Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Firig a kusurwar dakin ya isa wajen ya bude kayan marmari ne su tufa, ni'ibi, goba, lemo, ayaba, da mangoro, sannan ga wani hadadden ginger drink, ga juice nan kala-kala irin wa'anda Mami ke so, sahabi ya dauko ayaba ya bare daya ya soma ci sannan ya bare daya 44 ya je ya mikawa Mami ta amsa ta ci, itama ta nufi firig din ta tsiyayi juice ta sha ran ta ya yi mata san yi ta dubi Sahabi ta yi murmushi, ya yi hanzari ya je gare ta ya jawo ta ya rungume ta ce, wannan hidima da su Husna ke mana bai yi wa mu basu kunya mu shige a yau", yace, 'Yauwa my Mami ni ma abinda na gani kenan look duba jikin bangon kofa wani kati ne aka lika mana duk na murnan zuwanmu, amma fa ba zan so na tursasawa zuciyarki ba yadda ki ke so haka zan yi". A tsaye su ke tsakiyar fakin iskar A.C na kada su, Mami ta kwantar da kan ta bisa kafadarsa ta dama yayin da ta sakala hannayenta tsakiyar bayansa, ta ce, Bana iya canza ra'ayin su Husna da Usman a gaskiya sun tabbata masoya na kwarai". Sun dauki tsayin minti goma a tsaye suna gudanar da (love making) sannan ta janye tace "Ana fa jiranmu a falo", ya ce, Bayan ma jiran ba mu bayas da faralli ba, abinda za'a yi sai ki soma yin alwala ni kuma zan je nasa a kwaso mana kayan mu". Mami ta shiga kewaye ta tura kofa a bayan kofar an manna wani dan karamin kati mai dauke da rubuta da ruwan azurfa an rubuta, you are highly wellcomes with all our love, wato muna maku kykakyawar maraba a bisa dukan kaunarmu, muma fata zaman ku da mu zai dada zurfafa kauna da zumunci mai karfi a tsakaninmu amin. Dear Usman and Husna 45 Always yours Mami ta shafi katin da yatsunta alamun yabawa ta yi murmushi, sannan ta sakarwa jikinta ruwan shawa ya ratsa kwarin bayanta kuzari da sabon karfi ya rinka shigarta, ta dade tana shekawa jikinta ruwa sannan ta zare fant din ta, dan kanfai ta aje shi a wajen wanke baki (sink) ta yi alwala ta dauko sabon tawul ful wanda Husna ta aje masu a kewayne ta tsane tsab, ta bude kofa ta fita ta samu Sahabi ya kammala shirya masu kaya, ya mike ya nufi kewaye, yana rufe kofar sai wannan katin ya kai ma idonsa gaisuwa ya karanta cike da jin dadi a ransa, sai ya dubi wajen (Sink) in da Mami ta bar dan kan fanta ba tare da ta wanke ba, ya yi murmushi yace, "Kai su Mami manya, ita dai raguwa ce, yasa sabulu ya wanke tas ya shanya mata a inda kae shanya kananan kaya a nan cikin kewayne. Abinda Sahabi ya ki yadda ya fahimtarwa kan sa shi ne, mami na daya daga cikin 'ya'yan hutu abin nufi shi ne gaba daya 'ya'yan iyana kowacce da 'yar aikinta, Mami har ta gama zaman gidansu bata iya wanke rigar nononta balle dan kanfanta inda ta yi wanka nan take barinsa mai aikinta zata kula da sauran bayani. Saboda haka yanzu tun da ta zo gidan sahabi shi ke wanke mata wa'annan abubuwan kao da yaushe yana ganin kamar ta gaji ne, bai san tsabagne rashin tarbiya ba ne. Turarukan da Mami ta ckaude suturar da jikinta da su, sun faye sanyin dadi ga azabar taushi irin na mata dai, na Sahabi kuwa mai karfin nan ne irin na maza masu karfin jini nan da nan gidan su Husna ya dauki kamshin dadi na tabbacin kawai amarya da 46 ango a gidan. A falon ma Usman da Husna sun yi wanka suma sun yi canji sun zuba tsadadda shadda mai maski mai ruwan cincinbale, Husna tace, Nasan dai a gajiye kuke mu zauna bisa kafet ne ko ko mu dai yi ta nasara jan fata mu haye bisa tebir? Mami tace "A zauna a kasan ya fi sakewa", Usman yace, Gimbiya kenan, wannan ko zkai bari mutumin nawa ya je ofis? Ta yi dariya ta ce, haba Usman kawai matar da zata hana miji zuwa ofis? Yace, Akan ki za a fara? Tace Dan Allah kar kai man addu'a, insha Allah ba zan hana ba". 'Yan aikin su Husna Mary da Sam suka shigo da kayan dina, duk wani abinci mai sa yawun dan adam ya gudana Husna ta aikata ma bakinta, an ci an sha, an yi sharholiyar ban dariya, ta yabawa Husna, akan iya tsare-tsarne girkin ta. To a haka dai sai da su Mama da Sahabi suka kwashe kwana uku a gidan su Husna, kuma duk girke-girken da kae ma su Mami da kulawa da kae ba su ta musaman Husna ke aiwatarwa, sai dai ta baiwa Mary 'yar aikin umami saboda Usman mutun ne mai tsabta ba zai iya cin abincin mai aiki bа. Sun rabu ana ta begen juna kwarai ko sun mori wa'annan kwankai uku cikin jin dadi da walwala sun kuma kara shakuwa Usman da Sahabi Mami da Husna, Usman ya so kwarai ya baiwa Sahabi shawarar zaman aure amma ya kasa ganin kwatakwata da fuskar da za'a yi ma sahabi zan cen iyalinsa duk wanda ya kwana daya da su ko ya wuni zungur da su zai gano Sahabi ke ma Mami biyayyar aure ba 1 ita Mami ba bayan a al'adarmu da addininmu matá aka sani da biyayyar aure, (Alah ya shirya mana da zuri'a) A yankari ma dai bata canza zani ba yadda rai ke so haka kac bata, Sahabi bai da lokacin kowa sai na mami illa dai duk bayan kwana biyu ya kan yi ma Hajiyarsa waya ya gayas da ita, idan ya yi gidansu mami sau daya ya taba samun iyana sai su Anti Zainab don haka ma bai cika yi ba ka'idar kullun itacc idan sun fita yawan yada rana suna zagaya leke dabbobi, ma'aikatan masu tsabtace dkaun yankari za su shiga dakin su mami a gyara masu ko ina fes, kawashe kayan da suka fidda aje a wanke, amma ban da kanfan Sahabi da hankicinsa da na Mami da rigunan nonon ta da siket din ta wa'annan kao da yaushe sahabi ke wankewa bai taba damuwa ba balle har ya zargi wani abu. A yau suna yawon yada rana la'asar lis, Sahabi ya kara matse ta a jikinsa ta dago kai ta dube ta ce "oh ni, so ka ke ne na shige cikin kirjin ka ne? ya ce, da zan iya mami da na manne ki a kirjina kila na samu gamsuwa, kin san ko dazun da na yi ma Hajiya ta waya cewa ta yi tun farko da mun sani kasashne turai na fita da ke yadda za mu ji dadin holewa sosai", Mami ta ce, Ni ka sani ko cikin kejin can ka kai ni in dai zan kasance tare da kai na tsayin awa ashirin da hudu cur walahi ban damu ba, bukatata ta biya", Sahabi ya dora labbansa tsakiyar kan Mami ya sumbaci gashinta sha'awa ta zo mai ya kara narkewa a jikinta kai ka ce ba a tsaye suke ba kuma a gaban 48 1 3 L kejin giwaye, sun dan yi nisa da wasu gungun family, amma gaskiya zaman amarcin sahabi da Mami ta bata shi ta rage masa kunya kashi biyar daga cikin ashirin gaban jama'a yanzu Sahabi yana iya hada jikinsa da na ta amma ada ina!. Kwanansu goma sha daya cif a yankari a ranar za su bar garin a Kaduna garin gwamna haka nan dole amarci zai ragu domin za'a koma aiki, Sahabi ya gama shirya masu kaya ya mikar da katon kawatunsu tsaye ya dauko karamin na kananan kayayykainsu shi ma ya kammala da shi ya aje kusa da inda ya aje babban, Mami ta kare wasannin motsa jiki ta zauna dirshan tana gwama lumfashinta tsane tace, "Sahabi ya amsa "yes my love ta ce 'Kai man alkawari za ka sake dawo wa da ni nan yankari bayan wata shidda kuma ka nuna so da kaunar da ka nuna man na wannan karon', Sahabi ya kyalkyale da dariya ya je ta bayan ta ya durkusa ya kwantar da hannayensa bisa wuyanta suka dira bisa kirjinta, yace, ko ni na yi irin wannan tunanin da asubar yau domin raina ya yi daci ganin shikenan mun bar wannan hutun! To amma shawarar da na yanke itace hutunmu na gaba warri za mu kawai wani waje mai kyau na hutawar masoya ire-irenmu insha Allah za ki so wajen, zan kai ki ta yi murmushi irin wanda ta saba yi mai idan ya yi mata wani abu na bajinta, ta mika mai la6banta ya yi abinda ya fi so. Kamar yadda suka saba duk tafiyarsu sai yamma suke isa,w annan din ma haka ne da mangarib lib suka isa gida. Sahabi ya yi ma Hajiyarsa waya, yace, 49 2 Hajiya isowar mu kenan Sallah kadai muka yi, tace, sannunku da sauka yaya Mami ya amsa lafiya lau Hajiya gata ma ku gaisa, (kan Mami na bisa cinyar Sahabi) don haka sai ya manna mata wayar a kunnneta, cikin shagwaßa tace, Hajiya ina wuni, yaya su hafsat? Ta amsa duk lafiya lau, to ga Sahabin hajiya, ya amsa yace, "Gobe za mu koma aiki Hajiya Hajiya tace, Ya son ranka! Kai ta zuwa hutu domin kan ka farau aurc? Ya yi dariya yace, ka ji hajiya don Allah, tace, 'To kuna son wani abu ne? ya ce, 'Eh Hajiya muna son abin ci, in da hali direbanku ya kawo mana, sannan azo da Hafsat saboda safe' hajiya ta ce, don nan da wata daya kada kasa ran Hafsa zata zo gidanku ta kwana saboda sun fara karatun jarabawa an kusa yi masu hutu, kuma direba na baya nan ya je Zariya tun jiya dibo mahaifinsa bai lafiya, amma me zai hana ka turo Ya'u ya amsar ma ku ya ce to shike nan ga shinan zuwa. Da za su kwanta ya bar wa Ya'u sallahun da safe ya je kara komawa gida zai amso masu kalaci. Hakan aka yi da safe Ya'u ya je ya amso masu kayan karya kumallo hadadde yadda dai Sahabi ya saba tun farkon rayiwarsa. Sai karfe goma sha biyu da 'yan mintoci suka sami tafiya ofis, Mami ce ta soma fitowa harabar gidansu sanye da wani lanfaya les mai ruwan gwaiduwar kwai ta lanfaye jikinta ruf, hannayenta kunshin aurenta ya fita sai na kunba da ta yima kanta ya yi kyau domin a cewar Sahabi yama fi son kunshin na kunbar ta, dahan din da ta watsa a 50 masangalin tsintsiyar hannunta guda tkawas ne sun kame ta, da zabba wa'anda suka shiga da awarwaronta sarkar da 'yan kunnne kirar dubai ce fnedal da 'yan makale, takalmi da jaka kanana sai tsadar tsiya. Ta tsaya tana rausaya yayin da Sahabi ya rinka baiwa motar ta wuta ya yi rubas ya fiddo mata ya kawo mata har inda take tsaye, motar ta Mami sabuwa ce ful a yau zata fara takata, wani aminin mahaifinta ya bata ita gudunmawar biki, motar na da masifar kyau irin masu mannewa bisa titin nan ce, kalarta mai ruwan ganye ce amman ganyne ya turu, sai wata munafukar walkiya irin ta daukar hankalin jama'a. wato 206 kenan, ya fito Mami ta shiga ya leka ta taga yace, "Ke Mami I'm jealous', ina kishi ta ce, 'Amma da ka ba ni kunya, bayan ka gama da komi nawa bana iya sarrafa zuciyata da kaunar kowa illa kai, haka nan bana sha'awar komi ni dai sai Sahibina Ab-kar! To wa kuma zan iya duba, in ma wani gaulan ya tsaya sha'awar Mamin Sahabi wallahi ya sha haushi. domin ni dai an san don rai daya aka halittani; ya shafi kumatun ta suna dariya yacc, "You should take care please, ta ce I promise you I will; sai da ya ga fitar ta sannan ya koma ya debo kayan tafiya ofis ya tayas da tashi motar ya tafi ya soma biya wa asibitin da Hajiyarsa take aiki, ya same ta a ofis sun dan gaggaisa yace, Hajiya na zo na roki arziki ina son a rinka kawo mana abinci na yamma da na rana kafin mu sami mai aiki, Hajiya ta yi shiru tace, Sahabi ba zan ko so na kawo ma ku abinci ba har iya lokacin da ku ke so, to amma matsalar itace kana 51 nufin ita mami ba za ta taba shiga kicin ba sai 'yar aiki in haka ne ko ashe bata cika mace ba, kuma kai kullun abincin mai aiki za ka ci kcnan, ban ce ba za a nemo mai aiki ba, amma itama ya dace acc ko sau daya a rana tana shiga kicin, to ina anfanin na'urori da mahaifiyarta ta saya mkau a ka zuba mkau a kicin? Sahabi ya amince gaskiya Hajiya ta sanar da shi to amma ta ina zai bullowa Mami domin bai ga tana da niyya ba? Hajiya ta ci gaba, idan gani na ne to ranar da na yi tafiya yaya za ku yi? Ya ce, 'Ai nufinmu Hajiya shi ne a dai sami mai'aikin sai su rinka yi tare, ba wai mai aikin za'a bar ma aikin abinci ba", ta ce, ku dai yi tunani, za'a ci gaba da aiko ma ku amma randa mai aiki ta zo sai a bar mani gidana mu huta,af mahaifin direbana ya rasu, an jima zani zariyan da su Sa'adiya don haka sai ka sami lokaci ku je gaisuwa kai da Mami, ya yi mai addu'a yace, insha Allah za mu je. Wannan kenan, Sahabi ya is aofis gaba daya aka soma yi mai sowa ana murnar yi mai barkwanci ga ango, Mr Obi ya doki kafadar Sahabi yace, a gaskiya ka yi sa'ar mata lalle tana kula da kai, ka ga yadda ka yi haske da kiba? Sai Mallam Jibiril yace, 'Wai amaryar fa fara ce sol irin jinsin larabawa ina ganin ta soma shafawa Sahabi haskneta; aka kyalkyale da dariya gaba daya, sannan oga Ibrahim yace, A gaskiya muna murna da ganinka Sahabi ka mori aure domin you look happy and healthy masha Allah- Allah ya bada zuri'a dayyaba' aka amsa amin. 52 *** * Sati biyu aka samu su Mami na zuwa aikin ofis kullun gidansu hajiyar sahabi kae kawo masu abinci, anti Zainab ce mai nemowa Mami mai aiki ko waссе aka kawo sai Mami tace bata yi mat aba ta yi tsofa ko tace ta faye kazanta, an yi jiran wadda ta yi ma Mamin aikin lokacin tana gida amam shiru bata dawo daga ganin gida ba, rannan daiw ata Rawar Anti Zainab ta samo masu wata katuwa mai suna Kiristi mutuniyar Ghana ce bata jin hausa, daga yamesu sai ko dan burokan turanci, ganinta mai siffar karfi Mami tace yawuce ta yi mata, aka tsadance abunda za'a bata dubu goma sha biyar a shekara, mai biyan Sahabi ya ce, ya amince. Mai mkaon a samu toshewar baraka a'a sai ma matsaloli suka soma kunno kai, Kiristi irin mutanne Kauyen nan ne tikis masu talauci wanda ba su iya girkin komi ba sai aikinw ahala gidan su Mami kam ana gyara shi kal-kal komi na Mami hatta kanfai ita ke wankewa tas, kewaye da ko ina fa cikin gyara ya ke. Ranar farko Sahabi ya baiwa Ya'u kudi masu yawa aka yo cefane raga-raga, ranar ta kama asabat duk suna gida babu zuwa ofis, sai ya cije yace, Tо Mami yau sai a fara yi man girkin amarci nima na yi alfahari da irin girkin mata ta; ta yi 'yar dariya tace, na shiga kicin! To mnee ne amfanin zaman Kiristi, ai ni ko agidanmu ban taba shiga kicin ba ko da dora ruwan zafi, wallahi ban san yadda kae dafa ko da shinkafa ba, babu dalilin da zai s ana yi ma karya a 53 kan abunda bai zama tilas akai na ba. Sahabi ya ji wani dam, an ya ko kawai shashashar macen da bata iya girki ba aduniya kai karya ne, wannan wacce irin rayiwa ce! Yanzu me ye abin yi? Tabbas dai ba zai hauta da fada ba, ko ya matsa mata domin abisa duk kan yanayin Mami wannan zance haka ykac, tun farko ma ya dace ya gano ko gidansu yaje ruwan sha bata iya kawo masa illa tasa a kawo, babu abun yi sai lallashi domin dai ya san Mami na son shi a dalilin soyayyar yana hadawa da lallashi insha Allah zai shawo kan ta har ma wasu matan su zo koyin girki wajan Mami. Ya gyara zama ya matsa kusa da ita ya kamo hannunta ya soma wasa da 'yan yatsunta yace, Mami na gano manufarki amma kin san abinda na ke so da ke shi ne, ki jure a dalilina ki shiga kicin ki rinka yi mana dan abuncinmu da gani sai ke ita kuma kiristi ta girka na ta da maigadi da Ya'u da sauran baki masu shigowa, idan kin man haka wallahi kin birge ni kin kuma nuna man lalle ina da matsayi, kuma ma aikin wannan zamanin Mami bai da wuya kawai na'urori wa'anda cikin minti talatın komi ya nuna, kuma duk muna da su, ki jure nima ofis zan koma yanzu, saboda ina da aikin don nan da wata daya da kyar zan kammala in ba na sami mai taimkao ba, amma zan bıya gidan Jabiril na ji ko zai sami lokaci ya taya ni me ki ka cc, tawan? Mami jikinta ya yi san yi akaro an farko ta soma tsanar aure, don me za'a tkaura wa mutun akan abinda bata ga gidansu ana yi ba, dole ne kuma ta yi abinda Sahabi ke so domin bai dace ta 54 a ni na ke 애 ey ta al iri d ik n a ט batawa abinda tafi so rai ba; ta yi murmushin da bai je ciki ba, tace, to zan shiga kicin amma komir ashin dadi kada ka zarge ni, yace, "Haba ni na fara komi a hankali kae yi kin san Allah ni a shirye na ke mu rinka shiga kicin din tare ko daman Ubangiji bai ce mu mai da ku bayi ba don dai an maida girki cikin neo ne kuma meo na iyaye mata ne, mu kuma mu fita mu nemo mana. Da kar ya ja ta zuwa harabar gidansu inda motarsa take, a nan ma sun dade tsaye yana daga cikin, mota zaune ita kuma ta kama marfin kofa ta rike, koma mu ce ta kwatnar da rabin jikinta a marfin motar har yanzu dai lallashin ya ke yi, tace, af to Abkar me zan dafa? Ya ce, wallahi mami ba ni da zabi komi, ki ka ga dama ki dafa, ni dai buri na naci girkin sahibata kamar sauran maza, ya yi dariya amma ita ta yi dan siririn murmushi ya dan lallaba ta ya nufi ofis, ita kuma ta nufi kicin. Kiristi na 'yan goge-gogneta wadda bata son zama haka, kamar jikinta na mata kaikayi, nan da nan cikin burokan turancinta ta ce, Anti me kike so? (Anti take cc ma Mami,s anan kuma ta kira sahabi Uncle) Mami tace, wareware ledojin nan na nama da na kayan miya mu gani, Kiristi ta debo manyan robobi daga suto ta ware kaji manya-manya ya zo da su har guda shidda, sannan ga naman rago mai kyau wanda ya dace asa a (oven) a gasa sai naman shanu na yin miya, sannan ga kayan miya wa'anda ya dace a gyara a aje a firiza a kalla sun yi masu sati biyu, kudin da Sahabi ya baiwa Ya'u na cefane kimanin dubu goma 55 ne, haka nan tun rannan yasa aka cika firij din falo da su kankana gwanda, Icmo ayaba mangwaro da tufa, Sahabi namiji mai iya kula da iyali matar cc dai ko zata zama matar kwarai? (Ga mu dai muna ta bin su aka sa kiristi ta yanka nama ta wanke shi kalkal kamar ana wankin jariri sabuwar haihuwa, har saida ka fidda zakin naman tas, ta fiddo injin markade daga ita har kiristin ba su iya markaden ba, amma sai Mamin ta karanta takardar da ke cikin kwalin ta g aya ma kiristi yadda za ta yi, nan da nan kirsiti ta yi markade Mami tace ta iya kunna kuka kiristi ta ce 'Е Ya'u ya nuna mata da zata dafa masu ruwan shayi tace to ki kunna ki yi miya wadda za'a ci shinkafa da ita, tace 'Yes Anti ita kam kiristi yadda ta ke son aikin ta ko bata iya abu ba, sai tace, to gudun kada ta batawa mami rai, a nan Mami tace ta fere dankali ta hada cikin shinkafar a dafa, wato yadda kac dafa shinkafa a watsa dankali a ciki. Mami na tsaye na kallon kiristi ta dauko tukunyar miya ta zuba nama ta zuba manja ta zuba mangyada ta zuba markaden kayan miya, idan muka auna mangyadan da manjan sun fi markadne kayan miyan yawa tirkashi! Aka zuba magi da gishiri ta rufe ruf ta dora bisa kuka gas, sai aka koma sito aka farke buhun shinkafa aka debo kusan tiya daga aka wanke aka zuba ruwa aka dora bisa wuta duk Mami na kallo, zuciyarta cike da tsanar Sahabi, in dai dole sai ta zo kicin lalle za su bata kwanan nan kenan. A sito din su Mami kimanin shinkafa ce ta kai buhu talatin, danya ta tuwo buhun goma, ta dafawa 56 t 1 , e i i 31 13 Z a a k buhu ashirin, katon na taliya ashirin, garewani ashirin, katon na magi uku buhun gishiri ashirin,w annan gara ce iyayen Mami suka kawo ma Sahabi, haka sun kai ma Hajiya Aisha rabin komi na Sahabi. Kiristi na gama fere dankali ta watso cikin shinkafar a lokacin ko tafasa shinkafa ba ta yi ba, mami ko ta koma falo ta murdo tauraron dan.adam tana kallon irint ashar bakantar nan wadda Sahabi ya ke son ya soma hanata bayan basu da wani aiki a gidansu sai su kai asuba suna kallon irin wa'annan tashoshin, batsace kiri-kiri can ta yi nisa ita kadai a falo Sahabi ya yo mata waya ta layin gidansu,t a dauka tace, 'Yes hello Mami ce yace, 'Nima Sahibinki ne, ya gida, lafiya yace, wallahi kamar na dawo gida na ta ya ki aiki amma aikin ofis ya ritsa da ni ba hali gobe ma lahadi dole sai an zo tace, Nima gobe salun za ni, su wanke man kai na ya yi dariya yace "Ke ko gashinki ai ya sha ruwa da yawa wannan watan kila ma ya soma tsami" ya kyalkyale da dariya,t ace, "Au haka ne ma, shikenan ka jama kan ka daga yau yace, 'Haba beby na ke kin soma kar kisa na hadi zuciya na mutu ta yi dariyar da ya fi so, suka dade suna sokoncinsu, yace, Afa yi maan farfesu ta amsa a dakale 'To' sun aje waya ya yi shiru yana dubar konfutar da ke gabansa idan har zai yi zancen abincin lalle zai ji mami ta canza murya to wai ita bata tunanin abinda ya dace ne, kamar yadda shi ya ke tunanin abinda zai kayata mata rai a koda yaushe any way Mami bkauwar aure ce zata saba a hankali, zai cig aba da lallashinta, ba kuma zai taba 57 tona asirin gidansa ba har sai wannan matsalar ta zama tarihi, yanzu ya gano ma'anar jama'a da kae cewa Allah ya bada hakurin zama, maganar dai kenan ayi hakuri ita cc addu'ar aurc, ada ya dauka mene ne na hakuri tana so yana so ba auren dole akai masu ba ayau ya soma sinsinar dalilin cewa ayi hakuri insha Allah zai yi bai ga abinda zai gagaresa ba. Mami ta shiga kicin ta ce ma Kiristi ta dora farfesun kaji, kiristin a nan har ta yi hankali ta се, 'bata iya ba, ko ita Mamin zata yi waya gidansu Hajiya a gaya masu yadda kac yi Mami taji haushin Kiristi ta rufe ta da fada tace, zancen banza mnee ne abun wuya a farfesu da har za ki ce na yi waya gidan surukai na? Ta ja tsaki ta fita zuwa falo, ta zauna tana jin zafin sahabi duk dai shi ya ja mata domin ita ko a gidan ubanta da wuya taci abinda aka dafa a gidan komi dadinsa, tsarin rayiwar mami itace da safe ta sha tea da ckae ko biskit wani lokacin ma haka nan, da rana ta aika ko taje da kanta Mr Biggs ko Bkaers Delights ta sawo abincin dari biyar taci, da daddare ta sha ice-cream ko juice ta yi kwanciyarta ko tasa mai aikin abincin Babanta a gasa mata kaza, bata son ta aika masu anti Zainab don taimkaon girki domin ta san 'yan tsegumin cikin gidansu na da yawa daman an ason aga faduwar ta, haka nan me zai sa ta nunawa uwar mijinta da danginsa cewa bat aiya girki ba? a nan ma wani tsegumin ne balle can gaba? Amma bari ta nemi sháwarar aminiyarta Maryam Bishir, ta yi mata waya tace, "maryam wai kin ji Sahabi dole sai 58 abinci na zai ci, ni ko dai kin san komi? Maryam ta cc, Ba na ga kin sami Kirsiti ba, ko bai iya biyanta ne? ta cc, zai iya mana, Maryam tace, zancen banza, yanzu ke son da kike masa har zai ja ki zuwa ga wahalar da uwarki da ubanki basu saka ki ba, ki bude mai ido tun yanzu ba sai zama ya yi zama ba, a lokacin baki iya lankwasa shi, idan bai iya cin na kirsiti to zaman me su Mr. Biggs su ke? Kada dai ki yadda da ya rinda amsowa a gida, Mami ta yi ajiyar zuciya tace, "Ai ba ki san sharrin ba Kiristi bata iya farfesu ba yanzu ya yo waya yace ayi mai ya kenan? Maryam tace, Dole za ku hakura har ta iya kar ki soma neman taimkao gidan kowa kin san 'yan tsegumi ta kwallawa mai aikin Hajiyarsu kira tace, wai ya kae farfesu ne ta gaya mata? Tace to Mami ashe ma abun duk shirme ne wai kazar da ruwa da kayan miya za'a hada shikenan, suka bushe da dariya aka aje wayar. Mami ta koma kicin ta iske Kiristi tana ta gurzar naman kaji ta wanke fari kal-kal yadda babu zan cen dadi balle ya yi amfani a jikin dan adam, Mami tace, sai ki hada komi da komi kamar yadda ki ka hada miya amma banda mai. (Kai wannan abun haushi da ban dariya da yawa ya ke a gidan Sahabi da Mami) wai Kiristi har da dan durkuso da yi ma antinta Mami godiya nand anan ta hada ta dora. Mami an fito falo cikin sanyin A.C ga Pineapple juice mai sanyin gaske cike da tanbulan tana kurba ta kunna tashar Sky movies wasan dai da kae yi inda

Chapter 4 of 13