cé, 'To
Hajiya sai Hajiyar tace, Uwani shiga daki, tashi
Hafsat raka ta dakin da kika zauna a nan zata zauna,
bayan su fita daga Hajiya sai Sahabi da Mami a falon
hajiya tace, Duk wani shirme Mami da kuke zartas
wa a gidan nan ina son a daina matsalar rashin girki
kinga in da ta kai mijinki,w annan kuma duk mai
sauki ne, irinw anan rashin kular tafi illa ga yara
Kanana yanzu idan da Allah ya ba ku rabo da wuri
haka zaki ki kula da yaran ki bar wa su Kiristi 'yan
aiki sune abincinsu sune kula da ciwonsa sune komi
nasa har tarbiya ta zo 'yan aiki za su ba 'ya'yanki
tarbiya, Mami wannan ba rayiwa bacc, idan za kj,
canza to idan ko ba canji ba zan dauki sashanci ba.
Aure mami amanar Allah ce, ke amanar Sahabi ce shi
ma amanar ki ne, daidai da sakan dayanku ya zalunci
daya Allah f aba zai kyale sa ba, to me ke damun ki
aurcn so ku ka yi fa Mami? Na yi zaton kafi kula da
abinda ka ke so?
120
To ga dai Uwani nan na kawo duk yadda na ke
ma iyalai na girki tare da ita na ke yi,s aboda haka ta
san komi ta iya komi, dole ta sa ido akan Sahabi
domin ciwon da ya same sa mai son kula ne. Ina baki
shawara ko in ce ina son Mami ki samarwa kanki
kykakyawar tarbiya, domin wallahi sai an sami tarbiya ta gari sannan ake samun kwanciyar hankali
har a sami ci gaban zama bazan taba so a ce gidan
sahabi ya rushe ba, kullun ci gaban zamana ke so
amma ba ci baya ba, ina fatan za ki amince da abinda
na shirya maki.
Bayan Hajiya ta dade da yin shiru Mami ta daga
kai a hankali wanda ta fara kallo Sahabi, t alura babu
komi a ransa illa farin ciki sai kuma haushi ya kama
ta wato shi dan gata! In haka ne itama ai 'yar gatance
idan har so ake a gaya masa gaskiya me zai hana a
kira lyana, sannan Hajiyar ta yi wa'anan
maganganun. Shi mai uwa a bakin murhu ko? Ta
juya ta dubi Hajiyar tace, shikenan ko Hajiya?
Hajiyar ta dubi tsabar idon Mami lalle yarinyar na da
masifar kyau amma dai bata da tarbiya, ta mike ta
koma daki abin ta.
Hajiya ta ce, Sahabi tun farko ka zamanto bawa
ga yarinyar nan, tabbas yanzu ina tausaya maka, an
ya ma kuwa kana da daraja a idon yarinyar nan? Ina
gargadinka, ka koma hanyar Ubangiji, ina kana
nemawa 'ya'yanka tarbiya ta gari". Sahabi ya ce, ina
iya kar kula ta Hajiya amma insha Allah zan ci gaba
ta mike ta kwallawa Hafsat kira shi daman Abba na
cikin mota yana jin kida.
121
Sahabi ya mike Uwaní ta dawo raka su Hajiya,
Sahabi ya kira ta yace ta zot a kwashe kaya a falo, shi
ko ya je ya yi wanka don ya kara jin karfi domin
Rafafunsa suna yi mai nauyi da rashin karfi. Ya shiga
dakin mami ya ce, Mami kin yi bacci ne? kamar ta ga
ya mai bakas amma har yanzu tana tausayinsa saboda
rashin lafiyarsa domin ta san baig ama wartsakewa
ba, sai ta ce, Haba ya za'ai na yi bacci bayan baka
kwanta ba, ya yi dan murmushi ya je kusa da ita ya
kwanta, suka kudundune juna ba don komi ba sai don
kulawa, amma zukatansu cike da tunane-tunane.
Kwana daya kwana biyu a ranar kwana ta uku,
Uwani ta kai matukar kule Mami, domin abinda
dangin mami da mami su ke cewa, Hajiya ta kawo
Uwani a jami'ar tsaro wadda in mamit a zo sakawa
sahabi guba Uwani za tai gaggawar karewa, saboda
tsananin kulawa duk wani surutun 'yan uwan mami
yanzu takai bata sauraronsu,t ana dai jiran Iyana ta
dawo daga Abuja ne ayi wadda za'ayi. Zuri'ar sahabi
da Uwani sun hana Mami zartas da komi tamkar ba
Sahabin t aba, kuma ba gidanta ba wa'anda ta saba
iko da su.
A yau ma dai Sahabi ya sanar da ita baki da baki
yana da isassar lafiya, don haka sai ta shifya, amma
ita duk wanan ba shi ne gaban ta ba, abinda ke tayas
mata da hankali ya fi gaban lissafi, mahaifinta
Abduljalal yana gari amma bata sha'awar ko kadan ta
kai mai korafin damwuarta domin ta san mutun ne
mai son abu komi filla-filla in ta dauro yana iya bin
122
bayan su Hajiya, kuma ma bata tat ganin wanda ya
ke so ba tamkar Sahabi.
Sahabi ya riga ta zuwa shinfidar su a yau, mami
ta je ta zauna a bakin gado ta zuba fuskarta a tafunan
hannayneta, ta yi shiru, a zaton sahabi ya dauka
Mami addu'a take yi, don haka ya saka mata ido
kawai. Tsayin lokacis annan ta sauke hannayenta ta
ratsa daya tsakanin Sahabi ta zuba mai ido, ta cikin
(dim light) ya hangi kyallin hawayncta, ta kawo
ajiyar zuci cikin kuka, a lokacin tace, Sahabi I'm
leaving! ya kwalo ido domin ya dan rame ya ce, me
ki ke nufi ina za ki?t ace, Dole ne mana zan bar ka,
zan kuma bar maka gidanka! Ya ce, A wane dalilin?
Ta ce, Sahabi ni fa yanzu a matsayin guba na ke a
gidan nan, to na zauna na ci gaba da halaka ka, ya
daga mata hannu ya ce, look Mami duk abinda ke
gudana tsakaninki da 'yan uwana da na ki 'yan uwan
ina kallo, ban ga dalilinw annan ruda ni ba, ni dai na
yi imani Ubangiji Allah shi ya aiko man da ulcer ke
muna tarc da ke ko ban tare da ke wannan dole ne,
laifinki daya a wajena Mami shine ba kya tattalina
kamar yadda kowacce macen kwarai ke ma mijinta,
kuma a zahiri wallahi ba kowanne dan uwa zai ji dadi
ba yaga dan uwansa a wulakance, kamar yadda
dangin kowacce diya mace ba za su ji dadi ba suga
miji na wulakanta 'yar uwarsu, shi yasa na yi iyakar
kokarina naga cewa kai na da ke hade ya ke, don
gudun irin wannan 6acin rai, na shaida maki I love
you, I need you and I want to be with you for the rest
of my life, to bayan wannan me ki ke so na ce ma ki
123
Mami? A nan ta langa6e, kukan ya ci gaba da zuwa
mata shar-shar, ita a son ranta ya kori Uwanit abas su
Anti Zainab sun ce za su kawo masu mai girkin Iyana
ta rinka masu abinci.
Sahabi ya biya bukatarsa son ran sa ba tare da
takura ba ko alama, sannan ya rungume matars aya
soma sharara baccinsa cike da nishadi, sai dai ita
Mami ba baccin take yi ba, hanyar da za samu a korar
mata Uwani kawai take nema, babu ma dalilin da zai
sa ta hakura da gwarzon miji tankar Sahabi, ta san
tana murza shi son ranta amma shigowar su Hajiya
cikin al'amuranta ba karamin batanci ba ne.
Yau kwana goma sha uku da sallamar Sahabi
daga asibiti sauki kam ya samu, bayan haka har ma
ya yi wani dan haske na alamun samun lafiya Mami
ta dawo aiki ta fito daga motarta tana rufewa, wayarta
GSM ta soma karar jiniya, ta fiddo daga cikin jaka ta
latsa Hello Mami ce! Iyana ta ce, 'sannu Mami kuna
lafiya ya jikin mijin na ki? Ta ce, lah! Iyana lafiya lau
kina ina wallahi ina son ganinki Iyana, tace, sauka ta
kenan ina gida, me ke faruw ana soma jin zance
barkatai wajen su Zainab Mami na rike da hannun
motarta ta juya ta dubi harabar gidansu babu kowa sai
maigadi daga waje, tace wallahi Iyana an yi sake duk
zuri'ar mijina sun jagula man lissafi yanzu sam
Sahabi ya fi sauraron 'yan uwanshi da ni, amma dai
har yanzu bai soma wulakanta ni ba, sai dai 'yan
uwansa sun fi ni iya komi a gidan nan.
Iayana ta yi shiru tace, Maganar ta isa haka nan
ki saurari sako an jima ta hannun Zainab, ta ce, Tо,
124
suka yi sallama ta rufe wayar, ta shiga gida, Zainab ta kawo sako da yamma ta ce, Iyana ta ce Ga wannan ki/ yi duk yadda za ki yi Sahabi ya ci a cikinsa, wannan kuma ko ki shafa masa a jiki ko a ruwan wankansa. Mami ta yi shirut ace, Amma fa da wuya yadda
wannan muguwar Uwanin ke tsaye kan sahabi ba ni da halin bashi komi, Anti Zainab ta ce, you should try mana; tace, zan jarraba amma dai.....
Duk iya kar kokarin Mami babu maganin da ta
samu ta jaraba akan Sahabi, ita kuwa Iyana duk Malaman da take hulda da su ta aika masu sun kuma
bada sakonni, amma sakonni sun ki shiga cikin Sahabi.
Yau sahabi a guje ya shigo gidan, kasancewar.
kuma jumma'a ya kira Mami ta zo da sauri tana son
jin bayanin, ya mika mata wata zungureriyar takarda,
ta zauna a masangalin kujera tana karantawa, ta dafe
Kirji ta ce, Tafdijan! Oil Company Ab-kar! Ya ce, Ga shinan fa, kin san na dade ina son aikin nan, wallahi
tun kafin mu yi aure na ke rubuta masu sai bana
Allah ya ci she ni, ta yi murmushi itama dadi ya cika
mata rai tace, gaskiya na yi farin ciki!" Yanzu suna
nemana a Rivers a Babar Hedkwatarsu Part-Harcourt,
ta lumshe ido tace, ba dai can za ka zauna ba ko? Ya
ce, Ina kuma na sani saí na je na gani, idan can ne
mnee ne? Ya dube ta yana lunshe ido, ta yi murmushi
ta ce, yanzu shikenan sai ka tafi ka bar ni Ab-Kar?
Ya ce, ikon Allah ashe rigima zamu yi ba kya son mu
cigąba Mami, ko ko barin na ki aikin za ki yi? Та се
125
Σ
haba wasa na ke maka, kawai ga fa jirgi ga waya ga
motoci me zai matsa mana.
Amma cikin ran Mami wanan itace hanyar
wargajewar shirin dangin mijinta, kai gara da Allah
ya kawo wannan aikin a daidai wannan lokaci komi
ma ya tarwatse ta huta.
Dangin Sahabi kaf uwa da Uba sun yi farin ciki
da samun ci gabansa. Sun yi shawara da Hajiyar sa
Uwani ta dawo gida domin zaman su ba zai yi tasiri
ba da Mami.
A daren Lahadi daren da Sahabi zai yi tafiya,
abokansa da dama sun hallara har Mami ta ji zafin
zuwansu domin sun hana mata sakat tana son sakewa
ta ji dadin yin sallama da shi.
Sun dauki lokaci mai tsayi suna hira Sahabi da
abokanansa, ba su rabu ba sai karfe daya saura na
dare, bayan ya yi masu rakiya, ya dan tsaya ya baiwa
maigadi salallahu, ya kebe gefe daya da Ya'u shi ma
wasu sakonnin ya ke bashi, har tsayin wannan
lokacin Uwani na nan kicin ta zaman jiran ta bashi
madara kamar jariri, ya yi 'yar dariya ya ce, in da
madara da wani abu kika hada man ba zan iya sha ba
to don dai madaran ce, zan taimaka na sha, ma ita ta
yi 'yar dariyar ta ce, to mu kwan lafiya yallabai yace
Allah yasa na fa gode kwarai da gaske Allah ya bar
zumunci Uwani irin wannan yawan godiyar da ya
kan yi ma 'yan aiki yana bata ran Mami, sai ta ga
yana zubar da martabarsu. Ya yi addu'o'in rufe gida
ya kuma rufen sannan ya kutsa kai dakin Mami abin
mamakinsa tana zaune bisa doguwar kujerarta wato
126
irin (lazyman chair) ga hasken wutar lantarki
kwanyar rike da katon novel a hannunta, ta jima tana
karatun littafin amma bata fahinci labari daya ba,
saboda tsananin damuwa da tasa kan abokan mijinta
ba damuwa akan tafiyar mijin na ta ba. Ya tsugunna
gabanta, ya ce, ina tuba sarauniya tace, ka damu da
zaman jira na, wa'anda su ka fi ni sun dauke hankalin
ka gaba daya; ya ce, Ni ke na kan ji kai na ya yi man gingirin idan kin fadi maganganunki akai tsaye yanzu
ke kina iya barin kawayneki idan sun zo gare ki! Don Allah ki rinka tunani kan al'amuran duniya; Ya
mikar da hannu ya amshi litafin ya rufe ya aje kusa
da kafafunta, ya rike hannunta dukka biyun yana
wasa da tafin hannunta tare da yawan tsura mata ido
fuskarsa cike da fara'a ita din ma ta manta da komi
sai tsananin nishadi a tare da ita. Ya mike ya zauna
kusa da ita, ta ja 'yar farar singiletin da ke jikinsa ta
ce, duk f ayau da rigar nan ka yini a jikinka, ba ka ko
jin ka yi tsirarci, ya kyalkyale da dariya ya fada bisa
jikinta, ya ce me ki ka ce? Tace, Ni don Allah daga
man jiki kada ka karya ni, ka gudu Rivers ka bar ni
da jinya, komi nace ai kunnenka ya ji ya ce, Mami
kamar so ki ke ki tsani Rivers din nan, kin dai san
halin mijinki Mallam ne babu masha'ar da zan gani ta
burgeni face in hanyar Allah ne.
Bana tsoronka a Rivers, kasan abinda ya ban
takaici yan gidanmu ne, suka tsorata ni a yau da suka
shigo daki, suka ce man wai shi Sahabi yau haka zai
yini d asingileti da dan gajeren wando bayan duk
cinyoyinsa gargasa ne? ko yana tsammanin ku kadai
127
ne a gidan? To bana so ka saki jiki da irin wannan
al'adar a gurin mutane, kasan dai Rivers kasar
inyamirai ce: ya yi murmushi, ya lakuci bakin Mami
da dogon yatsansa ta yi kokari ta kai ma yatsan cizo
ya goce hannun shi bisa dogon wuyanta ya jawo ta ya
soma rada mata irin zancensu wanda su biyu kadai ya
dace su yi, sun fi awa daya zaune a kujera suna
aiwatas da love makin mai tsabta kafin su mike ko kо
Sahabi ya mike da Mami bisa kafadarasa. Asubar
farko Mamice ta soma son tashi, Sahabi ya zuba mata
ido ta hasken da ke shigowa daga taga yace, Mami
ina zaki? Baka sauraron Kiran sallah ne ko so ka ke
ka makara? In ji Mami, yace na gode da hakurin da ki
kai da ni a daren yau harki ka hakura da bacci: ta ce
kar ka damú wanna na cikin abinda ba za mu taба
mantawa ba a tarihin rayuwar auren mu;.
karfe shidda Sahabi ne zaune a mota sun doshi
Rivers ga kayan abinci nan kala-kala Uwani ta shirya
masa, mahaifiyarsa da yan'uwansa da Uwani har ma
da abokan sa sun kyautata masa, itama Mamin mai
yawan bata masa a daren jiya ta yi mai abubuwa da
bai iya gusar da su daga ransa sai dai kuma ya yi
alkawari zai dauki lokaci bai zo Kaduna ba, don ya
sami isasshen lokaci ya fahimci aikinsa haka nan ya
baiwa Mami lokaci ta yi nazari a kan rayuwar
aurensu.
Satinsa biyu kacal da tafiya Mami ta soma yi mai korafi gidan ya kan yi mata girma idan dare yayi ta waya kenan ya kan bata amsa me zai hana ki dawo da Uwani ta rinka taya ki kwana? Idonta a rufe fuskarta
128
a tsuke ta bashi amsa da cewa, ALLAH shi rufan asiri
in don haka ne me kannena sukeyi? Ya ce, ni wallahi
da za ki birge ni, ki kuma kayatar da ni da sai ki
koma gidanmu wajen Hajiyata ki zauna a can har na
dawo, gidan mu kuwa abar wa kiristi da su Ya'u, ta
wannan hanyar ne kadai nake ganin za ku yi
kyakyawar fahimta da su Hajiyar mu kuma wallahi
Mami ki ka gane halayyar 'yan Uwana sai kin mayas
da su 'yan Uwanki na Uwa daya Uba daya tayi
niyyar jan tsaki amma ta fasa domin ta tuno da
gargadin da ya yi mata, tace, ina dai da niyyar
tambayar ka ni kam zan koma gidanmu sai ka zo,
amma ni ba zan iya zama gidankuba, dama dai tare
da kai ne: yaji zafi shima yace, ban yadda ba domin
ni ba irin wa'anna sakarkarun mazan ban ne, ba
amince ba; ta sha mur tace, lah!lah!! Sahabi menene
kuma na son yin zagi don na ce ina son komawa
gidan mu, ni fa na fara gajiya da halayyarka zan fa
sanarwa da nagaba da mu, komi na nema
amincewarka sai ka dauki zafi da ni, ko dai ka gaji da
ni ne Sahabi? Ya ce, kin ji halin na ki ko, a kullum ba
kya son na fadI ra'ayin zuciyata sai ki ji zafi, sai dai
nabi son ranki, to ban dai amince ba idan kina zuwa
gidanmu ki je idan ba kya zuwa ki zauna a gida sai
anjima; ya matse wayarsa.
Sahabi ya kan so ya yi ma Mami waya amma tun
lokacin da ya taba yi ya ji ta tsayc-tsaye sai ya manta
da ita ya rungumi aikinsa kai tsaye. Gidan da suke
zaune gucss hause ne, na ma'aikatarsu su biyar nc a
gidan kowanne ciki da falo amma fa sun kayatu
129
ainun, usa da dakin Sahabi na wani mutumin kogi
ne tun daga get din gidan zuwa harabar gidan an
shirya yadda mazauna iden suji dadl, sannan an
saki kayan alatu a ko ina cilki da bai din gidan idan
mutum n ciki ya kan manti a nijeria ya ke. Babm
abinci kuwa Sahabi bai da matsala saboda
ma'aikatarsu ta tanaji wajen na musamman don hirya
wa jama'arta abinci, saboda haka sai abinda ranka ya
ke-so ake dafa maka lokuta da yawa Sahabi ya fi yin
oder tuwon shinkafa ko sakwara da daddare abinci,
rana kaji kuwa da naman shanu ana juye mai launilauni, babu wani banbanci da gida kaduna, wata daya
da yan kwanaki oga dinsu Sahabi ya soma fahimtar
Sahabi mutum ne me kwazo da zafin aiki, saboda
haka sai ya sa shi gaba a kullum aiki ne ba dare ba
rana karfe daya biyu shine lokacin zuwa gida don su
kwanta wannan yasa Sahabi ya manta da duk wani
boki da zakin aurensa da Mami, bai da lokaci tunani
balle har sha'awarta ko jin zafin batancin da take mai
ya bijiro masa.
A daidai lokacin da ya cika wata biyu rabonsa da
iyalansa awanan lokaci ya soma tunani zuwa ganin su
Mami amma sai kuma shugabansa ya ce, masa za su
aiki lagos a gobe, kuma ya tafi da shiri domin yana
jin aikin na su kila har london zasu na yan kwanaki,
to hakan ta sha fruwa a yan' tsakanin nan, ba su,
Delta ba su Abuja, don Abuja kusan duk bayan
kwana biyu ne su je aiki su dawo Rivers, kwanansu
daya rak da yini daya a legos aka shirya musu biza ta
tafiya England a can din ma aiki kwana biyu suka yi
130
a rana ta uku suna Abuja daga abuja ne Sahabi yayi
wa Mami sako (by Courier) a ranar da ya aika a
wannan rana sakon ya isketa, a ofis ta amsa ta sa
hannu. Bata bude ba sai da ta tashi aiki a rannan bata
wuce gidansu ba kamar yadda ta saba a yan kwanakin
nan sai ta wuce dakin mijinta, a dakinta tayi daidai da
kaya takalma kala uku kowanne da jakarasa wa'anda
ake masifar ya yi a zamanin sai rigunan bacci sumа
uku, sannan agogon hannu wata yar siririya mai
tsadar gaske, a lokucin da Sahabi ya saye ta yaso kwarai ace shi zai daurawa Mami a hannunta domin
sanin kansa ne zata manne da fatatta ta yi kyau
saboda yanayin halittatta. To itama Mamin ta bude
tana yaba agogon a hannunta kafin ta yi ajiyar zuciya
ta daga yar karamar wasikarsa:-
My Only Mami,
Ya ki ke? Naso zuwa kwarai wallahi aiki ya yi
yawa, aikin kuma na tafiye-tafiye, wannan shi ne
dalilin.
Love always
Ab-kar
Takardar taso tayi mata dadi amma tasan Sahabi
ya rage kaudin soyayya a rubuce, amma kuma tasan
yana sonta, abinda ya fara bata tsoro game da tafiyetafiye da ya yi mata korafi shine, duk tsarabar da ya
aiko mata taga daga london ya siyosu, kwanan sa
131
nawa a london kenan? Bata faye son zuwa aiki
Kasashen urai nan ba, komi yasa? Ta jawo wayar ta
ta nemi layinsa amma wayarsa a rufe take, wanna ya
kara jagula ranta, sai ta rubuta mai text, shiru shiru
shiru bai bata amsa ba, har ta gaji ta kwanta bacci ta
hakura
Cikin bacci karfe biyu daidai amsar ta ta shigo,
ta dauki wayar da take ajiye kusa da filonta, ta duba
shi din ne, ta ce, Ab-kar ka tayas da ni bacci; ya ce,
Sorry love wallahi yanzu na ke tashi aiki; ta bude ido
tace, me ya sameka kasan lokaci kuwa? Ya ce karfe
biyun dare Mami naga sakonki tace ch tabbas haka
yake abinda na rubuto maka yace, Mami ni kaina zan
fi so ki zo amma babu hali saboda tsarin inda na ke
ba halin aje matar aure, kuma aiki na ba na zama ba
ne, kin ga yaya zanyi ki zo man hutu! Kiyi hakuri ina
nan zuwa kwanan nan, ni kaina wani lokaci na kan
shiga cikin 6acin rai, kin dai san ma'anar sunan
wannan jihar wato (Ruwa) to akwai ta da rafuna ko
ina saboda haka sun kayata ta da gurarèn jin dadin
al'uma, na kan so ace nayi dan gajeren hutu ni da ke,
amma kiyi hakuri har su mallaka min gidana domin
naji oga ya ce idan munyi wata shidda zan zauna
Abuja amma nan din ma zirga zirga ce; Mami bata
san lokacin da ta saki tsaki ba ta ce; kasan ALLAН
wallahi har cikin raina na fara tsanar wannan aikin na
ka: ya ce, haba don ALLAH kar ki sa gwiwata tayi
sanyi mana: ta çe; kamar yadda na rubuto maka na fi
sha'awar ganinka fiye da sakonninka, mu yi bacci
lafiya: ta rufe, wayarta.
132
Sahabi ya tsaya galala yana kallon wayarsa kafin
ya kashe ya girgiza kai yace, Mami na kenan muyi tsiya muyi dadī kamar da gaske tana zuwa nan kwana daya ana biyu dole muyi fada.
a
Su Hajiya da su Anti hadiza kan jure haka nan su kawo ma Mami ziyara don dai su duba lafiyarata,
amma lokaci lokaci ne sukan yi dacen samunta
gidan amma lokuta da yawa sai dai su bar sakon abida suka zo mata dashi hannun su kiristin ko Ya'u.
wani lokacin kuma akan dole Hajiya kan yo mata
waya ace ta shirya za su kobarkar haihuwa ko
gaisuwar rashin lafiya na yan'uwansu Hajiyan ko
aminanta, wai don dai kada ace an bar Mami haka
nan, mijinta bai nan su kuma ba su kula ta, amma duk
wannan bai sa Mami ta saki jikinta da dangin mijin ta
ba.
Tun ana sauran kwana hudu Sahabi zai zo
Kaduna ya rinka turawa Mami text na cewar ga shi
nan zuwa insha ALLAH daga Abuja zai taho kaduna
kuma sai ya yi mata kwana biyar ko shidda, Mami ta
kan yi banza da text din sa, domin ita a ganin ta
Sahabi ya wulakantata ace har wata biyu dayan'
kwanki bai zo ba, ita kam ba zata iya zama yar tsaron
gida ba, ko yar rakiyar Hajiya anguwa.
Ranar laraba Mami na tasowa aiki gidan su ta
wuce, ta yi wance dakin su anti Zainab bayan jikinta
na bata lalle rannan Sahabi zai zo, hatta kawarta me
zuga ta Maryam Bishir ta bata shawarar kirki inda ta
ce ya kamata ran da Sahabi zai zo ki zauna gida ki yi
masa kyakyawar maraba Mami.
133
Karfe biyar da rabi daidai bawa bai gwada lokaci
Sahabi ya iso gidansa na kaduna a cikin galleliyar
motarsa wadda wajen aikinsa suka bashi ga cikakken
direbansa peter, but fin motarsa cikc take fam da
tsaraba. ko super holland turmi shiddace ya aje ma
Mami biyu hudun yace aje ma Hajiya da su ga lcs
guda biyar na Mami biyu na kannansa uku, sauran
tsarabar kuwa kayan ciye ciye ne, ya hada peter da
Ya'u suje gidan Hajiyan ya ce, azo mai da Uwani
daga nan,
su kan su Uwani sun yi shirin zuwan Sahabi
domin abinci hatta peter sai da ya ture, uwani da
kiristi da Ya'u sune suka gyara ko ina suka shirya
komai, Sahabi ya shiga dakin baccinsa ya zauna
gefen gado ya yi sukuti, a iya tunaninsa bai san
dalilin da ya sa Mami ke masa irin wannan cin
Kashin ba, wai duk masu auren soyayya haka suke
tsintar kansu koko dai shi ne dai marasa'a? komi yace
zai aiwatas kan Mami aikin banza ne, sam bata
tsoransa balle shakkarsa, haba don ALLAH duk irin
zakwadin da ya ke.yi na son ya zo ya ganta amma
wai ita bata damu da ganin sa ba, kuma mako ba zai
zo ba, ina amfanin ace bata gida har zuwa irin
wannan lokaci? Shin ko dai addu'a zai fara yi ne idan
har Mamiba Alheri ba ce agareshi ALLAH ya rabasu
anan kuma so ya yi rinjaye. Sam bai iya yin wannan
addu'ar kai tsaye!
Mami ta yi anfani da karim magana nan da ake
cewa (kowar bata ya sani, kowar gyara ya sani)
saboda haka sai ta daidaici daidai lokacin shigarsa
134
masallaci sallar isha'I, sannan ta shigo gidan. Su
Uwani ana ta kai kawo ta yi sallama ta shiga, anan ne
Uwani bayan sun gaisa ta ce, O'ohh amaryar ce sai
yanzu? To mun cinye tsarabar sai ki jira wata: Mami
ta dan yi murmushi amma cikin ran ta ta soma
tsinewa Uwani, ta bude dakin ta ta shiga, ta yi wurgi
da kayan ta ta mikar da hannu ta Sabuli ribon din da
ta tukke gashinta, ta yi war ta shiga ta yi wanka ta fito
ta saka zulun buwar riga ja, tana tsaye tana sharce
gashinta zuciyarta na ta tiriri dangane da zuwan
Uwani, gaba daya ma ta tsani zuwan Sahabi har bata
kwadayin ganinsa ya fi minti goma da dawowa daga
masallaci a bisa dole ya doshi fakin Mami, ya shiga
ya tsaya yana kallonta ita ma ta dago ta dube shi,
abinda idonta a gani ya bata tsoro domin ya yi kiba
ya yi fari, irin farin nan mai kyau, ko lokacin farkon
haduwarsu Sahabi bai kai kyan haka ba, nan da nan
sai zuciyar ta ta saduda tabbas Sahabi bai tunanin ta
don haka ma ko kusa tasan bai damu da ita ba, shirme
take yi akansa, idanunta su kai rau, rau kwalla ta
cicciko, ta jure cikin rudani ta ce sannu ya ce menene
sannu: wai kina ko da hankali Mami a matsayina na
mijin ki na dauki lokaci mai tsawo bani gida amma
ace a wannan lokacin ba za ki iya tsayawa ki nuna
man mutuntawa ba ta zahiri a ko da yaushe sai dai na
sami kyautatawa daga wasu jinsin jama'a
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 13