankali, mahaifinta sai da ya kai matsayin M.D na Bank of the North kafin ya yi ritaya. A koda yaushe kunnen mami manne ya ke da wani dan mitsitsin dan kunnen dayiman inda duk ta juya yana sa kin wani haske mai kashe ido, a hannunta kuwa ta zuba zabba uku na dayiman a 7 2 tsakiya sai zinari guda biyu, sannan tana yawan canza 'yan hannu wato bangus kenan a kullum ka ga mami kai ka yi zaton jikar King Fahad ce na Saudiya. Rungume a hannunta G.S.M ce da wani katon novel na Barbara Taylor mai suna (To be the best.) Sahabi ya karanci littatafan soyayya iri - iri а lokacin yana turai amma bai taba ganin macen da aka siffanta ba ta siffantu sosai kamar mami Abduljalal, duk wani tunaninsa da addu'arsa yana ganin ta dace akan mami, a lokaci guda itama mami ta so shi a ranta ina ace, wannan gay din bai yi aure ba kila da ta so shi har sun yi aure tare to amma ganin maama da mami ranta ya bata ya yi aure har ma ga 'ya'yansa nan. Tsayin lokaci Sahabi na tsaye ya mutu murus da son mami yayin da ita kuma mami tana zaune a kujera ta mutu mus da son Sahabi har bata son azo kan ta don kada su rabu da Sahabi. Kowanne ya yi nisa da tunanin dan uwansa can Sahabi ya hango mami 'yar diyar Hadiza na kutsawa cikin mutane ya yi sauri ya kwalla mata kira ya ce "MAMI" anan take ta rugo zuwa gare sa tana dariya ya yin da mami Abduljalal itama ta yi zambur ta mike ta amsa "Na'am" jama'a da yawa suka rinka yi masu dariya ita ma ta ji nauyi da kunya ta dan rangwadar da kai gefe guda tana murmushi, shi ma cikin murmushin ya rinka bata hakuri ya ce, "please I'm sorry, ki yi hakuri sunan ku ne ya zo daya", ta dube shi ido cikin ido ta ce, kada ka damu ance suna linzami, sunan ne ya zo daya", kawai sai suka dan shafa'a suka zubawa junan su na tsayin lokaci mami ce ta soma komawa ta 8 a 1a C a f a ka a ya ce in ir a zauna, tunani ya rinka shigarsa yanzu idan har mimi ta tafi bai san komi daga gare ta ba an ya ba zai shiga ruda ni ba? Kuma ma shin kamar yarinya irin mami ta raue tsayayyen miji a hannu? Gabansa ya fadı ras! Amma an ce faduwar gaba asarar namiji! Yana rungume da mami sannan yana rike da hannun maama ya matsa kusa da mami Abduljalal ya fanyi gyaran murya ya ce, "Ranki shi dade don Allah ko akwai credit a wayarki ki ban aro ina son zan yi ma maman yaran nan waya nan da nan kishi ya sauka a zuciyar mami, wai ma don rainin wayo da wayarta zai baiwa matarsa hakuri akan ya dade bai dawo gida ba bayan tare da 'ya'yanta ya ke", sai kawai ta sha bula ta cc "Babu credit" anan ne kuma maama ta yi caraf ta ce "Uncle wayar mamanmu ta lalace tana wajen gyara itama da ta Babanmu take anfani" Sahabi ya dan sha mur maama ta 6ata mai lamari anan take ya canza shawara ya ce, okey! Okey!! Haka ne, ba ni don Allah mami ina da card cikin mota zan saka maki ina son na yi ma hajiya ta domin zata ga ban je cin dina da wuri ba yau", ya dan langabewa mami kai, ita ko tuni mami dadl ya lullube ta da ta gano su maama ba 'ya'yansa ba ne lalle single ne kenan, yarinyar ta kira sa uncle wato kawunta sannan ta yi zan cen maman ta da Babanta, lalle shi kanin iyayonta nc. Mami Abduljalal ta yi murmushi ta mika masa wayar ta ya bata ajiya yaran ya nufi cikin motar sa, ya bude wayar mami ya gano lambar wayar ya zuba cikin tashi wayar sannan ya soma dan binciken text 9 din da aka aiko mata ya soma cin karo da na kawayc Kawaye kawaye can na saurayi gabansa ya fadl dam! Amma ya tsaya haka nan tabbas ya san bai yi dai dai ba ya ga sirrin ta sai dai kuma ya zaku ya san matsayinsa. Ya cimmata har ta gama cinikin ta ta sayi na ta ta zuba a ledar kamfanin sannan ta sai ma su maama kowannce roba uku uku ta yi ma kowacce ta ta ledar, ya dubi mami tsakiyar ido ya sakar mata da annurin kauna tare da cikakkar fara'a ya ce, "Amma na goda, nawa ne bill din ku gaba daya? Ta ce, haba kada ka damu ko babu komi (Name sake) dina na saya mawa, yayi godiya kwarai suka nufi motocinsu. Mami ta soma tafiya, Sahabi na biye da ita a baya, har sai da ta yi kwanar shiga anguwar su wato Sultan Road, sannan Sahabi ya matsa mata hon ita ma ta matso mashi alamun yin bankwana. Duk kwadayin mami a rannan cokali uku tasha na ice cream ta baiwa Rannata sauran. Gidansu mami babban gida ne sama da kasa dakauna bila adadi sannan daga can gefe an yi wani sassan domin maza wa'anda kan zo daga gida maiduguri. lyayan Mami Abduljalal da iyalan tsantsa 'yan boko ne irin 'yan bokon zamanin nan ma'ana an sakarwa 'ya'ya tarbiyarsu da rayuwarsu duk tana hannun su an basu cikakken enci wanda ya zaır gurbatace. Ma wuyaci ne Hajiya iyana ta yi wata daya cur zaune da iyalanta daga yau, tana waccan Rasar sai ka ji gobe ace tana waccan jihar har - kar kasuwancin ta, kudi kam ba mu san wanda iyana ke 10 son ta yi ba, ita kadaice wajen M.D Abduljalal sai 'ya'yansu shidda mata hudu maza biyu mami ce babba sai Hawwa Sa'adat, Hasan da Husaina sai auta Sagir. 'Abduljalal da iyana sun yi yawo cikin kasar nan da dama ta fannin aiki amma kusan rayuwarsu a kaduna suka fi yin ta, tana rikon kannan ta da kannan mijinta maza da mata don haka a kullum gidansu cike ya ke da jama'a. mami Abduljalal, ta kare karatunta a jami'ar Abuja ta karanci fannin turanci ne zallah yanzu shekaraunta ashirin da biyu cif, mahaifinta ya samar mata aiki a Schoolarship board anan Kaduna yau wata uku kenan da soma aikin ta suka hadu da Sahabi. Ko da ta dawo gida ta aje motar ta a harabar gidansu ta wurgama daya daga cikin samarin gidan 'yan makullanta ta ce, don Allah an jima ka yi man fakin din ta a runfa" ya ce, ba za ki sake fita ba ne? ta duba agogo ta ce, "yau zan yi bacci da wuri gobe akwai daliban da za mu yi ma intabiyu a ofis yanzu ko tara da rabi ta yi", ya ce "Aminiyarki ko yanzu ta koma gida ta so ganin ki sosai, ta ce komi dare ki je tana son ganinki, maryam Bishir ba", mami ta jefar da hannu gefe daya ta ce, "manta da maryam don Allah akwai abunda ke gaba na", ta kutsa kai cikin babban falon da su kan yi dandali mata da samari ana sharholiya sai akai asuba suna kallon tasoshin Kasashen turai babu mai kallonsu balle ya ce masu don me? Ta dan zauna jim ta sha ice cream cokali uku ta baiwa kannan ta sauran ta mike ta haye sama 11 Σ zuwa dasinta, ta zauna bakin gado ta yi tagumi tana turin irin tsayi da kyan tsari na Sahabi, dogo ne sosai har rankwafa ya keyi fadin kirjinsa yasa ake ganin kamar Katon namiji ne amma kuma dan siriri he idan ya tube, irin mazan da akc kira mai kashı daya zaki, haskensa kadaran kadaham babu mamaki ko anga 'ya'ya san sun yi fari domin yana yaro fari ne sol, bai faye manyan ido ba amma akwai dogon hanci, da baki mai fadī da siraran la66a, akwai majinar gwamna a kasan hancinsa dalilin kenan idan yasa tabarau ya kan fita daba da sauran matasa shigar kayansa akodayaushe shirt da wando sai ko kaftan da wando Abubakar Sahabi kenan. Mami ta janye kafafunta cikin takalmanta ta yi luw da idanunta lalle ta san ta yi samari kala kala da 'yan arzikI da 'ya'yan banza taso wa'anda ta so ta bar su a lokacin da ta ga dama, amma fa Sahabi kila daban ya ke a zuciyar ta da sauran maza, na farko dai ta san zai yi tsoron Allah sannan da gani ya ilimintu da ilmin zamani, haka nan ta san zai iya nunawa mace so, tabbas irin dai namijin da take jira, ada har ta hakura da auren Safiyan dan tsohon ministan sufira amma a Karshe dole tasa aka warware baikon saboda bai da abubuwan da take son ta samu jikin mijinta. Ta yi bacci sama sama can ta farka tunanin Sahabi ya sake dawo mata lalle ada ba so ta yi ba shirme ne da safe tunanin ne dai da zullumi ke manne da ita, har ta je ofis komi cikin sanyin jiki take aiwataswa. A wannan rana 'yan gidansu sun ga canji amma tunda ba rashin lafiya take yi ba babu wanda 12 ya kula, la asar sakaliya ne ta yanke shawarar ta koma Dizza gidan ice cream ko Allah yasa ta yi sa'a shi ma ya dawo don ya duba ta, amma tunda ta isa harabar ta rinka wurga ido ko zata ga motarsa Accura legend mai ruwan bula mai haske tun daga nan ta sare rashin ganin ko mai shigen motarsa, ta shiga a yau ma babu wani cinkoso, don haka ta sai ma Kannan maryam don ta rage radadin zuciyarta amma abun haushi ta samu an ce maryam ta nufi Bauchi yau da azuhur. Sai da akai kwana uku sannan mami ta soma neman hanyar da zata manta da Sahabi. Amma shi ko can a wajen Sahabi ya fi mami kidima amma ya jure ya kI sanarwa da 'yan uwansa, sai da ya yi shirin bacci ya nemi shawara a wajen sarki Allah, ya yi alwala mai kyau ya gabatas da karatun alqur'an tamkar yadda ya saba, sannan ya zauna bakin gadonsa ya karanto sabbi sau daya tak, ya tofa dai dai inda zai sa kan sa bisa filo ya rokI Allah ya nuna mai alhairin mami, ko sharrinta. Haka ya rinka yi har tsawon kwana uku, tun ranar da ya dora idonsa akan ta, wannan istahara ce in gagtatta ga duk mutum da ya dayayyta Allah. Sahabi ya yi farin ciki da yadda ya rinka ganinsa da mami a mafarki amma zakwadI da foki sai ya dan ja mai birki ya rinka ganin ko son da ya ke wa mami ne mai yawa har shi yasa ya ke ganin komi a mafarki, sai kawai ya nufi wajen mallam Adamu na anguwan sarki wajensa ya ke karin karatu duk asabat da lahadi kuma aminin mahaifinsu ne. ya gaya mai komi, 13 소 C. sannan yace, ya ka gani a mafarkin? Sahabi ya ce, A ranar farko na ganni da mami a wani katon gida ta rabe ni ma na rabe sai yara kanana ke ta wasa a gidan, a rana ta biyu, mami na kwance a gado mai kyau ni ina ta fama da wasu yara, amma ban san yaran ko na wane ne ba, sai a daren jiya na ganni ina sauka a wani bene har na zo matakalar karshe sai mami ta miko man wani yaro". Mallam Adamu ya yi shiru yana nazari sannan ya ce, To Sahabi kamar dai kullun yadda na sha ga ya maka al'amarin ubangiji babu wanda ya san gaibu, idan ma mun ce ga abunda zai kasance an jima wallahi mun yi karya saboda shi ubangiji mai canza al'amuransa ne a ko wane lokaci, shi ne anfanin yawaita addu'a, kaga idan sharri ya zo za'a iya mai da shi alhairi. Tabbas istahararka an nuna mayuwaci ne ba'a yi aurenku da ita ba amma kuma abun tsoron shi ne renon kananan yara abu ne mai wuya balle ga namiji gaskiya ganin karamin yaro a istahara yana nuna mana fitinu saboda yara kanana fitina gare su, amma ba lalle ba ne ace za'a sami fitinu a tsakanin zamanka da mami, ta yiwu ko da 'yan uwanta zaka rinka rigima ko ita ta yi da na

Chapter 1 of 13