Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
zai yiwu ace ya tsaya can kasar wa'anda suka shirya 559 wasan to amma ina a yadda duniya ta lalace, sai addu'a wanda zai iya kwabawa iyalinsa ya kwaба. Kiristi ta leko tace, Anti abincin ya dafu mamit ace, To ta je sito kawai set din kuloli masu guda uku ta dauko ta wanke ta zuba abincin ita Mami da Sahabi sannan ta zubawa maigadi ta kai mashit a kuma kai ma Ya'u ko ta kira sa ya dauka. Kiristi ta yi yadda aka cc. Mai gida Sahabi ya kuke aiki ya je bisa wa'annan in jina ya koma bisa kumfuta har dai can ya ji kamar zai fadi ya shafa cikinsa yinwa ta ci kariinsa ya duba agogo biyar ma ta shige, yace, "Wai gara aje gida ko ba don abinci ba don aga kykakyawar amarya ma ai ya dace ya kulle komi sai gida, Mami na tsaye wajen takalar shiga falonsu a harabar gidansu Sahabi ya yi hon maigadi ya yi sauri ya bude get, suka yi ido hudu da ita ta daga mai hannu shima ya karaya kan motarsa sannan ya sun baci tafin hannunsa ya daga mata, tayi irin murmushin nan najin dadi ta sunne kanta cikin kafadunta alamun jin kunya, ya fito ya dauko wata leda a bayan motar sai da ya kusan isa gare ta sannan mami ta karasa a hankali ta taryeshi ya bude hannun sa na dama, Mami ta shiga cikin hakarkarin sa, suka shiga cikin gida kowannne su cike fal da fara'a, kai tsaye dakin baccin su suka shiga Mami tayi tsaye tana dubarsa ta rungume hannayneta bisa kiji shi kuma yana kokarin fitas da kayan shi ya fiddow ata jallabiya ya zuba, ya isa gare ta ya yi mata yanw asanni, ta gamsu sannan yace, raka ni falo man na ci 60 abinci ko na sami kuzarin kula ki sosai, hala har kin ci na ki? Tace, Na zauna ina jiranka mu je mu ci, ya rike hannunta suna tafe yana tsokanarta da zance, yace, "Mc ki ka dafa mana? Tace, gaskiya Kiristi na baiwa umarni ta dafa mana ta dafa shinkafa da dankali an kuma yi ma farfesu. Yace, to bai dai so ba, amma ya danne sanin kan shi ne idan yace, ta kawo kayan lanbu da ruwa, Kiristi zata kwalawa kira ta ce ta kawo don haka sai ya tsaya gaban firij ya debo masu. Foodflask na farko da ya soma budewa na shinkafa ne, sai dai ba iya banbancewa shin faten dankali da shinkafa ne ko mnce ne? sun hadu sun narke gaba daya ba'a iya banbance shinkafa balle dankalin, a karo na farko Sahabi yayi mata tsawa yace, Mami mnce ne wanan? Ta sha mur tace, me idonka ya gane maka shinkafa ce! Ya bude filas na miya mai yayi mai anbaliya ya zubo, nan ma ya ja tsaki ya bude filas din farfesu babu mararraba da miyar ja irin miyar nan wadda tumatur zalla bai nuna ba, ya ja tsaki, ya tsaya ya yi shiru, ya ce, an ba masu gadi? Kan Mami a sadde tace, 'Eh' yace, to a kara masu wanan idan za su iya ci, ya dauki kayan lanbu ya koma falo ya zauna bisa doguwar kujera ya murda talabijin zuwa ga tashar N.T.A Kaduna, ya soma cin ayaba sannan gwanda ya koma kan tufa ya jawo lemo, duk bai samu natsuwa ba, ransa na mai zafi, ko me kuma zai yi don dai ya zauna lafiya da Mami, lallashin ta dai zaic ig aba har Allah ya sa ta amince ya ncmo mai koya mata girki kunya ma kawai ta ishe 61 shi ta maigadi da Ya'u ace wai daga iyalansa aka fiddo wannan kwamacalar. Mami tuni ta koma dakin baccinsu, shi ko daga falo bai zarce ko ina ba sai masallaci, aka sallaci mangarib da shi sai ya jawo alkur'ani ya soma karantawa bai tsaya ba har sai da akai issha sannan ya tsaya ya yi kirari ga sarki Allah a karshe ya roki Ubangiji ya kawo mai mafita game da al'amarin aurmesa. Ya koma gida falon gidan zuwa kicin ko ina tsit itama Kiristi jikin yayi san yi ganin abincinta ko Ya'u ya kasa ci sai maigadi ya zuba aleda zai kaiwa almajirai a can anguwarsu Judunwa. Sahabi ya shiga dakin baccinsu yace, assalamu alaikum Mami da ke tsaye gindin madubi tana daura zani ta amsa ba tare da ta dube sa ba, super holland mai ruwan cincin bale ta zuba dinkin ya kame ta tsantsan, yace, "E ye 'yar gaye kenan har kin yi wanka, ni ma ki ban minti goma yanzu zan fito, ba ta dai tsinka ba, tana gama wa ta mide akan kujerar da ke cikin dakin baccinsu wato (Lazy man) ta soma karanta wani novel din ta na turanci Sahabi ya fito yana shirinsa tare da dan fitonsa da 'yar waka, ya saka kananan kaya, ya je gaban ta ya zauna kusa da ita ya ja mata hanci, ta ture hannunsa, ya ce "Haba my dear me zai bata mana rai bayan mun mallakawa junan mu zukatanmu, don Allah kada ki yadda wani dan kankanin lamari wanda za mu iya maganinsa ya tsaya mana a gaba har. ya hana mu cin moriyar kuruciyarmu, yanzu me kike so na yi kin san dai ba zan yadda ba ki kwana da yinwa? Mami ta lumshe ido zan cen yayi mata dadi 62 sosai can tace, Wai mnee ne amfanin irin su Mr. Biggs da su Bkaers Dclight? Ka baiwa Ya'u mana yanzu zai kawo mana abunda ranmu ke so, a gaskiya zan ga ya ma ni da man su ke dauke man lalurar yinwa ta, in dai abinci ne matsalarmu wannan ba dalili ba ne tunda ba a kauye mu ke rayiwa ba". Yace, "Su Ya'u fa da maigadi? Tace Kiristi ta rinka dafa masu har Allah yasa ta iya yace, kin kawo shawara amma tashi mu je da kan mu mu sawo goben mun aiki Ya'u ta dauko gyale wanda ya dace da alanfarta ta yana a kafada amotarta akai tafiyar. A Mr. Biggs Mami ta yi ma kanta hade-hadne N500 na sahabi ma hakan su ka yi take away, sai suka sayi kke da biredi don kalacin safe daga nan suka tsaya a (Farm Fesh) suka sayi madara mai san yi da gardi kamar kala uku farm fresh Sahabi yasa aka kawo mai madara kindirmo mai zaki kofi daya, ya kwankwade sanyin harabar da san yin nonon ya rinka yi mai dadi a gabobin jikinsa. Sun dawo gida aka zauna Mami cike da nishadi suka ci suka sha madara ita kam ta koshi sosai amma shi ango ba dai haka aka hore sa ba, ammai horo da abincin gida lafiyayya. Amma kaunar Mami a ransa ya hana ya ga aibin komi, suka kwanta da wuri don su mori amarcin su a kuma tashi da wuri domin zuwa aiki. Kawai wani hutun karshen mkao su Mami da Maama 'ya'yan Anti Hadiza suka matsa akai su yini gidan Uncle Sahabi, Anti Hadiza tasa direbansu ya kai su, tunda suka je. sai kallo suke yi da Mami irin kallace-kallacneta da ta saba, sai dai ta sa kiristi ta 63 debo masu juice a sito har karfe uku suna famar shan juice har sai da Kiristi ta gama jalof din shinkafa, Mami tace a zubowa su Maama, ga dai yinwa ta matsawa yara sannan ga abinci an kawo sun kasa ci, na farko kawai tsananin barkono ga masifar gishiri ga mai na shake ka, yaran nan suka kasa cin ko cokali biyu suka aje. Ganin haka yasa Mami ta yi ma Sahabi waya a ofis ta ce, karfe nawa zai dawo gida? Ya ce a gaskiya ba lokaci tace idan ka tashi ka zoda abin cin ka, ni zan aiki Ya'u ya sawo mana nida su Maama, ya ce, 'To' ta shiga fakin baccinsu ma ajiyar kudin Sahabi ta debo dubu daya ta aika aka yo masu take away ita da su Maama. Har su Maama direbansu ya zo daukarsu amma Sahabi bai dawo ba, biskit da lemon gwangwani ta zuba masu a leda. A wanan dare Mami 'yar gidan Anti Hadiza kwana ta yi zawo, nan da nan hadiza ta yi anfani da aikinta ta tambayi yaranta dame-dame suka ci a gidan uncle sahabi su ka gaya mata tsab a nan ta gano iallar da Mami ta samu ta bata allurai da magani zawo ya tsaya, babu zancen zuwa makaranta da safe, abubuwa suka damu Anti Hadiza amma bata son yi ma Hajiyarsu maganar gudun kada al'amura su dagule, daga irin haka ne rigima kan shiga tsakanin dangin miji da matar dan uwa, amma kuma ta bar gidan dan uwanta ana sayen abincin, wannan ba mutuncin su bane, dole zata sami hanyar warware wannan matsalar. Wannan kenan, watan su mami uku cur da aure jijiyoyi da katon kai su suka bayyana tattare da 64 Sahabi, duk wanda ya san Sahabi kafin ya yi aure da farkon watan sa na aure idan ya gan shi yanzu bai yadda shi ne, ya zama jijiya ga wani irin tsufa ya lullubesa duk na sanadiyar rashin more aure ne, yinwa ce dare da rana, wai ya auro 'yar hutu, idan yana ofis bai da hutu aiki ne mai yawa a gabansa domin yayi hutun jkai da kaya aka ne, idan yana gida yana famar tarairayar Mami, haka dai tashi kaddarar ta zo mái sai addu'a. Sa'adiya ta yi ma Anti Hadiza waya, bayan sun gaisa da 'yar hirarsu tace Anti bawai zan cne gulma ba ko tsegumi shin yaushe rabonki da ganin Sahabi? Anti Hadiza ta ce, yau za'a yi sati uku kenan ko? Sa'adiya tace, kune likitoci ya dace ki bincikesa wannan irin jijiyoyi! Labaran da na ke ji wajen yara abin ba dadin ji, Hadiza ta ce, Ai ni yara na har zawo suka yi a dalilin sakarcin da kae yi a gidan Sahabi don haka an dai na kai su, zan bincika don kada gidan ya lalace har ya zamanto bai gyaruwa, kin ga ba za mu so hakan ba, domin mun fi kowa farin ciki ace Sahabi ya zauna lafiya da matarsa, ko ba komi shi ne babba da a gidanmu kuma ya auri macen da ya ke so baida ce ace ya sami tangarda ba hakan na iya sa shi ya zama rudadde game da kowacce irin mace. Wanshekare daga ofis Anti Hadiza ta yi ma Sahabi waya,t ace tana son ganinsa, yace 'Me zai hana su zo da daddare shi da Mama? Tace, Ina son ganin ka ni da kai sirri ne, yace ina nan zuwa idan mun yi breka ya iske ta a ofis din ta, ta kulle don kada a dame su ta dauko kula da farantai guda biyu 65 tace, To bissimillah ta soma zuba masu wainar shinkafa mai dadin gaske irin wainar 'yan Bauchi da miyar kaji yadda taga Sahabi ya shaga yana cin wainar sai ta zuba guda uku kacal ta bar masa sauran, rabon Sahabi da ya ci abinci irin haka har ya soma mantawa, Anti Hadiza ta rinda tausayinsa cikin rintsi kwalla ta zo mata ta matse, wai Sahabin da Hajiyar su ke shiryawa abinci kala-kala fiye da na kowa a gidansu yau shi ne ya lalace da sayen abinci? Sai da ya gama ya bude dan mitsitsin firig na ofis din ta ya tsiyayi lemon ginger ya sha. Yace, 'To Anti lafiya kae nemana? Ya duba agogo yace, kin san irin, aikina tsauri ne da shi,t ace, 'Eh haka ne, ka yi gaskiya ama wai Sahabi dan gata kamar kai da Mami a garin Kaduna me ya yi mkau zafi da ba za ku dafa abinda ranku ke so ba sai kun je wani Mr Biggs can kullan kuna yawon neman abinci kamar gwauraye, ya yi shiru bai son zancen gidansa da kowa tunda dai shike son mami dole ya jure da kowanne iri ne halin ta" yace, Ba haka ba ne anti, gaba daya aiki mu ke zuwa, kuma Mami da ni muna da kyama, duk da na san mahaifiya ta ma aikin ta ke yi amma kada ki manta kowa da irin halinsa, ina hakuri ne a hankali har ta saba da hidimar aure Anti hadiza tace, 'Amma kuma an ce kara tun yana dan ye kae lankwasasa idan ya yi gauri to...'. Sun yi shiru na tsayin lokutta, sanan yace, yanzu me ye abun yi? Tace, Wai girkin ne ba ta iya ba, koko kuyya gare ta? Ya ce, ina jin duka tace, idan haka ne dole Aisha ko Hafsat ta dawo gidan ka ta koyar da ita da 'yar aikin 66 ta ku Kiristi na ko wata daya ne, ita Mamin sai ta rinka aje Hafsat din makaranta da safe yace 'E to ana iya yin hakan, amma bana son kuma Hajiya ta san wannan matsalar' tace, ka da ka damu na san dabarar da zan yi ba tare da Hajiyar ta san manufar mu ba, yace, 'Ni baban bakin cikin ma shi ne wannan Kirsitin irin arnan nan ne masu warin tsiya wallahi idan ta shigo falo kawo wani abu sai falon ya fi mintia shirin yana warin ta, yanzu kwata-kwata bana iya shiga kicin saboda ita, anti Hadiza tace, Ai daman illar irin wa'annan arnan kenan, to babu wankan haila balle wankan janaba sannan ga warin kashi ga girman daji cikin kazanta, abinda za ka yi shi ne Mamin zaka matsa mawa ta sawo mata roll on masu kyau tasa ta yi wanka da sabulu mai kamshi sau uku a rana tana shafa (rollon) to lalle za ku sami sauki ya duba agogo ya mike yace, 'To shikenan zan jaraba sannan ina sauraronku. Kamar yadda Anti hadiza ta tsara an nunawa Hajiya ne ana son Hafsat ta je ta taya Mami zama kila juna biyu gareta, amma fa nace kila, wannan ko shi hajiya ke son ji don haka nan da nan ta amince, tunda Hafsat ta je ta shirya kayanta a dakin da ke kusa da falo, ta shiga kicin ta soma da Kiristi inda ta ga an girka shinkafa da miya a shashance ta koya ma Kirsit yadda kae miya da dafa shinkafa, ta sanar da ita ta rinka aunawa da wani jan kofi haka nan man gyada dole ki auna don kada ya yi yawa, ki dai na hada manja da mangyada, kowanne kawai inda ya ke da daraja, Kiristi da ykae tana son aikin ta tsaya sosai 67 ta saurari Hafsat abinda bata gane ba ta yi tambaya. Da yamma ne tace, ma Mami, Anti Mami yau dai da daddare ki zo mu yi ma yaya Sahabi Funkasu ko nafulawa ne, domin idan muka kwaßa shi da yis awa daya ta isa ya tashi sosai, Mami ta yi murmushi ta ce ki bari sai gobe, sai hafsat cikin wayon ta da iya hila tace, to Anti mu yi biredi mana, wani iri ne da Hajiya ta koya man dadin tsiya wallahi, kin ga breadmeker din ki babba ce, iya kar mu mu zuba komi da komi ita zata kwaba sannan ta gasa biredin ta kuma kashe duk da kanta, a nan dai hafsat ta hilan ce Mami tas, har ta jata suka fita shofin na kananan kayan girke- girke baking powder, Yis, Filawa kori, theme, da dai abubuwa kanana da dama, suna kicin har misalin karfe goma na dare Mami dai bata saka hannu daga Kiristi sai Hafsat ke ta girki su dafa wannan su kashe wannan a kalla a daren nan sun yi girki ya kai kashi biyar dadi da murma suka lullube Sahabi yana zaune a falo shi da gimbiyar sai ya rinka kwallwa Hafsat kira ta kawo wannan yace ta kawo wannan ya rinka yi mata fara'a fiye da kullum, wanan ya soma batawa Mami rai wai me kae nufi ma shin da zuwan Hafsat har ta kama daki ta zuba kaya, kuma me yasa Hajiya ta dame ta da waya kullun tana gaishe ta ta na tambayarta shin babu dai wani abu ko? Da safe kamar jiya hafsat ce abin kiran sahabi bakinsa a bude fuskan nan cike da fara'a komi ita ta iya ita ya ke tambaya, ya soma cin abinci wanda ya saba ada can, sun kare kalaci Mami ta koma dakin baccinsu sahabi ya bi bayanta, ta rungume hannu bisa 68 kirji ta ke fuska tace, 'Me ke faruwa ne, na ga wani canji wanda ba haka mu kai da kai ba, yau kwanan Hafsat nawa? Wannan iya yin da sanaben da take yi na manee? Ya yi shiru amma ta soma kai shi iya wuya fa, ya ce, 'Na lura Mami gaskiya ce dai ba kya so, mnee laifin Hafsat, aumeki fa take rayawa, sau nawa 'ya'yan su Anti Hadiza na zuwa nan su yini da yinwa don sun taimaka maki cikin sirri an kawo Hafsat komi ya daidaitu sai ya zama abin jin zafi? Tace, su wa suka taimaka man? Yace, Ba wata ba ce Antin ki ce Hadiza", ta ce, What! Wacece haka Hadiza na ke aure ko kai, ita zata tsara man gidana ko kai, waye ya yi mata katsalandan a gidanta? Sai ta jira sai ranar da na haifa 'ya'ya idan na bar 'ya'yana suka je gilan ta ta hana su abinci, koko ta taba ganin kwanona gidan ta ina rokon abinci ko ina rokon maka? To a bar ni na yi rayuwar da na ke so, iyaynea da suka kawo ni duniya basu tkaura man ba, babu mai tkaurani. Yana ta kallonta ashe dai aure is not easy, tafdijam! Mamin da ya ke so kenan ta ki fahintarsa tow acece zata iya fahimtarsa? Yace, "look Mami ofis za mu mun ma riga mun makara, iki yi hakuri sai mun dawo zan fahimtar da ke, ta ja tsaki tsuw, tace, zan cen ka ke so na riga na yanke magana, bana zama da Hafsat 'yar sirrin Hadiza, wai har ka iya zama da 'yan uwanka ana tsegumi na, to ban yin abinda su ke so, tsarin dana girma da shi shi na ke so, idan na mutu su auro ma wata, ta bude kofa ta fice, ta je da 69 kan ta ta tayas da motar ta bata ko kira Hafsat ba ta yi tafiyarta, sai shi Sahabin ya aje Hafsat makaranta. A ofis sau biyu Sahabi na aikawa mami text babu amsa, ya yi waya tana ganin lambarsa ce ta kashe, yau ma kin zama fos din ta yi ta koma nan da nan ta umarci kiristi ta kwashe mata kayanta tsab daga babban dakinsu na bacci ita da Sahabi ta yi nata dakin da ban ta shiryo abincinta daga Bakers Delight ta yi kwance a daki tana kallonta tana cin abincin ta, itama Hafsat da ta dawo ta shiga kicin ta shirya abinci mai kyauta ci nata ta aje wa su Sahabi na su a tebir. Shima ya dawo ya ga canjin da dakinsu ya samu hankalinsa kwarai ya tashi, amma dai ya tuna shi ne mai gida shi ya kawo Mami dole yayi hakuri da ita, haka nan kuma dolensa ne ya daidaita tsakaninsu Hafsat domin tun zuwan Hafsat ya soma dawo wa hayyacinsa, wata kasala da yawan jin jiri ya rage ji yanzu. Ya doshi dakin da Mami ta zabarwa kanta, ya murda ya shiga ba tare da ya yi sallama ba haka nan fuskarsa ma babu wani annuri balle ayi zaton fara'a. Ta dube sa kasa da sama ta mayas da fuskarta bisa kawatin T.V yace, Mami kenan! Yanzu ke ce za ki man haka ko to manee abun burgewa don kin raba mana dakida gani sai ke agida, ba ni fa da wadda tafi kusa da ni kamar ki a yanzu, tace, don Allah bana son zakin baki, ka je ku yi hidimarku da 'yan uwanka, ka bi shawararsu ai sun fi ni kusa da kai, ka manta ne? ya dan kada kai yayi murmushin ta kaici yace, 'To zo mu je a ci abinci, sannan azo a zauna a yi maganar, ta 70 ce, Allah ya sawakc ai ni ba mayya ba ce, da za a tursasa man abunda ban so, idon ka baya gani ne ka duba mana ai ni na ci nawa, ina kuma tsammanin abinci duk abinci ne, in banda san iyawa na wasu mata, sahabi va ga dai Mami ta yi nisa dole ya fita ya je ya ci abin cinsa, bai so ko kusa ya hango Kiristi domin tana tayas mai da zuciya. Bayan ya dawo masallaci ne sallah isha'i, ya koma dakin da wai Mami tace ta zaba wanda shi har yanzu bai amince ba, dole ta koma yadda suka saba ya je ya zauna tana rike da wayarta tana aikawa da text, ita da aminiyar ta ne maryam suna shirmnesu ne can na tuna da, amma bata gaya mata halin da take ciki ba, ya fi minti goma sha biyar a zaune bata ce dashi uffan ba duk abinda yace bata amsawa can ta kare text din ta ta jawo remote na C.D din ta ta karo wakar da ke yi, yace, kin san wani abu Mami, gaskiya ya dace a yi wani abu akan kiristi din nan ta dan maida hankalin ta gare shi tana neman karin bayani, yacc, aiki da ki ka sata ta yi maki yau wallahi lokacin da na dawo na shiga dakin baccin mu, naji dakin ya dauki warinta wai ke warin kiristi baya damun ki'ne? Mami tayi shiru, eh ta san lalle kiristi na irin warin kashin nan to amma ina ruwan su da warin ta tun da ba zama falo ko daki daya su ke yi da ita ba, zuciyarta ada ta soma sauka amma kuma yanzu yana so ya kara jagula mata lissafi, tace yanzu kanta tsanar taku ta koma, in don ni ka kori kiristi a yau din nan, ba matsala,' yayi yar dariya yace, bazan cne kenan ba, ta tsagal galo masa tace, look Sahabi 71 kan iya bawa Hafsat duk ukon gidan nan bai daman ba, ni yanzu so na ke ka kyalc ni kayi hidimarka da Hafsat na yi hidimata ni kadai! Yace, ni so nakc ki taimakawa kiristi tinda ke take ma hidima, bana son nayi baki ki ce ta kawo ruwa ko lemo a falo, duk ta cika falon da wari zuciyata na tashi bana jin dadi a gaskiya, saboda haka ki debi kudi ki aika Hafsat ta sawo mata rollon da sabulai masu kyau kisa ta rinka yin wanka.sau uku a rana ina ganin kila mu sa mu saukinta ko? Mami ta galla mai harara tace, mc zai hana ka baiwa Hafsat kudin ta sawo kai kuma ka rinka shafa wa kiristin roll on din, sarkin iya yi,' ya bude baki yace wai ikon Allah! Haba Mami menene na zafi kewai daman can ba a zama ayi shawara da ke ne. har abada sai dai na bi shawararki amma ni a matsayina na mijin ki ban isa ince ayi ba ayi, haba Mami kiyi tunani nima fa mutum ne kuma namiji mai so ya nuna mutuncin gidansa a idon duniya, idan har ban yi shawara da ke ba to dawa zanyi, shin menene anfanin auren kuma mene ne amfanin da iyayenmu suka ba mu damar mu auri wa'anda ran mu ke so, ai don a zauna lafiya, wallahi a shirye na kc na yi maki duk abinda ranki ya ke so ba ni kuma da niyar na 6ata maki dai-dai da rana daya Mami' Ya dan tsaya a nan ya yi shiru amma ita Mamin ta kawar da fuskarta can gefe, zuwa can ya soma jin shehsekar kuka, Sahabi ya dafe kai ya tsananta da tunani yanzu me ye abun kuka anan? Abinda ya zo a zuciyar Sahabi shi ne duk yadda akai su mami haka nan suka girma kara zube, ba kwaba ba tsangwama. babu 72 wanda ya tsaya basu wata cikakkar tarbiya, kila ma daga su Anti Yesmin su Zainab sai kallon tashoshin turawa sune tarbiyarsu Mami a cikin gida, duk ma yadda akai su mami basu san ace masu a'a ba sai dai ace ch. Tirkashi yanzu shi ya zai yi kenan tunda shi dai Maki kadai ya ke so. kuma kwatakwata al'adunsu da tarbiyarsu tasha banban yaya kenan za ai wannan zama? Wa'annan sune tambayoyin da suka addabi Sahabi domin kansu ya soma daukar zafi. Ya ja dogon lumfashi a ransa ya karanta 'yar karamar addu'a ta neman saukin lamura. Ya mike ya je gare ta ya kamota ya doro bisa Kirjinsa ya soma lallashi a nan ma ya kwashi kusan awa daya kafin ya shawo kanta ta yi shiru, yace, "Tashi mu je dkai mu kwanta, ta ja tsaki ta ture shi tace, ina nan ba wani dakinka da zan sake shiga, yace, come on Mami please ki huce mana, an taba hushi da miji, hushin kuma da ba dalili? Ta mike ta shiga kewaye ta yi buros din bakin ta ta kuma wanke fuskarta saboda kukan da ta yi sannan ta shafa lotion din baccinta ta koma ta saka riga rbacci, ta kwanta abinta, Sahabi ya bita da kallo kawai shi ma y aje ya yo shirin bacci ya kulle ko ina na gidan ya tofe ko ina da addu'a sanan ya bi mami dakinta ya kwanta kusa da ita ya so ya yi zancen da ya ke jin zai sa ran Mami ya yi sanyi, to amma shi ma sai ya sami tasa zuciyart a cushewa da dacin rai, har ita mami ta sami bacci can ya juya ya dauko ta cka ya dora a jikinsa ya kai bakinsa daidai kunnneta ya rinka yi mata radar how murch he love her. a 73 Kullun dai kawai abinda Mami kan tsana game da Hafsat, zan cen wai ta koyi girki wanan ma bai taso ba bai cikin tsarinr ayiwar Mami, itama kanta kiristin ba komi ta iya ba in ban da jalof da doya da miya saui shinkafa da miya, to ba laihi ta koyi amfani da yawancin na'urorin Mami,s aboda tsanarlin yawan aiki su wankin Mami gyare-gyare, komi dai kiristi za ta yi, to itama Hafsat yanzu nauyin ya fara yi mata yawa saboda kannan Mami sun soma sarfatar gidan sahabi, ita kuma Hafsat tana tsananin karatun (Final year) din ta ne to sai Sahabi ya lura an mayas da Hafsat 'yar girki ita da Kiristi kullun tana kicin, bata da lokacin karatu kannne Mami agaban Sahabi suka ce, ta gasa masu mcat pie da ckae tace 'To' ya koma dakinsa da kunfutarsa yana aiki, sai kuma ga kawayne Mami har su biyar a nan kuma za su ci dina don haka Mami ta kutsa kai dakin Sahabi ta yi sallama ta bude dirowar

Chapter 5 of 13