Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
auren, ni da kai komi tare wanka tare kawai zai shiga tsakaninmu amma ko wajen ofis ne Hajiya za ka ga kafarka ga tawa, za ka san ka yi auren cimgam! Sahabi ya yi zuru yana jin ta domin 29 zan cen ya yi mai dadı haka ya ke son su yi da matarsa don haka ma ya tsani 'ya'ya da yawa, 'yar yarinya 'yar kimanin shckara goma sha takwas ta yi sallama ta shigo daukc da kayan ti flask na ruwa zafi sai kofi da biskit short bread da ovaltine madara peak milk da suga, kaida kowa ya san wa'annan sune kayan tin Sahabi idan ya zo hirar dare. Da kan sa ya hada tin domin yarinyar ta so ta hada mai amma ya hanata. Ya soma sha, sannan ya ce, Mami ya dace, ki matsawa iyana asa mana biki kin ga yanzu dai ta na gari kada kuma ki sake ce man ta yi tafiya sai ta dawo", ta ce, "Ka yi hakuri su sami natsuwa daga bacin ran auren Rabi'a da Ali sannan sai su sa bikin mu ko" ni ma ba zan so ace iyana ta sake yin tafiya ba ba'a yi komi ba akan mu". Ya bar Mami a wannan dare ya isa gidansa sha daya da rabi na dare, ya kammala al'adun rayiwar sa ya kwanta bisa gado ya jawo G.S.M ya aika mata da text ita kan ta ta kasa bacci tunaninsa kawai take yi, ta duba text din sa ta yi dariya ta sumbaci rubutun text din da ke cikin wayar, sannan ta rubuta masa amsa, bayan tafiyar ka kawu Abdukarim yazo daga maiduguri sun yanke lokacin aurenmu" ai ko ran nan har karfe hudu na sulusu dare Mami da Sahabi ba su yi bacci ba, sai da sahabi ya yi naci da kunata ya tursasa Mami ya ji yaya aka sanya ranar bikin", itama ta ja mai rai sosai sannan a karshe ta rubuta mai nan da sati uku cif ina nan manne da kai shikenan? 30 Da wannan ya rufe wayarsa yana murmushi. Bai ma yi kokarin yin bacci ba sai yayo wanka da alwala mai kyau ya zo ya soma aiwatar da nafila. Kafin ma Sahabi ya kai ma Hajiyarsa labarin sa ranar bikin su har iyayen Mami sun aika mata. Cikin kwana ashirin din nan babu wanda ya huta daga cikin zuri'ar su Hajlya Aisha Birnin Kebbi da zuri'ar su Dr. Ahmad Shu'aib a Sokoto ba karamin shiri su ke ma auren Sahhabi ba, haka nan mahaifiyarsa da 'ya'yanta anan kaduna. Can bangaren gidan su Mami ma hakan sauran kwana tara akai Mami gidan sahabi iyana ta tura mata wajen Hajiya Aisha a nuna masu gidan da sahabi zai zauna da Mami Hajiya Aisha ta sa Abba ya kai su Sullubawa road gidan da sahabi ke zaune, tun Dr. Shu'aib na da rai ya gida gidan ya kuma ce ya ba sahabi kyauta saboda hankalinsa da irin kwazon sa a makaranta haka nan kuma yana jin dadin ganin tun yana fan shekara shidda bai iya sallah a gida sai a masallaci, harabar gidan tafi gidan girma don haka nema da ya soma neman auran Mami Hajiya Aisha tasa shi ya kara gina katon daki ya bulla ta gaban dakunan bacci hudu, haka nan Hajiyar tasa an rushe sito an hade da kicin an sami sabban kicin saboda a cewar ta, shi ne yanzu uban 'ya'yanta dole su rinka zumunci da iyalansa ga kuma zuri'arsu ta sokoto dole ne girma ya hau kansa kamar yadda mahaifinsa ya rinka yi zamanin ya na raye, ya kan debo 'ya'yan kannansa kamar uku zuwa hudu ya nemar masu babbar makaranta shi ne cin su shi ne shan su, shi da ita Hajiya Aisha yanzu haka daga ace 31 wane ya zama director sai wanda ya zama lawyer ko likita irin su ne kuna masu kula da zuwa duba Hajiya Aisha shi ne a ganin ta in ba su shuka alhairi ba ai da babu mai kula ta ita da 'ya'yanta. Sahabi ya ce, "Тo Hajiya ina za mu samu sito kuma? Ta cire gilashinta ta kara nazarin gidan ta ce a gina daga wancan korido kaga daga sito sai a shiga kicin kenan. Tsarin ya yi fasali sosai, bayan an kare gyare - gyaren ne za'a soma fenti ya nemi Mami a waya ya tambaye ta wane irin fenti take so? Ta yi murmushi ta ce, "Ayi kalar motarka high blue" ya ji dadI sannan yace, me yasa ki ke son kalar da na fi so? Ta ce, wallahi a lokacin da muka soma haduwa a wajen shan ice cream na dauki lokaci ina nacin son kara ganin mota mai wannan kalar kila ko na dace na ganka, amma shiru to sai kalar ta zame man ado a zuciya babu kalar da ke burge ni sai ita. To matan da iyana ta aika su gano mata gida sun yaba gidan sosai babu ma dakin da hajiya tasa aka kara ginawa girmansa yayi masu domin setin gado da madubi da ma'ajiyar kaya da akai ma mami oda daga China sai babban daki, don haka dakuna uku da falo daya suka nema, aka barwa Sahabi daki daya da falo. Biki da daurin aure a maiduguri aka yi, tun ranar laraba su anti hadiza da yawancin yan uwa kamar su goma sha biyar suka isa maiduguri gida daya iyana ta aje ma su anti hadiza wato dangin ango, shi ko Sahabi da abokansa da yawa a guess house din kawu Abdullonr akai mnru ssesauki zan ce ne dai na 'yan ilmi ta fannin ango da amarya don haka kowanne na nima gwani nc, sai ko harka ta 'ya'yan banki suke ta shan kanshi (NAIRA) babu wanda ya nuna gazawa wajan bada hakkin aurc, bayan ka'idojin da musulunci ya gindaya haka nan al'adun ma ba a bar su ba, duk an cika ka'ida. Yawancin 'yan biki ta jirgi suka dawo Kaduna kamar ango su anti Hadiza sun yi hakuri sun biyo motoci ne saboda dangin amarya masu yawan gaske da suka nace da son lalle dole sai sun zo sun ga dakin mami tunda ita ce diyar farko da aka fara aurarwa gidan M.D Abduljalal, don haka sai da su anti Hadiza suka tsaya suka ga kowa ya sami mota sun kuma biya kudin motocin sannan suka baro maiduguri zuwa Kaduna, ranar asabat kenan ran da aka daura aure. Suma su mami gidansu aka sauke ta wato sultan road, sai wanshekare ran lahadi su anti Hadiza da zuri'ar su suka je bikon amarya. Zuwa gida Sahabi a sullubawa road, wajen karfe tara na dare aka yi shirin zuwa cin dina wadda ma'aikatarsu refinery ta shirya masa. Wannan ina ta shiryu ainun Sahabi da mami sun yi kyau kwarai matuka. babban abokinsa na kan-kan ya gabatar da komi, ainihin tarihin Sahabi da yadda soyayyar sa ta ke da mami, anan ne ma ya kwallawa mami, kira ta ko yi har da ido ta firgita yayin da ta amsa Rasa - Kasa na'am ya ce, "kar ki manta wannan itace kalmar farko da Sahabi ya yi amfani a farkon haduwarku amma Allah cikin ikon sa ashe ya kira matarsa, gaba daya holl din aka tintsire da dariya mami ta ji kunya ta dora kanta bisa kafadar mijinta 33 1 Sahabi ta cc, "yanzu Ab-kar haka ne ko? Ka fadawa usman sarkin tsokana sirrin haduwarmu! Dubi yadda ya firgita ni tankar yadda ka taba firgita ni a farkon haduwarmu! Sahabi ya kwanto da bakinsa dai dai kunnenta ya cc, "Ki man wannan hakuri, Usman ya dau bashi amma zai ci...." Sahabi na lallashin amaryarsa can daga sama, Usman ya kwallawa Sahabi kira ya ce, "sahabi ina fatan za ka cika dan halas ka ririta Mami sosai, domin tun a maiduguri na lura Mami zinariya ce a gidansu, ina son ta zama dayiman a gidanka, tabbas na san zaka iya, aka yi dariya yayin da Sahabi ya rinka daga kai nuna alamun ya amince, sannan ya ce, Mami kina daga cikin mata masu sa'a a duniyà, idan har kin kula da cikin sahabi da tarairayarsa insha Allah ba za ki ci karo da matsalolin auren zamani ba, domin abokin nawa runbu ne bai wasa da ciki", aka bushe da wata dariyar. Sai misalin karfe goma sha biyu da minta arba'in, su Mami suka iso gida, bayan sun yi sallama da jama'a. Suna isowa gida sahabi ya amshi G.S.M din Mami ya manna su a caji. Sahabi na da yaron gida mai natsuwa kuma malami ne mai suna Ya'u, gyaran gida ya kan yi ma sahabi sai wanki, amma ko soya kwai baya yi masa sai dai ayo ma Sahabi daga gida, tun farko ya sanar da sahabi jinsin gidansu ba su taba tukwanan girkin mata, saboda haka sahabi na sa shi ko wanne irin aiki amma ban da girki. 34 Da sassafe Hajiya Aisha ta turo dircba da Hafsat da kayan karya kumallo kala kala akwai kosan nama da fanken kwai da filawa ga soyayyar agade sanna tasa Aisha (Auta) ta gasa masu biredi wanda aka kwaba zalla kwai da bulu ban kana ci yana narkewa a baki da zuma ma da 'ya'yan inibi akai kwabin. Angon da Amaryar ba su fito falon ba sai karfe goma sha daya da 'yan mintoci na safe, sun kammala kalaci suka fada wanka sai gab la'asar sannan suka fito suka iske Hajiyar ta sake aiko da abincin rana shi ma kusan kala hudu ga sakwarar doya sanna ga farfesun kifi ga kuma sinasir wanda ya yi falan falan din nan ya yi gardI ko ba miya ba komi za ka iya ci, sai kunun gyada wanda aka daure da shinkafa, ya yi fari sol da daddare ma haka Hajiya Aisha ta shiryo mau jerin kuloli tamkar masu cikin mota. Kwana bakwai cur Hajiya Aisha na aika masu da abinci safe da rana zuwa dare kala kala kuma 'yan'yanta Hafsa da Aisha sai 'yar aikinsu tinc ke shirya komi. Ita kan ta Mami tasan cewa a gidansu ita 'yar gata ce, amma ta amince shi ma sahabi dan lelen ne, wani abincin idan ta ci takan yi santi ta ce, "Abkar Hajiya na son shagwaba ni da cima da yawa, na soma ji riguna na sun kame ni bana son kiba fa sosai, sanin halin ku mazan zamani ba ku faye son mu yi kiba ba ko" ya ce, very good korafinki na farko da Hajiya ki rubuta an jima idan Hafsa ta zo sai mu bata ta kai mata", ta ce "Lah! Ba haka ba ne, rufan asiri? Wanshekare suka shirya ita da sahabi sai Sokoto, a can din ma komi ya daure mata kai gidan sarauta ne 35 aoba rin ginin turawan zamanin da can, an yi ginın a fidda sasse sassa. gidan anguwa guda ce, an yi tsarin irin na sarakunan turaywan kasar faransa, sassan Di. Ahmad ne aka baiwa yahabi a zamanin yana da rai shi ne sarkın mahaifarsu amma anan sokoto su ke zaune, sassan da ke kusa da shi na waziri ne kanin Dr. Ahmad haka abın ya kasance masu abunda ya Kara rikitarwa da Mami kai shi ne kowanne Kwai da kwarkwata zalla 'yan ilıni ne gaba da baya kai ka ce a zuri'ar su sahabi aka kirkiro ilmin zamani, ga su da yawa amma kuma son junansu su ke tsakani ga Allah. Ana shiyo masu abinci dare da rana da safe iri iri daga gidaje masu yawa, amma kuma da wuya sahabi da Mami su ci abinci su ka dai a rana, koda yaushe 'yan uwa kan zo a zauna ana ci ana sha ana kuma debe masu kewa sati daya suka yi a sokoto su ka yi shirin komawa kaduna. kifi busasshe da kwai har sai da su sahabi suka rasa inda zasu zuba domin but ya cika fam da tsaraba. Wani tsohon kakan sahabi ya aika akai kiran sahabi ana gobe za su koma yace, sahabi nasa an yi man kiran ka ne saboda na aika wa Hajiyarka da kyautar sadaka har guda biyu nace a baka amma ta kI amsa. wai zamanin mahaifinka ma bai amsa ba balle kai ni ko a ganina taimako ne a gare ka, kuma gatanci ne akai maka hakan zai sa ka sami kyakykyawar kulawa, amma ina mutunci ku zauna da mace daya bayan kuna 'ya'yan manya masu daraja ai gara ku bari darajar ku ta fito fili; tunda ya soma zancc sahabi zuciyarsa ke 6ace bai taba jin wannan zance ba, tabbas yasan gudun ransa kada ya 36 Baci shi ne dalilin da Hajiyarsa ta KI sanar da shi, ya yi na sanin zuwan su Sokoto tsoron sa daya shi ne kada ma a daga maganar har Mami ta ji a tada mata hankali a rikitar masa da kwanciyar hankalin gida, don haka bai tsaya bata lokaci ba, ya cc, "Ai abunda ba zai taba yiwu ba ne, wannan ba irin rayuwa ta ba ne don haka ne ma Hajiyar bata ga ya man ba, don Allah kada ma a kara yi man irin wannan tunanin", Dattijo ya yi ma sahabi zuru shi a rudaninsa har yasa an shirya 'yan mata biyu 'ya kimanin shekara goma sha shidda shidda zai baiwa sahabi a matsayin makulla, a ganinsa yin haka zai kura birgesa ya daukakasa, amma sam sahabi ya Ki. Ya koma gida ya cimma, Mami yau har ta yi wankan dare ba tare da shi ba, ta shafa mayukanta na 'yan maiduguri wa'anda akan kwabawa amare 'ya'yan wanc da wane ta zizara turaruka a gaba - gaba na jikinta, sai wata irin hoda mai kyau da tsada da iyana ta sawo mata a saudiya ta shafawa fuskar ta nan da nan fuskar Mami ta koma kamar kwan lantarki, sai ya dauko kwarar maganin da iyana ta bata wadda tacc, kullun ta sha kwara faya idan ya rage saura awa daya su sadu da mijinta, da kofin ti za'a sha, shi ma a saudiyan ta sawo mata. Rigar da ta saka da ita da rashinta duk uwarsu daya uba daya, tana zaune bisa kafet a dakin baccinsu tana kallon tashar daya daga cikin na tauraron dan adam, wasan kwaikwayo ake yi na rikin aure, ya dauke hankalin Mami tsab, sahabi ya dawo tun daga hanyar falonsu ya soma shakar kamshin amarcin Mami, bai taba jin 37 Kamshi mai tada sha'awa irin wannan lalle ya amince muddun mace zata shafa irinsa ta fita ta ratsa ta gaban maza tilas ta dawo gida ta yi wankan janaba tamkar yadda ya zama tilas suma mazan sai sun yi. Ya isa gare ta ya zauna dirshan a gabanta ya kura mata ido babu kiftawa na tsayin lokaci sai da kallon ya razanata sannan tasa baki ta hure mai ido, ya hade yawu ya ja ajiyar raı, suka yi dariya. Yace, amarsu ta ango kai Mami akwai wanda ya dace da angwanci iri na? ta kada kai ta ce, "Babu domin naka na sani, ban san na sauran maza ba! Suka kyalkyale da dariya ya matsa jikinta sosai kamar zai hade ta lunfashinsu ya hade suna anfani da iska daya, can ya ce, Anya yau zan iya wankan nan ni kadai ita kam Mami ta soma nuna don haka shiru ma amsa ce, ya nuna mata kauna ta zahiri, kamar yanzu aka mallaka mai ita sun yi soayya sun yi wasanni na lokaci mai tsawo, a kullun suna kara fiddo salo - salo na zakulo sha'awa, hakan ko na faruwa ne saboda masifar son juna da suke, idan sahabi ya bullo wani sabuwar hanyar ya kan jira ya ga yanayin Mami shin ta gamsu ko ta yaba? Lokacin da suka isa kaduna mangarib ta yi don haka sahabi ya bada shawarar su wuce gidan Hajiya Mami ta ce "E ko don saboda mu aje masu wa'annan kaya su kifi", ya cc, 'Ai wa'annan na ki ne" ta ce haba sahabi yaushc za mu yi amfani dasu, bayan ka ceji bi za mu wucc Bauchi State mu gama hutunmu" to itama Hajiyar ganin kwan da kifin akwai yawa sai ta ce, Mami a raba biyu mana ku je gida da rabi" Mami ta ce, "a'ah Hajiya ku bar shi kawai idan yayi 38 ma ku yawa ne ana iya kaiwa su anti Hadiza" to abunda dai su Hajiya su ka dauka Mami mai son zuri'ar mijintă nc. A nan gidan Hajiya su kai dina su kai sallah anan ma su kai hira sai can wajen karfe goma na dare sauka nufi gida tare da Hafsat zata kwana a can. Hafsat ita kadai ta mike da safe ta shirya masu kalaci mai kyau toye toye kama kala uku daman ta zo da yawancin kayan amfani da ga gida, ga ti ga kunun tsamiya saboda sahabi wani lokaci ya kan so koko da kosai ko kunun gyada ko kuma kunun tsamiya. Sun fito daga dakin baccinsu daidai lokacin da suka saba fitowa, Mami ta doshi tebirin cin abinci ta cc, "wai Hafsat nan gaba sai kun sa an kara bude man kofa in wannan gara" Hafsat cikin dariya ta ce, haka mu ke so yaya Mami mun iya kiwo kenan". Da rana ma doll man da farfesun kaji da kunun zakI ta yi masu, amia da yamma Hajiya ta aiko da hura mai kyau da Jamil yogot don haka sai harfsat ta gasa masu naman rago wanda ta aikı Ya'u ya sawo a anguwar Sarki. Gaskiya ko shi sahabi ya yabawa Hafsat da kokarin da take yi na kula da su. Wanshckare da safe koko da kosai mai kyau Hafsat ta shirya masu a cikin kosan ta daga kwai ta yanyanka cikin kullin kosan, a idonka zaka iya amincewa Rosai ne amma lokacin da ka ke ci a bakt sai ka rasa ko menene don dadi. Sha biyu na rana su kai shirin tafiya Bauchi, abun mamakin sahabi da Mami shi ne lokacin da hafsat ta soma fiddo masu kaya don Ya'u ya shirya 39 masu a mota sai ta fito masu da hadadden kek da zafinsa ran ta nade da jarida ta saka a plastic roba mai rufi, shi ma a kwabin kek din ya sha inibi da suga hade da zuma irin dai wanda ba a ba yaro mara kunya ga hadadden juice wanda ta zuba a kula ta watsa Kwankara. Sahabi ya nunawa Hafsa godiyar sa a zahiri haka itama Mami saboda sahabi mutun ne mai son yabawa mutumin da ya kyautatawa cikinsa. Su ka biya ta gida suka aje Hafsat kai tsaye suka dauki hanyar Bauchi. Sahabi ke tukin motar Mami na zaune ta gefensa dan kidan da suka saka na wakar 'yan sudanis ne, kidan yana da laushi da sanyi a kunne, sahabi ya lura Mami zata soma yi mai bacci sai ya ce fiddo wayarki na ba ki aiki! Ta fiddo ya ce nemo man usman abokina ki sanar da shi ga mu nan bisa hanya zuwa gidansa" ta ce, haba don Allah dazu da safe fa ka sanar da shi zamu zo, kuma kasan yana ofis ka bar shi mana ya yi aiki". Sahabi ya juyo ya dube ta suka murde idanunsu cikin idon juna ya rinka ransayar mata da kwayar idonsa sannan suka yi murmushi ya mikar da hannu ya shafi haßar ta ya ce, "Be a nice girl kin ji" ta amsa cikin shagwaba da cewa da man cen nice, ta nemo usman a G.S.M din sa, jin muryar mace ya kara duba numbar sosai bai dai gane ba yace, "Assalamu alaikum" a murtuke Mami ta kyalkyale da dariya ta ce, "Wai wanna fa ai kai ne ragon maza ka ke tsoro, 'yan matan zamani? Ko madam din tana kusa ne? ya dai cije ya yi 'yar dariya har yanzu bai gane mai magana yana kuma tsoron tambaya kada a kara yi mai 40 wata shegantakar, ta се, Aa tabbata mijin ta ce, to Mami din sahabi ce" ya yi ajiyar zuciya ya bushe da dariya ya ce, "Ba kya da laihi, laihin mijinki ne, za mu gamu kuma, ya kina lafiya" ta cc, "lafiya lau, muna nan bisa hanya nan da awa uku insha Allah zamu iso", ya cc, "muna zuba ido, a ofis na ke na bar madam ta na shirin taryar ku, ki buga mata ga wayar ta...." Suka yi sallama ta nemi Husna matar usman lokacin Husna na cikin wani super market wayar ta rinka kukan tsuwan mashin ta 6alle jakarta ta fiddo wayar sannan ta raße gefen da babu jama'a sosai ta amsa "Hello Mami ta ce, "Husna ni ce Mami" ta ce, lah amma kin kyauta da ki ka neman, dear ya ce man yau za ku zo ko? Tа се, wallahi muna kan hanya ma yanzu insha ALLAH, ALLAH kawo ku lafiya don Allah Mami wane irin drink ki ka fi so ne? Mami ta yi murmushi ta ce, haba Husna, kowanne is okcy; ta ce, "Ai babu kunya tsakaninmu; Mami ta, ce na fi son (eva) amma pincapple juice Husna tace angon fa Sahabi? Tace, wai shi wannan yana ganin ire - iren wa'annan ba su faye damun sa ba in dai zai ga su kunun zakI mai wadatattcen kayan kamshi ai kuma shikcnan" Husnata ce, "Ka ji sauran mazan jiya, to sai na cc Allah ya kawo mana ku lafiya" Ta amsa 'amin Mami ta juya ta dubi Sahabi tana lumlumshe mai ido ta ce, Ab-kar na ci gaba da bacci na ko na dai kammala da sakonka", ya cc, amma bayyana man aikan da na yi maki ba", ta ce, ka daure idan mun je Zaka ji daga bakin mutumin na ka" ya yi murmushi こ ya ce, kai wannan idon na ki yana jin bacci da yawa gara na hakura da hirar yanzu ko na sami ta an jima, Mami ta nade kafafunta tsab cikin kujera ya kara karfin A.C ko minti goma ba ta yi ba duk jikinta ya saki alamun bacci mai nauyi ya dauke ta. Lokacі - lokaci sahabi idonsa na bisa titi rabi yana kallon kyakyawar matarsa wadda ya radawa suna Sleeping Beauty tun wata ran a Sokoto da ya bata kimanin awa daya yana kallonta yayin da ita ko take ta bacci, ya rasa a wane yanayi Mami tafi kyau tana bacci ko idan tana zaune ido biyu koko idan yana making love da ita? Shi dai yana mamakin masoya, abinda marubutan suka fi nunawa zamanin ma'aurata kan dakusar da zumar amarci, to shi dai har yanzu bai ga chanjin hali ba a wajen Mami, ko awa nawa zał yi yana (makin love) da ita bata nuna mai gazawarta illa ma ta kara karfafa mai gwiwa, sannan irin kallon da take mai yana birgesa wanda kan dasa mai sha'awa a rai, tun ranar da ya soma zuwa wajenta ta ke mai irin wannan kallo amma har zuwa yau bata dai na ba, haka nan abu daya ya fi birge shi da kara kaunar Mami wato shi kadai take ma wannan kallon bai taba ganin ta dubi kowa da irin wa'annan idon ba tamkar Mami na da rigar idon guda biyu daya tashi ce ta musamman dayar ko ta ya ku bayi. Sai da suka isa Bauchi ya latsa na'ura gilashi ya sauka kasa iskar garin Bauchi ta soma ratsa Mami a hankali a hankali ta bude ido, ta dire idanunta bisa kan mijinta, shi ma na sa idanun sun yi jajur alamun gajtya da rashin isasshen bacci, don haka ya za6I su 42 je yankari inda za su huta sosai babu kowa balle a dame da hira hatta wayoyinsu rufewa za su yi idan sun so magana sun nema da kan su. Ta mike zaune sosai ta gyara jikinta, ta се, "Allah sahabi kai ma kana bukatar hutu kaga idanunka kuwa, ya ce, yana iya! Ta dube shi cikin yanga ta ce, ya ka iya kamar yaya? Ya ce, "ni fa maigida ne yanzu nauyi ne akai na nauyi bisa nauyi ko? Ta kai mai duka ta ce naugthy man ya ce, yau dai ba za mu iya wuce wa yankari ba ko? Ta ce, "Don me ka daure don Allah, ko Usman ya baka aron direba ya kai mu ya dawo, bana son kwana gidan mutane" ya ce, gara ko ki saba, domin 'yan uwana za su so ki je ki kwana haka ma amine na. Mami na jin bayanin Sahabi amma dai abinda zuciyarta ke raya mata da ban, ita a ranta ta dauka babu yadda za ai ta sauka gidan su tare da Sahabi har kuma ta hole rayuwarta bayan akwai masaukan baki wato (Hotels) barkatai ko ina a duniya, ta danne ma zuciyarta bata ce ma Sahabi komi ba. Usman na tsaye bakin matakala ta biyar a kofar shiga gidansa ya rungume yaransa Fesal mai kimanin wata shidda, ya tarye su da murna Sahabi ya amshi Faisal ya yi masa dan wasa sannan ya mikawa Manir yaron, suka isa falo, a nan ne Husna ta bullo daga kicin tana tafi da hannaye cikin murna ga waka tana Oyo-yoyo! Suka zauna ana ta barkwanci da gaishegaishe irin na abokan da ke son juna, anan kuma Husna ta mike tace, to a bani makullen motar ka Sahabi a kwaso kaya, a nuna ma ku dakinku saboda 43 bakarta shiga kewaye ko? Nan da nan Sahabi ya firgice a tsorace ya rinka satar kallon Mami, da gani dai kasan ya na tsoronta ne a bisa wani abu, sai yace, An ya! An shigoda kayan nan kenan ai sallah kawai za mu yi mu wuce yankari. Usman yace, Haba Sarkin angwance, wane kai, wallahi ba ku isa ba, ku hana man mata zama ta huta yau yini tayi hidimarku amma ku ce wai ba za ku yi mana kwana biyu ba, banda wanan ma mitin mu ke yi amma dole na tkaura ma'aikatanmu na dakatar da mitin din a dalilin zuwan ku. Sahabi ya yi sukuti ya rasa madafa, ga dai gaskiya kiri-kiri yana ganin Usman ya fadi sannan ga gajiya likis ya yi amma kuma a fuskar Mami taki bashi hadin kan da zai ba Usman amsa ya nuna shi ma magidanci ne ya jure yayi hikima yace, bari dai mu yi sallah sannan mun ga ya ma ku komi kenan". Husna ta shige gaba ta nuna masu sassan baki wanda kawai nisa tsakanin zuwa na su dakin, ta koma falo gurin mijin ta suka dubi juna su kai dariya wadda kawai magana cikin dariyar su. Dakin da aka ba su kawai kewayen wanka da na bayan gida, dakin tafkeke ne, ya sha kayan shimfidu na alfarma, sai kamshin Ambi pu (room freshner) ya murde da sanyin A.C. Sahabi ya lura da dan karamin

Chapter 3 of 13