Shcoolership. lyana ta ce, Dolensa ne
ma ya biya, ina laifinki ma da ki ke son karatun, duk
ba ga 'ya'yan 'yan uwansa ba nan suna zaune a gidan
nan ba karatu ba sana'a, sai in ya fita msallaci ko
cikin gari su kwashe mai kudi, amma ku 'ya'yan
cikinsa ne zai wahalad, shima ya san ba ni za ai ma
diyana haka ba. To bayan tafiyarta da marece
Abduljala ya kira Mami daga shi sai ita sai Allah
yace, mami ni nasan ban isa na gaya maki ba, kuma
kema ba ki daukan a bakin komi ba tamkar
mahaifiyarku, a zatona ke ce babbar diya ta zaki
zaman mani mai ceton gidan nan daga bala'e, duk
shashancin da su Zainba ke yi ina sane karfina kawai
aka fi na zuba masu ido, sun ki aure tun da suka
kashe aurensu ba su da sauran sha'awar yin wani saı
aikin masha'a, idan har ba ki hankali ba wallahi sai
sun dulmiyar da ke bisa irin hanyarsu, kuma ina kara
jaddada maki wallahi wallahi a wannan zamani samin
miji irin Sahabi yana da matukar wahala, idan wani
ki ke hange to wannan yaron ya mallaki komi. Ba zan
hana ki ci gaba da karatu ba, amma ki tallafi aurenki
shi ne gaba da komi, idan kina sha'awar rayiwar
aurenki ta zamanto irin ta Iyana ce to ina ta ya ki
bakin ciki sai kuma in ce kaico da ke Mami.
Tun da ya soma magana kan ta a sadde amma
wannan lokacin ba kukan take ba amma dai ranta a
151
bace yake, saboda tun fil azam a rayiwarta tafi
babanta fiye da lyana, tama fi sabawa da shi
abaya ne ma har take iya hira da Iyana, a nan ta
mai alkawarin zata yi abinda yake so,a mma ita d
kada ya hanata zuwa karatu kasar turai, ya ce ya
wannan taci gaba da neman makarantar amma dai zai
yı magana da Sahabi kafin komi.
A can Rivers ko da Sahabi ya ji yadda ta kasance
da Mami ta bar gidansa har na tsayin kwana ki sun yi
waya da Hajiya tace zata tura su Anti Hadiza ya сe,
Bada yardarsa ba, a kyale su ta yi abinda ranta ke so.
Tun daga wannan rana ya share Mamida ga ransa
kamar wasa ya fara tsanar kansa dama ya ci gaba da
zama da ita tun ada ba abinda ya ke so ya ji ta aiko ko
iyayenta sun ce basu yin wannan aure.. haka kawai
kamar ita kadaice diya mace a duniya.
Mahaifinta Abduljala da kan shi ya kaita gidanta
ya kuma shiga har falonsu ya ga komi lafiya yace,
Bata bukatar kudi ko makamancin haka? Ta tuno da
akwai ma wasu kudin a dakin Sahabi ya aje mata
sannan ta ga kudinda ta ki amsa cikin akwatinta,
gaskiya bata son komi ya kara mata nasiha mai tsinke
jijiyoyi, ta hakura zata zauna don kaunar mahaifinta
amma ba don tana sonz ama da Sahabi ba.
Sahabi sun yi waya da Sa'adiya ta gaya mai an
ce mahaifin Mami da kansa ya maida Mami gidan ta,
ran Sahabi ya 6aci domin yana ganin girman iyayenta
bai iya musa masu komi. Mami takan kwanta ta rinka
tunani da tausayin mahaifinta, domin sanin kan ta ne
bai mori rayuwar aure ba saboda yadda Iyana ke
152
masa tamkar dan ta, bai dace ana yi mai cin kashi irin
haka ba, irin su sahabi ya dace ace ana cusganar
mawa, ta tsani Sahabi babu abinda ta ke so irin ace
yau gata ta sami karatu ta bar kasar, ai dole su rabu
da Sahabi kamar yadda shi ma a can ya tsane ta har
bai son ya tuna wai akwai nąuyin wata aba akansa
wai Mami.
Tun Hajiya Aisha bata damu ba da rashin
zuwansa abu ya soma damunta, dominr abonsa da
Kaduna an kwashiw atanni, kuma a yanayin aikinsa
sun aje shi Abuja sau biyu ya kan fita turai ko jihohin
Kudanci da ke da mai, aike ne yana yo masu akaiakai haka nan sakonnin Mami ta hannun hajiya ya ke
biyo wa yadda ba hali taki amsa. A yau Hajiya ta
soma yi mai korafin tun daya dawo Abuja ya dace ya
rinka zuwa Kaduna ko sau daya a wata. To ya jure ya
zo a wannan satin duk yadda Mami ta dauki Sahabi
ya wuce nan, a zaton ta wai kudin da ya yi ne suke
gaya mai karya ko me? Duk da ba su magana amma
ta sanar da Ya'u ya shaida masa ya je gidansu
Babanta na nemansa, kememe Sahabi ya ki zuwa, a
nufinsa in ma Abduljalal ya nemai ta waya yace
Mamin ce bata ga ya mai ba, saboda yasan fada dai
zai mashi su zauna lafiya da ita, to wannan kalmar ta
gundureshi, amma kuma ba dalilin kiran kenan ba,
dalilin shi ne na batun karatunta ne.
Duk abinda zai bar mata ya aje a dakinsa, da
yaso ya bar komi hannun Uwani amma sanin
Riyayyar da take nunawa Uwani ya fasа.
153
2
***
Gidan da aka ba Sahabi a Wuse ne zone 2,
makwafta sosai da amininsa Ibrahim kuma daya daga
cikin manyan Sahabbansa, wannan ba karamin dadi
ya yi masu ba, ada a hotel ya ke kafin ya sami gida,
yanzu da ya sami gida Ibrahim yace abincinsa kaf
daga gidansa za'a rinka shirya masa, hatta yaro
Ibrahim kin amince ma Sahabi ya yi ya dauka, da
kyar Sahabi ya dauki yaron gida.
Shi wani abin cin ma Sahabi kusan ya ce a gidan
Ibrahim ya soma ci, ba'a taba nuna gazawa da shi ba.
Umma kenan matar Ibrahim aminiyar Husnar
Usman da Zainba din Abu Said, mata ne 'yan usuli
wa'anda suka san hakkin mutum sannan sun lakanci
zaman duniya duk iya yin mace sai dai ta yi kos din
hila a wajen wa'annan mata, kowacce kuma ta fito a
gidan da ya dace ace an yo auren mutunci.
Ummalkulsum diyar wanit sohon ma'aikacin
gwamnati ce a can cikin garin Gombe, Ibrahim
hidimar kasa ta kaishi can Allah ya hada shi da
Umma a lokacin tana shirin shiga jami'a, mahaifin
Umma ya dade da rasuwa sun girma ne cikin kulawar
'yan uwansu maza ya rasu ya bar matan aure biyu da
'ya'ya goma sha uku maza 7 mata 6, dukkansu kuma
sun shahara a cikin Nigerian nan ta mu, domin
babban yayansu Umma wanda ya zan shi ne da na
farko a gidansu mai suna Kanal Kalil gwamna ne a
daya daga cikin jihohinmu a zamanin mulkin
154
Shugabe Marigayi Sani Abacha. Gaba daya kannansa
kowanne ya kama gabansa mazan sun kammala
karatu sun yi aurc, matan ma kowacce ta horu da ilmi
an aurar da ita sai 'yar autar su kadai ta rage wato
Nana ta kammala jami'a zata fara hidimar kasa,
Kanal Kalil ke rikonta yanzu haka cikin takun saka
suke, saboda aurenta ya zo, wanda ke nemanta shi ne
Kanal Ahmada minin Kanal Kalil ne na zahiri
matarsa daya 'ya'yansa biyu, kusan ma abinda ake
iki Kanal Kalil ya bashi, yayin da Asma'u itama
'ya'yar Nana din ce ta baiwa wani kanin mijinta da
ke masifar son Nanan wato Shamsu, ita dai Nanan
tana dai jin yadda za'a yi saboda duk wa'anda ake
rigimar domin su basu birgeta.
Kanal Kalil a Abuja suke zaune da iyalansa, to a
wannan lokacin da Nana ta soma hidimar kasa ya
sami cig aba inda aka maido shi rikon jaji, yaso ace
ya aurar da nana kafin ya koma jaji amma rigimar
auren bata bashi halin hakan ba, gidan kaninsa wanda
ke aiki a Presidency wato Kabir ya so nana ta zauna
amma Umma da Ibrahim suka roko arziki dole ta zo
gidansu saboda Umman na da tsohon ciki.
To yanzu duk wani girke-girke Nana ke yi a
gidan Ibrahim bata yadda Umma ta yi komi, saboda
nana ta horu a gidan yayyunta maza da mata,
kowanne gida ta je ba kasafai suke sakarwa 'yan aiki
kicin ba su a ganinsu masu yin haka ba mata ba ne.
Wani abin mamaki tun Nana na karama bata da
wata sha'awa sai ta aikin asibiti da son girke-girke,
don haka ne ma duk mukamin da Kanal Kalil ya rike
155
lokutta da yawa Nana ke shirya mai abinci, har matar
Kanal din ma ta saba, itace ma ta bada shawarar
Nana ta yi digiri din ta a fannin girke-girke a nan ne
ma Nana tace, to adda idan na yi digiri a wannanf
annin taimakon me zan yi a kasa? Kanal Kalil ya yi
dariya yace, ke dai akwai ki da shagwaba, Ina laifin
idan ki ka sami aikin koyarwa, ko da iya ke ma ganin
wanda za ki aura ai kila ba za ki aiki ba a gidansa,
amma zai iya bunkasa maki guraren shigowar kudi,
kin san mutumi na ke son ki ko Ahmad? Nana ta bata
rai, Kanal Kalil ya ce, ki saki ranki zai baki duk iya
irin lokacin da kike so, har sai kin fahimci irin son da
ya ke ma ke wanda ba za ki iya goce masa ba.
A iya sanin Nana Kanal Ahmad duk ya karade
zuri'arsu babu wanda bai ci alhairinsa ba, ita daita na
ganin yaya zata iya zama da mutumin da bai damunta
balle har ya burge ta? Ko da ta matsawa yayarta
Asma'u ta bar kanin mijinta ya fito don dai ta yi
anfani da shi ne ta kori maganar su Ahmad, to amam
sai ma ta haddasa masifa tsakanin Asma'u da Kanal
Kalil.
Nana baka ce Suduf babu abun da ke haskakawa
a jikinta daga fararen idanunta sai hakoranta, bakin
Nana irin bakin da ake alfahari da shi ne mai sheki da
dibar ido, kyan idon ta kansa ka shagalta da Kalar
Nana tana da yalwar gira domin duk sati sai ta je
salun sun gyara mata ita saboda tana neman ta hade.
Nana tana cikin mata matsakaita bata faye tsawo ba
balle gajarta, tana da yawang ashin kai har ya kan so
ya yi mata nauyi akai saboda yawansa, a kumatunta
156
akwai lotsa, da ta yida riya sukan lotsa har guda biyu
a kowanne gefe, wannan da kyan idonta da yawan
fara'arta ke bata ciakken farin jinin maza da mata,
akwai ta da silin gurun wuya guda biyu.
***
***
Wannan zuwan da Sahabi ya yi Kaduna gidan
Hajiya ya soma isa, bayan yaci ya koshi, ya ce Hajiya
a bisa dalili biyu na zo Kaduna tace, Allah yasa
alhairi ina jin ka yace na farko na ga lafiyarku na
biyu maganar Fegunan nan namu wa'anda ke garki
Abuja na gadon mu ina son ki ban takardun dan ina
son a cikin satin nan zan soma ginin gida na a Abuja
ta yi dariya tace, Ai ina tsammanin daga nawa sai na
ka ne a Garki Abuja amma na sauran yaran ba a nan
Garkin su ke ba, ta mike ta je daki ta yi dogon
bincike ta zo mai da su ya amsa ya duba yana dariya
yace Duk karshenta sai na zo mun yi ciniki da
Sa'adiya can gaba, don ina sha'awar filayenta Hajiya
ta ce, ai ko in Sa'adiya ce ka sha kudi, ya ce insha
Allah zan iya ina tsammanin gobe ma zan koma
Abuja; Hajiya bata ce komi ba tunda ta san gidans
arziki ake ba. aba wani zaman
Ko da ya isa gidansa wanka ya yi ya shiga cikin
gari, yana gidan Abu Said, duk sha'awa tana
damunsa yadda Ibrahim ya ke da diya har ga wani*
cikin shima Abu ga na shi 'ya'yan, kowanne gida
157
gwanin ban sha'awa, amma shi gidansa ba 'ya'yan
sannan ba kwanciyar hankalin.
Wanshekare ranar asabat ya shirya, Mami ko
bacci bata fito ba ya ce ma su yau zai koma Abuja
saboda hidimar shirin gininsa. Kafin ya shiga gidansa
a Abuja gidan Ibrahim ya kutsa kai sai yaronsa ne ya
shigar da kayansa gidansa. Ya shaidawa Ibrahim
game da batun gininsa ne ya ke son ya rakasa wajen
wani kamfani da ya zabi irin tsarin ginin da ya ke so,
suka rankaya sai can. Ginin dai bai yi yawa ba irinsa
a kasar nan, wato an dauko sihirin gine-ginen kasar
Hongkong ne. Gaba daya hankalin Sahabi ya karkata
ya juya kan al'amuran gininsa, sai ko aikinsa wanda
ke bunkasa ta inda kudi ke shigo masa tamkar a
majigi.
Suna isowa gida Sahabi da Ibrahim kenan a nan
ne kuma Nana ta dawo kasuwa ita da direban
Ibrahim, suna kallon juna wato, Nana da Abubakar
Sahabi sai zuciyar su ta buga a lokaci guda ba tare da
dayan su ya san dalilin ba, Nana ce ta yi saurin kawar
da idonta daga kallon Sahabi, amma sai har ta gama
gaishe shi ta soma yi ma Ibrahim bayanai na wasu
laluran can daban, Sahabi bai dauke idonsa ba akan
ta, ta shiga gida, Sahabi cikin muryar da bai amince
tashi ba ce, ya ce, wacece wannan Ibrahim? Ya ce,
baka san nana ba, ai kanwar Umma ce, Ubansu daya
a nan take zaune tana hidimar kasa kasan Kanal Kalil
ya koma jaji mai rikon ta kenan, ya ce, wallahi ban
taßa ganin taba. Nana ta fi minti goma da shiga gida
amam zuciyar Sahabi bata daina dakan uku-uku ba,
158
yaushe rabonsa dajin haka akan diya mace? Fiye da
shekara uku tun zamanin nemansa da Mami, bai sake
yin wata magan aba mai tsawo da Ibrahim har
kowanne ya shiga gidansa. A nan ne kuma lissafi ya
kwancewa Sahabi na tsananin tunanin Nana shin wai
me ma ya hana shi bin Ibrahim can gidansa.
Misalin Karfe goma sha daya na dare har a
wannan lokacin Sahabi na zaune a kujerar farko,
kamar an tsafe shi tun daya shiga gida tunani ne dai
ya ke yi bai taba raya ma ransa zai sake son wata
daya mace ba, balle ya kai ga tunanin aure, wai ya
ma samu ya kare lafiya da ta gidan wadda ta zame
mashi kaya, ina kuma zancen ya karo aure ai kila
Mami kashe shi zata yi da takaici, amma da ya tuno
da fuska da cikar halittar wato kirar Nana sai ya ji
zuciyarsa ta bada dam mamakinsa daya ya sha
haduwa da ire-iren Mami da ire-iren su nana da ma
wa'anda suka fi su komi amma don mi bai ji abinda
ya ke ji a yau ba? sau nawa 'yan mata na tunkararsa
ko ajirgi ko a wasu gurare amam bai iya bin su! A
nan G.S.M din sa ta soma busar sarewa kamar ya
tsinka amma ya dauka ya ce Yes Ibrahim (domin ya
ga nambar Ibrahim din) lafiya ko? Ya ce, ina ko
lafiya? Gaban Sahabi ya kara tsinkewa a zatonsa ko
ya tsinci dami akala ya ce, me ke faruwa? Ibrahim ya
ce Madam dina ke nakuda, lalle haihuwa ce, zamu
asibiti shi ne nace bari na sanarwa amini kuma
makwabci. Sahabi ya yi ajiyar rai yace, ikon Allah ka
ce za mu asibiti yanzu, uwar dakina ba lafiya assha,
Allah ya sauke ta lafiya.
159
Nan da nan kowanne ya fiddo motarsa, akan idon
Sahabi nana ta fito dauke da katuwar jaka da karamin
akwati a kafarta italiyan Silifas farare sol ta saka
doguwar riga mai ruwan cincinbale, bai iya kallon
kowa sai nana, har Ibrahim ya wuce rungume da
Umma a kafada da kyar ya iya gaishe ta, dukkan
idonsa na kan Nana.
Asibitin dai kayatacce irin dai tasu ta 'yan
gogewa, daga Ibrahim sai Umma ma'aikan asibitin
suka amsa, shi din ma Ibrahim sun aje shi wani daki
na musamman in da ya rataya wata riga da safar kafa
tamkar likita mai shiga tiyata, a nan zai rinka hangen
Umma ta taga su Nana da Sahabi an aje su falon
farko na musamman har Nana ta zauna sai ta mike ta
nufi wata nas ta tambaye ta ko ina kewaye ya ke? Nas
din ta nuna mata,ta shiga ta yo alwala ta dawo ta
balle jakarta ta fiddo dan Karamin alqur'aninta wanda
bai fi girman tafin hanu ba, ta soma karantawa, tana
rokin Allah ya sauki Umma lafiya, Sahabi ya dade
yana tunani duk ya dace ya binciki Mami sanin
addinin ta a tun farkon haduwarsu amma sam bai
kula ba, ya tsurawa Nana ido, ya raya a ransa wato
bayan wani tsananin kyau da ke gare ta sannan tana
da cikar natsuwa,ta yi addu'a ta shafa shi ma ya
shafa, sai yanzu suka hada ido cikin ido, ya yi mata
fara'a itama ta yi, ta birgesa kwarai matuka, ya matsa
kusa da ita, sai yanzu ya ji tana kamshi wani (body
spray) mai taushi yace, Hala Umma ki kai ma addu'a
ta ce "Eh ya ce zo mu je cikin mota na ina da wani
littafin addu'o'i sai mu duba ta mike suka jera zuwa
160
inda motarsa take ya bude ya shiga yayin da nana ta jingina da motar ta dora hannayenta saman motar ta daga kai tana kallon sararin samaniya, har ya fito ya
tsaya yana kallon kwayoyin idonta, wa'anda suka
Kara razanar da shi ya ce, Nana! Ta sauke kanta
sannan ta amsa kiransa.
Ya bude wata addu'a mai mahimmanci ya soma
karantawa yayin da Nana ta rinka binsa da amin, sun
sami kimanin minti ashirin suna ma Umma addu'a
sannan ya rufe littafin ya mikawa Nana littafin yace,
kina da irinsa? Ta rinka dubawa a hankali can ta
girgiza kai tace, ina da shigen irinsa, amma babu
wasu addu'o'in a ciki, ya ce, ki dauki wannan ki yi
anfani da shi tace lah! Amma fa na gode, wallahi na ji dadi na gode yace, babu komi ki man addu'a nima
Allah yasa next year kamar yanzu ina taryar bebina
kamar Ibrahim tace dan wannan insha Allah zan yi
maka addu'a, kana nufin kace man kai da Mami ba
ku da yaro? Ya kura mata ido yana mamakin tasan
shi tasan Mami, amma bai nuna mata ba sai ya bata
amsa yace, ki bar Mami da shirme mana wait soron
haihuwa take yi, Nana sai da ta kwantar da katan
sannan ta yi murmushi domin itama bata san dalili ba
ta cika jin nauyi da kunyar Sahabi amma kuma bata
son ya gane tan ajin kunyarsa, babu wanda ya sake
cewa kanzil can Sahabi ya ce, Nana na tambayeki
mana amma da sharadin zan ji gaskiya, tace, wallahi
in har na sani zan gaya maka yace, Madallah yanzu
'ya'ya nawa kike sha'awa Allah ya baki? Nana ta
vani juyar da kwayar idanunta ta lumlumshe su,
161
Nan da nan kowanne ya fiddo motarsa, akan idon
Sahabi nana ta fito dauke da katuwar jaka da karamin
akwati a kafarta italiyan Silifas farare sol ta saka
doguwar riga mai ruwan cincinbale, bai iya kallon
kowa sai nana, har Ibrahim ya wuce rungume da
Umma a kafada da kyar ya iya gaishe ta, dukkan
idonsa na kan Nana.
Asibitin dai kayatacce irin dai tasu ta 'yan
gogewa, daga Ibrahim sai Umma ma'aikan asibitin
suka amsa, shi din ma Ibrahim sun aje shi wani daki
na musamman in da ya rataya wata riga da safar kafa
tamkar likita mai shiga tiyata, a nan zai rinka hangen
Umma ta taga su Nana da Sahabi an aje su falon
farko na musamman har Nana ta zauna sai ta mike ta
nufi wata nas ta tambaye ta ko ina kewaye ya ke? Nas
din ta nuna mata,ta shiga ta yo alwala ta dawo ta
balle jakarta ta fiddo dan Karamin alqur'aninta wanda
bai fi girman tafin hanu ba, ta soma karantawa, tana
rokin Allah ya sauki Umma lafiya, Sahabi ya dade
yana tunani duk ya dace ya binciki Mami sanin
addinin ta a tun farkon haduwarsu amma sam bai
kula ba, ya tsurawa Nana ido, ya raya a ransa wato
bayan wani tsananin kyau da ke gare ta sannan tana
da cikar natsuwa,ta yi addu'a ta shafa shi ma ya
shafa, sai yanzu suka hada ido cikin ido, ya yi mata
fara'a itama ta yi, ta birgesa kwarai matuka, ya matsa
kusa da ita, sai yanzu ya ji tana kamshi wani (body
spray) mai taushi yace, Hala Umma ki kai ma addu'a
ta ce "Eh ya ce zo mu je cikin mota na ina da wani
littafin addu'o'i sai mu duba ta mike suka jera zuwa
160
inda motarsa take ya bude ya shiga yayin da nana ta
jingina da motar ta dora hannayenta saman motar ta
daga kai tana kallon sararin samaniya, har ya fito ya
tsaya yana kallon kwayoyin idonta, wa'anda suka
Kara razanar da shi ya ce, Nana! Ta sauke kanta
sannan ta amsa kiransa.
Ya bude wata addu'a mai mahimmanci ya soma
karantawa yayin da Nana ta rinka binsa da amin, sun
sami kimanin minti ashirin suna ma Umma addu'a
sannan ya rufe littafin ya mikawa Nana littafin yace,
kina da irinsa? Ta rinka dubawa a hankali can ta
girgiza kai tace, ina da shigen irinsa, amma babu
wasu addu'o'in a ciki, ya ce, ki dauki wannan ki yi
anfani da shi tace lah! Amma fa na gode, wallahi na
ji dadi na gode yace, babu komi ki man addu'a nima
Allah yasa next year kamar yanzu ina taryar bebina
kamar Ibrahim tace dan wannan insha Allah zan yi
maka addu'a, kana nufin kace man kai da Mami ba
ku da yaro? Ya kura mata ido yana mamakin tasan
shi tasan Mami, amma bai nuna mata ba sai ya bata
amsa yace, ki bar Mami da shirme mana wait soron
haihuwa take yi, Nana sai da ta kwantar da katan
sannan ta yi murmushi domin itama bata san dalili ba
ta cika jin nauyi da kunyar Sahabi amma kuma bata
son ya gane tan ajin kunyarsa, babu wanda ya sake
cewa kanzil can Sahabi ya ce, Nana na tambayeki
mana amma da sharadin zan ji gaskiya, tace, wallahi
in har na sani zan gaya maka yace, Madallah yanzu
'ya'ya nawa kike sha'awa Allah ya baki? Nana ta
wani juyar da kwayar idanunta ta lumlumshe su,
161
-
amma a zahiri ita bata san tana yi ba, amam sai
zuciyar Sahabi ta sukurkuce ta kanannade na juyayin
Kauna cikin sha'awa tace,w ai da nasan wannan
tambayar za kai man da ban yi saurin rantsuwa ba (ta
dan kanne ido) sannan ta ce, idan san samu ne
wallahi ina son 'ya'ya da yawa, a kalla biyar ko
shidda kasan 'ya'ya rahama ne, saboda kamar akai na
naga misali kala-kala, saboda ban san Uba na ba ban
san uwata ba duk sun rasu, sai yayye na wa'anda
suka rene ni suka ban tarbiyar da suka samo daga
hannun mahaifanmu, to shi ne na ke ganin, ko a nan
ai haihuwa ta zamanto rahama a gare ni ko? Ta dubi
Sahabi cikin idon sa, ya amsa mata ya ce, wallahi kin
yi gaskiya, domin akai na ma na amince da hakan,
mu takwas iyayen mu suka haifa amma a gaskiya
wani lokaci har ji take Hajiyarmu kamar mun yi mata
kadan saboda kowanne mu akwai ta hanyar da ya kan
debe mata kewa.
Sun jima suna wannan hirar wadda ta dauke
dukkan lokacinsu a Karshe Sahabi bai san dalili ba sai
kawai ya ji bakinsa ya furta cewa Nana za ki yadda ki
zama mata ta ta biyu? Ta wani zuba masa ido cikin
jin nauyi da kunya ta ce, kai ko don Allah me yasa ka
yi wannan tunanin? Ba dai zan cen so zai sa ka ce na
aure ka ba, saboda ban ga sabon da muka yi ba da zai
s ana shiga ranka, don haka ina rokonka arziki kada
ka kara man irin wannan maganar: Cikin sarkewar
murya yace, 'Ko dai ke ce ba kya so na, ko kuma mai
matar ne bakya so, ko in ce kin tsaida miji! Tacе,
idan da ka fahinci bayani na na rayiwata da son
162
haihuwata ba za ka zargan ba da rashin son zama da
matarka ba.
Ibrahim ya fito a gigice ya ruko Sahabi ya ce
wallahi ta haihu ans ami yaro! Sahabi ya kankameshi
amma idonsa akan nana wadda ke zakwadi cikin
maradin murna tana fadin Alhamdulillah, mun gode
Allah suka diba agogo karfe daya da minti uku na
dare Ibrahim ya ce, karfe daya saura minti goma
daidai ta haihu ka ga a musulince asabat kenan ba mu
shiga lahadi ba! Sahabi ya ce, Me kake so mu yi
maku yanzu? Ya ce ka kai man nana gida don ta
karade 'yan uwa da waya ta sanar da su batun
haihuwar a nan asibitin za su bata duk irin abincin da
take so, saboda haka zan zauna da Umma da sabon
yaro na a nan.
Hakan ya fi komi dadiw ajen Sahabi, a mota duk
yadda ya bullowa Nana sai ta kauce. A karshe da zai
aje ta ya jure ya ce, ina ganin dai na yi maki tsufa ko
Nana? Ta balle marfin kofa zata fita, ya ce, ji mana,
don Allah mene ne lanbar G.S.M. din ki? Ta gaya
mai a gurguje, kan Sahabi kamar komfuta nan da nan
ya dauke ya yi sauri ya zuba cikin ta shi G.S.M din
yana hangenta ta shiga gida a ransa yace kai yarinyar
nan bata son sa domin ko irin waiwayen nan batai
masa ba.
Ya shiga na shi gidan cikin kwanciyar hankali da
wani irin sanyin rai ko ba komi a yau yana jins a
tamkar kowanne namiji.
Ya fiddo (diary) din sa ma'ajiyar rubuta sirrinsa
ya yi sharhi mai yawa na canjin rayiwar da ya tsinci
163
A
kansa a wannan rana na farko a yau ya fara shiryeshiryen ginin gidan da ya ke mafarkin mallaka a
rayiwarsa na biyu yana jin a ransa ya hadu da macen
da ya ke jin itace tushen warwarawar matsalar
rayiwar aurensa, yana jin a jikinsa shi ma zai zauna
da macen kwarai, ta girmama shi ta mutuntashi
kamar yadda ake wa sauran abokansa. Ya rufe diary
ya mike ya yo alwala ya gabatar da nafila tare da
shugaban Istahara wadda Manzon Allah (SAW) ya yi
koyi da ayi wato idan har abu alhairi ne za ka ji son
abun a tare da kai ko yaushe yana karuwa idan ko
babu alhairi za ka ji abun na fita ranka a kullun.
Duk irin tsananin aikin Sahabi bai hana shi
tunanin Nana ko yi mata waya, cikin kwana shidda
kafin suna sun saba sosai da juna, sai a wannan
lokacin ya gane duk girkin da ake aiko masa daga
gidan Ibrahim ashe Nana ce mai girkawa, wannan
kuma ya kara ruda Sahabi.
Ana gobe suna ya yi mata waya da yamma akan
ta zo ta raka shi su yo ma bebin sayayya. Ta fito
kuwa inda ta yarfo kwalliya, da wani farin les mai
rashin nauyi amma kai da ganin yadda ya lafe jikin
Nana kasan zai yi tsada, ta tusguda daurin kallabinta
gwanin ban sha'awa saboda ana hangen walkiyal
gashinta tuli guda ta inda ta faure shi a keya ga gyale
irin na 'yan matan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 13