amma ba
daga ke ba, me na yi maki na tsana haka? Ta kasa matse
kwallanta cikin hawaye ta ke magana, ta ce yanzu kai
ne me bakin gaya man haka? Yaushe ka damu
dani, ka zo garin saboda ni ne wa'anda ka zo domin
135
su ai ka neme su, kana isowa ka nemi 'yan uwanka
da Uwani, ni ko waya ka yi man ka sanar dani
zuwanka? Ni na san matsayina a wajenka, don me
zan matsawa kaina da zaman jiranka, in da farkon
aurenmu ne na rantse wallahi ba ka iya nesa da ni har
na tsayin lokacin da ka dauka. Ya zauna bakin gado
ya gyara baki ya ce, To menene kuma na kukan in
har maganar gaskiya za'ayi, saunawa na ke zama ina
gaya maki ga yadda yada ce mu zauna, amma sai ki
basar da ni, wallahi kin ga abinda na ke tsoratar
mana, amma dai har yanzu ba mu makara ba, ki
gyara halayyar ki na zama macen aure sosai, ni kuma
ki sanar da ni kuskure na wallahi a shirye na ke na
gyara kome, ta zauna bakin madubi tana tukke
gashinta ta ce, kai dai kawai ka je ka cuce ni, son da
na nuna maka ya kwaran, Sahabi sai abin ma ya dai
na bashi haushi ya soma dariya ya isa gare ta ya dora
hannunsa abayanta, yace, I do hope you still love
me, as I love you ta muskuta ta ture hannayensa tace,
kaje ka yi abinda ranka ke so is your time, ni ma
nawa lokacin na zuwa zan rama, ya rusuna yana
sunbatar sassan bayanta ya ce, haka ki ka zaba? to
shikenan.
Sahabi ya rinka sintiri daga falo zuwa waje
wajen su Peter sannan ya dire dakin Mami kamar
wani bugagge har dai ya kammala da komi sha daya
na dare ya kwanta saboda mami ba wai don ya gaji
ba, domin ya saba ya wuni tsaye ya kwana zaune
suna aikace-aikace, sun yi auratayya mai tsabta
domin su duka tsabtabtun ma'aurata ne, duk da
136
sangartar Mami a nan kuma Allah ya shirye ta bata
cikin sangartattun da basu da haramiya wato abin
nufi a nan yawancin yaran yanzu masu dabi'u irin na
su Mami shedanancin lalata sun fi karuwan kasar nan
illa domin su tsarinsu irin na turai ne, (Allah ya
shirya mana zuri'a amin).
a
Mami ta kwantar da kai bisa kirjin Sahabi tana ci
gaba da sheshekar kuka, Sahabi ya mikar da hannun
sa ya kunna fitilar bacci duk da bula ce mai duhu
sosai amma yana iya ganin hawayenta na diga
Kirjinsa, ya tsura mata ido, yasan dai dalilin kukanta,
don hake bai son tambayarta amma abu daya ya ke
bashi mamaki duk yadda ta rinka yarfas da shi tun
zuwan sa amma babu daya daga cikin hakkinsa
wanda ta danne masa, sai ma cigaba da ya ji ya kara
samu.
Ya mayas da hannu ya kashe wutar sannan ya
zuba hannayensa gaba daya ya rungume ta tsantsa, ya
ce, wai kuma mene ne yanzu? Tace, koma mene ne ai
ka sani tun da kai ke kulla komi, yace ban fahinta ba?
ta ce, Ni dai Sahabi in har akwai kauna tsakanin mu,
to mu tafi tare, zan dauki hutu idan na ga zan iya to,
idan na ga ban iyawa idan hutuna ya kare zan dawo
wajen aiki na, yace, idan kuma kina iyawa fa! Tace,
shikenan zan ci gaba da zama na hakura da aikin.
Sahabi ya yi shiru, ya amince matarsa Mami na
matukar sonsa, amma shi yasan ko ta je ba zata taba
iya wannan zaman ba, kuma rigima ce sun fara kenan
wanda na iya sanadin rabuwar shi da ita, amma dai ya
tsarata don a rabu lafiya yace, To shikenan ta shirya a
137
hankali, idan ya koma zai ma Oga dinsa bayani daga
nan bayan kwana 7 sai Peter ya zo ya tafi da ita.
Idan kuwa son ran Mami ne Uwani ke sata
wannan kukan ita bata son ta bude ido ta ga duk wani
mai halaka da gidan su Sahabi wannan shi ne ainihin
damuwarta, ita a tunaninta sun fita matsayi a zuciyar
Sahabi. ba Da safe fiye da karfe goma mami bata fito
amam shi Sahabi ya dade da fitowar har wasu
gungun abokansa sun zo tare ma suka yi kalaci, sun
ma wuce da alkawarin za su dawo an jima. Can
Sahabi ya fakaici idon su Uwani ya kwashi kayan
kalaci ya kaiwa Mami har daki ya tayas da ita, ta
dubi abuwan da Uwani ta dafa cikin borin kunya
tace, Ni yau konfiles kawai na ke so ya ce. Haba ga
agade da kwai da koda da dankali an soya ki daure
mana kici ko dan kadan, tace, Bana marmarinsu. Ya
kwashe kayan ya fidda kwalliyar mami yau na wata
hadaddiyar shadda ce, siket ne da riga amam rigar
'yar Firit ce iyakar ta gaban cibi amman dinkin ya yi
kyau da ita shaddar mai ruwan siminti ta baza turare,
ta shiga kicin cikih yauki da yamutsa ta hada abinda
ranta ke so, sai da Kiristi ake watsawa turanci har da
barkwanci, amma Uwani sai hararta ake yi, wannan
bai damu Uwani ba dominw anda ya fita ya kawo ta
gidan.
Mami ta shiga falo kenan zata zauna, adaidai nan
Sahabi ya shigo daga waje ya yi ma wani abokinsa
rakiya, yace, Yauwa Mami kin fito ba, zo nan don
Allah ina son ganinki, suka jcra zuwa ainihin dakin
138
baccin sahabi na da, kaya ne a jakunkuna birjit bisa
kafet, Mami mamaki kawai ya cika ta, yaushe Sahabi
ya shigo da wannan dukiyar? Ya juya ya dube ta
yace, cauna mana, ta zauna bakin gado ya zuge wata
bakar jaka a London ya sawo ta, ya fiddo wa da
Mami Sufofinta biyu da leshinta biyu da wani
material baki ne suduf y ana daukar ido, sai Shaddoji
galilah, amma dai material din ya fi daukar Mami ta
rinka yafa shi a kafada, Sahabi ya yi murmushi ya се,
Kema kin yaba da shi ko? Ni ma wallahi duk ya fi
tsuma ni, kuma ke kadai na saya mawa, a wajen
matar wani ogan ogan mu a Delta, kin ga waccan
jakkar duk kayan ki ne na kale-kale, ai ina jin ban yi
mantuwa ba ko? Ta kwantar da kai bisa kafadarta ta
ciko fuskarta da fara'a ga murmushi wanda ya juyar
da kwayoyin idanunta sukai matukar kyau, ta ce,
gaskiya Ab-kar tsaraba ta yi kyau Ya ce, Na ji dadi
tunda na zama yaron kirki, yau Mami ta yaba mani ta
ce, don Allah kada mu yi haka da kai ai ni ma
yarinyar kirki ce ko? Ya girgiza kai, ya juya yana
dariya ya jawo wata leda Shaddoji ne irin na maza
masu tsadar gaske, kala biyu ga turaruka kala biyu
'yan dubi ashirin da biyar ya dora bisa cinyar mami
ya ce, wannan na Babanmu ne na san za su dace da
shi ko ba haka ba, ga turamen holland uku ki baiwa
su Anti Zainba ai sun yi ko? Dadi ya lullubc ta, wane
irin kudi Sahabi ya samu haka ne ya ce, Mami na yi
tunani na rasa abinda ya dace na sai ma lyana domín
na ga ba abinda bata kawo wa na sayarwa saboda
haka ga kudi zan ba ki kila kin-san abinda ya dace da
139
mu kai mata, ita dai tama rasa bakin magana domin
taga hidimar ta yi yawa. Ya mike ya jawo jakarsa ya
bude ya fiddo dubu hamsin ya dora mata.
Ya kara jawo matcrial din nan "Ya ce, kada ki
dinka shi a nan, ki jira sai mun je Legos domin nasan
sun fi nan iya dinki, Ta ce, Ai daman! A nawa ka
sawo shi? Ya ce, Dubu talatin da biyar na so kwarai
na sawo ma Hajiyata to nasan ba zata daura ba sai ta
barwa su Hafsat; nan da nan Mami ta ji wani yu a
zuciyarta, ta daure tace, to sai ka sawo mata me? Ya
ce, Sufofi ne da lesisis, suma yaranta da su Uwani
haka, ki dan sami dubu biyar ki sawo ma Kiristi wani
abu a kasuwa. Ai tuni Mami ta tsani komi da Sahabi
ya sawo mata, shi kan shi Sahabin haushi ya ke bata,
ya yi magana tafi sau goma amma Mami bata tsinka
masa ba, sai dai uhm ko a'ah ko ta jinjina kai, Sahabi
dai ya fuskanci Mami ta shiga yanayin da ya tsana sai
shi ma ya tsani komi ya mike ya fice abinsa.
Bai tsaya ko ina ba sai wajen Hajiyarsa inda ya
sake ya baje ya manta da duk wata damuwa illa
walwala da jin dadin hirarraki, duk irin labaran da ya
fis o hajiyar ta sanar da shi ya dauki lokaci mai tsawo
a nan suna hirarsu, yayin da ita ma Hajiyar ta rinka
tambayarsa yanayin can wajen nasa, ya bayyana mata
komi dalla-dalla har ta gamsu da cewa lalle yana bisa
hanyar samun kudi, ba wai kudin kanfani ya ke ta'asa
da su ba.
Ko da Uwani ta ga la'asar lis babu Sahabi lalle
tasan ya ci abinci inda ya ke, don haka sai ta kara
adana masa na ranarsa. Shidda saura kwata na
140
yamma ya iso zida, wayarsa ta G.S.M manne a
kunnensa yana magana da wani ofisansu da ga Dalta,
har ya shiga falo ya zauna ya nemo takarda yana
daukar gundarin sakon da ake sanar da shi, ya fi
minti sha uku yana daukar sako, har Mami ta zauna,
ta yi tagumi tana kallonsa. Ta na tsanarsa a ranta,
amma kuuma gargadin su Zainba na danne
damuwarta.
Ya kammala da wayar ya nade takardar ya soka
aljihu, ya dubi Mami a gajiye ya cc, Uwargida ya dai!
Tace, lafiya lau, su Anti ga sun zo, Baba da Iyana
suka turo su ayi ma sannu da zuwa, tare da godiya
yace. haba babu komi, kin san dalilin wayar nan, aiki
ne oga ya turo man dole na yi asubanci naje Abuja
amma a goben zan dawo, ko zamu tare? Ta yi dariya
ta ce, muje mana don ma Abuja; ya ce, shikenan idan
munyi Sallar issha'e sai mu je mu gaida su Iyana
anjima ko? Ta ce, to.
Sun caba ado na ganin sarki zuwa gidan su Mami
duk mai kaunar su idan ya gansu zai yaba ya kuma ji
dadi babu ma kamar mahaifin Mami Abdujalal
wanda ke son Sahabi tsakani da Allah. Da asuba
Peter ya debe su sai Abuja ana aje Mami gidan
abokinsa Ibrahim amma sam Mami ta ki, dole sai
hilton Peter ya kai ta ta yi masu kamun gurin kwana.
Ta dan fita yawo ita da peter zuwa gidan kanan
Iyana da wata kawarta, sai karfe tara da rabi na dare
Sahabi da peter suka je daukarta zuwa hilton.
Wanshe kare ya kammala ayyukansa suka koma
kaduna to haka dai hutun Sahabi ya zamanta na
141
kwana biyar a kodayaushe dai shi ne matan Mami ce
mijin, sai dai ayi yadda ta ke so.
車車 ***
Kamar yadda Sahabi yayi wa Mami alkawari
sati guda ya turo peter azo a tafi da ita, ya rubuto
mata ta biya gidan Hajiyarsa ta zo mai da hura da
dambun nama, Hajiyar sa tayi muma da ganin tafiyar
Mami, domin tafi sha'awar ganinsu tare, tunda itacc
kariyarsa.
Tun Mami na sheka bacci a mota, har ta gaji
idanunta suka kekashe, sai azabar gajiyar tafiya tama
rasa abinda ke mata dadi ta sha lemon gwangwani
taci naman da Hajiya ta bata na Sahabi, sun tsaya
wani resturant ta sayi abinci amma kuma kyama ta
hana ta ci abincin. Ba su isa River ba sai karfe tara da
minti arba'in na dare kai tsaye peter ya kai ta
masaukin Sahabi kamar yadda Sahabin ya sanar da
ita gidan bai dace da matar aure ba yar mutunci a
harabar gidan abin da ya soma bata tsoro kabilu ne
zaune bisa kujerar kwando ana ta kwankwadar
barasa, gaba dayansu kuwa sukai wa Mami ca da ido
kamar mage ta ga bera, tun ana hankalin Mami ya
soma tashi, ta hana Peter fitas da kayanta daga but
G.S.M dinta ta soma tsuwwa ta balle jaka ta fiddo ta kanga a kunne, ta ce, Mami ce, sai ta ji muryar
Sahabi nan da nan gabanta ya fadi ras tace. A'ah me
ya faru kada dai kace man bazan samcka ba aа
142
dakinka! Ya ce sannunku da zuwa, hala kun iso ko,
wallahi na yi iyakar kokarina amma sam oga ya ki
amince man, ina nan Werri insha Allah komi danre
zan kasance, tare da ke, ki yi man gafara: ta ce Amma
dai wannan shi ne wulakanci kana nufin na zauna
cikin wa'annan kabilun ni gaskiya tsoronsu na ke
kyi! Ya ce, ka da ki damu na yi masu bayani cewas
matata zata zo, ba abinda za su yi maki ki kwantar da
hankalinki please!
Suka isa kofar dakin Sahabi makwabcinsa
musulmi ne mutumin Kogi ya fito ya mikawa Peter
makullai ya gaida Mami cikin girmamawa, a lokacin
ne ta soma jin dan san yi san yi kila zai iya ceton ta
idan wa'ancan sun zo afka mata. Tana shiga falon
Sahabi ta mayas da kofa ta rufe gam da makullai duk
da sanyin A.C da kayatarwar da akaiwa falon bai
kwantar da ran Mami a ganin ta zama da wa'ancan
komi na iya faruwa, ta shiga dakin baccin Sahabi
kato har ya fi na su na Kaduna girma, an shirya shi
sosai abu daya ya faranta ran mami hotunan ta ne kaf
a dakin baccin sa, ko wanne bangare, amma a falo sai
na shi da mahaifinsa da Hajiya.
Ta tsaya gaban gadonsa tana kallon wani
hotonta da ya dauke ta tana kwance daga ita sai shimi
a yankari. Ta kewaya bandaki ta dade zaune, tana
tunane-tunane, a karshe dai ta sakarwa kan ta ruwan
shawa, ta fito fes, ta yi zaune bakin gado ta zuba
tagumi duk dan motsi ta zabura a tsorace, haka dai ta
yi ta zirga-zirga ta sunce tawul din Sahabi ta jawo
jallabiyarsa ta saka sai karfe goma sha biyu da 'yan
143
1
.
mintoci na dare Sahabi ya dawo ya rinka kiranta а
hankali yana rankwasas tagar dakin baccinsu, ta
saurara a hankali ta tabata muryarsa ce, sannan ta
bude tagar ta mike mai 'yan makullan.
Yana shiga ya kamata ya rungume amma ita ko
ta saka mai kuka, ya shiga lallashi gadangadan, da
kyar ta hakura ta zauna ta sauraresa, ya ce Na ga duk
abin cin da nasa aka shirya maki ga sunan a falo ba ki
ci komi ba why? Ta daga idanun ta ta dube shi tace,
wallahi na yi dana sanin zuwa na, bayan bakar tafiya,
sannan yanayin gidan kwata-kwata bai yi min ba,
yanzu Ab-kar ya zan yi? Ya ce, A to komi na yi
kokarin nuna maki Mami ba kya yadda ke kan ki kin
san halina da son mu kebe mu yi hutu, tunda ki ka ga
ban gayyace ki ba, ai dole kin san babu hali ne, ki
kwantar da hankalinki babu abinda zai same ki insha
Allah! Ya shiga sunbatar da ta dauke dukkan
damuwarta da fargabarta sannan ta gusar mata da
doguwar gajiya, ta sami kuzarin karfin dogaro da
kanta, ya daga ta zuwa falo ya zaunar da ita ya jawo
kayan abinci ya cika mata filet ya tura a gaban ta ya
ce, 'To bissimillah tace, kai kuma fa? Ya ce, I'm
okey, ai duk inda muke akwai abinci zagaye da mu,
wannan na ki ne nasa akai maki oda zan shiga wanka,
kin amince? Ta juya ta dubi bakin kofa, tace, ka
tabbata ka kulle ko ina? Ya ce Haba Mami kada ki
rikita kan ki me za su yi maki, yanzu haka kowanne
tare ya ke da budurwarsa, ki manta da su don Allah
Ya mike zuwa wankansa.
144
Duk yadda ya saba nuna mata gwanintarsa ta
fannin soyayya bai ga alamar Mami ta gamsu ba
kamar yadda ya saba birgeta a kullun sukai love
making, yau dai da banbanci, bai kuma san dalili ba.
Da safe ma sun sha rikici kwarai da zai tafi ofis duk
da ta yi sa'a ba za shi ko ina ba a nan Rivers zai yi
aiki, da kyar ya shawo kanta ya tafi ofis, ita cikin
kuka shi kuma ran sa a bace, a gaskiya Sahabi ya
soma tsanar wannan aure, yadda mami ta taba cewa
takura ce, shi ma yau cikin ransa ya ce takurar ce.
A ofis haka nan Sahabi ya rinka aiki ba cikin jin
dadi ba, lokaci-lokaci yana kiran Mami ta waya
amma sai ya ji ta cikin kunci da damuwa, misalin
karfe biyu na rana ya samo shawara ya tuno da wani
dan uwansu Hajiyarsa wanda ke aiki a Inter-City
bank wato Abdullahi tun zuwansa Rivers sau biyu ya
taba zuwa gidansa amma suna yawan gaisawa ta
waya, ya yanke shawarar kai mami gidansu wajen
Iyalinsa sai lokacin bacci ya rinka dauko ta, nan da
nan ya yi ma Abdullahi waya, a mamakinsa har
Abdulahin ya so ya bata rai ganin ai shi ya zama dole
ne ma ya kai Mami gidansa tun da bashi da kamarsa
anan Rivers. Suna aje wayar ya nemi izzini zuwa
gida ya je ya sanarwa Mami shawarar da ya yanke,
nan da nan ta mike ta hada dan abinda zatai amfani
da shi ta bishi ya kai ta gidansu Rakiya. Ta yi murna
kwarai da ganin Mami, wannan ya karfafa zuciyar
Sahabi ya koma ofis cikin murma, ya shawo kan
wannan matsalar. Rakiya ta shiga ririta mami kamar
'yar tsana har itama Mamin ta sake sosai duk ta saki
145
ranta. Sun ma fara kulla shawara ran asabat za su
saye-saye wata kasuwa mai arhar kaya da kyau ita
Rakiya 'yar gari ta san kan kasuwar, a nan ne Rakiyar
tace insha Allah zan amshi kudi a hannun Abdullahi
na yi ma Hajiyar su Sahabi sarin zannuwan gado
yadda zata sayar a Kaduna taci riba sosai, wallahi ina
son hajiya, ina girmamata kamar ita ta haifi
Abdullahi saboda mutuncinta da kamun kanta, kin
san Abdullahi a hannunta ya zauna ya yi hidimar
kasarsa, idan yana yabonta har bana so, domín ni ce
zan nuna mai halin hajiya yadda take nuna man, kin
san haihuwar da na yi ta farko a hannunta na haihu
tace kuma na zauna a gidanta wallahi ni kam ta yi
man abinda uwata zatai mani, ki rinka addu'a kina
godiya wajen Allah Mami da Allah ya baki suruka
irin Hajiya.
Wannan zancen na Rakiya shi ya kara jagula ran
Mami, ita a yadda ta dauki Hajiya makiyiyarta, don
haka ma yanzu ta tsani Rakiya da Abdullahi suma
sun zama layin makiyanta, duk yadda ta tsani zama
masaukin Sahabi gara can sau dubu da ta zauna da
Rakiya tana wani yabon wannan muguwar Hajiyar da
bata san komi ba sai 'ya'yanta, (a shirmen Mami fa!)
A gidan Abdullahi Sahabi ya yi sallah mangarib
da Isaha'e, bayan sun ci sun yi kat, ya dauke ta suka
tafi. A nan Sahabi ya shiga yawo da Mami lungulungu har ma'aikarsu sai da ya kai Mami, ba su koma
masauki ba sai can cikin dare. Wan shekare da safe
yace, idan kin shirya Peter zai kai ki gidansu Rakiya
yau ni Imo zamu amma yau zamu dawo, sai dai na
146
san za mu yi dare sosai, don heka zan yi kokari na yi
ma Abdullahi waya na sanar da shi ta sha mur tace,
'Kar ka sha wahalar yin waya yau ba inda zani ya
fiddo ido me kenan kuma? Ta dube shi yadda ta saba
a wofance, Haka na ga dama sai me? Da zuciya ta
kule shi bai san lokacin da ya ce. 'Gaskiya, gaskiya ke
matsala ce Mami, nan da nan ta mike zaune ta се,
Nice matsala ko, to wallahi ka gama zama da
matsala, sai kai magani na, ina dalilin wannan takura
kai ban kira ka matsala ba sai kai!
Ya debe kayan aikinsa ya fice shi dai yinin
wannan rana bai san yadda ya gudanar da ayyukansa
ba, shifa ya soma zullumin Mami din nan ko dai wani
abu ya shafi kwakwalwar tane iyayenta ba su gane
ba? har yaushe za'a ce yarinyar ba ai mata komi ba a
ko da yaushe sai tsiya, kai wannan ya zarce rashin
tarbiya, yanzu kuma idan ya nemi ya kai ta asibiti a
diba kanta ta sa mai ihu ya dora mata hauka, shin to
mene ne abun yi, shi kam ya gaji!
Lokacin da ya dawo ko ina a bude bata kulle da
makulli ba, ya duba agogo karfe daya da rabi na dare,
gabansa ya fadi anya ko Mami na nan! Har ya shiga
dakin baccinsa gabansa na faduwa bal,6al a
mamakinsa Mami na kwance bisa kafet ko filo bata
saka ba yace, ikon Allah ya isa inda take ya tsugunna
yace, Haba Mami kamar yau'mu ka soma samun
problem ki yi man hakuri ki koma bisa gado ki
kwanta, ki tuna nan ba jihar mu bace, mu bakin
kwadago ne, idan rayukanmu sun 6aci wa zai damu
da mu? Sai mu imu, ta galla mai harara tace, wannan
147
ita ee cutar da ka yi man inda a Kaduna har ka isa ka
zo ka yi man wannan surutan marasa ma'ana, bari na
gaya ma, daga yau ba ni ba kai na gaji da kai ka fita
raina, kasan Allah idan kaci gaba da matsamanz an
koma harabar gidan nan da zama har sai ran da ka
gama ikon ka kasa aka mayas da ni gida ya jima a
tsugunne yana dubar kwayar idonta lalle da ta yi mai
abinda tace gara ya hakura da ita har ta koma
Kaduna, ba tare da ta wulakanta shi ba. Yace, Na
amince da sharudan ki, amma ni ma don Allah ki
taimakan ki koma bisa gado daga yau ba zan sake yin
abinda zai kusanto ni gare ki ba zan kasance a falo
har ki bar garin ta mike da sauri ta haye bisa gado ta
kudundune.
Kwanan ta bakwai cif ko gaisuwa bata hadasu,
hatta kudin da za'a sai ma su Hajiyarsa kayan lanbu
Peter ya baiwa, da sassafe karfe biyar ta gama
shiryawa, ya kawo kudi dubu hamsin ya bata ya сe,
zai turo mata da cek sati biyu masu zuwa, tace, ka bar
kudinka na ga yama gaskiya ka yi ma kan ka
maganin matsala, ba fa za ka sake zama da matsala
ba, ta yi mai wurgi da kudinsa ta fice, ya bita har
mota ya bude but ya turo a aljihun akwati ba tare da
ta sani ba.
A Abuja su ka ci abincin rana ana mangarib suka
iso kaduna tace ya wuce da ita gidansu,ta yi kuma
sa'a Iyana na nan, bayanta sallami Peter ya tafi, sun
kulle daki ita da Iyana, Mami ta hade kanta da gwiwa
ta shiga kuka wiwi, Iyana ta zuba mata ido kawai
tana kallon ikon Allah can ta nisa tace, Wai ya sake
148
ki ne? Cikin kuka mami ta daga kai ta dubi lyana
tace, Ni wallahi lyana yanzu neman sanadin da
Sahabi zai sakan na ke, na gaji da fitinarsa wai yanzu
ni Sahabi ke ma gori na zame mai matsala! Iyana ta
yi tsaki tace, To mene ne abin damuwa har za ki sawa
kan ki damuwa ki ta rusa kuka, daman can ke ki kace
kina son sa, tunda har ku ka kai tsayin wannan
lokacin ba'a haihu ba, ai kila ba rabo ne a tsakaninku,
saboda haka banga abin tayas da hankali ba anan,
inda kun haihu ne a tsurawa zuciya damuwa kan
'ya'ya, yanzu ba shike nan ba kowa ya kama
gabansa.
lyana tace, tashi mu je can falo wajen Babanki,
suna shiga Alh. Abduljala yasan ba lafiya saboda a
cikin kwayar idon lyana ya kan fahinci rigimar da ta
zo mai da ita ako da yaushe, ya hade yatsunsa ya
dunkule hannu yana jiran ya ji ko mene ne, can Iyana
ta zauna ta tsara yadda ranta ya raya mata zan ce dai
duk na bata mutun wanda ita kanta Mami ta yi
mamaki sanin Sahabi bai taba yi matan haka ba.
Abduljala ya dafe kansa yadda ransa ke masa
daci tamkar ya bar duniya domin shida i yana soń
zuri'ar Sahabi kuma yana son halayyar Sahabi koma
dai mene ne shi yasan ba duk ba ne laifin Sahabi dole
ne itama Mamin da laihinta. Abduljalal ya lumfasa ya
ce yanzu ke Mami raba auran shi ki ke so? Bata cc
uffan ba ta yi kuri da ido a kasa can tace, Ni Baba na
yanke shawara England zan koma na karo ilmi zan je
na yi Second Degree dina, Babanta ya ce, Ni zan
dauki nauyin karatun ko Sahabi? Ta ce Ni Baba kai
149
zaka dauki nauyi, yace, in dai ina da iko da ke kina
son kuma tafiya karo ilmin to ki koma gidan Sahabi,
ina son ku zauna lafiya ki je karatun a bisa umarnin
mijinki, yana rufe baki Iyana ta hau shida bala'e,
akan don bai san 'ya'ya mata shi ne ya ke son, bakin
cikin Sahabi ya kashe Mami to ita ba zata yadda ba,
ta mike ta bar falon, mami ta sadda kai tana ta
sharban kuka ganin yadda Iyana ke neman ta zagi
mahaifinta saboda ita ko da yake dai tasan Iyana ta
saba zagin mahaifinsu a duk lokacin da ya 6ata mata
rai, ko kuma ya nemi ya canza mata shawara, a nan
dai Alh. Abduljala ya rinka lallashin Mami wanda ya
san shirme ya ke yi sai Iyana ta ga dama zata bar ta ta
koma gidan Sahabi a wannan daren da shi ya ke
bukata.
Ko da Peter ya kaiwa Hajiya sakon Sahabi, ta ce,
saukar yaushe, yace, zuwan su kenan amma ya sauke
Mami gidan Iyayenta har da kayan ta gaba daya
Hajiyar bata zargi komi ba ta san sangartar mami,
amam da Peter ya ce, a nan gidan Hajiyar Mami tace
ya kwana sai ta san to akwai wani abu, a nan Hajiya
tace, Abba ya kai shi dakin baki ya zo kuma ya kai
ma Peter abinci, kafin ma a kawo mai abincin Peter
har ya shiga shawa, ya ji dadi da Mami ta ce ya
kwana a hannün Hajiya domin yasan kula ta
musamman har sai yace ta isa, ga alhairi da zai samu idan zai tafi.
Sai da Mami ta share kimanin kwana goma
zaunc a gidansu tana juya rayiwarta yadda ta ke so ba kwaba ba tsargwama. a wanan ranar ce lyana zata
150
Abuja suna sallama da Mami, ta ce, lyana na gama
rubuta takardar neman makaranta har kala biyu a
England, insha Ållah kuma zan samu idan ma baba
ya ki biya mani ina jin zan samu a biya man a ofis
din mu under
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 10 Chapter of 13