ka 'yan uwan, ko ma
dai wata fitinas can da ban, kamar tun farko na ga ya
ma yawaita addu'a zai kawo komi cikin natsuwa,
kuma Allah ma na iya juyar da komi".
Jikin Sahabi ya yi sanyi likis domin shi ada yana
ta murna ne a fassarar ta shi da ya yi ma istaharar sh
shi ne zai auri mami za su haifi wa'annan 'ya'ya da
14
u
ek
a
S
ur
va
sa
m
aub
un
yar
ne
ce
lan
ya
fa
ar
ka
ar
a
:e
n
T
日
t
ya rinka gani a mafarkinsa, to ashe abun ba haka ba
ne.
Mallam Adamu ya ce, kada dai ka canza ra'ayi
akan mami kaci gaba da zan cen ka, ko babu komi
yanzu fa shekararka talatin Sahabi ya dace ka ajc
iyali, addu'a zan ci gaba da saka cikin addu'a, kada
ka yi wasa da gaya ma sarki Allah ka ji", Sahabi ya yi
godiya ya mike ya kawo kudI sadaka ya baiwa
mallam.
Abunda ma ya dan razana Sahabi shi ne a
mafarkinsa na karshe ganin yadda ya ke sakkowa
daga bene tabbas ya dan ji bawai domin ba kasafai
ake son sakkowa bene ba a mafarki lalle dole matsala
ce, sai kawai ya ture duk wani tunani ya yi anfani da
hudubar mallam Adamu, soyayyar mami ta natsu
cikin ransa da gangar jikinsa, har baya zullumin
shawo kanta, domin ya san a tun farkon haduwarsu
ya soma tsinke mata jini ya lura da hakan ya kuma
tabbataswa ransa, sai dai ya dan karance ta lalle za ta
yi dan jan aji ko kuma miskila ce kawai?
Ya tuno da samartakarsa da 'yan mata a Canada
inda ya kwancewa wata yarinya baturiya jar fata sai
har sai da ya raba ta da ainihin saurayinta wanda a kai
mata baikon aure da shi, bayan a zahiri Sahabi ya san
ba wai kaunar gaskiya ya ke mata ba iya ka kawai ayi
samartaka.
Yana zaune a falonsa shi kadai ya jawo remote
ya rage karar T.V sannan cikin natsuwa ya rubutawa
mami text cikin wayarta kamar haka: MAMI
haduwa ta da ke a gidan ice cream ya haddasa man
15
canjin rayuwa saboda haka ni Sahabi Ahmad na ce
kulle...
Mami kwance ta ke a falo ita da Rannan
mamanta su anti Zainab da anti Yesmin ga samarin
gidan su nan zazzaune ana ta hirar duniya, kan mami
na bisa cinyar anti Zainab sai text din Sahabi ta shigo
G.S.M din mami ta dan yi fito alamun nunan an aiko
da text tasa hannu ta dauko ta bude, gabanta ya bada
ras, ganin sakon Sahabi ina ya sami nambar wayarta?
Wannan ba shi ne abun tambayarta ba, ta mike tsam
tana wata 'yar rawa tana rausaya ta ce, 'yan uwa sai
da safe yau ina da abun yi wanda ya fi komi
mahimmanci a rayiwata" ta haye sama a guje zuwa
dakin baccinta, su Yasmin akai dariya Samaila ne
yace, anti Zainab duk aji a kare bana kila mami ta
sami wanda ya fi karfin ta kwana biyun nan bata da
sukuni, in da hajiya na gida kila da ta matsa mata
mun san ko wanene" yesmin ta ce mami ce fa! Me
shegen zurfin cikin tsiya amma gaskiya wannan text
din bata kawa ba ce kuma ba ta dan bawan Allah ba
ce Sani", su Yakubu da Ibrahim su ka ce ina ma
ruwan ku da mami ne, koma wanene in dai mami ce
zata sanar da mu a falon nan sai kowa ya saba da
shi".
Ga amsar da ta baiwa Sahabi saboda ta riga ta
galabaita don haka bata tsaya wani jan aji ba ta ce,
"Mami Abduljalal ta amsa tayin ka ta ce CAS; wayar
Sahabi ta bada wata 'yar jiniya ya yi sauri ya dauka
ya duba ya yi harndala da amsa mami don haka sai
kawai ya yi mata wayu sai da ta duba taga nambarsa
16
da
a
a
a
a
2
ce sannan dadi ya lullube ta ta dauka, gaisuwar cikin
rudani aka rinka yin ta saboda wata irin soyayya mai
zafi ce ta afka masu a lokaci daya. Ya kira sunanta
cikin kasan makoshi "Mami" ta amsa a dan tsoracе
domin tabbas bata iya fassarawa kan irin yanayin da
Sahabi ya tsundumata, ta dai amince lalle maza suna
suka tara, haka nan wato duk irin soyayyar da za ka
yi a duniya soyayya dai daya ake, koma dai wanene
Sahabi Ahmad ta amince shi kan sa Sahabin take so
ba komi na sa ba ko na iyayensa. Daga can ya cc, na
ji ki a sanyaye ko na matsa maki da surutu ne kina jin
bacci? Ta ce "Bacci Sahabi ina tare da kai din? ya
lunshe ido zuciyarsa tai mai gardI mami ta samu sai
kuma me, sai addu'ar zaman lafiya, ya ce sunan
mutumin na ki na gaskiya Abubakar amma in kin fi
son Sahabin duk daya ne a gare ni domin ina son
sunayen duka", ta yi wata irin dariya wadda ta burge
Sahabi tamkar ya bude wayar ya rungumeta, ta ce wa
zai kI Sahabi masoyi fa kenan? Gaskiya zan rinka
dana kowanne zuciya ta ta raya man, sunayen duk
sun yi min kyau," ya ce, ko dai me sunan" ta ce,
"Gaba daya na amince" Sahabi ya dan yi murmushi
ya ce, "Kai lucky me yau ni dai nayi sa'ar wannan
rana ta wa ce ko kin san dama a wannan rana aka
haife ni? Ta ce, laraba! Daman hausawa sun ce wai
ranar samu kowa ya samu da ita zai kara samu," ya
ce "Na yarda, na zo duniya ran laraba na sami
amincewar my special one a yau laraba, ki kokari ki
haifa mana bebi a ranar laraba mami, "ta yi sheshekar
dariya, ta ce "tsoron haihuwa na ke ka yi hakuri da
17
wannan", ya ce, haba mami bebies ke kara dan kon
kauna" idan ya ce, mami ta kan yi kamar ta yi
tsuntsuwa ta hade shi gaskiya ya iya tsuma ta, ada ta
yi alkawarin ita ba za ta haihu ba saboda yadda ta
gani ta kuma karanto wahalar haihuwa amma yau
maganarsu da Sahabi ji yake ko zata mutu sai ta yi
mai abunda ya ke so," ya lunfasa ya ce, Ai ban faye
zari ba mami yara biyu sun ishe mu mace da namiji",
ta ce, "Wai lah! Sahabi zan baka litafin haihuwa ka
karanta, Allah zaka tausaya man, koko a saukake zan
so ka dubi tashar Reality T.V a tashoshin DSTV zaka
ga haihuwa a zahirinta da wuya ka yadda na haihu",,
ya kyalkyle da dariya, ya ce, kin faye ban dariya ga ki
da saurin raki, idan zan baiwa Hajiyata labarinki a
gobe har da rakin haihuwa zan sanar da ita", ta ce,
"Don Allah Ab-kar kada ka ce ina tsoron haihuwa in
tace ka canza ra'ayi fa! Ya ce, haba my dear no way,
babu mai iya raba ni da ke sai Allah, ita Hajiyarmu
ba haka take ba, ta amince da so don haka ba ta cika
katsalandam ba a al'amuran auren mutane sai dai ta
yi kyakyawar addu'a", wayarsa ta soma 'yar kara alamun kati zai kare hirarsu ta daren farko ta ci naira
dubu kusan biyar yace, mami ki dan jira ni zan saka
kati zan sake kiranki yanzu", ta ce ko ka bari ni na
kira ka, mana", ya ce "Haba Hajiyata yau ni ke
neman aure dole ni za'a caza", layi ya yanke, ya
dauko kati ya zuba sannan ya duba agogo karfe daya
ta shige ya sake nemanta a layi, ya cc, mami ya dace
mu kwanta gaba daya muna zuwa ofis gobe ko? Ta
lumshe ido ta ce, yadda mai gida ya ce ai haka za'a yi
18
1
1
1
1
"
ko? Ya ce, wai wannan amarya tawa da wayau take!
Ta amsa ko!
Cikin sati daya gidansu mami an gano an kuma
san ko su waye iyalan marigayi Dr. Ahmad Shu'aib
ya yin da dan lokaci gaba daya family din su Sahabi
an san mami 'yar gidan M.D Abduljalal su anti
Hadiza anti Sa'adiya da sauran kannen Sahabi ana
zaunc a falon hajiya Aisha mahaifiyar su, ko wanne
ya zubawa hotan mami Abduljalal ido, anti Hadiza ce
ta soma sharhi kan mami ta ce, ai ni na san Sahabi
son komi na sa ya zama daban dole ya auro mace mai
kyau irin wannan", aka bushe da dariya Sa'adiya ta
ce "Ai ni zalkin son da take nuna masa har tsoro take
ban, shekaranjiya sun je wajena da ita, na ce, mami
yaushe ne bikin na mu ne", ta ce, Sahabi za'a
tambaya", wannan zan ce ya yi ma hajiya Aisha dadl
domin ita dai tana son mai son na ta, ya yi murmushi
ta ce, ai sai ku shirya cikin satin nan mu je gidansu
mamin mu gaisa da iyayenta.
Anti Hadiza da Sa'adiya sun zo da kwalebani
turaruka har kwalba shidda designers masu tsadar
gaske da set din rigunan bacci da undis, Hajiya Aisha
ta yi murmushi ta ce, shikenan ni sai na huta ba sai na
kai ma matar ta ku komi ba", gaba daya suka ce a'ah
Hajiya ba mu yadda ba ai na ki da ban".
Kwana biyu Mami na sanar da kowa cikin gidan
har masu gadi cewa uwar mijinta da dangin mijinta
zasu zo. Duk da Hajiya iyana bata nan amma ta bar
sallahu ayi masu kyakyawar maraba saboda dai ko ba
komi Mami ce babbar diya a gidan.
19
R
Tun isar su Hajiya gidan M.D Abuduljalal su
Zainab da 'yan aiki suka rinka dawainiya da su, su
kawo wannan su dauke wannan hatta itama uwar
gayyar Mami tana manne da su kamar zata kwanta
masu, abu daya ya yi ma Hajiya Aisha cikas wato
suturar da Mami ta saka irin wandon nan da riga
matsattsu tsantsan wato hugs bakake wuluk ta rinka
karairaya kamar macijiya duk surorinta a bayyane su
ke, amma sai Hajiya Aisha ta rinka rayama ranta dan
Hajiya iyana bata gida ne shi yasa Mami ta yi
wannan shirmen dressing me zai faru? Mami ta mike
tamkar tarwada ta kamo hannun Hafsat ta ce, Hajiya
ku zo mu je falon Baba yana jiranku za ku gaisa.
A falon M.D Abduljalal gaba daya su anti
Hadiza da kannanta a bisa kafet su ka zauna illa
Hajiya Aisha da ta zauna kujerar da ke saitin Alhajin,
yayin da ita kuwa gimbiyar Mami ta je ta nade cikin
jikin mahaifinta shi ma ya rungume ta yana shafar
gashinta tankar 'yar shekara biyu.
Bayana 'yan hirarraki da ban dariya da suka
rinka gudana a tsakanin family biyu da suka zaku da
dokin jin dadin za'a kulla dan kon zumunta mai karfi
ta fannin auratayya. Can Alh. Abduljalal ya shafi kan
Mami yana mai kallon Hajiya Aisha dauke da
murmushi a fuskarsa ya ce wallahi kwarai na yi
murna da samun Sahabi a matsayin daya daga cikin sirikai na domin na yi mai intabiyu ya dace kwarai da ra'ayi na, haka nan kullun sai na shi ma Mami albarka da ta kawo man al'umar Sokoto da Birnin Kebbi za su zama jini na," gaba daya falon aka yi
20
'yar dariyar girmamawa Hajiya Aisha ce ta ce, Alhaji
mu 'yan Sokoto da Kebbi da ban mu ke da sauran
jinsin mazan da ke sauran jihohi? Alhaji ya yi dariya
ya ce, Bana so wannan maganar ta yi nisa a tsakanin
mu saboda tamkar na tsakalo magana ne, kowanne
mutun na duniya akwai baiwar da Allah yayi mashi,
amma a zahiri in mace na son ta more mijin aure
farko ta auri mutumin Kebbi ko dan Sokoto tabbas
sun san hakkin mace, amma son kai ya fi, anan sai in
ce a duniya babu kamar mutumin Maiduguri aka
bushe da dariya, Hajiya Aisha ta ce, "Eh lalle wannan
magana akwai son kai duniya gaba daya?
Alhaji ya ce, "To madallah na gode kwarai,
kwarai, idan mun yi waya da Hajiya an jima zan
sanar da ita kun zo, kuma abunda ido na ya nuna man
Mami zata fada hannun zuri'a ta gari, Allah yasa
albarka a shirya mu yi addu'a" sai a wannan lokacin
ne da aka soma addu'a Mami ta bar jikin mahaifinta
ta zauna kasa ta lankwashe. Ya kawo addu'o'c masu
na garta yana karantowa suna amsawa amin, suka fito
ana jin dadl Aisha 'yar auta itace ta debo kayan su
anti Hadiza ta baiwa Mami yayin da Hajiya Aisha ta
umarci yasmin ta nemo namiji ya fiddo kaya a but,
wato katon shidda na swan water katan shidda na five
alive yayin da shi ma Alhaji Abduljalal ya baiwa
Mami dubu hamsin ya ce ta baiwa su Hafsa da Aisha.
Bayan sun dawo gida sun iske Sahabi zaune a
falo yana jiran zuwan su, Hajiyarsa dai bata nuna mai
komi ba a fuskar ta ya ji dadin haka a zatonsa Hajiyar
ta yaba da komi, amma kuma ganin ta kI zama ayi
21
;
hira lokacin sallar mangarib bai yi ba amma ta shige
ta yo alwala tana zaune bisa sallayarta tana ta wuridi,
tabbas yasan akwai abunda Hajiyar bata so tare da
Mami, domin halayyarta kenan in abu bai mata ba sai
ta ga ya ma Allah.
Abu daya yasa Hajiyar ta kyale Sahabi game da
Mami shi ne tun farko mallam Adamu ya zo a asirce
sun yi binciken su kan iyayenta lalle Abduljalal ya
samu shaida mai kyau an ya bi halin sa domin hatta
karatun islam da sallar da su Mami su ka iya ance shi
ke tsare su yana koya masu, 'yar kwaba da uwa ta
dace ace ita ke yi to a gidan su Mami shi ne mai yi,
haka nan duk irin sangartar da akai ma su Mami a
gidansu sa'a daya Abduljalal yayi ba su cikin group
din 'yan matan kaduna masu shaye - shayen banza
da sace - sace ga shegiyar karya ta ba gaira ba sabar
sannan duk wani iyar shege da da namiji zai yi suma
wa'annan 'yan matan na gaba, batun ma karatu
wannan ma ba nasu ne sai karyar zuwa makaranta
kullun amma ba karatun ba ne. ita dai H. Aisha ta
sinsino akwai wata rashin tarbiya da bata dace da
zuri'ar ta ba, amma dai ba komi ta san halin Sahabi
namijin duniya ne zai fi karfin iyalinsa insha Allah.
Sahabi ya dubi 'yan uwansa ya ce, Anti Hadiza
yaya na ga Hajiyar ta mu kamar da matsala? Ta yj murmushi ta ce, "a'a kada ka damu sun yi murna da
mu sosai, kasan Hajiya dai, ina ganin dressing din mamin ne, to yaran yanzu yana da wuya ka hana su saka irin wa'annan kayan", Sahabi ya ce, kin san Allah bata fitowa waje a irin haka sai ta dora
22
jallabiya a gida kafai ta kan sanya, Allah Mami na da
tarbiya anti.
*** ***
Haduwar Mami da Sahabi kwata kwata wata
shidda su ka yi amma sun amincewa rayikansu daya
bai iya rayiwa sai da dan uwansa, sun kagu kwarai a
mallakawa kawunansu junansu, ta ka'idar musulunci,
duk wani aboki da Sahabi ke ji da shi ya kai shi ya ga
Mami sun kuma yaba, kowa ya kan ce gaskiya kun yi
mugun (Marching) wato sun dace a takaice abokin
Sahabi daya ne yace, "wai lalle ka isa asaka a news
line a yi hira da kai domin nasha jin labarin Mami ta
wulakanta maza masu son ta, amma kai haka gaba
daya ta mato kan ka tamkar ta hade ka, ban yadda ba
'yan Sokoton nan kuna da lakani" suka bushi da
dariya.
Ita ko bangaran kawayen Mami akwai lokacin da
Mami ta rinka tuka Sahabi a motar suna yawo da
wani marecen lahadi a karshe suka tsaya wajen shan
lemo anan ne suka hadu da kawarta Jamila Idris suka
dan kebe wajen motar Jamila shi ne Jamilan ta ce,
Gaskiya gaskiya you are a lucky girl, ke yarinya ce
mai sa'a domin addu'ar 'yan matan gidanmu itace
mu auri miji daga Sokoto ko Birnin Kebbi, sai muka
ji maryam Bishir ta ce mana ke kin samu tsantsa, don
Allah dubarsa ga tsayi ga mutunci ba irin samarin
garin nan ba yawanci shashashshu Mami ta kara
lumshe ido ta rungume kafadar Jamila ta ce, "Wallahi
23
Jamila Ab-kar yana da mutunci kwarai ni ban taba
saurayi mai kunya da tsoron Allah irin sa ba in kin ga
Sahabi ya saki jiki sosai da ni to yana aiko man da
text ne a waya a kullun darc sai na farka na nemo text
din sa na karanta raina yayi man dadI" Jamila tacc,
"Ki rike sa ki kuma kula da shi da kyau irin su sun yi
Karanci, sannan ga tsada! Gaba daya suka kyalkyalc
da dariya ta ce kin ya ba da rabin raina insha Allah
zan kawo shi har gida ya gaida mutan gidanku".
A kwai wani darc agogo ya nuna karfe uku na
sulushin dare, Mami ta kasa bacci, domin Sahabi yayi
tafiya Sokoto shi da su Hajiya yau kwana biyu ba su
tare sau daya ma su kai magana a waya, domin
G.S.M bata isa can Sokoto ba don haka babu damar
aiko da text ita kuwa tafi jin dadin ganin text din sa
domin yana rubuto mata abubuwan da ke fasa mata
kai yana tsinke mata jijiyoyi. Ta ja tsaki ta jawo
G.S.M din ta ta rinka dawo da irin text din da ya aiko
mata a baya tana jin sanyi a ran ta ga irin su: -
Mami morning greetings does'nt simply means
good morning it silently says that I thought of you
when I woke up, hope you're okey.
Anan ta tsaya ta yi shiru tana tunanin cewa lalle
irin so daya sukewa junansu ita da Sahabi ta kara budo wani text din inda ya ke cewa: -
Mami you know what? I did three things today, I
miss you, I miss you and you know what am doing right now am missing you:
Randa ya aiko mata da wannan text ta yi dariya sosai kamar yadda yanzu ma da ta dawo da shi bayan
24
sai ta rinka kyalkyatar dariyar ita kadai a daki, ta
sake dawo da wanda yayo mata a daren da zai yi
tafiya, tafi son wannan text fiye da kowanne, wato
Goodnight Mami I sent two angels to look over you,
but they all came back and said angels don't look
over angels.
Jin dadin wa'annan text yasa Mami bacci mai
nauyi. Wan shekare ya kama lahadi su Sahabi suka
dawo a motar Hajiyar ne da kanwar mahaifinsu
gwoggo Inno da anti Hadiza da Sa'adiya da direba a
motar Sahabi su Aisha ne da Hafsa sai Abba, yana
isowa dai dai A.B.U Zariya daga nan G.S.M ta soma
aiki ya tsaida motarsa ya aikawa da Mami text,
sannan ya ci gaba da tukI, ga abunda ya rubuta.
Mami someone told me that hrs is 365 day, one
week is 7 days 1hr is 60 mins but no one told me that
one second without you is eternity.
Text din ya sami Mami a lokacin tana tare da
Hajiyarta ta zaunar da Mami tana lissafa abubuwan
da take so Kawata mata gida da su, ganin sakon
Sahabi yasa Mami ta kwalla kara ta ce, Iyana ki yi
hakuri oga na na bisa hanya ba zan iya ci gaba da
lissafi ba. Ta dauki G.S.M din ta tana tsatsalla kafafu
ta shige daki abin ta.
Iko sai Allah! In ji Iyana.
Su kadai suka san yadda suke ji da junansu a rai,
don haka ko da iyayen sahabi suka zo daga Sokoto da
karfinsu suka je neman aure, aka ce ana son su je
maiduguri ba su bata lokaci ba suka je da murnar su
da jin dadinsu, suna fadin ko bayan duniya aka ce
25
mujc idan har ana zuwa ai dole muje, wanda zai baka
gudan jini! Ai ya fi ka har abada. Duk abubuwan
al'adun 'yan maiduguri babu wanda ya gagari iyayen
Sahabi duk sun yi.
To meke faruwa ne, ga shi dai tafi kowa murnar
acc Sahabi ya yo mata text amma sai muka ji Sahabin
cikin rudani da rashin ganin amsar Mami amma dai
ta ce tana son ganinsa bayan sallar issha'i, saboda
haka bara mu bi shi muji me ke faruwa ba dai aurcn
Mami zata rushe ba ko, kamar yadda tasa aka rushe
mata baikon baya?
Ya koma gida ya shirya tsab cikin kananan kaya
farare sal sai dan ratsin baki, turaren da Mami tasa
iyana ta sawo mai ci Dubai ya shafa kadan, bai ji
dadin yadda Mami ta taryesa ba domin ta zuba wata
shadda ganilah mai maikon tsanwa suduf siket da
riga ta dinka, a gaskiya ko ba a idon sahabi ba a idon
kowa ma Mami na kyau da komi, amma a yau matsalar daya ce wato fuskar Mami ta yi fari sol idanunta sun kara girma, saboda rashin gyara ta, ta
zauna a daidai kusa da kujerar da Sahabi ya zauna, ta
ce, Abkar ina gajiya? Ya ce, Babu ta sake cewa me kake so na sanarwa Anti Zainab? Yace, for goodness ke Mami me ke faruwa ne yaya za ki fito man haka tamkar kin yi kuka, sannan ki daman da cewa mc na ke so zan ci idan ma har na zo da yinwa a yau kam na hakura ni ki gaya man abunda ke damunki". Ta dan sadda kai Kasa na dan lokaci sannan ta dago suka kulle kwayar idanunsu hudu na lokaci kila sakan uku sannan ta nisa, ta ec Ab-kar me ke damun
26
mu ne mutancn yanzu a gani na mun fi mutanen da
ilmi mun fi su jin dadl domin Allah ya kawo mu
zamani na ci gaba, haka nan mun fi su, to amma me
yasa suka fi mu kwanciyar. hankali? Haka nan yanzu
za a kulla soyayya mai tsanani har daya bai iya
rabuwa da dayansa ga dukiyar ga hutun ga ilmin
amma kuma ba kwanciyar hankali why! Ka san
abunda yasa yau wuni na yi ina tunanin wa'annan
tambayoyin amma wallahi Sahabi na rasa amsa,
abinda ya jawo man tunanin shi ne na sha ba ka
labarin 'yar uwata Rabi'a wadda ke auren Ali dan
nan Kaduna ne amma yana aiki a Nigerian Embassy
can London, duka duka shekara daya kenan da yin
aurensu, wallahi Sahabi lokacin da Ali ya soma
kyalla idonsa akan Rabi'a kai kace baya da sauran
rayiwar kan sa a duniya, ya so Rabi'a son da ban taba
gani ba sai ko kai na da kai, yarda mu ke kusan
kwana bisa waya su ma haka suke yi, tunda su kai
aure sun fi sati ba su yadda kowa ya san inda suke ba,
amma wallahi bayan wata biu da na saka su a ido
tamkar a rannan Ali ya soma ganin Rabi'a son nan na
nan. Me kuma zai faru akwai lokacin da Rabi'a ta zo
Nigeria daga London, amma saboda tsabar soyayya
sai Rabi'a ta kasa yin kwanakin da ta ce zata yi nan
da nan ta shirya ta koma wajen Ali me zai faru ta isa
gidansu Ali na ofis amma abinda ta gani shi ne ma
farin rikicewar gidansu, wato rigar nonon budurwarsa
ta gani a dakin baccinsu, to ka ji sanadiyar rushewar
gidan Rabi'a da Ali, sun fi wata hudu ba zaman
lafiya, shi ne a daren jiya ya bugo ma Iyana waya wai
27
ya basu notice na awa goma sha biyu su aika gidansa
na nan kaduna a kwashe kayan Rabi'a in ko ba su
aika ba zai ba masu gadinsa umarnin su fiddo mata
kayan ta bisa titi saboda ya saki Rabl'a saki uku".
Sahabi ya dan muskuta ya gyara zama ya
fuskanci Mami sosai cikin natsuwa da kamewa ya ce,
amma Mami kin so ki ban kunya, ashe akwai
wa'anda za ki iya hada su da mu? Look! Abunda na
ke son ki gane, duk rayiwar da ki ka ga tangarda ta yi
tasiri to wallahi an bar dokar Allah, tabbas za mu iya
samun kan mu cikin bala'i fiye da na su Rabi'a duk
ko irin son da mu ke ma juna wato idan na zamanto
mai cin amanarki ko kuma kin zamantoi mai cin
amanata, kinga abu biyun nan sune amsar
tambayoyinki cin amanar aure da kuma barin dokar
ubangiji fakat! Mami ina son tun yanzu ki fahince ni
akan irin hali na, ba wai alfahari ba amma bana jin
zan iya zama mai cin amanar mata ta, sannan kuma
matar da nake so fiye da kowacce irin mace a duniya,
a gaskiya Mami zamu shirya rayuwa wadda babu mai
sanin sirrin mu daga ni sai ke haka nana ba wai irin
rayuwar nan za mu yi ba ta yaudarar juna ba a'a
rayuwa irin dai wadda manzo ya zo mana da ita. Har
abada ni Mami ba zan sakarwa kowa zuciyata ba sai ke, balle wai har na baiwa wata kai na, kuma a gidan da yazan na mu ne na raya sunar manzo, don haka ki saki ran ki, in don ni Sahabi ki yi ma sauran mata
rantsuwa kin auri salihi tsantsa, komi ma ya faru ki yi kuka da kan ki amma ba ni ba".
28
Mami ta rintse ido tuni Sahabi ya gama mata
komi ta amince da shi 100% yadda aka wuni yau ana
fallasar halayyar maza, ita yanzu ji take lalle zata iya
rantsuwa nata da ban ne wato Sahabi kenan. Mami ta
debe kafafunta ta dora bjsa kujerar da takc zaune ta
nade gaba faya, akoda yaushe daman irin zaman
Mami, kenan amma ban da in ta je aiki ofis, ta noke
fuskarta a kafadu tana irin murmushin nan na jin
kunya ka yi ma masoyi laihi shi ma yayi murmushi
ya cc, "Kin gamsu da bayanai na ko? Ta cc, "Wallahi
na amince" ya ce, Na gode, ina son ki yi magana
akawo man ti, mami ta mike cike da yaukl zuwa
falon da su anti zainab su ke, yayin da Sahabi ya bi ta
da ido yana kallo, shi dai koma menene yana dai son
Mami komi na ta kuma yana birgesa har yana ganin
ta, a ganinsa zai iya yafe mata komi ta yi masa
sannan ya ci gaba da son ta. Mami ta dawo ta zauna
ya ce, you are a very lazy woman ke dai raguwace tin
ma ba kya iya daukowa sai kin bada umarni a kawo
ma mijinki! Lalle zan sha shagwaba" ta ce, Ai lalle
gara ma ka saba, kai kuma ga mulki na lura" ya
kyalkyale da dariya ya cc, "Kin sani ko sarki za ki
aura! Ta amsa caf dijam! Kar kasa nace na fasa, ina
zan iya zama da kai kullum kana can fada tare da
fadawa, sannan cikin gida mata hudu ne ko biyar sai
na yi kwanaki kafin na samu sakewa da kai, ai bana
iya irin wannan
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 13