Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
na san 'yan uwan Sahabi mutane ne masu son zumunci da son junansu, mu ba su hakkin zumunci mu ga abinda za su yi, idan mun g alalacewar ta Sahabi ta yi yawa, wallahi yanzu duk ya fi mu tsufa na san ko rashin kwanciyar hankali ne ya saukar masa da hakan. To wannan kwaranniyar ita ake ta famar tsegumi a gungun abokan Sahabi can Abuja da Kaduna, yayin da cikin zuri'ar Sahabi abin ya soma matukar damunsu, Hajiya kuma ta ce, aci gaba da addu'a Allah zai maganin abin, amma ko an ce za ai fitina ba itace ma fita ba, Shi ko sam gani ya ke boye-boynesa bai bari na san abinda ya ke ciki ba, a zatonsa kowa kalonsu ya ke lafiya lau. Gidan su Mami ne kadai da kawayen take dauka auren Mami (is perfect) wato ana zaman lafiya tana daya daga cikin masu tarihin aure babu matsala, basu san tsiyar da take shukawa ba don miji kam ta yi sa'a bai cikin 'yan zamani. Don haka ma yanzu wani lokacin ko ta taso aiki sai ta wuce gida abin ta iyana da Abduljalal ba su damuwa tunda sun fahince auren 105 Mami da Sahabi har yanzu ba matsala, sai lokacin da taga dama ta koma gidan Sahabi tun yana tsananin damuwa har ya soma sawa ransa dangana. *** *** Yau Laraba tun da ya dawo daga masallaci sallar asuba, a falo ya kudundune bisa doguwar kujera, da casbaha a hannuns aya na lazimi, ya san kwana kusan uku kenan bai jin dadin jikinsa amma a safiyar yau ya fi jin nauyi da kasala, kirjinsa ya faye mai za fi da radadi, kome zai sha? Dole ne ko yau ya je asibiti ko kuma ya yi ma Hajiyarsa waya, ya jawo karamar redio ya murda muryar Amurka, Kabir Isa Jikamshi ne da Aliyu Mustapha ke sallama bai san kowanne shiri suka kammala ba, ya dan ja tsaki lalle bai da lafiya yau har bais aurari labarai ba, ya tuno zai aikawa Aliyu Mustaphan Sokoto sako ta Internet a dalilin dan uwansa ne ta fannin Hajiyarsa kuma suna zuminci sosai da Sahabi, amma sai shirin Yusuf na Kura Baban Hafsat ya dauki hankalinsa wato a shirin iya ruwa fidda kai. Kafin Sahabi ya koma В.В.С London da karfe bkawai tuni zazzabi ya rufe sa ruf, ga kirjinsa na ta Kara suya, yana son ya yi amfani da G.S.M din sa amma ya barota a dakin baccinsa in da yasa ta (on charge) ga Mami ba waniz aman arziki suke ba balle ya kwalla mata kira, duk ya kosa Ya'u ya shigo domin yana can waje yana wanke masu motoci, ya kwanta lamo, shi kadai yasan yadda jikinsa ke matsa mai, ya saba da yawan zazzabi 106 amma zamanin yana sakandire, tun da ya shiga jami'a bai iya tuna ko sau nawa ya yi Ciwo, Insha Allah da ya yi ma Hajiyarsa waya zata taimaka masa da magunguna. Bakwai da rabi daidai yana ji B.В.С. su ka yi sallama da kyar ya iya fiddo hannunsa ya kashe redion, lumfashi sama-sama, irin dan baccin nan an mai zazzabi ya rinka dibarsa. Mami daga daki ta ji yau gidansu shiru, sai kwaramniyar Kiristi daga can kicin, ada ta saba a bisa al'adun Sahabi ya kan kunna muryar Amurka sai B.B.C. London wani lokacin ya mayas da faifan C.D. na karatun alqur'ani cikin muryar Ahmad Suleman ko na Limamin madina ko limamin Makka babu dai kirar da bai sakawa, wani lokacin ma ya kan cika gidan da wa'azin ja'afar Adam, duk da tsaurin Mami ta kan so wa'azin Mallam ja'afar Adam. To amma yau bata ji sautin komi ba, haka nan irin zirga-zirgar Sahabi da ya kan yi, wato ya kai ya komo amma shiru. Nan da nan duk da ta fita harkarsa sai taji babu dadi, domin dai sabo wani abu ne, kuma ma dai ta san tana son Sahabi ra'ayinsu ne dai kawai ba iri daya ba. Zaunė take gindin madubinta tana 'yan shafcshafneta take wannan tunanin, ta tsurawa madubi ido ta na kallon sigarta har yanzu ita mai kyau ce amma raman nan bata yi mat kayau ba, wai me ke damunta ne, tabas suna son juna ita da Sahabi to me yasa ba su iya zaman kwana biyu yanzu sai sabani ya shige su? Shin wa ya fi dacewa ta kai kukan tane don samun shawara mai kyau? Ko kadan bata son ta kashe auren 107 ta, saboda samun wanda za ta lankwasa kamar sa da wuya, ko da ya ke bata lankwasa Sahabi tunda ya ki amincewa da ra'ayinta ita ta san da ya mori aurnesa fiye da zatonsa. Ta mike ta saka kayanta, tana tunanin yau ba za ta fita ba zata zauna a falo sai taga fitowarsa ta tabbatas lafiya kafin ta fita zuwa ofis. hannu, zani da Jaka da G.S.M din ta rungume a rigar da dankwali iri daya gyalen ne mahadin jakar, ta fito, kwas-kwas, kwas karar da takalmanta ke yí kenan, ta iso falo sai ta yi turus ganin Sahabi a kudundune, ta jefas da komi ta isa gare shi ta tsugunna ta sa hannu ta dafa kafadarsa, 'Sahabi Sahabi, Ab-kar', ya dan bude ido kadan duk sun yi jajir me ke damunka Ab-kar? Ya bude baki, ya ce, Ban sani ba mami, kirji na ya fi damuna, don Allah kisa hannu ki rinka danna man kirjina a hankali kila na iya yin wanka ta zauna gefen kujerar ta dan yane rufar da ya yi ta soma danna mai kirjin, amma Mami taje jikinsa za fi, rau ta ce, Sahabi, kawai zazzabi fa! Ya ce, 'Eh amma na fi damuwa da kirjin, tace, sannu sahabi, yace yauwa, ta mike tace, ina zuwa ta je ta dauko dan Raramin tawul da ruwa a roba ta zo ta soma goge mai jiki, ta mikar da hannu tana shaf amai kirjin yace, 'Yauwa na gode Mami' ta dau lokaci tana yi mai haka sai da ta ji ya soma lunfashin bacci ta mike ta je kicin ta umarci Kiristi ta kawo ruwan ti a filas da kofi da suga da madara da ovaltine ta zauna jikin Sahabi sosai ta tsura mai ido, kamar zata ba shi lafiya, can ya yi kokarin ya juya sai ya yi ido hudu da Mami, ya tsura mata nashi idon,r abon da Mami ta yi 108 mai kallo irin na yau har ya soma mantawa, kallon yana birgeshi, ko kila ita bata sani ba ne oho!. Ta taimaka masa ya juya amma jikin ya kara tsananta da za fi, ta ce, sannu Ab-kar ka tashi ga shayi, kuma ka dunga ma kwanciya ba magani? Ya jure ya zauna, yau itace ranar farko da Mami ta hada mai shayi da hannunta. Yana gama sha ya shiga kewaye da sauri ya amayas tas ya kuskure bakinsa ya fito ya kara kwanciya, Mami ta dube cikin kaduwa tace, Na yi ma Hajiya waya an ce, suna dakin ganawa? Ya ce, Nemo man anti Hadiza, a nan ma ta sake yi ma Hadiza waya tana bakin aikinta, taga wayar mami ta amsa da sauri ta ce, Yaya lafiya ko Mami? Tace, Anti Babu lafiya wallahi baki ga Sahabi ba, hadiza ta ce, "Assha, aje wayar zan zo yanzu, Anti Hadiza sanin halin lajiyarsu tafi son akai iyalan ta asibitinsu (Nursing home Ibrahim Abacha Memorial) saboda haka sai ta nemi Abba ta G.S>M din sa ta yi sa'a yana bisa hanya zai zo wajenta tace juya mu je gidan Sahabi yanzu Mami ta yo minw aya tace bai lafiya. Sun iske su a falo daga shi har mamin sun yi yare-yare Anti Hadiza ta yi 'yan tambayoyinta akan dole dai ta ce su je asibitin Hajiyarsu. Har suka is alikita ya duba Sahabi ya bashi gado, amma Hajiya basu fitoda ga mitin ba, a matsayin hajiya Aisha na itace Senior Metron a wanan asibiti Sahabi ya sami kulawa sosai amma dai ba su ce ga ciwon da ke damunsa ba, misalin karfe goma sha biyu na rana Hajiya ta fito a harabar asibiti duk motocin iyalan t ane, ga motar Mami ga motar 109 Hadiza ga ta gida wadda Abba ya zo da ita can ga ta Sa'adiya abinda ta soma tambayar wasu nas, nas da suka tarbeta shi ne me ke faruwa yau asibitin ya hade da iyalai na? Suka amsa mata Sahabi ne babu lafiya, har likitoci sun bashi daki. Hajiya Aisha bata ta sake cewa komi ba, ta nufi dakin da aka warewa Sahabi, daya daga cikin kayatattun dakunan asibitin, ta murda kofar ta shiga, gaba daya aka soma gayas da ita su Anti hadiza kenan, wani likit ana auna jinin Sahabi, ya gam aya juyo ya gayas da Hajiya sannan ya yi mata bayanin jininsa lafiya lau bai hau ba, sannan ya dauko rifot din Sahabi da ke jikin gado yana nunawa Hajiyar, suna kan bincike an kai jininsa awo ana son asan sakamkao a kalla kashi uku a binda jininsa ya kunsa, haka nan an debe bawalinsa shima ana neman sakamkao kamar biyu, gaba daya suma lab muna sa ran zuwan su nan da 'yan awowi. Hajiya ta nisa ta kara zuba idanunta da ke boye cikin gilas akan Sahabi, sannan ta sake jefawa likita tambaya wane taimako akai mashi? Ya amsa an bashi allurai na (Pain reliver) da na bacci har sai mun gano ainihin ciwonsa, ta ce Alah ya sawake, gaba daya dakin aka amsa amin, Mami na can zaune ta gefensa inda ake mai darin ruwa ta dafe mai hannu sanan ta yi tagumi da hannu daya, duk ta yi zuru-zuru, Hajiya ta zaga ta inda take ta shafi kan Mami sannan ta dan rungumo ta a jiki ta ce, Ba komi mami ki kwantar da hankalinki zai ji sauki yana tare da kwararrun likitoci sai kawai Mami a wannan lokacin ta ji kwalla sun 110 zubo mata na tausayin mijin ta sanan 'yan uwanshı da Hajiyarsa da ta tsana ta ji duk ba haka suke ba, yadda Hajiya ta rungumo ta, sai tayi da na sanin yin abubuwan da ta yi abaya. Hajiya ta cigaba da shafar bayanta na tsayin lokaci, sannan Hajiyar ta shika ta ta soma shawagi da idanunta cikin dakin tana kallon kowa dai-dai ta dire idonta akan Anti hadiza na lokaci mai nisa sannan ta fita zuwa ofis din ta, Anti hadiza ta san matsayin kallon da Hajiyar ta yi mata, don haka ta san kira ne a boye ta ido, sai ta mike ta bita ofis sun jima suna shawarwarinsu daga karshe Anti hadiza ta koma ofishin ta da niyyar sai da yamma idan Sahabi ya farka daga bacci zata dawo sannan kuma kila sakamkaonsa ya fito an san abinda ke damunsa. *** *** *** Bayan an yi sallar issha'e Mami an zaune bakin gado tana mai fuskantar Sahabi rike da fitel na abinci tana rike amam shi ke ci da hannunsa, ya rinda kokarin gyara zama, ta mike ta zare filon ta mikar da shi ya mike bayansa, sannan ta cika kofi da juice ta mika mai ta zauna, ya ci gaba da cin abinci ba wai don yana so ba abisa tilastawas likitoci, daki ciki da falo ne a falon su Abba ne da sauran 'yan uwansa, a dakin in da Sahabi yake daga Sahabin sai Mami sai su Anti Zainab da Anti Yasmin da lyana da suka zo duba shi sannan Sa'adiya da mijinta suma suna zaune, Hajiya da Anti hadiza tare suka iso, aka shiga gaisawa tare da jajantawa juna, a nan Mami ke cewa 111 a gwadawar jininsa an kawo sakamako daya an sami tayifod kadan, Hajiya dai tamkar bata gamsu ba ta ce, 'Ni kirjin shi ya fida mu na, don haka na ke son a sake hanyoyi gwadawa, Sahabi ya ce, don ma ba ki ji ciwon da na ke samu da shi ba, yan zun haka abin cin nan da na ke ci a zaba ya ke karawa kirjin nawa, Hajiya ta dubi hadiza, Hadizan ta ce, ya dace a yi Exray da safe in Alah ya kai mu ko Hajiya? Та се, Abinda ya dace dai kenan, mami ta ce, akwai likitoci uku da za su duba shi da karfe tara na dare din yau, Hajiya t ace, 'Ace su saman a ofis ina jiransu. Sun sami Hajiyar an gama tsare-tsarne abinda za a yi mai gobe da safe, kowa ya koma gida, an bar Abba da Shehu su ne za su kwana a falo inda Sahabi ya ke a bakin Sahabi na gadon jinya an shinfida wa Mami katifa, amma har misalin karfe sha biyun dare mami na bisa gadon jinyar duk da zafin jikin Sahabi bai sa sun rabu ba, can ne ma yace, ta rage karfin A.C san yi ya ke ji, ya kudundune sosai cikin bargo, amam duk da haka tana tare da shi, misalin karfe ukun dare yace, Mami cikina, tace, me ya faru kuma ya ce, bayan ciwon ciki yana man za fi tankar ana hura wuta, ta matsa kararrawa nas. biyu suka shigoda sauri, su Aba ma sun shigo nan da nan jikin Sahabi ya rikice bayan ya dume da jante ya rinka kumaji gabanin asuba ya soma suma. Tamkar su Hajiya da likitoci a nan suka kwana, kowanne na iya kar kokarinsa na neman ran sahabi, sai Rarfe takwas da rabi daidai na safe aka shigar da shi kunfuta rum don aunc-aune, an yi mai (Scarning) 112 sannan an mayas da shi dakin Ex-ray, tsayin lokaci likitoci da su Hajiya ana gwadawa a karshe sun gano, ciwon Sahabi filla-filla ulcer ce, Hajiya a lokaci guda ta ritnse ido tana salati a cikin ranta ta tsani mami tsanar da bata taba zaton zata yi ma dan adam ba. Tasa aka kira Sa'adiya da Anti hadiza da mami a ofis din ta ta ce, gaba dayan ku a nan ku ba jahilai ba ne, sanin kan ku ne, babu abinda ke haddasa cutar ulcer sai yinwa, ta dan tsaya tana kallon tebirinta cikin dacin rai, sannan ta ci gaba, Mami da ke za mu yi kuka abisa rashin kularki kin ga inda kika tura Sahabi, burinki ya cika ko? Mami ta sadda kai ta soma sheshekar kuka, Hajiya taci gaba na kira ki ne, don na gargadeki, an yi na farko insha Allah an yi na karshe, ba zan kara sa ido abinda ya faru baya ba ya sake faruwa, don haka daga yau sai yau, baki da sauran bakin da za ki hana 'yan uwan shi shiga harkar gidanku, wannan tilas ne ya zama dole. Mami ta koma dakin Sahabi taci gaba da 'yan koke-kokenta, 'yan uwansa kaf sun nuna mata tsana a hili kuma ko a gaban wa, hatta itama hajiyar yanzu 'yar gaisuwa kan hada su, yayin da na ta 'yan uwan yawan zuwan su asibiti dubiya sun san rigimar da ta kunno kai tsakaninS ahabi da Mami suma sun ara sun ya fa sun dauki mugun za fi da zuri'ar su sahabi, don haka idan an hadu a asibitin abubuwa maras kyau da dadi kan faru. Su kam likitoci tunda sun gano ciwo ba su yi sako-sako ba sai kokarin magance ta. A yau ma dakin tantsan ya ke da 'yan uwan Mami da na Sahabi 113 4 ana zaunc, ana dan jefa magana lokaci lokaci, ita dai mami sai yanzu ma ta fahinci sahabi sosai,a she don tsabar son da ya ke mata ako da yaushe yana kokarin kare ta bai yadda aga laihinta a bisa wanan dalilin sai taji son da take masa ya karu bata tunanin iya rabuwa da shi, sai ma ya zamanto batancin da yan uwan shi ke mata tankar suna kara zuga ta ne da Kaunarsa G.S.M din Sahabi ta rinka wani dan taken algaita alamun ana son magana da shi, sai mami ta dan kawad da kai tana zance da Anti Yesmin, sai Sahabi cikin siririyar murya wadda bai son magana sosai ya ce, 'Mami" ya nuna mata G.S.M din sa da ido, ta dauka cikin garari da isgilanci tace, Yes hello Mami ce; ya ce, mami ina gajiya Ibrahim ne daga Abuja na ke magana, dazun nan na samu' labarin Sahabi yana asibiti? Ta ce, wallahi kuwa ya ce, Allah ya bashi lafiya me ke damunsa ne? a nan Mami kuma duk ta raina kan ta, ta soma 'yan kame kame, ta ce, ciwo ne dai ga shi nan na zamani da ya dami jama'a, sai dai Allah ya sawake mana, ya ce, amin, don Allah ace ina gaishe shi sai an zo dubiya. Su Sa'adiya da 'yan uwanta sai wannan ya dubi wannan, wannan ya dubi wancan, suna dan murmushi su Anti Zainab kuma sai 'yan harareharare ana sakin dan tsaki. Saboda Sahabi idonsa biyu Anti hadiza ta rangwanta masu, dómin bata son su yi abinda zai bata masa rai tunda ga halin da ya ke ciki. To wanan al'amari na auren mami da sahabi sai abinda kuma Allah ya yi, domin an zuba masu ido 114 yanzu kam sosai, 'yan uwa ransu ya yi mummunan baci haka ma abokansa wanda duk ya zo asibiti ya ji ciwon da Sahabi ke yi sai haushi da kunya su kama shi. Abu Sa'id tare da abokai uku ya zo, sun kebe da Anti hadiza yana ta fada ya ce, a gaskiya idan ku Anti ba za ku iya zartas da komi ba to mu kam Kungiyar abokansa ashirye muke, yaushe za ace mutun kamar Sahabi mai son ya ga ya ciyar da kai ka koshi sanan ya yi ma alhairi yau shi ne kwance gadon asibiti saboda horon yinwa kai Anti wannan masifa fa ta isa ina dalilin soyayyar yinwar da zata ja maka cuta, Anti hadiza tace, kuma dai kun fada ai ku kwantar da hankalinku mun kammala shirin mu tsaf, mu dai addu'ar mu Allah ya bashi lafiya, duk wannan kadihurin da take yi na wannan lokacin ne, tun farko abinda yasa ka ga an kyale ta har shekara daya da auransu ta mayas da Sahabi sahorami dalilin hajiyarmu, to yanzu ko hankalin ta ya fi na kowa tashi,t ace ta amince da komi amma ban da ciwo! Tun da mami ta zo duniya bata taba shiga rayiwa mai wuya ba irin ta dan zaman su asibiti da sahabi kwana biyar su kai ana jinyar Sahabi amma yadda Mamit a rinka ji tamkar ta shekara biyar cikin kunci da bacin zuciya, idan ma yanke shawara ta yi ta koma gida ta bar auren Sahabi, to ai ba mijinta ya yi mata ba, kuma ma su Anti Zainab sun ce sai dai ayi kare jini biri jini ba za'a taßa yadda a raba Sahabi da Mami ba domin a cewas su wannan hassada ce kawai ba don 'yan uwan Sahabin sunda mu da shi ba. Sau 115 2 2 tari da yawa idan an faye matsawa Mami da ido ma kawai ta kan bar masu dakin finyar ta shiga kewayе da ke manne a dakin na Sahabi ta rufe ta zauna ta yi kuka mai kunar rai ta wanke fuskarta ta fito, wasu kan gane Mami kuka ta yi amma wasu ba su gane hakan matsalar aume zamani kenan, lyaye su ke tsunduma 'ya'yansu cikin fitintinu kala-kala, amma daga bisa ne a fake da zagin zamani ne, yanzu ita dai Mami mun amince abinda ke faruwa kenan a gidaje da dama a kasar nan tamu, abinda 'ya'ya ke so shi za su yi, ba kwaba ba tsangwama, to yau ga abinda tafi so, ko ya sille mata ko ta yi masa sanadiyar shekawa barzahu, duk a dalilin rashin samun kykayawar tarbiya wadda subhanahu wata'ala ya umarci iyayen kwarai su baiwa 'ya'yansu, Mami ta sha tuno da irin wa'azin da sahabi kan mata a wasu lokuttai amman sait a watsar da shi tamkar ba diyar musulmai ba, yace shin wai Mami me ke damunki ne kamar ba diyar babban gida, yaushe zamu rinka abin karanta a kullun, bana ce, abincinda muke sawo wa ba babu dadi ba ne, a'a, abinda ke damu na shi ne babu wanda zai shigo gidan mu ya ci abinci, kin ga ai wannan ba rayiwa ba ce, kuma ni f aba yaro ba ne, Mami ina sane da rashin girmamanin da ki ke yi man a kalla ko a shekaru na na ci mukamin da za a ce kina ban girma, amma kin ki, shin ke wai ba kya saurarne wa'azi ne? Rissar Nana Fatima in da ta je ga mahaifinta Manzonmu Manzon rahama (S.AW) ta ce, ita kam aiki ya yi mata yawa a gidan mijinta Sayidina Ali (AS) duk wahala itacc. Manzon Allah ya yi shiru 116 sannan ya ce akwai wata mata a cikin birnin Madina idan ba ki sannu ba sai ta riga ki shiga aljanna saboda kular da take ma mijinta da dinbin biyayyar da take masa; Ahan hankalin Nana Fadima ya yi mugun tashi, har ta kuduri niyyar sai ta gano wannan mata, a hankali ta gano ta, tuaje gidan ta nemi,matar zata zo kitsoematar ta amince amma da sharadin sai in ta sanarwa mijinta idan ya amince, to ya amincen ta je tare da dan ta Hasan amman sai matar tace a'a ban yi maiki izziní ki shigo ba domin a jiya ke kađai ki ka ce man saboda haka ke kadai na shaidawa mijina ban ce mai za ki zo da Hasan ba sai ki koma sai an sanar da shi za ki zo da Hasan idan ya amince ki zo, a nan ma ta sanar da shi yace e ya amince, Nana Fadimah ta zo lamma kuma sai ta zo wanan karon da Husaini a nan ma imatar ta ce, aida Hasan ki ka ce ba Husaini ba,s airan sanar da iko da gidan, a nan sai Maigidna yá ceridan har Nana Fadimatu diyar Shugabanmu Manzon rahama zata zo gidan nan da dukkan mutanan Madina to na amince mata d tio sbna Nana Fatima ta zo wannan baiwar Allah na yi amatarkitso katsam, mijinta ya dawo ta ko kyalc nana Fadima ta koma gare shi tana taryarsa ta sauke kayan da ya 2o da su ita soma goge mai jiki tana ta gayas da shi cike da kulawa da biyayya tana kuma yaba masa akan kokarin da yake yi da su, ta kawo mai wannan ta jawo mai wancan duk dai hanyar farantawa tun da yasshiğo ita, matar nan take yi,ta rasa me ma za ta yi anebidon ajin idadin mijinta? Iyakar girmamawa da mutuntawaianatar nan ha nunawa mijinta, wanan. abu 17 テ kuwa Nana Fadima na makale na kallon duk abinda ke wakana, jikin ta ya yi san yi, ta amince da lalle mahaifinta ya yi gaskiya, wannan baiwar Allah na daraja auranta fiyc da mata da yawa a duniya, babu abinda za ta yi ba tarc da amicnewar mijin ta ba Sahabi ya dube ta amma kaar yana watsa mata garwashin wuta, ko alama v a'azinsa bai shige ta ba. to ire-irne hakan ya sha faruwa amma ana watsar da Sahabi. Yau a asibiti duk ta soma nadamar kin jin wa'azin da Sahabi ke mata. Ko da aka sallame su a rana ta biyar Sahabi ya warke tangaran sai dai kuma rashin karfin jiki, misalin karfe daya na rana suka isa gida, ita dai Mami ta kira wannan lokaci da canjin yanayin rayiwa, saboda ko a gidan na su jama'a ne bila adadi 'yan uwansu na Sokoto ma sun zo don haka gidan cike ya ke kai ka ce Mami ce ta haihu, zan cne abinci kuwa sai dai a Fidda a bayas domin ko ta wane gida aiko da shi ake yi, girki kuma na musamman ake yi, mami dai na cikin daki tare da 'yan uwanta ila kawai zuciyar taf ba masaka tsinke duk zullumi ne da fargaba shin yanzu kuma ko wane irinz ama za su yi da mijinta? Lalle ta dai san yana sont a amma kuma 'yan uwansa da Hajiyarsa suna da matsayi a zuciyar Sahabi, bata ma san cewa matsayinsu ya zarce kima ba sai wannan dan lokacin, an ya ma ko za su bar Sahabi ya ci gaba da zama da ita? Can daya gefne su kuma 'yan gidan su su ruda ta domin sai yanzu suka san auren Sahabi na da mahimmanci domin sun ci 118 burin janye sa su raba shi da zuri'arsa. Ta matsu kwarai ta ga an bar masu gidan su ko taje wajen sahabi ta ji mene ne nasa canjin? Tun da bata sami sakewa ba har yanzu balle ta san matsayin soyayyarsu. Karfe goma duk mata sun koma gidajnesu, har 'yan gidan su Mami, sai Mami a yane labulen tagar ta tana kallon harabar gidan su, motoci biyu suna nan tsaye ama na abokan Sahabi ne, ta ja tsaki suma abokan na sa ta fita hanyar su, domin ta lura da 'yan take takensu, Ibrahim na Abuja da matarsa Umma su kadai ne ba su nuna mata komi bada suka zo duba sahabi a asibiti, kamar Mami zata saki labule sai ta ja ta tsaya jin mai gadi yana kokarin bude get, motar Hajiya ce sirikarta, a cikin motar Hajiya ce da Aba sai Hafsat da Uwani mai yi ma Hajiya aiki. Mami ta yi ajiyar zuciya sannan a lokaci guda ta ja tsaki, em kuma Hajiyar ke so a wannan lokaci, Allah ma ya sawake ba za a bar mutun ya huta shi da mijinsa ba, in ku mayu ne kunci kan ku; wannan itace maganar da Mami ta rinka fadi a hili ita kadai a daki, ta shiga kewayenta ta hada Sabulen wanka masu kamshin gaske, ta soma sabule farar fatar ta sai da ta ji ta yifes kamshi ya ratsa fatar jikinta sannan ta tsane ta fito, ta zauna gindin madubi tana ci gaba da 'yan gogc-gogneta fatar Mami ta debi walkiya amarya dai sosai, ta shafa farar hodar ta mai daukar hankali sait a mike a yau rigar baccinta mai nauyi ta saka zulunbuwa har kasa, ta jawo wani dan kwali ta kulle kai ta yi niyyar zuwa falo ta gaida Hajiya, amma da 119 1 さ ta tunoda wani irin kallo da take samu da ga Hajiyar tunda aka gano ulcer a tare da Sahabi sai ta fasa zuwa, tana jint soron hajiya sosai Hafsat ta rankwashi kofar dakin Mami kamar sau daya tace Anti Mami kin yi bacci ne? ta ce a'a ban yi ba, Hafsat ce, ta ce 'E Hajiya na kiranki a falo. Mami ta fito zuwa falo, ta zauna kusa da Hafsat, shi Sahabi ma zaune ya ke bisa wata luntsumar darduma, madara ce a hannunsa yana kurba. Ta ce, sannunku Hajiya ya gida? Ta ce, lafiya, ga Uwani nan na kawo mai min abinci zata zauna a nan saboda girkin abinci, kan Mami a Sadde ta

Chapter 8 of 13