Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yau bai dace ba ace tun da akai rasuwar nan ba muz auna mun yi magana ba sosai da sosai ko saboda rayuwar kannarnki, wannan zan ce yayi ma Mami gardi domin tana son ayi ta ta kare saboda dai rayuwarta ba wani anfani tsakaninta da Sahabi, nan take ta shirya. Yadda suka tsalo ado suka zo cikin raharsu,s ai ayau Abduljala ya yi farin ciki da Mami, nan da nan ya bude masu falo na musamman suka shiga aka sha hira sosai. Sannan Sahabi ya ce, baba na zo wajenka da Mami a matsayinka na mahaifinta don ka zama shaida a nan Abduljala ya yi sukuti yace, mene ne? Ya ce a zato na dai Baba ban taba kawo ma karar mami ba kuma ba wai don muna zaman lafiya ba ne, a'a ina ganin dai ko an kawo karar ta ta babu amfani saboda irin tarbiyar da Mami ta samu kenan Baba ka yi hakuri ba ina son cimaka fuska ba ne, a'a ina amaye maka kululun da ke damu na ne, to a yau din ba ban kawo ta kara ba, na kafa ka shaida ne a matsayin mahaifinta, shaidar kuwa itace, Mami na dauke da ciki 181 2 na har na tsayin wata hudu ama ta je asibiti a debe mata saboda zata yi tafiya turai karatu, to na ji na amince tana iya tafiya bayan duniya ma amma ban yadda ta je da ciki na ba, haka nan ban yadda ta zubar man da ciki ba, in wani abu ya sami wannan cikin to wallahi zan yi sanadiyar kai ta kurku ku ta kare rayiwarta a can a dalilin ta yi kisan kai. In kuma kin dauka karya ne ba zan iya ba, ga fili ga mai doki mu zuba ni da ke. Abduljala zuciyarsa na tafasa ya ce, Mami kice man karya ne sharri ake maki, ba ki nemi zubar da ciki ba, Mami ta yi shiru yayi tambayar duniyar nan ba amsa. Sahabi ya ce, wallahi baba kaga ma takardun ni ina da shaida duk in da za'a. Ya nuna mai takardu ya duba ya girgiza kai yace, tur da ke Mami Sahabi ya mike zanbur ya ce ki zauna a gidanku ki yi duk abinda ranki ke so amma ba zaki kisan kai a gidana ba, kuma ina kara tuna maki ko cikin nan ya zube daga Allah ne ba zan kyale ki ba, don bazan iya amince ma raina ba. Ya yi wa Alh. Abduljala sallama ya fice abinsa, Gidan su Mami basu waiwayi Sahabi ba; gidan su Sahabi ma ba a waiwayi su Mamin 182 ba, illa dai kawai su Hajıya an duka ga addu'a. Rannan Sahabi ya zo wajen Hajiyar rai a bace hankali a tashe, yace, Hajiya Kalil dai yayan Nana yasa rana zai daura auren Nana sauran sati uku, amma kuma wai ta gudu can wani kauye a kasar Gombe, ni abun damuwata yarinyar nan bata san love din uwa ba bata san love din uba ba, sai ni kadai ta ke so, shin anya ba'a dauki alhalin ta ba kuwa? Kuma na je kauyen da ta gudu gidan kanin Baban su ne, wallahi ba ki ga yanayin gidan ba, ba irin gidajen da ta saba zama ba ne; Hajiya ta ce, ban ji dadinw annan labari ba, to kai din ma ka ga yadda ka koma kuwa ka yi hakuri za mu shirya mu je muga Iyayen nata. Mota biyu Hajiya ta shirya ta maza daga Sokoto da ta Hajiya da 'ya'yanta, har Gombe, suka soma sauka gidan maman Abdul, daga nan maman Abdul ta yi masu jagora ita da mijinta har gidan Iyayen Umma, an yi sa'a Kanal Kalil ya zo aka rinka cusa mai magana, mahaifiyar Kalil tace, kaiwa Allah ka dubi girman Manzo ka hakura da zancen Amadu din nan, kamar yadda Nanan 183 tace ne zuwan Sahabi ai rahama ne ga rikicinka da Asma'u ba ace dai ta auri daya daga cikin wa'anda ku ke so ba, wannan Sahabi shi ne zabin Nana kuma daga ni zabin Allah, domin ya yi maganin duk wata rigimar gidan nan akan Nana. Kanal Kalil cikin cika yana batsew ayace, na ji sai aban lokaci na yi bincike na kuma yi nazari, su same ni a can Kaduna gidana. Cikin sati biyu kusan kullun Hajiya sai ta tura su Mallam Adamu gidan Kalil, har yau dai ba ashawo kansa ba, Hajiya ta ce wai Mallam Sahabi kuwa ya sa ka yi istahara akan wannan aure na Nana? Yace E to, ya yo man waya tun lokacin da ya soma nemanta, duk wanan rigimar ba komi Hajiya kafin dai ta je gidan ne, amam da zarar an yi auren za'a samu natsuwa a tare da yarinyar. Ku kwantar da hankalinku ba komi insha Allah. Sahabin da kan shi ya yo ma Hajiyar waya yace, to Hajiya na je Gombe an ce dai an bani nana yau ma sauran sati biyu daurin aure da biki. Gidana na Abuja komi ya kammalu, kayan da na yi oda daga Italy sun iso tun watan jiya, yanzu tunda hankalina ya kwanta zan je na yi kiliyarin din su. A nan za 184 ai bikin ne a Abuja? In ji Hajiya ya ce, Eh, ai ita Nana ma tace, yini daya ne bikin nata bata son bidi'a, ran juma'a za'a daura aure a kawo ta rannan ran asabata yi yini kowa ya watse, hidima ce, gatanan kan Sahabi ga aure ga sabon gida, gida kuma ba irin wanda irin mu ya ku bayi muka saba gani ba, idan ma mun yi dace da ganin irin sa sai a finafinan turawa ko 'yan kudu. Nana ta shige sukuf gidan mijinta Sahabi, in ma sakayyace to a gaskiya Allah ya yi ma Sahabi, domin Nan aji take dashi kamar kwai, abinci sai dai wani ya iske wani, bayan wannan ma nana ce mai kula da hankicinsa, singileti, panties, hatta takalmansa Nana ta adanasu a ma'ajiyarsu daban, kayansa itaсе mai fidda wanki na dry cleaning daban wanda yaronsu zai wanke ya goge daban, tana da yarinyar mai tayata aiki amma Sahabi sai ya kwana uku bai sa yarinyar a ido ba, nana ce dai a dama da hagunsa, in dai suna tare basu gundura da juna su yi ta hira har idan mutun na gidan ya rasa wai me suke fadawa junansu ne? Nana ta saba da su Hafsat da Aisha kamar ciki daya suka fito 2 185 dan lokaci Kankani nana tana ganin ta sami uwa, wato Hajiya kenan. Mami na fama da tsohon ciki ta ji labarin auren Sahabi, bata yi mamaki ba, tasan dole hakan ta faru saboda wulakancin da ya yi mata a gaban mahaifinta abin ya daure mata kai,w ai Sahabin da ta mayas banza, shi ne ya yi mata haka? Kuka ma bai da amfani, duk wanran ma ba shi ne matsalar ba ta gidansu tafi da munta, saboda Abduljala amininsa ya bashi auren kanwarsa a Kano don haka yanzu bai da lokacin kowa sai na zukekiya kuma kamilarliyar amaryarsa, domin ya baiwa su Anti Zainba notice ko su yi aure ko su koma gidajen iyayen su can maiduguri, hatta samarin gidan masuyin sakarcin yace a koma gida na kirkin kamar su Baba Sadiq ya nemar masu aiki ya kuma samar masu gidan zama. Cikin dare haihuwa ta zo ma Mami a zamanin Sahabi ana gabar amarci shi da Nana, su kannen Iyana wa'anda aka dauko don su lura da mami ada can mami ta tsani su lyagana amma yau saboda tsananin azabar ciwon haihuwa bata san lokacin da ta rungume Iyagana ba tana kuka tana fadar zancen da ba su kamata ba, tabbas yau ciwon 186 haihuwa ya saukarwa da Mami ladab a fili da zuci. Da asubar fari Mami ta haifo sanbalelen yaro mai kama da ita, komi na Mami, inda diya macece kila da an yi Mami 'yar small. Saida aka sallame su suka koma gida sannan Iyagana tasa Zainba ta yi ma Hajiyarsu Sahabi waya tace Mami ta haihu kuma lafiya lau sun yi murna, fiye da zaton dan adam, kafin kace me ye wanan zuri'ar su Sahabi sun cika gidan makil da kayan su na beby rakatakam, wannan ya dauka ya yi mai addu'a wanan ya dauka ya yi mai addu'a, addu'a kam ya shata, tun da ya zo duniya hannun a baki Iyagana ta ce, don Allah kusa mana baki ta soma bashi nono Mami tace, ita so take ma su tafi da shi suba Sahabi dan shi, Hajiya ta dafa Mami tana yi mata nasiha tace, Haba mami idan kina fada da Sahabi sai ki yi hushi da dan ki,w annan dan Mala'ikan Alah me ya sani a duniya, ki tuna hakkin da da mahaifi, ba wai ba mu iya rike shi ba ne a'a kín ga Sa'adiya ga tanan da jariri sabon baihuwa zata iya hada su ta shayar baki daya, 1o amma ke da jaririn na ke tausayi, can gaba a ki nadamar da babu amfani. 187 kugunta da marar ta duk sun bude hatta cibiyar ta ta fito fili, ta dora hannu a mara, jikinta ya kara tsinkewa ta yadda koma mene ne a jikinta ya soma zama gudan mutun, ta fashe da kuka tana zagin Sahabi akan ya cuce ta, wai ciki! Kuma da Sahabin da ta tsana a yanzu? Ta maida kayanta ta koma daki ta balle sabon babin kuka. *** *** Sahabi ya linke takardu ya soka a aljihu yace, ba komi Hajiya zan yi maganin al'amarin ya mike zai fita tace kada dai ka yi hushin zuciya ka aikata aikin dana sani, ya ce, kada ku ji komi Hajiya zan bi komi a hankali. Ya isa gidansa a lokacin mami na gida tana kwance a falo, ganin motarsa ta mike da sauri ta shige daki, a ranta bata so zuwan sa ba amma wani bangaren tana so don in ta kammala da zubar da cikin zata sanar da shi zancen tafiyarta. Ya iske ta cikin dakin kowane cikin mamaki shi da ita, domin kowannensu borin kunya ya cika shi, ya ce, Au Mamis hi ne kika boye don kin ji zuwana, ine gajiya? Tace lafiya lau? Ya jure ya zauna kusa da ita, ya kamo wancan ya kamow anan 188 lyagar a yi masu barka aka miko masa jaririyi mai addu'a mai makon ya ji tausin Mami sai ma ya rinka jin haushinta, wai wannan kyakkyawan yaron zata zubar mashi? Son dansa ya shiga rans aya yi ma Allah godiya. Cikin dacin rai ya dubi Mami kamar ya ce mata babu abinda ake bukata? Amma kuma sai ya fasa ya dube ta ya watsar ya aje jaririn gefen kafarta inda take kwance ya juya ya fice. Ta yi iyakar kokari ta yi kuka kwallan suka ki zuwa, kirjinta ko kamar zai tsage don bala'in bakin ciki, wai ma Sahabi a cikin mutane shi zai yi mata haka! Ta kurawa dan su ido yayin da yaron ya soma kukan son nononsa amma kamar Mami bata cikin dakin, bata dauke shi ba, sai can Iyagana ta shigo a guje ta dakawa Mami tsawa tana yi mata fada, Mamin ta dube ta galala tamkar mutun mutumi, har dai Iyagana da fahinci halinda Mamin ke ciki ta isa gare ta ta rike ta tana bata magan a anan en Mami ta fashe da kuka, ita kuka jariri kuka. A ranar suna ya zo ya ci sunan Abduljalal hajiya da Sahabi suka zabar masa. Da azuhur motoci shidda niki-niki da akwatuna na bebi da maijego da 'yan uwa 'yan suna suka isa 189 gidan su mami a cikin ayari har da Nana ta yi kyau ta yi kyau har ta gaji zinari da zinari dai sun kama jikinta sai haskakawa kawaita ke yi, kamshin ta kuwa na (Ihsan colection ne) don haka da gani kasan matar wani ce wadda mijinta ya kama kasa, itama kanta Mami tana ganinta nan da nan ta sare ta amince jar fata ma suna suka tara, bakar fata ma da ranar ta, da gani babu tambaya Sahabi da 'yan uwansa sun sami irin tasu, nan ne kishi ya nemi kashe ta don dai kwanan ta na gaba. Shekara daya cif da auransu nana ta aje ma Sahabi 'yar diya mace sunanta Aisha amma suna kiranta Ihsan. Babu abinda ya canza a zamansu, har tsokanar ta ya kan yida cewa ina son na ga hushinki Nana, ta kan ba shi amsa bana maka fata don ba ni da kyau in na yi hushi. To ba wai zuri'ar Hajiya ba kadai hatta zuri'arsu ta Sokoto yanzu Nana ta yi karnene a cikinsu domin lungu-lungu tabi ta saba da su, duk wani biki yadda su Anti Hadiza za su itama daga Abuja zata je tare da Hafsat wadda ke zaune tare da ita tana karatu a nan jami'ar Abuja. Yadda ya shirya gida a Abuja yanzu haka ya kusan kammala wani a Kaduna shi din ma 190 ya kusa na Abujan. Mami ta amince bata son hail va amma kuma mai iya raba ta da danta sai mutuwa, don haka akan dole ta janye girman kanta ta roki mahaifinta dan ya roki sahabi ta koma dakinta tun da dai ba sakinta ya yi ba. Alh. Abduljala ya je har Abuja ya iske Sahabi a ofis sun gaisa sosai sannan ya zare gilas din idonsa kogin idonsa cike da kwalla yace bana son kace man komi ni nasan ka sami kwanciyar hankali wadda ba ka samu ba tare da mami, amma ka dubi girman Allah ka dubi darajar Iyaye ka yi hakuri ka bar Mami ta dawo gidanka. Tamkar Abduljala ya daба mai wuka a kahon zuci nan da nan ya tunbure rai ana so a 6ata mai rayiwa kenan,- me ya ke so a mace wanda bai samu ba a Nana? Abduljala ya katse tunaninsa ya ce, ka yi hakuri tunda ka ga na zo har ofis din ka ni nasan Mami ta canza ne, idan ada ne ai da ban matsa maka ba ka dai taimaka mani. Irin kwallan da ke zuba a idon Abduljala dole ya ce to ya amince, amma zai yi tafiya sai in ya dawo. Kasar Taylan suka fara zuwa Nana da sahabi da 'yar diyarsu Ihsan, sannan Japan a 191 Kasar Toki ne Sahabi ke fadawa Nana bukatar mahaifin Mami me kika gani? Tace kana zaton kishi zai sana baka shawara kada ka zauna da matarka? Haba SAN ai ban cika diya mace ba kenan ina sane da ita fa na kallafawa raina son ka, ba abunda ya dame ni da ita, ka dawo da ita wallahi, ka taimaka mata yace kin san Allah idan na tuna zan sake zama da mami har zazzabi na ke ji? Ta ce, kada ka damu ka tuna yanzu ba ita kadai bace, kana zaton zan kyale ta ta yi ma irin abubuwanda ta yi maka ada? Kasan Allah daya ne, ba faďa ba zagi, ko dai ta canza hali ko halin ta ya koreta, tana tsammanin maza irin ku ba tsada ku ke yi ba dan ta samu zata wulakanta? Ya fada akan nana ya makalkale ta suna kyalkyatar dariya tace, kada fa ka yi ma Anti Hadiza asarar ‘ya'ya kasan a wayar da ta yi man kwanan baya tace, 'yan biyu take jira. Ya bude baki fuska cike da fara'a shi ko ba'a fada mai ba yasan Nana ce uwar 'ya'yansa kuma gurun hutunsa abin biyan bukatarsa aminiyar shawararsa a kullun. 192 *** *** Mami ta koma, itama ta shige sabon gida da dan saurayin dan ta Abduljala, bai faye waye ba Ihsan ta fishi wayo duk da ya fita girma, ta zama shiru-shiruda ga sahabi har 'yan uwansa yanzu tausayinta suke ji. Nana ta kwallawa Hafsat kira ina Karamar jakar nan? Ta ce wacce mai takaddu a ciki? Ko wadda aka zuba shaddoji da atanfofi? Tace A'a me takardunta ce, Gaba daya duk mun zuba a mota! Nana tace very good, na gidan Anti Bilki ne, kin san zamu tsaya Funtuwa kafin mu shige Sokoton Sahabi ya shigo ya ce, Hello my Queen na ji ana zancen zuwa Funtua ba na ce ki jira sai mun je London mun dawo ba? ta ce Haba SAN na yi ma Anti alkawari 3 x fa kenan kuma ni kadai take jira ta fitas da litafin nan ka ga ya dace ai taja ma jama'a rai? Ya ce, wane littafin kuma? Ta ce Na Girke-Girke mana, na yi mata alkawarin zan rubuta mata wasu, to na gama tuntuni ko a daran jiya mun yi waya nace zan je Sokoto zan biyo na kai mata, yanzu kuma sai ta ji shiru? Ya daga hannu ya 193 . ۳ ce, Yes kin fini gaskiya. Ki gayas man da ita kice ban manta da sakon taba kar ta yi hushi da ni don Allah tace, ka san halin Anti ba ruwanta yanzu haka ma ta manta da wannan ya ce yaushe za ku baro Sokoto? Tace kwana uku za mu yi, ina jin zamu Birnin Kabbi ni da Anti Hadiza ka san za mu kai kudin auren Abba ko? Ya ce na san da wannan zan dai jira ki a Kaduna. Ya dauki Ihsan yana mata wasanni sai da ya raka su har cikin mota ya ga tashinsu sanan ya tafi hidimarsa. *** *** *** Bayan wanan tafiyar da 'yan watanni Nana ta haifi 'yan tagwaye maza, Ahmad da Muhammad. Anti Bilki ta aiko mata da litafin girke-girke a matsayin gudunmowarta ta 'yan tagwaye. Duk macen da ke ji da kanta ta je suna a cikin kayan sunanta zata tsinci littafi mai suna mu koma kicin na Anti Bilkin Funtua. 194 Mata sun yi murna sun yi alfahari da wannan littafi Nana na shan waya akan ko litafin ya je kasuwa? Itama Mami ta zauna a tsanake ta karanci littafin tun tana jin za fi saboda kishi har ta soma natsuwa tana baiwa kan ta shawar alalle Anti Bilkida Nana sun yi gaskiya MU KOMA KICIN wanan ma kamar dan ita aka yi saboda har yanzu bata sami kan Sahabi ba ko ya zo weekend a gidansu ya ke cin abinci. A karo na farko Mami ta yini zungur a kicin tare da sabuwar mai aikinta, domin tuni Kiristi ta yi aure ta sami Mairo 'yar karamar yarinya. Yau ta iya tuwo, ta iya miya, tun daga wannan rana Mami bata sake zama ba, sai koyon girki. Musamman ta yi ma Anti Bilki addu'a lokacin da sahabi ya zo ya ci abincinta ya zauna dirshan shi da dan sa Abduljala wannan yasa mamita aje aiki domin kudi na Sahabi matarsa bata bukatar komi a duniya sai neman lahira. Wata irin sabuwar mota ce Sahabi ya sayawa Mami da Nana kalarsu daya mai suna (Jeep C.R.V) ja ce shar mai kashe ido Mami ce a ciki ta tuka zuwa tudun wada ta shiga 195 ce, Yes kin fini gaskiya. Ki gayas man da ita kice ban manta da sakon taba kar ta yi hushi da ni don Allah tace, ka san halin Anti ba ruwanta yanzu haka ma ta manta da wannan ya ce yaushe za ku baro Sokoto? Tace kwana uku za mu yi, ina jin zamu Birnin Kabbi ni da Anti Hadiza ka san za mu kai kudin auren Abba ko? Ya ce na san da wannan zan dai jira ki a Kaduna. Ya dauki Ihsan yana mata wasanni sai da ya raka su har cikin mota ya ga tashinsu sanan ya tafi hidimarsa. *** *** *** Bayan wanan tafiyar da 'yan watanni Nana ta haifi 'yan tagwaye maza, Ahmad da Muhammad. Anti Bilki ta aiko mata da litafin girke-girke a matsayin gudunmowarta ta 'yan tagwaye. Duk macen da ke ji da kanta ta je suna a cikiń kayan sunanta zata tsinci littafi mai suna mu koma kicin na Anti Bilkin Funtua. 194 Mata sun yi murna sun yi alfahari da wannan littafi Nana na shan waya akan ko litafin ya je kasuwa? Itama Mami ta zauna a tsanake ta karanci littafin tun tana jin za fi saboda kishi har ta soma natsuwa tana baiwa kan ta shawar alalle Anti Bilkida Nana sun yi gaskiya MU KOMA KICIN wanan ma kamar dan ita aka yi saboda har yanzu bata sami kan Sahabi ba ko ya zo weekend a gidansu ya ke cin abinci. A karo na farko Mami ta yini zungur a kicin tare da sabuwar mai aikinta, domin tuni Kiristi ta yi aure ta sami Mairo 'yar karamar yarinya. Yau ta iya tuwo, ta iya miya, tun daga wannan rana Mami bata sake zama ba, sai koyon girki. Musamman ta yi ma Anti Bilki addu'a lokacin da sahabi ya zo ya ci abincinta ya zauna dirshan shi da dan sa Abduljala wannan yasa mamita aje aiki domin kudi na Sahabi matarsa bata bukatar komi a duniya sai neman lahira. Wata irin sabuwar mota ce Sahabi ya sayawa Mami da Nana kalarsu daya mai suna (Jeep C.R.V) ja ce shar mai kashe ido Mami ce a ciki ta tuka zuwa tudun wada ta shiga 195 can kasa kusa da kasuwar bacci, ta karya daidai Getso resturant, sannan ta dauki layin gidan Kifi a daidaí gidan kifin ta hango inda take nema wato Shagon Anti Bilki,ta tsaya bakin Shagon duk matasa aka yo mata ca da ido, ta shiga ta zabi dukkan litatafan Antin ta biya har zata tafi ta juya ta ce ma yaron in ka je kace ina gaida Anti ya ce, to amma wa zance? Ta yi murmushita ce, kace mata Mamin Nana da Sahabi. Har motar ta bace yaron na mamaki. 196 TUNA BAYA Tun zamanin da na soma wallafa littafi, wa'annan bayin Allah suna tare da ni, tafe su ke da kafarsu gare ni aike bisa aike, waya a kullum ba su taba nuna min son komi su kai mani sai na mayas masu ba, amma a kullun suna kokarin su nuna man zuminci da kauna ta fisabilillah a bisa baiwar da Allah ya yi man. Bana iya tuna iyakar alhairin da su ke man, sai dai Allah ne shaida ta domin ina yawaita addu'a akan ya hada mu a aljanna Fiddausi. Ta farko:- Hajiya Ummu Dasuki Uwargidan Maman Daura Nafisa Ado Bayero Mrs. Garba A.D Kano Hajiya Anisa Shehu Galadanci Mrs. Tajuddeen. 197 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 13 of 13