Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aje kudinsa ta fiddo kusan dubu biyar yace me kuma za'a saya? Ta cc ba ka ji na yi baki ba ne, Mr Biggs zan aiki Ya'u ya ce, yadda ke ma ba kya cin abincin gidan nan suma dole sai na saync, Allah ya shirya!. Ta dube saroro tace, kudinka na taba shi yasa za ka gaya man haka, ta ja tsaki ta rufe kofar bam. daman ransa a bace ykae ya bita yace rike mata hannu yace, daga yau karki kara yi man tsaki, in ko ki ka sake ranki zai baci a gidan nan, kafin ma ya ji amsar ta ya /saki hannunta ya koma dkai abinsa, amma dai babu wanda ya ji su a gidan. a D Mami ta zauna suna ta hira amma hankalinta bai tare da ita, abin mamaki lokacin da Hafsat ta gama abincin sahabi sai ta cika cooler daya ta hada farantai da komi da komi da kuma kkc da meat pie din da Kannan Mami suka sa ta yi masu ta kai masu, kawayen mami suka soma santin dafuwar shinkafa da ruwan kwkawa suka ce ke Mami wanan wacece? Tace, 'Kanwar Sahabi ce,' Suka ce, to ki yi a hankali in har da aure tsakaninsu dole ne ma ya aure ta wannan hanhun ke ko mutuniyar mun san ki da shegen son jiki kullun kina yawo Mr Biggs hala dai yanzu kin dai na ziyara? Aka tintsire da dariya, tace, Yanzu ko na ke ziyarar su Mr. Biggs wa zai man aikin ga wannan aure da na lakabawa kai na ke abubuwa dai kanana ga su nan,' Hauwa tace, Gara ke Mami ni fa auren da ky na iya sati biyar ina zan iya wannan fitina, amma ke na ga Sahabin na ki kawai natsuwa ga kunya, Mami ta yi murmushit acе, В alaifi kin fadi gaskiya kam. Bayan komi ya kammala baki sun koma gidajen hattà kannan sun gaji da sharholiyarsu sun tafi,da suka tashi tafiya ne Mami ta ce ma kaninta Hasan kace, Iyana ta je Abuja ko? Yace 'Eh, tace, Amma Baba ai yana nan? Suka ce Eh yau ya dawo daga Legas, tace, Ga takarda ku kai masa don Allah ku ce mai ina son ganin amsa yau, ya ba baba Sadiq ko cikin diribobinsa a kawo man. Hasan ya kai ma Alh. Abduljalal takarda, ya manna gilas dinsa ya karanta wasika kamar haka:- 75 Da Fatan kana lafiya Baba. Don Allah Baba ina son kudi, kasan in nace ina son kudi lalle na matsu nc. Diyarka mami Abduljalal ya dan yi tumani sai ya tuna halin yau kila basu da kudi ne daga ita har mijin, ya kuma dace ya taimaka masu tunda dai shi ya rage masu mahaifin sahabi ya rasu, nan da nan ya dauko dubu dari cif ya ce a kai ma Mami. Baba Sadi ya jima yana matsa hon a gidan Sahabi mai gadi bai da niyyar budewa domin a ganin Maigadi kamar dare yayi tunda har Sahabi ya rufe gida, can maigadi ya lcka suka gaisa Baba Sadiq har kun yi bacci ne, maigadi yanzu sha biyun dare Baba Sadiq ne daga gidansu Mami don Allah a shaida mata. Maigadi ya je ya rankwashi kofar falo a zamanin Mami na dakinta tana kwance tana takaicin yin aure, in dai haka aure ya ke bata gama anfaninsa ba a wajen ta tunda Sahabi ya rike mata hannu ya yi mata fada bata sake saka shi a ido ba har suka kwanta, wato shima ya soma hakura da ita kenan? Wannan ko itace rana ta farko da suka raba shimfida. Sahabi na dakinsa yana tilawar alqur'ani mai girma ya ji maigadi, ya tsaya ya mike ya fita, Maigadi yace, yallabai Baba Sadiq nc daga gidan su Mami, yace muje bakin get din lafiya dai ko? Sahabi ya leka yace, yaya Baba Sadiq, ina gajiya? Baba Sadi ya fito daga mota yace, yallabai "lafiya lau" Shabi yacc, Yaya dai? Ya amsa, Alhaji ne ya aiko ni wai na kawo ma mami sako ko Hasan aka ce ta aika kuma ayau take so shine yace na zo na 76 bata, Sahabi yace, 'Mami kam ta kwanta Sadiq yace, 'Ai tunda gaka sai ka amsa da kai da ita ai duk ſaya ne. Ya amsa su kai sallama. Sahabi ya zauna falo ya zubawa kudin ido, kai wannan masifa ko da yawa take daga wanan fitina sai wannan, wato ita zata fara nuna mai gadara bai isa ko kadan ya nuna mata kuskure ba, dole kaoda yaushe ita ke da gaskiya bai yi wuwa ya biye mata tunda ya yi lallashin bata ji ba zai soma yi mata wa'azi kila Allah ya shirya masa ita. Bai tayas da ita ba sai da safe bayan ya kintsa ya gama kalaci mai kyau amma daga Hafsat, sai ya sami mami a daki itama ta kammala har tana zabar takalma daga jakkar da suka dace ta sa, sai ga Sahabi yace, ina kwana? Tace lafiya yace, kin aika gida kina son kudi ko, to ga su jiya kin yi bacci Baba Sadiq ya kawo maki, amma ina son ki fahimci abu daya, so da kauna ya hada mu mami har abada ba zan taba muzanta ki ba, auren nan da muke yi don mu bautawa Ubangijinmu ne ba don mu saba masa ba, ki tuna da abinda Subhanahu wata'ala yace, wato da zan umarci wani ya yi ma wani sujuda to da mace zan umarta ta yi ma mijinta, anan Mami ki dubi matsayin mijin wajen matarsa, shin mene ne laihi na don kawai an kawo kanwata ta taimaka maka mu kare mutuncin kan mu?. Ta mike tsaye ta gyara gyalenta a kafada ta dauko makullen motarta ga G.S.M. din ta manne a tafin hannu tace, yaya ka gama? Ya girgiza kai gami 77 da murmushi yace, mu yini lafiya yasa kai ya fice, itama ta fice. Yau Mami bayan ta taso daga aiki a Classyburgers. Ta tsaya ta zabi abincin da yayi maka dadi ta biya ta doshi gida. Ta iske ko ina na gidanta ya kaure da kamshi na abinda Hafsat ke girkawa, tana zaune a falo da litattafan birjik tana tilawa tana kuma lekawa kicin dubo girki, a nan zuciyar mami ta yi kuna a gaskiya ta sakewa Sahabi yana son kawo mata raini a gidan nan dole ne yau ayi mai yiwuwa ko ita ko Hafsat. Lokacin da Sahabi ya dawo aiki ya hango mami ta fito daga sito tana fiddo kwalayen juice tana zubawa a firij, da alamu kamar fuskar Mami a sake take, ya dan dube ta cikin kasaita, yace, Hello Madam ya ki ke? Ta juyo a yangace ta ce, i'm okey, ya ofis? Yace, mun gode Allah, aiki ne as usual, ta shiga daki shiko ya nufi wajen cin abinci, ta tsalo wanka sannan ta sheko kwalliya ta fito cikin wata irin shiga ta alfarma, wani yadi ne mai daukar ido, kalarsa ruwan hoda amma ya turu kalar dinkin siket da riga ne, rigar an tsuke tunda ga kirjin har kugu amma ta sauka kasa sosai hanun ma ya dago ya kuma yi tsawo, babu dan kwali sai dogon gulae madadin dan kwalin, shi ta rufa tun daga sama har zuwa wuyanta, ta yi kyau fa gaskiya. Takalman ta sai daukar kunne suke ta isa falo tace, Sahabi na tafi lunching din Fati Garba, ya dube ta tun daga sama har kasa mace har mace amma bata cika 100% ba, rashin kula da cikin miji. Yace, Na so yau ki kai 78 Hafsat wajen telanki ya auna ta, tace, yau kam ba zai yiwu ba kasan matsayin Fati! Ya ce, 'Haka ne, sai kin dawo, don Allah kada ki shige karfe takwas. Tana bisa titi tana tukin motar ta kowa ya ganta kamar ya dauka ya hade ta, amma ba su san mami ko shinkafa bata iya dafawa, ba kyau har kyau, ga ado ga kuma dukiyar adon. Ta zauna wata kujera daga can baya a lokacin amarya na cashewa ita da ango a gaban masu kidi, tunani kawai Mami ta ke yi, wai wata hudu da su ka wuce ita da Sahabi kae ma irin wannan shagalin amma yau ga Sahabi ya zame mata dan zani, yanzu ita Fati gani take bata iya hada kowa da Sagir? Shima a ransa hakan ya ke gani, to mnee ne dalilin da so ke zama ki? Idan da 'yan mata za su nemi shawarar ta ita kam da sun tsaya ga samartaka da yan matanci kawai ya isa, ba su kai ga tkaurawa kan su ga aure ba, yadda ma ta fahimci Sahabi bai damu da al'amuranta ba sai na su Hafsat, wai ma ta kai ta wajen tela? Dole fa ta budewa Sahabi ido game da kilababbun 'yan uwan nan na shi. Ta Mamin Sahabi ta juya ta mika mata hannu Maryam, ta kama ta zagayo ta zauna suna mai fuskantar juna, maryam tace, ran amarya ya dade, Mami ta dan duka kusa sosai da Maryam ta ce, 'Na tsani aurne nan Maryam kin huta da baki yi ba, haba don Allah kada ki kayas man da gaba man, in ji Maryam sai Mami ta ce, ba haka ba ne, still ina son Sahabi abinda na tsana 'yan uwansa ina ruwansu da gidana so su ke su mayar da ni 'yar renon 'ya'yansu shi ma sahabin na rinka renonsa tamkar jariri to ni irin wa'anan abubuwan ke 79 sa na ji na tsani auren da shi ma Sahabin. Ke ma Mami kin yi saurin sake masu ne, yaushe ku kai auren da har za ace sun soma katsaladan a gidan ku, mami tace, Wai! Ba ki san wa'annan ba wai su masifar son juna suke yi, Maryam ta ja tsaki tace, ina ruwanki da kaunar su, ke son da ki ke masa ai yafi nasu, kin san Allah zan gaya maki, ki raba sahabi da wa'annan tarkacne mutanne gaisuwa ma ta musulunci su yi a waya, ko ba kya son sa ne? Mami ta yi tagumi ta yi shiru ta tuno daren jiya ta yi kwanan kunci a dalilin kaurace matan da Sahabi ya yi, insha Allah baza ta sake amincewa hakan ta faruba, ta daga kai ta dubi Maryam tace, 'Wallahi Maryam har yanzu bani da gwani kamar sa, ni dai canza tsarin rayiwa da yake yi min kawai ke hada ni da shi, tace ki manta da wannan ki ci gaba da nuna mai so ba wai kyale shi za ki yi ba, ai sai su yi nasara. Can mai waka ya dau lokaci yana wasa mami aminiyar Maryam ga amaryar Sahabi da ranarki, suka mike suka nufi filin rawa suna tafe suna hirar su wadda ta shafi auren Mami, a fage Mami ta 6alle bandir na dubu biyar itama Maryam haka suna likawa amarya daga bisani suka rinka likawa junansu. Suka koma wata rumfa Maryam tasa 'yan hidimar biki suka kawo forozin cikin soyayya, suka ci sosai aka kawo masu juice Mami bata sha ba tace me je Maryam ki raka ni farm fresh musha madara mai san yi. A farm fresh sun zauna a waje mai san yi suna shan madara sun yi kyau wasu maza biyu masu aji 80 suka rinka son su tankawa si Mami, amma har Maryam bata ba su fuska ba a dalilin auran Mami, a nan ne har Maryam fin tace, To kin ga a nan gaskiya ba kowa zai so ya kyale matarsa ta rinka zuwa irin wa'annan guraren ba, dole ne mallam Sahabi ya yi kishi! Suka yi dai murmushi. Tkawas saura 'yan mintoci Mami ta shiga falon gidansu, Hafsat ta ce, Anti sannu da zuwa, tace, yauwa sannu da gida, ya sahabi fa? Tace, yana masallaci, itama mamin ta shige daki ta yi sallolin ta, ta gama ta koma wajen madubi ta gyara fuska hoda da janbaki ta kara domin Sahabi ya sha gaya mata janbaki na yi mata kyau. Ta mike kamar ta je falo amma sai tace bari ta bashi lokaci ta san halinsa runbu ne, yanzu abinci zai ci, idan ya gama ta je su yi magana, amma sai taji an turo kofa, ya dube ta da irin fara'ar nan ta kauna, yace, Mami yau kin yi min kyau shi ne ko kice na raka ki bikin? Ta dan dube sa a yangace tace, in da ka so zuwa da baka...' ya yi sauri ya talalfe ta yace 'Mami' cikin dariya, ya rungumeta cike da wasanni wanda ya saba mata har ya kai ga kashe wuta, ta yi sauri ta kunna, tace Baka fa ci abinci ba? yace, manta don Allahc an an jima na ci tace, A'ah ka je ka ci abincinka, sannan a gaskiya zan ga ya maka wallahi! Wallahi!! Ba zan iya zama da Hafsat a gidan nan ba a yadda abubuwa ke tafiya, haushi ya kama shi yace, me ki ke son na yi? Tace Та bar man gidana na yi rayiwata da kai yace, in ba hakan ba fa, Mami cike da rashin kunya tace, yadda ita ke ba ka abinci haka nan kafin ka ce Mami ko 81 kiristi ka kira Hafsat sau goma a gidan nan to har lalurar auratayya ka je na yafe ku yi da Hafsat. Ya dafe kan sa yace Innalil....' Wani kunci da bai taba ji ba a zuciyars asai a wannan rana, duk wata muguwar sha'awa da ya ke ji ta Mami sait a gushe, yanzu da haka sharrin mata ya ke amma har wasu mazan kan iya tara mata hudu a gida yau ga guda daya wadda ya ke so kamar ransa tana bata mai rai har bai son ma ya bude ido ya ganta. Yace, mami tunda kika iya budar idona ki ka gaya man haka babu irin zagin da ba za ki maun ba, haka nan tabbas komi za ki ce man na an baki son 'yan uwana, insha Allah daga yau Hafsat ta bar maki gida. Ya mike a sanyaye yaf ita, ya iske Hafsat a kicin tana shirye-shiryne abinda za'a ci da safe don tana son shiga daki ta yi karatu, yace, Hafsat maza fito da dukkan kayanki za ki koma gida, cikin murya mi kauri jin haka yasa Hafsat ta razana, ta yi hanzarin fitowa ta shiga daki ta hada komi nata, ya kira Ya'u ya dauketa zuba mata a mota, ya ja sai gida wajen hajiya Aisha, Hajiyar na zaune itama tana rubuta wani rifot ganin su kwaran kwaran ta san babu lafiya, ya dade zaune ba irin tambayar da Hajiya ba taima Sahabi ba amma sai ajiyar zuciya, ya ki fadin komi sai a karshe yace, hajiya Mami na fama da lack of home training wato tana fama da rashin tarbiyar daga gidansu, ta tsuke baki abinda ya dame ta kenan atun ranar haduwarsu da mami tace Allah yas hirya ba hushi dai za ka yi ba, sai addu'a sanan ka mike da nuna mata iya gaskiyarka, kada kuma ka kuskura ka 82 la le la a ta 3. la n a i, ai in di n si la i, ai la yi la ar la ar ns a ci yi mata sanyi-sanyi da dokar Ubangiji, idan ka jure wa'annan Allah zai baka sa'a a kanta, in ko ba haka ba kai ne wahalalle. Bai dai sanar da Hajiya irin zafin da mami ke hada masa ba. Ya koma gida bai ma dubi abincin da Hafsat ta shirya mai ba, ya hado ti mai zafi ya sha ya nufi dakinsa yayi alwala ya gabatar da nafila da addu'a sannan ya soma karatun alqur'ani ya gyara shinfidarsa ya kwanta, tunani sannan bacci da mafarkai barkatai suka ritsa da Abubakar Sahabin Manzo. Ita ko 'yar gatan gidan Abduljalal da Iyana har talatainin dare ta kasa bacci a zaton ta sahabi zaida wo ya kara neman ya biya bukatarsa da ita a nan ne zata kara nuna mai matsayinta ya zarce na kowa a gare shis annan kuma ta sauraresa don dai ya rinka tsoronta, ta rinka tukuburi, duk yadda ka ayi sun yi gumar ta a gidansu, tunda haka ne ma ta fita hanyarsa dag ayau baza ta sake haďa jiki da shi ba har sai ya gane kurnesa. Da safe babu mai saurarne wani kowane zuciya ta cika sa taf, zaman kuma Mami da sahabi ya koma irin aurne zamanin nan, wato ga dukiyar ga abubuwan jin dadi ga dimbin so da kauna amma rashin tarbiya ta hana aci moriyar ribar rayiwa. An koma irin rayuwar da ana aikne Ya'u kwaran-kwaran da kuloli sayne abinci, yawancin abokan Sahabi na cikin gari ko sun zo sai dai su sha ruwan sanyi da juice ayi hira su tafi, idan 'yan uwan sa ne Kiristi ce zata kawo abinda ta dafa mai iya ci ya ci wanda bai iyawa ya tsame hannu wannan kenan. 83 Yau wata shidda cif da aure sahabi ya dubi kalanda a son ransa ya so shi da Mami su yi ko hutun kwana uku ne su kadaice daga jama'a zuwa wata Kasa African countries ko kuma wata jiha cikin jihohin nan masu tashe su more rayuwar aurnesu, amma ina! Shi rabonsa ma da Mami ko yana iya tunawa ma? Duk ya komade ya motse kamar dan shekara hamsin, itama Mamin wannan karon ta rame ta yamutse, da ganin ta ba kwanciyar hankali, sun rasa gwani a wajen girman kai a cikin ko da ya ke a gaskiya Sahabi ba shi da girman kai, fata mai dai aka yi, tunda bi kam ai yana iyakar kokarinsa. Kao da yaushe idan Iyana na garin Kaduna tana kai wa diyar ta ziyara, tsarabe-tsarabe irin su kayan ciyc-ciye su na kwalliyar mata iyana kan kawo ma diyarta a yau ma ta zo mata da wasu karori da na sha irin na anfanin kara jin dadin jima'in mata Mami ta amsa ran ta a 6ace ta bude wani dan kawati a ban daki ta aje. Iyana tasa hannu ta shafi sassan wuyan Mami tace, wai ranar me kike ne a 'yan kwankain nan? Ni na ga mijin nkai kamar ba zai yi fitina ba, to me ke sa ki rama, ko ciki gare ki? Mami ta yi yar dariya tace, Iyana ciki! Ni jiya ma na yi wanka ba abunda ke damuna, fitinar zuwa aiki dai ce in na dawo gida bana samun hutu yawan baki da dai 'yan Kananan abubuwa wanda ada ban saba ba, Iyana a matsayinta na babbar mace wannan bayanin na Mami bai gamsar da ita ba, ta tabe baki tace, bana son ki kwari kanki in dai ya soma bullo maki da halayyarsu ta maza ki sanar da ni, don in kai shi wajen malamai 84 i na, saboda ban yi boranci ba banga dalilin da yayana za su yi boranci, ina anfanin dukiyar da na ke tarawa, in har ban yi ma ku maganin da za ku sakata ku wala ba a gidan Ubanku da gidan mazajncku, mamit a yi jigum murna ta lullube ta amma yanzu bata jin Sahabi ya yi mata abinda zai sa akai shi gidan Malami, tace, wani abu Iyana, kin san idan ina da damuwa ke zan iya sanarwa, ni dai kawai ina jin aure na da wuya koko soyayya ce ke da wuya? Iyana tå yi dariya tace, 'Mamina manya kenan, dole ki zama jaruma ki zama mai jan ra'ayinsa a kullun, shi zai sa ki mallake zuciyarsa da ra'ayinsa har ya ji bai iya hada jikinsa da kowacce irin mace, ki yi hakuri kin ji Mami, kada ki yadda ya ga gazawar ki. Mami ta ce, 'To' amma dai a ranta bata san wacce hanya zata iya kai kanta wajen Sahabi ba! komi take so sai dai ta yi mai text shi ma haka sai dai ya turo mata text idan yana son ya sanar da ita sako. Yau ma bayan Iyana ta tafi ta tura mai text akan cewa zata Rimi Driver gidan kawarta Turai za ai Birthday party din yaronta, Sahabi yana gani ya tsaya tunani shi koma za su ta6a haihuwar da Mami oho! Zan cne da Mami bata yi mai kenan tunda su kai aure amma gaskiya yana son jariri a gidan su kila ko don ganin jaririn Mami ta zauna da shi cikin mutunci ya ja dan tsaki ya rubuta mata amsa kamar haka:- Mami a dawo lafiya: ta duba ta ga amsa kamar hadin baki itama tsakin ta ja, wai Sahabi shi ne a yau zan cne soyaya ta gagare shi rubutawa ada ko baya gajiya da 85 3 rubuto mata. Ran ta ya dan sosu kwalla ta zo mata amma ba su fito ba ta danne damuwarta. Ta tsala ado kamar yadda ta saba idan zata fita zuwa sha'ani. Farin les tas ta saka ga zinaran nan ya kama ta radam. Gab da mangarib Mami ta dawo gida ta karyo kan motar ta cikin harabar gidansu amma ta lura suna da baki motoci ne har guda biyu, ta fito ta yafa gyale a hannunta ga jaka a rataye kalar gyalen sannan ga jakar leda a hannunta na tsarabar gidan da ta je ne na bikin cikar shekara daya na yaron Turai. Ta tsaya tana kallon lambar motocin bata gane dayar ba, amma dayar ta san ta T.J ce wato jijjani. Can tunani ya zo mata ba shakka wannan motar Usman ce abokin sahabi na Bauchi. Ta shiga falo gabanta na dar, dari-dar wai idan har Usman ne, ya za ta yi kenan ga shi basu shiri ita da Sahabi kuma gashi bata son surutu,t a ki jinin ace za'a zauna ana masu fada don a shirya su, balle idan da wanan uwar iya yin ne Sarkin kissa matar Usman Husna, tana wani jida miji kamar zata sake haihuwarsa. Ta ji hayani a falo sai da ta yi sallama kamar sau biyu sannan aka amsa mata, Sahabi ya yi hanzari ya taso ya tarbe ta yace 'yauwa mami kinda wo ba, mun fa yi man yan baki ga mutuniyar Husna da angonta Usman itama mamin dan danan ta saki rai ta shige masa su ka isa falon ana ta barkwanci, Usman yace, Na so na yi hushi Mami, sai ace man kin tafi liyafa abokina na gida zaune, a takure duk rashinki ya baibaye shi? aka tintsire da dariya tace, Haba Usman ina za shi taron mata? Sun 86 dan jima ana hira sannan sahabi ya janyc Mami suka shiga dakinta, yace, Ina son kisa a gyara masu dakina ko ni sai na dawo nan, ko kin ga na koma wani daki daban? yin hakan ba zai zame mana tsegumi ba? tace "Ya zan yi dole ka dawo nan din wannan kuma ya kara dagula ran Sahabi amma ya kyale ta tunda ma ya zai yi. An shirya dkauna kamar yadda yace, an sawo abinci kala-kala a Mr. Biggs da Classyburgers da kan shi Sahabin ya je ya sawo komi da komi har wanda za ai kalaci, aka ci aka koshi, amma abinda su usman suka dauka shine don Mami ta je anguwa shi yasa akai sawo a waje haka nan sun san halin Sahabi mutum ne mai son burge jama'a. An dauki tsayin lokaci ana hira har Husna ta so yin bacci, ita da Mami suka nufi dakunansu su ka kwanta, amma Usman da Sahabi suka dosa wata sabuwar hirar ba ji ba gani. Usman akwai labaran da ya ke son ya tambayi Sahabi amma ganin Sahabi na yawan duba agogo lokaci lokaci, tun da Mami ta shiga bacci, idan Sahabi ya so ya saki jikinsa can kuma sai ya tsurawa agogo ido, Usman ya san irin wannan begen dole akwai abinda ke ran Sahabi, can Usman ya soma mikewa ya aje kofin tin da ke hannunsa ya ce, sahabi ya dace mu kwanta haka nan, akwai gajiya a tare da ni, Sahabi ya yi ajiyar zuciya shima ya mike yana dan gajerne murmushi, da alamun faduwar gaba a tare da shi, kai idan ka ganshi ka yi zaton rannan zai 87 1 shiga angwanci a dakin amaryar da akai masu auren dole. Sun yi ma juna sai da safe kowanne ya doshi dakin da matarsa Usman kawai labaranda ya ke son ya tambayi Sahabi amma ganin Sahabi na yawan duba agogo lokaci lokaci, tun da Mami ta shiga bacci, idan Sahabi ya so ya saki jikinsa can kuma sai ya tsurawa agogo ido, Usman ya san irin wannan begne dole kawai abinda ke ran Sahabi, can Usman ya soma mikewa ya aje kofin tin da ke hannunsa ya ce, Sahabi ya dace mu kwanta haka nan, kawai gajiya a tare da ni, sahabi ya yi ajiyar zuciya shima ya mike yana dan gajerme murmushi, da alamun faduwar gaba a tare da shi, kai idan ka ganshi ka yi zaton rannan zai shiga angwanci a dakin amaryar da akai masu aurme dole. Sun yi ma juna sai da safe kowanne ya doshi dakin da matarsa ke kwance. Husna ta ajewa mijinta komi na bukatarsa kafin kwanciya, ya kammala ya kwanta ya karanto addu'o'insa ya shafa ya kuma shafawa Husna, a nan ne ya jawo ta a jikinsa ya kira sunanta kamar yadda ya saba ya kuma fi kowa iya kiran, a hankali a natse cikin hikima da fasaha. Ta amsa kasa-kasa kamar mai masa rada, haka din ya ke so, ya ce, na yi fa missing Faisal ke fa? Ta ce, Haba ina tare da kai ya zan yi rashiN faisal ai ka hade ko ina, ya ce, kin san na saba na yi addu'a na shafa maki na shafa masa yanzu sai na ji duk na tsargu kamar na yi rashin wani abu, kin ga ko faisal ne; Husna ta yi. dariya a hankali wadda iya karta kunnne Usman, ta shiga yi mai wani irin (love making) mai shiga jika, 88 wannan shi ke karawa Husna kima da faukaka a zuciyar Usman, a ko da yaushe ta kan yi saurin shige masa da nuna so da kauna ba sai wai shi ya nemo ta ba, wannan ke kara jin bai iya samun tankar Husna a duniya. Sahabi ya tura kofar dakin Mami a hankali tsoron kada ya tayas da ita cikin firgita, ya yi mamaki sosai da ya ga Mami ta bar (dim light) wato wuta mai dishewa, yana iya hange dogon wuyan Mami bisa filo da kanta ya langabe, dakin ya yi san yi kwarai, ta rufa da katon (bed cover) a yadda ya ga rufarta ta rage masa mayafin wato za šu iya rufa tare kenan, wannan ya dan karfafa zuciyar Sahabi ya shiga kewaye ya wanke baki da (mouth freshner) ya fito ya zauna bakin gado ya yi addu'o'insa. Ya jawo mayafi ya shiga ya rinka lunfashi a hankali, ya kurawa Mami ido na tsayin lokaci, yana tunanin yadda zai kai jikinsa ga matarsa ämma yana kuma tsoron irin amsar da za tai masa, domin har ya manta rabonsa da Mami, kuma yana jin dacin kalmar da ta ga ya mai wadda tasa ya yi fishi da ita, to amma dole ya hakura ya neme ta tunda yau ga shi

Chapter 6 of 13