Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jami'a ta watsa shi a kafada. bata son rike G.S.M din ta a hannu don haka ta dauko 'yar Karamar jaka ta jefa wayar a ciki. Kamshinta mai taushi na tsayawa a ran Sahabi, shi ma ya fito ya yi sa'a bata kure sa ba wajen kwalliya domin irin 164 ya basar bai takura mata ba. Sun tsaya a wani shahararren shagon saide-saide, komi (mother care) ya nunawa nana ta rinka fiddawa bebin, tun nana na Kiyasta irin dubunnen da za'a caji Sahabi, har ta ja ta tsaya ta ce kudin sun yi yawa, ya ce, ba yaron abokina za aima sayayyar ba, kuma dan uwar dakina ko kin manta ne, Kila ma suna na za'a saka masa ta dan bude ido tace, Na yi zaton ma yaya Ibrahim ya sanar da kai ya ce, wallahi bai gaya man ba haka nan na cafka. Sun gama da na bebin ya tsaya akai ma Umma nata a kalla ya kashe dubu saba'in. Sun dade tsaye a kofar gida wajen duhu Sahabi ya kwantar da kai bisa sitiyari yana ta kakasheta da lafuzza masu sanyi ita kam ta soma bada kai amma rigimarta na da yawa, wai yaya zata yi da yayanta Kanal Kalil? Umma na zaune bakin gado tana shayar da yaronta nono su Husna da su Zainab duk sun iso, duk dai wata matar aboki ta zo don halartar sunan gobe, in banda mamin Sahabi da ta fi karfinsa. Nana ta shiga da ledoji niki-niki ta jibga bisa gado Umma ta daga kai ta dube ta tace, Daga ina kuma? Nana tace, in ji Sahabi, na ki ne da na bebin' Husna ce ta soma dubawa, tana daga kai tace, Mama Umma lalle kin tabbata uwar dakin Sahabi irin wannan leshi! Aiko zan ba Usman labari kun amshe mana Sahabi Zainab ta ce, sai ki zauna nan Husna bayan na soma jin Kishin-Kishin Mama Umma zata zama sirikar Sahabi? Umma tace, ku rufan asiri da yaya Kalil, da su Mami, wai Nana da mijinta; Husna ta ce, don Allah kada ku 166 ya basar bai takura mata ba. Sun tsaya a wani shahararren shagon saide-saide, komi (mother care) ya nunawa nana ta rinka fiddawa bebin, tun nana na Riyasta irin dubunnen da za'a caji Sahabi, har ta ja ta tsaya ta ce kudin sun yi yawa, ya cc. ba yaron abokina za aima sayayyar ba, kuma dan uwar dakina ko kin manta ne, kila ma suna na za'a saka masa ta dan bude ido tace, Na yi zaton ma yaya Ibrahim ya sanar da kai ya ce, wallahi bai gaya man ba haka nan na cafka. Sun gama da na bebin ya tsaya akai ma Umma nata a kalla ya kashe dubu saba'in. Sun dade tsaye a kofar gida wajen duhu Sahabi ya kwantar da kai bisa sitiyari yana ta kakasheta da lafuzza masu sanyi ita kam ta soma bada kai amma rigimarta na da yawa, wai yaya zata yi da yayanta Kanal Kalil? Umma na zaune bakin gado tana shayar da yaronta nono su Husna da su Zainab duk sun iso, duk dai wata matar aboki ta zo don halartar sunan gobe, in banda mamin Sahabi da ta fi karfinsa. Nana ta shiga da ledoji niki-niki ta jibga bisa gado Umma ta daga kai ta dube ta tace, Daga ina kuma? Nana tace, in ji Sahabi, na ki ne da na bebin' Husna ce ta soma dubawa, tana daga kai tace, Mama Umma lalle kin tabbata uwar dakin Sahabi irin wannan leshi! Aiko zan ba Usman labari kun amshe mana Sahabi Zainab ta ce, sai ki zauna nan Husna bayan na soma jin Kishin-Kishin Mama Umma zata zama sirikar Sahabi? Umma tace, ku rufan asiri da yaya Kalil, da su Mami, wai Nana da mijinta; Husna ta ce, don Allah kada ku 166 zama masu son kai mana Sahabi ya cancanci matar kikir kamar Nana, shin wai ba mun riga su mami aure ba, in Mami na da hali har sahabi ya isa ya soma kwadayin aure, ni kam na tsaya masa insha Allah bana shi ma sai ya ji dadin rayiwar aure; Zainab ta ce, kyale Mama Umma kin ji Husna ai mu yau kwana uku kenan ni da Abu mun saka Nana da Sahabi cikin addu'armu, insha Allah sai mun yi nasara. Nana dai na zaune ta rufe fuskarta da gyale, maganganun su Umma kadai ke mata ruri a tsakar ka. Ta mike ta nufi kicin ta duba abinda ke gare su sannan ta nufi yin sallah. Bayan ta idas ta koma kicin ta shirya abincin Sahabi ta aika masa. Wanshekaran suna Ibrahim ya iske sahabi a gidansa sun dade suna hira, can Ibrahim ya сe, Sahabi na zo ne don na gargade ka akan nana, a gaskiya ko alama ban yi zaton za kace kana son aurenta ba, da tun farko na yi maka kashedi, saboda akwai mai son ta tunta na karama ta hanyar Kanal Kalil kuma amininsa ne, bayan wannan ma, rigimar da ke tsakanin kanal Kalil da yaya Asma'u bana so acc muna yinta ni da shi da Umma saboda auren Nana yanzu ko gidansa Asma'u bata zuwa, kasan ko uwarsu daya Ubansu daya ka yi hakuri idan matsalarka ce da Mami zan taimaka maka ka samu matar kirki. A nan Sahabi ya tsaida shi ya ce, No! No!! No!!! bana sha'awa! Nana son ta kadai na ke yi ba wai wani dalili zai sani aure ba idan haka ne na sa mahaifiya ta mana ta nemo man matar kirki, ka yi /167 hakuri Ibrahim, ba zan iya kyale Nana ba sai in naga ta yi aure? Ibrahim ya taße baki ya ce, wannan ruwanka, ni dai idan Kanal ya ji maganar don Allah ka fidda ni ka fidda Umma. Tamkar ya kara haukatar da Sahabi, yanzu ma kirikiri ya ke shiga gidan Ibrahim, don ya yi zance da nana ya kuma riga ya rikitarwa da nana lissafi kaf, har itama ta soma tunanin sai dai in ta mutu babu aure amma 100% Sahabi ya yi mata, babu makusa game da shi. A yau ya je Legos aiki, duk kokari ya ke su fito wani dan gajeren mitin don ya keße da Nana ta waya, amma sai ya jiw ayarsa ta hannu na kira yanzu ko ina ya ke bai rufe wayarsa saboda Nana, kada wani abun ya taso ta neme sa ta rasa. Ya dauka ya yi sallama amam sai ya ji hajiyar sa ce, tace yanzu a ina ka ke? Ya ce, Ina nan Legos ne muna dakin mitin ta ce da kun fito ka kirani ya ce in ce ko lafiya Hajiya? Та се lafiya lau. Yana fitowa bai yi tunanin kiran Nana ba sai Hajiyarsa, ta ce, Ina fatan ba a cikin mota ka ke ba. Ya ce A'a ina cikin ofis din mu ne na nan Legos da wayar ofis ma na kira ku, ta ce To sai ka dau hakuri a bisa hakurin da ka ke da shi, sannan duk wani dacin rai ka aje gefe guda ka tausayawa matar ka mami domin a yau mun yi rashin mahaifiyarta Iyana". Ya dauka da salati da fadar Inna lillahi... ya kare da cewa, Hajiya me ya faru da ita? Ta ce, sun sami mummunan hatsari a bisa kan hanyarta ta dawowa nan kaduna yanzu ake shirin kaita, Na tura Kannan ka 168 su duka uku mazan ga hadiza nan ta iso za mu biya mu wuce da Sa'adiya don mu kasance muna can za'a kaita. Ya ce, Nima daga Legos nan zan taho Kaduna, ayi masu gaisuwa sai na zo. Su Hajiya ba su isa ba sai da ta biya ta dauki Malamanta mata su biyu suma su Abba ta ce su biya su tafi da malaminsu na anguwar Sarki wato Mallam Adamu. Suna isa su Mami da kannanta da dukkan sauran jama'ar gidan ana ta shure-shure ana kuka wasu na bugun kansu da bango, sai mahaifinsu ne Abduljalal ke falo yana karatun qur'ani, Hajiya Aisha ta daka masu tsawa gaba daya ta ce A uzubillah me zan gani haka, wannan shirmen na ku ne zai dawo da ita? Ku je ku yo alwala kowa ya zo yayi mata abinda zai iya, wannan shi ne, gatancin da zai shiga tsakaninku a yau. Nan da nan Hajiya tasa gida ya natsu me salati na yi me istingifari na yi, amma ita Hajiya da 'ya'yanta da wa'annan Malamai biyu, suka tasa gawar Iyana a gaba suka bude Kur'ani mai girma suka sauke mata Yasin kafa 7 da Tabaraka da Kananan surori suna mai rokon Ubangiji yasa ta zama mai ceton Iyana a ramin kabarin ta. Hajiya Aisha da wa'annan Malamai da kansu sukai mata wanka fes sukai mata sutura suka feshe ta da turare dizayna sannan suka dukufa kwararo mata addu'o'i ingantattu ga mamaci, har aka raka Abduljalal shi ya ma ya karanto nasa addu'o'in ya tofa mata a kunne, a nan Hajiya Aisha ta ce, Alhaji a madadinta da lyalanta tana mai neman gafararka, kwalla ta ciko aidon sa, Mami sai ya fada a kasan kunnenta amma darajar su 169 Allah ya gafarcemu baki daya na yafe mata muma Allah ya yafe mana aka amsa amin. Tuni Iyana ta tsufa a gidanta na gaskiya, daga ita sai Allah sai ko halinta yau duk abinda ta yi a duniyar nan ta mu mai cike da rude, zata bayyanar da abin ta. (Allah ka shirya mu kasa mu cika da kyau da Imani amin). Karfe hudu Sahabi ya yo ma Abba waya akan ya dauko motarsa ya tarye sa filin jirgi. Tunanin Nana yana nan tare da shi, yau litinin sun saba yin bude baki tare shi da ita a gidan Ibrahim, ya tabbata a yau zata yi rashinsa amma kuma ya jita damu damutuwar Iyana sosai har ta rinka tunasar da shi addu'o'in da za su rinka yi ma lyana, tare da yin alkawalin yi mata shinfidar nafila ta musamman a yanzu da sun aje wayar a karshe ta rokesa ya yi iyakar kokari ya kwantar da hankalin mami domin kasan ba wanda ya fika kusa da Mami a yanzu. Da wannan tunanin ya sauka gidan su mami, gidan kam ya cika tantsam a harabar waje babu masaka tsinke, zuri'arsu ta Maiduguri ta iso aminai da 'yan uwa na kusa da nesa sun bayyana. Sahabi ya kutsa nan ya kutsa can yana ma surukansa gaisuwa, sannan shi da su Abba suka shiga cikin gidan anan din ma abun babu dama mata ne bila adadin, a haka Sahabi ya rinka rintsatsawa har cikin dakin Iyana inda ya hango Mami rungume bisa cinyar Hajiyarsa amma rike da cashabah a hannunta sai dai duk iyakar kokarinka baka iya ganin kwayar idon Mami don 170 azabar ja. A haka Sahabi wani irin tausayi ya zo masa ya mikc ya koma kofar gida. Suna nan wajen zaman makoki sai da akai kiran mangarib sannan ya nufi gidansu inda Hafsat da Uwani suka shirya masa kayan bude baki ya koma gidan sai tsakar dare ya sami ganin mami ya yi iyakar Kokarinsa wajen kwantar mata da hankali a karshe ya bar ta anan gidansu shi kuma ya nufi gidansa in da su Ya'u suka ci gaba da yi mai ta'aziyya. Wanshekare bai san iyakar kudaden da ya kashe ba na fannin abinci a gidan Abduljala itama Hajiya da su Anti Hadiza an yo dahuwa iri-iri daga gidajensu zuwa gidan Abduljalil A ranar sadakar uku gaba daya matan abokan Sahabi su Ibrahim kenanda Usman su Abdullahi da matayensu sun zo yi ma mami gaisuwa, amma da shi ke Mami ba mai cikakkar tarbiya bace ko ta dauki Abubakar din Umma balle ta yi mata barka,s ai su Hajiya ne da su Anti Hadiza su kai ta nuna farin cikinsu akan haihuwar Umman ga shi har an saka sunan Sahabi amma sam Mami bata tsinka ba. Direban da ya kawo su Umma ya dan ke be Sahabi ya yi mai gaisuwa sannan ya ce, ranka shi dade ga wasika in ji Nana Sahabi ya ji dadi fiye da tsammanin nana domin ya fiddo kudi ba baiwa direban amma bai san ko nawa ba ne ga wasikar:- 171 SAN Dear, Ya ku ke? Ya karin hakurin mu? Allah ya gafarta mata muma in tamu ta zo Allah shi yafe mana. Na so zuwa kwarai to amma ina jin kunya kuma ban san yadda mamiz ata amshi al'amarinmu ba wannan shi ya hana ni zuwa. Don Allah ka da ka manta ako da yaushe kana raina. Yours truly, NANA SAN Insha Allah Sahabi kawai a kidime ya ke yana ma'amalla da jama'a ne amma sam hankalinsa Nana ta kwashe tsab, ya rubuta mata amsa a 6oye ya baiwa direba. Sai da aka yi sadakar bakwai a wannanr ana ne Alh. Abduljala ya hada kan Mami da Sahabi ya yi masu nasiha a nan ya ce wa Mami tunda an yi sadakar bakwai ya dace ki bi mijinki ki koma gida. Abinda ya daurewa mami kai shine me ya hana babanta ya yi ma Sahabi zancen tafiyar ta makaranta England bayan tuni ya yi mata alkawarinz ai yi ma sahabin zancen tafiyarta? Domin ita kam yanzu makaranta ta zamar mata tilas, saboda haka nan suke zaman doya da manja da Sahabi rabon da wani abu ko da magana ya shiga tsakaninsu tun zuwan ta Rivers. Wannan ba karamin ba kantawa Mami rai ya 172 1 yi ba, zata cigaba da hidimarta iyaka ta sanarwa babanta in lokacin tafiyar ta yi. Suna cikin mota mami da Sahabi ta yi tagumi tana ta sharben kuka shi dai lallashi ya ke yi a ganinsa rashin mahaifiyarta ne amma ita jin takaicinta ta rasa mai share mata hawaye a duniya saboda ita ta amince Babanta ya fi son Sahabi da ita bayan ita kadai tasan bakin cikin da ya ke tura mata. A kan dole Sahabi bai yi niyyar shiga fakin Mami ba amma dole ya je, saboda gargadin Nana bai son ya saba alkawari mami na kwance lamo bisa gado har yanzu kwallan ke fita mata, ya je ya zauna baking ado ya kamo hannunta ta runtse ido hawayen suka ci gaba da jika girar idonta, yasa hannu ya goge, yace, Mami kamar yadda na sha gaya maki kuka ba zai dawo mana da ita ba, wallahi inda kina yawaita mata addu'a ke kanki za ki sami sauki a ranki, ki tuna fa Sarki Allah ne ya yi kiranta yaya za ai ta zauna don mu mu ji dadi? Ako dayaushe mu zauna cikins hiri zamu iske su, domin su da suka tafi basu yi sauri ba, mu kuma ba mu dade ba, rayiwarce haka aka fara haka zata kare, ki ma Allah godiya da ya bata yaya, anfanin 'ya'yan nan addu'a, ta dan bude ido ta dube shi cikins anyin murya tace, N agode Sahabi, a nan ya ji dadi a ransa sai yau Mami ta yi mai kallonr ahama, ya duka yana sunbatarta. Gaba dayan su babu wanda ya yi la'akari da komi suka shiga aiwatar da auratayya, amma kuma dai zukatansu babu dadi har suka yi suka gama kome ne ne dalili? Sahabi ya duba lokaci karfe tara da 'yan mintoci na dare sai kunya ta 173 kama shi ya mike zuwa turakarsa ya yi wanka ya fita harabar gidansa ya yi zaune kan kujerar kwando cikin duhun filawa, sai hasken farin wata kadai ke haskasa. Ya jawo waya ya rubutawa Nana text kamar haka My Sweety ki ban ma'anar SAN Kwance take da gaskiya na makwafinta a hannu, ta ajiye tasan dai kila shi ne amma babu tabbas tunda yana tare da mami a wannan satin da wuya ya nemota da dare irin haka, ita har yanzu bata san irin zaman da suke yi ba domin a kullun yana nuna mata komi lafiya lau. Ta dauka ta duba, daga dai Sahabin ne rahin ran! Ta rubuta masa: Idan kana son sanin Mana'ar SAN sai ka yi rantsuwa zaka rike amana. Sakon ya je garesa duk dai ya na zaune a tsakiyar filawoyin harabar gidansa ya karanta, ya yi dariya ya sake bata amsa:- Wallahi na dauki amana har karshen raina, idan ma da alqur'ani ke ki so zan iya rantse maki, don na tabbatas maki ni mai rikon amana ne a gareki. Na ki Text din ya je mata ta kyalkyale da dariya bayan ta duba, sannan ta rubuta masa amsa haka:- Duk musulmin kwarai bai yiwa musulmi dan uwansa fatan shan alqur'ani, To balle kai rabin rai, (Sahabi amanar NANA) wannan shi ne ma'anar SAN ka amince na ci gaba da kiranka MY SAN? Sun kwashe fiye da awa biyu suna zantattukansu cikin text na so da bege a karshe ya danna mata waya aka dan kashewa juna jiki suka yi sai da safe. Da safe bayan ya kintsa mami da ban maganganu, sai ya nufi gida wajen Hajiyarsa, bayan 1.74 sun dan jima suna hirar mutuwa a karshe Sahabi yace Hajiya daman ina son na zo maki da wata shawara, amma ganin al'amarin na kwan gaba kwan baya sai na dan dakata, shawarar kuwa itace Hajiya ina neman aure! A nanta ke ta tsaya cak tana kallonsa don son karin bayani, ta ce Aure fa kace? Yace, kwarai ko Hajiya? Ta ce Rigamar ta ka da Mami ta kai dole sai ka kara auren? Ya ce Eh to gaskiya har da rashin kwanciyar hankalin na damu na, amma kuma a gaskiya Hajiya ina son Nana! Sun yi shiru na tsayin lokaci, hajiyarce ta soma magana tace, Ba zan iya hana ka aure ba, amma kuma kar ka ji da wai ba zan taba amincewa ka kara yo man auren sonr anka ba, dole sai na yi bincike akan irin zuri'arsu da halayyar gidanda tarbiyarsu da irin halin ita kanta yarinyar Sahabi yace Hajiya yarinyar kanwar Umma ce matar Ibrahim a 'yar fahimtar da na yi mata akwai ta da tsoron Allah tana da natsuwa kamar dai su Umman Hajiya tace,w annan binciken kane zan yi nawa, halin Umma bai taba zama halin Nana. Hajiya bata amince da lale Sahabi ya yi nisa da son Nana ba sai bayan wata hudu da yin maganarsu, domin ya kai kansa ga su Kanal kalil bai kuma ji ta da dadi ba, don haka har ya soma tsiyayewa wato alamun rama saboda shi Sahabi sakaran jiki ne da shi dan abu kadan sai ya zabge ya rame dan kwanaki kadan sai ya maida jikinsa. Da ta lura da matsalolin sun rincabe masa, ga Mami har yanzu babu hadin kai 2a rigimar gininsa sannan ga zirga-zirgan aiki yau yana can gobe yana kasar waje, sanan ga uwa uba 175 nanar da ya kallafa ransa akai a ganin sa itace Karshen matsalarsa kwata-kwata Kanal Kalil ya yi mai iyaka da ita ganin ta ma ya gagara sai waya wadda wayar ma akan jima kafinta samu sukuni ta bugo. Hajiya Aisha ta tuno da tsohuwar aminiyarta wadda sun taba zama a wajen aiki tare, sun yi makwabtaka kusan lokaci daya ne ma su kai goyon 'ya'yansu wato ana kiranta Maman Abdul, mutanen Gombe ne, suna can zaune a Gomben bayan mijinta ya yi ritaya. Hajiya ta shirya direban ta da Uwani ta cika but da tsarabar dankali da doya sannan ta yi ciakken bayani a rubuce ta aiki su Uwani har Gombe da yake fitattu ne nan danan suka gane gidan. An yi muma kwarai da zuwan su bayan sun kintsa, Maman Abdul ta kware wasika ta kwanta, tace, ikon Allah ai Uwani al'amarin na gida ne kin ga yarinyar dakin nan kawar Nana ce ta kut da kut. Nana ta girma ba uwa b uba, amma zuri'arsu mutanen mutunci ne, sun rene ta hanyar da Allah ke so ni kam kwanan baya yarinyar dakin nan kece mani nana ta samiw anda take so mutumin Sokoto ne amma yana aiki Abuja har na ke cewa Nana lalle kin yi sa'a mutanen Sokoto jama'ar aure ne domin akwai mutunci,wallahi har tarihin, zamana da su Hajiya na bata ban san wai dana Sahabi ake so ba masha Allah na yi murna sosai da wannan al'amari yadda zan Sada ciakkar shaida kan ta tamkar yadda zan bayas ne a kan Sahabi da iyayensa. ko alama kada ayi shayin komi game da al'amarinta ita dai uwani sai wangale 176 baki da zuba godiya zuwa ga rabbi take duk dadi yа kamata. Wanshekare suka dawo dauke da zungureriyar wasika. Sai da Hajiya ta gama shan kanun labari daga bakin Uwani sannan ta karanci takarda inda kuma gwiwoyin Hajiyar sukai sanyi, domin maman Abdul ta fayyace mata komi, wato duk halin da Nana take ciki Rabi diyar Maman Abdul ta sani don haka ta nemi Rabi don karin bayani Rabin tace, Gaskiya Mama Nana na cikin mummunar matsala domin a yadda ta sanar da ni yau a waya 'yan uwa kaf sun juya mata baya, banda Adda, Umma itama Adda Umman bata iya fitowa fili ta goyi bayan Nana, don Kanal Kalil ma cewa ya yi in bata amince da zabinsu ba to ta bar masa gida, ita kuma a yadda ta gaya man dazun in har ba su amince da Sahabin ba zata bar masu gidan. To wannan bayanin na Rabi shi Maman Abdul ta rubutawa aminiyarta amma a karshe tace ba wani abu kada a karaya a ci gaba da addu'a aure da rigima ya kan zamo alheri, nema a nan daga yau zan soma azumin kwana bakwai tare da nafiloli masu karfi, insha Allah in har da alhairi aurensu za mu yi nasara. Hajiya ta rike wasika rai 6ace tana yi ma Uwani bayani sai ko itama Uwanin ta sha mur ranta ya басі kwarai murna ta koma ciki, amma kuma Hajiyar ta yi juriya ta rinka karfafawa Uwani rai ta mike ta je inda kabinet din su yake ita da tsohon mijinta marigayi Uban 'ya'yanta ta rinka zakulo litattafai amma duk na addu'o'i nau'i nau'i ta zauna a tsanake tana fiddo 177 addu'o'in da ya dace ta dukufa Anti Hadiza ta yi sallama ta shigo ita ma abisa dukkan alamu da wani bacin ran ta zo. Ta durkusa ta gayas da Hajiyar sannan ta koma bisa kujera ta zauna, ta zuba ta gumi da hannu bibbiyu, Hajiya ta yi ajiyar rai tace, ke kuma mene ne? ta ce Wallahi Hajia Mamin matar Sahabi ce mana, ni har tsorota ke ban, na ya ko wanan abokiyar zama ce ta kirki? Uwanita yi karaf ta ce, ina kuwa ni zan ba ki labari ni da ke ganin zahir! Hajiya tace, Allah ya sawwake, me kuma ta yi duk da ya iba mata ido yaga iyakar gudun ta? Hadiza ta c/anzu nan wata colleque dina Dr. Bello da ke aiki a wata asibiti mai zaman kanta, likitar bayerabiya ce, ta same ni har gida da wa'annan takardar,w ai mami ce ki shirye-shiryen zuwa England karatu har ta gama komi shi ne aka ce ta kawo rifot din ta daga asibiti na shaidar lafiyarta to ana cikin awon fitsarinta da jininta sai aka bata rifot din tana da shigar ciki wata uku da 'yan kwanaki yanzu ta je asibitin su Dr. Bello ne a kwashe mata cikin, kin ji bala'i fa? Hajiya ta rintse ido tana ta addu'ar kaucewar bala'i daga zuci, daga can kuma ta fada a hili tace, ikon Allah shi kuma Sahabi irin tashi Kaddarar auren kenan! Oh Allah kai mana maganin wa'annan bala'o'i, wai abunda mu ke mafarkin samu kullun mu ga jinin Sahabi amma shi ne Mami zata yi mana haka! (duk irin taurin ran hajiya sai da kwalal ta ciko idonta) Uwani ta yi sauri ta bar falon domin kuka ya zo mata. 178 Hajiya ta hada kan kanan Sahabi gaba dayansu ta raba masu addu'o'in da take ganin ya dace ayi ma Sahabi. Kowanne yana amsa a lokacin ya dukufa yayin da Uwani ta shiga girka abinci da safe ta yi kosai a rabawa yara da rana tiwon shinka miyan kaji a rabawa yara da gidajen marasa galihu, sun yi ma Sahabin waya ya kuma zo a wanshekarc. Hajiyar ta sanar da shi ta kuma bashi takardun ya duba a tsanake, a nan ya shiga dogon tunaniw ato a ranar da lyana ta kwana bakwai da rasuwa ya je yana lallashin mami har suka... lalle ya amince a wannan dare Ubangiji ya aiko masu da wannan rabon domin shi ma ya yi mamakin abinda ya yi alhali bai da sha'awa balle ya ce, ya biya bukata, rashin saninsu daya ne,w ato ada can ire-iren kayan da'anda Iyana ke bai wa Mami ne suka hana ta samun ciki domin yawanci duk na tsarin iyali ne don dai da halshen Larabci ake rubutawa. Saboda haka ita mami ta saki jikinta bata taba tsammanin wani abu mai kama da suna ciki zai iya faruwa da ita ba, a wannan 'yar saduwa da suka yi dashi, don haka ma rashin ganin al'ada bai dame ta ba, don ta saba yin hakan, ta samu karuwar kasala sai yawan bacci amma tunda ba cikin ta taßa yi ba wannan ba zai sa ta gane tana dauke da dan Sahabi ba. To a ranar da aka bata tabbacin cikin ne da ita, ta koma gida da sauri ta fada kewaye ta sunce kayan jikinta kaf ta tsaya gaban madubin kewayenta, daga nononta abin ya soma firgita ta domin sun yi tantsantantsan ta tsurawa madubin ido tana kallon surar 179 Wa'annan maganganu yasa mami ta hakura, a gaban hajiya ta soma bashi nono. Nana ce ta rinka amsar kudi tana yi ma jariri da uwa saye-saye, a daren da za su taho Kaduna Sahabi ya rinka duba kayan da Nan ta saya yace, wa'annan lesis din kuma fa? Та ce Na mejego ne ko? Ya ce a wane dalilin kuma ni dana kawai nace ki ma sayayya, ta ce, SAN! Ashe haka ka ke, don me za ka tsani Mami irin haka, ni fa bana son haka, don sai kasa na rinka zullumin ni ma ko hakan za kai mani ya mike ya isa gare ta, ya zauna daf da ita ya ce, nana kamar yadda na ce maki ba na son zancen mami to mu bar ta a haka, amma ga ki ga ta nan bari ku kai mata wa'annan kayan za ki ji tace ba ta so, ta ce E ka dai bata ai hakkin ta ne, zamanka take kuma kai ta yi ma haihuwa ba wani ba, darajar dan ta taci abinda ya fi hakan. Sahabi ya tabe baki ya rungumo Nana yana yi mata rada, suka kyalkyale da dariya. Suka isa gidan Hajiya a nan ya aje Nana da kayan da suka zo da su, Hajiya ta yaba sayesayen. Sahabi shi kadai ya je gidan su Mami ya shiga har dakin da take jegon, ya gayas da su 180 Haiiva ta hode bos fa a karshe dai ya ce. Mami Baba na gari? Ta ce, "Eh yana nan ya ce, ya dace muje mu ganshi a

Chapter 12 of 13