kuma Wanda yakeda matsayi da ikon mulkin BOYEM dan haka a duniya kaf yanzu ASIM ne kadai zaayi wa wannan karar sai kuma ‘dan da har abada bazai taba dawowa BOYEM ba,
To idan sultan da ASIM duka suna cikin masarautar waye zaa bugawa wannan sautin idan ba Wanda baya nan ba kenan shi dinne ‘dan mistress din BOYEM ya dawo Bayan shekaru masu yawa.
Jin Aslam tayi tana Neman rasa ganinta sbd shock da mamaki mai girma dan kuwa kwana da wuni sukeyi tareda kowace daqiqa ta rayuwarsu suna rokon Allah ya hanasa dawowa Masarautar da rayuwar sultan har abada dan haka ayanzu datake kasa yadda da shi dinne ya dawo doguwar Rigar sarauta me fadi da tsayi tareda adonta janyo ta Dora Akan Kayan baccin dake jikinta ta nufi kofa ta fice zuwa bangaren mahaifiyarta da a lokacin take tsaye tanason daga kafafunta zuwa toilet amma komai nata yayi nauyi takeji hakama kwata kwata kanta ya kasa dauka ko kawo tinanin LEUL BOYEM zai taba dawowa Masarautar BOYEM din sbd an tabbatar mata da babu alkhairi ko kadan a dawowansa gareta da zuriarta dan haka bata taba yin qasa a gurin aikin da har abada bazai taba dawowaba amma alamu sunata nuna hakan bazai samu ba dan haka aiki akeyi tuquru Akan mahaifiyarsa bazata taba shaawan dawowansa ba zataita hanasa dawowa duk kuwa yanda take Jin tsananin so da kewansa bazata iya bude Baki tace ya dawo ba dan haka wannan ya saka hankalin HAILE kwanciya koma dai menene su samu ASIM ALMAZZ ya hau mulkin BOYEM idan ya hau ko yaushe NUAB ya dawo din sun sai riga sun samu abinda suke so buri ya cika.
Aslam na isowa Kai tsaye bedroom din mahaifiyarta ta nufo jakadiya dake palon karshe na hutawan HAILE tana bawa masu gyaran palon umarnin tsarin da zaa sauya cikin girmamawa ta kalli Aslam din zata gaidata amma ko ganinta Aslam bataiba ta wuce ciki Kai tsaye daidai lokacin da HAILE ta isa kofar toilet din mai girma da tsari zata shiga,
Shigowan Aslam ya saka Hailen dakata wa cikeda mamaki mai dan girma idanuwanta Akan Aslman din sbd ganin lokacin da Aslam din ta taho
Bude Baki tayi zatai magana Aslam ta rigata da cewa
‘Ya dawo,
Shine ya dawo Bayan shekaru Mamee,
Ya dawo Masarautar BOYEM,
‘Dan mistress din Sultan ya dawo Mamee,
Ya dawo a daidai lokacinda muke kokarin ganin mun cimma burinmu kota yaya,
Mamee tayaya zaki kawar da sultan daga duniya ASIM ya hau mulki a yanzu wannan yana masarautar?
Tayaya zamuyi aure yanzu?
Tayaya komai zai tafi yanda mukeso a yanzu da wannan din ya dawo?
Tayaya sultan zai bar duni……..
Wani lafiyayyan mari HAILE ta sauke mata cikin kidima da rikicewa zuciyarta na wata irin rawa sbd gabaki daya Aslam wata irin mahaukaciyar zuciya ne da tinani da ita, matiqar zata shiga tsananin baqin ciki da bacin rai haka zata ringa tona asirin zuciyarta cikin tsananin baqin ciki da Zafin zuciya dayake fiddata hayyacinta dan hakanne ya saka haile bata barinta magana koina sbd zata iya aikata kuskuren da zaiyi karshen rayuwarsu gurin magana idan takai maqurar bacin rai,
Marin da HAILE tayi mata ita kanta hayyacinta barin jikinta yakeyi da abinda Aslam din ta fada dan kuwa bazai taba yiyiwa ace NUAB ALMAZZ ya dawo Masarautar BOYEM din ba dan haka tafi yadda da sultan ne ya fita kila ya dawo batareda saninsu ba dan haka Kai tsaye toilet ta fada kafafunta na dan rawa hakama zuciyarta na tsalle.
Alwalar sallar asuba zatai amma gabaki daya ta rikice hannuwanta rawa sukeyi bata Kama ruwa ba alwala tayi ta fito har lokacin kafafunta rawa sukeyi zuciyarta data kasa yadda da abinda Aslam ta fada amma sai bugawa takeyi sosai tana Jin batada Sauran nutsuwa idan zuwa tayi ta tabbatarda waye ya shigo akai wannan sanarwar.
Kallan Aslam dake Zaune cikin matsanancin yanayi tayi zuru ta bude Baki tace
‘Kije kiyi sallah zan tabbatarda me yake faruwa idan na kammala komai da kaina zan tafi gurin sultan dan tabbatarda komai.’
Miqewa Aslam tayi batareda tace komai ba sbd jikinta dayake matiqar a sanyaye babu kowace irin kuzari a tattare da ita dan kuwa a duniya babu abinda zai iya kashe zuciyarta lokaci daya ta buga irin ace bazata samu cikar burinta na aure ba Wanda shine maqasudin ragewansu Akan ASIM ALMAZZ ya hau mulki,
A yanzu rana tsaka idan NUAB ALMAZZ ya dawo BOYEM tabbas zasu samu babban katangar da zata iya shiga tsakaninsu da burinsu duk da bawai yadda zasuyiba zasu iya aikata komai Akan cikar burinsu ciki kuwa hadda kawar da rayukan wainda baa taba tinani ba.
Ficewa Aslam tayi zuciya da gangar jiki ba nutsuwa hakama HAILE tada sallarta tayi itama zuciyarta babu sukuni.
*****Motocin daya bayan daya suna zuwa can quryar harabar da iya jinin sarautar suke isa can a Jere suka fara Parkin daya bayan daya cikin tsarin da suka saba motar LEUL dince a tsakiya
Kai tsaye suka fara fitowa daya bayan daya aka bude kofar da LEUL BOYEM yake Zaune ya ziro kafafunsa cikin izza waje kafin ya fito gabaki dayansa yana shakar iskar Masarautar datake jininsa,
Lumshe fararen idanuwansa masu kyau da kwarjini me zafi yayi yana Jin Wani bangare na zuciyarsa yaja cikewa da gurbi me Zafin dayake ciki da wani sanyi me ratsa zuciyar sbd Ayau gashi inda mahaifiyarsa ke rayuwa yana shaqar iskar Numfashi daya da ita,
Gabaki dayansu a tsaye suke qyam babu alaman gajiya ko buqatan Hutu a tattare dasu ko kadan saima karfinsu mai daga hankali dayake sake bayyana.
Sarkin bayi ne cikin wata irin gaggawa ya iso gurin tareda tarin bayin da suka zube qasa gabaki dayansu kansu a qasa suna gaidasa batareda sanin yabar gurin ba Kai tsaye bai jira komai da kowaba ya doshi bangaren mahaifiyarsa shi daya tak sbd babu me hurumin shiga bangaren matan sarki idan ba ‘yayansu ba dan haka gabaki daya Yaransa suna tsaye a inda motocin su suke babu alaman sauki ko rahama ko daya a fuskarsu.
Aleey ne ya sanar da sarki bayi LEUL BOYEM ya Riga ya wuce bangaren mahaifiyarsa nasa bangaren suke buqatan a kaisu dan tabbatarda tsaronsa.
Babu bata lokaci Kai tsaye aka wuce dasu bangaren nasa me girma Wanda yake part guda mai tsari da kyau,
Duk da baya nan babu shekarar da baa sauya furnitures da komai na bangarensa sbd haka doka da kaidar take,
Komai na sauyin da ake masa ahankali ahankali yana tafiya ne da cigaban zamani da ake samu har zuwa yanzu da aka zuba duk wani luxury na rayuwa da zai basa Hutu da nutsuwa isasu,
Komai a tsare yake da duk abinda zai saka yaji kaman yana gidansa na Moscow kawai dai yar qura ce sosai itama a take Sarkin bayi ya fara bada umarnin a fara gyara.
Dakatar dashi Aleey yayi cikin nutsuwa da buqatar full control na kulawa da komai daya danganci lamarin LEUL komai qanqantarsa,
Babu abinda babu a Masarautar BOYEM na Jin dadi da biyan buqata dan haka take Aleey ya bada umarnin a fara sauya komai dake bangaren a cikin kankanin lokaci dan haka ba bata lokacin Sarkin bayi ya saka a fara fidda Kayan a fara shigo da wasu da suka fisu komai.
******Sultan YASAR a daidai lokacin da sautin qarar dawowan magajin dayayi shekaru yana jiran wannan ranar ta dawowansa a wannan lokacin wayar sa ne da wishmah ayanah ghaz wadda a tare sautin ya shiga kunnuwansu ya isa ga zuciyarsa yana sanyayar da wani gurbi me girma da yayi shekaru a zuciyarsa,
Ahankali sautin yake sake ratsashi ya rufe idanuwansa masu kyau da kwarjini yana jan wani Numfashi me dumi ya saukesa a hankali tareda bude idanuwansa Akan fuskar Ayanah dake bayyane kan screen dinsa shiru ta zuba masa ido a sanyaye bata iya cewa komai.
A natse cikin sanyin nutsuwa ya sauke ajiyan zuciya datake dauke da shirin zartarwa da shirin fuskarta abubuwa da dama a masarautar da wainda suke cikin masarautar dan kuwa wannan ranar yake jira Wanda NUAB ALMAZZ zai kawo kansa masarautar da kansa amma kuma fitarsa da kansa ya rasa kenan saida umarnin sa dan kuwa shine yake riqe da cokalin juya rayuwarsa yanda yaso har sai ya cika masa burinsa daya dauka akansa tin daga ranar daya diro duniya,
Burinsa daya saka ya banzatar da abinda yakeso fiyeda komai da rayuwarsa.
Kallan Ayanah yayi a natse ya Lumshe ido akanta ya sake budesu akanta kafin ya bude Baki cikin mulkin dayake yawo jininsa shima da sautin daya shigeta yace
‘HAYATEEM dinki Zaki me BOYEM ya dawo gareki a matsayin cikakken namijin da BOYEM ke buqata’
Motsa idanuwanta tayi akansa tana Jin maganar tasa ta sauka cikin hankali da tinaninta harma da gangar jikinta dan haka ta motsa tana tashi Zaune da kyau duk da bata karfi ko kadan sbd rashin lafiyan datake cinta,
Juya kanta tayi ahankali zuwa kofar ficewa bedroom din nata datake ciki daidai nan sultan ya kashe wayar yana jinginar da bayansa ga lafiyayyar kujeran dayake Zaune ta bedroom dinsa tareda dake rufe idanuwansa ahankali zuciyarsa na yin dum tareda shiga tinanika da dama.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
53
Ahankali tafara Takawa tana nufar kofar bedroom din nata idanuwanta na kafe kofar da idanuwanta tanajin jikinta na qara rasa karfinsa da kuzari,
Duk takunta daya nauyi kirjinta qaruwa yakeyi ta daga hannunta da baida karfi ta Dora a kirjinta tana dafe sa sbd kaman gangar jikinta bazata iya daukan nauyinba Wanda tsawon shekarun tana jinsa amma Ayau yayi tsananin da jikinta ke sake sakewa ta isa kofar ta zubawa hannun kofar idanuwanta da sukai jajir a take batareda tasan menene takejiba a yanxu kuma,
NUAB kuwa tinda ya doso bangaren bayin dake hanyar gabaki dayansu suke zube qasa kansu na yin qasa dan idanuwansu basuyi darajar da zasu kallesa ba dan haka ko motsi me sauti babu me yi tsit hanyar ta dauka badan babu mutane ba Sedan tsananin bada girma ga jinin BOYEM.
Tinda ya tinkaro din shima kowane takunsa dawo masa da kowane Taku da yayi a ranar barin masarautar yake,dawo masa da takun da yayi a ranar daya rabu da mahaifiyarsa,rayuwarsa sanyi da hasken idaniyarsa wadda se yau ze sake haduwa da ita,
Babu hanyar da zata isar da shi bangaren mahaifiyarsa ko daya data bace masa duk da akwai manyan gyare gyare da sauyi da aka samu me yawa amma dai mahaifiyarsa na nan inda ya barta dan haka babu jiran komai Kai tsaye gurinta yake nufa.
Koda ya iso kofar bangarenta dayake dauke da sunan wishmah Baro Baro a jiki wani irin Numfashi me sanyi ya sauke yana dawo da kallansa kan Maa sakinah datake fitowa a hankali cikeda mutuwan jiki da mamaki idanuwanta na sauyawa da wani irin kallan datake masa zuciyarta na sake narkewa dan kamannin jinin GHAZ dayake bayyane a fuskarsa musamman Abaas Wanda yafi Kama da Ayanah sak dan haka kasa cigaba da kallansa sakinah tayi tana qasa da idanunwata hawaye na taruwa a cikinsu,
Maa tenya ma a sanyaye take fitowa dan tarbansa a matsayinta na jakadiyar Amminsa dan haka saukar da idanuwanta qasa tayi daga kallansa tana jinin Wani irin girmammen farin ciki da mutuwar jiki a lokaci daya dan haka bude Baki tayi zata fara gaisuwa da kirarin dayake dolenta…..
Katseta yayi Kai tsaye da muryansa data saka bayin dake bangaren sake Shan jinin jikinsu kansu a qasa,
‘Na dawo Maa’ ya fada a natse Kai tsaye yana kallansu su biyun zuciyarsa cikeda kauna da girmansu,
Tenya ce kauna da matsayin dayake dashi a cikin ranta ya danne matsayinta na jakadiyar sa data mahaifiyarsa ta dago tana fidda Wani murmushin farin ciki mai sanyi tace
‘Barka da dawowan me BOYEM da kansa,
Barka da dawowan Hayateem me zuciyar uwa da uba,
Barka da dawowan Zakin mazan boyem,
Barka da dawowan me jinin boyem da ghaz,
Barka da dawowan magajin asali na BOYEM,
Barka da dawowan LEUL me uwa uku’
Numfashi kawai ya isa saukewa yana kallan Maa sakinah da adduoin tsari kawai take jero masa a zuciyarta da ko bata bayyana ba ya sani haka take ita koyaushe bakinta a cikin adduar basa kariya da tsari daga kowane Sharri take kuma baa fili ba,
Ciki suka juyo suna qarasowa suna gaba yana bayansu dan yi masa iso ga inda mahaifiyarsa take,
A babban palon suka tsaya dukansu suna basa hanyar wucewa palo na gaba shi kadai dan isa ga mahaifiyarsa,
A natse ya wuce ya isa kofar ya saka hannunsa ya bude tareda saka kafarsa ciki idanuwansa na dagowa kallan kofar dakinta data bude itama tana fitowa da tsananin sanyin kafafu idanuwanta da sukai ja suna sauka akansa batareda ta kyafta ba
Shi kansa idanuwansa jajir suka a lokacinda ya kafeta dasu yana mata kallan da kowace gabar jikinsa ke amsa tsananin kaunar dayake mata.
Kasa motsawa tayi daga inda take cak duniyarta na Wani irin Juyawa sbd kasa yadda da abinda idanuwanta ke gani,
Da gaske ne NUAB dinta ne a gabanta kokuwa ire iren gizon da yake mata ne shi da Abaas,
Shi kansa mutuwar tsaye yayi a gurin dayake yake din yana kallan kowane yanayi da mahaifiyarsa ta koma Wanda hadda manyanci dayake nuna tsufa Yazo a tattare da ita ga ciwo fa qunci da damuwa da kadaici tareda rashin cikakken tinin kanta dan haka kan idanunwansa suke sake yin ja radadin rashin lokutan mahaifiyarsa da aka rabasa dasu tin kuruciya suna dawo masa dan kuwa an hanata yarintar ‘danta kaman yanda aka hanasa yarinta a gaban mahaifiyarsa,
An hanasa samun kulawa da tattalin a lokutan ciwonsa da baqin cikinsa kaman yanda kowane ‘da yake samu daga mahaifiya ko mahaifansa,
Shi shikadai yake ciwo yayi jinyar kansa ya kula da kansa ya tsayawa kansa yayiwa kansa komai tamkar marayan da baida uwa baida uba baida gata,
A lokutan ciwo mai tsanani da dama yayi kukan rashin mahaifiyarsa da dumin jikinta kadai zai iya basa warakar dayake nema da sassaucin kowace irin azaba amma duka an hanasa samun hakan an hana mahaifiyansa samun basa hakan daga karshe dai Bayan shekaru Ayau Allah ya hadasu haduwan da mutuwa ce yanzu kadai zata rabasa da ita badai kowane ‘dan Adam ba komai matsayinsa kuwa a duniya.
‘HAYATEEM’ bakinta ya bude ya furta a hankali cikin wani irin sautin daya saka gabaki daya tsigar jikinsa tashi ya tako bai tsaye komaiba ya janyota jikinsa ya rungume da Wani irin karfi yana rintse idanuwansa da har wani radadin yaji suke masa.
Sake ambatar sunansa tayi da sautin daya sake tada duk wata tsigar jikinsa tana Qanqamesa ta fasa wani irin kuka mai qarami da sanyayar sauti tana Jin nauyin kirjinta yana fadawa qasa ahankali ta sake qanqamesa tana ambatar sunansa.
Dagota yayi ya Kama fuskarta da tafukan hannuwansa biyu yakai bakinsa tsakiyar kanta yayi kissing cikeda tsananin kaunarta ya sake juya gefen fuskarta yai kissing ya dago hannuwanta duba biyu yayi kissing kowanne ya sake rungumeta jikinsa tsamtsam yana Jin kaman bazai taba iya rayuwa ba daga ranar da wani mummunan abu ya sameta dan itace kuzarinsa kuma itace weakness dinsa dazai iya bada komai nasa da kansa akanta.
Kuka takeyi sosai tana Jin zuciyarta kaman zata fashe da tsananin kauna da son ‘danta Wanda bata taba ji a ranta zata gansa a gaban idonta ba,ta cire rai daga ganinsa har rayuwarta ta fita tabarta,
Da kewa da radadin rashin sa take kwana take tashi tareda wuce kowace daqiqar rayuwarta amma bakinta kaman an riqe bata taba iya cewa ya dawo koyaushe sedai kada ya dawo bama zata iya tina yaya bakinta ya iya furta masa tana son dawowansa ba kuma duk da ta furta din bata saka ran zuwan nasa ba bare ganinsa ba dan haka take Jin Wani yanayi na tsananin farin cikin rayuwarta a karo na farko Bayan shekaru masu yawa cikin qunci da baqin ciki Ayau ruhinta ya dandana dandanon farin ciki da samun abinda zuciya ke so dan haka take sake qanqamesa da rashin kuzarin datake fama dashi tana rufe ido sbd kuka.
Sun jima a hakan tsawon lokaci kafin a natse ya zaunar da ita Akan sofa mai Laushi yana riqe hannunta cikin nasa cikeda dukkanin kulawa da bayyananniyar kaunar datake shigarta tana sake kashe jikinta akansa tana kasa dauke idanunwata Akansa farin cikinta a bayyane.
Hannunta ta daga ahankali ta Dora Akan fuskansa ta shafa tareda sakin murmushin daya saka idanunwansa qarasa rikidewa jajir sbd Ayau itace ranar farko dayaga murmushi Akan fuskar mahaifiyarsa tinda ta haifesa,
Bude Baki yayi da Wani irin sauti daya sake sakata shafa fuskarsa tana ganin kammanin da bazata taba mancewaba shimfide a fuskarsa yace
‘Ammi,Ammi na dawo gareki bazan taba sake rabuwa dake ba koda zan rasa komai Akan hakan,
Ammi bazan iya sake rabuwa dake ba,
Ammi zan nema miki lafiya da duk abinda kikeso nayi miki Alkwarin cika miki shi,
Ammi zan tafi dake na Nemo miki Abaas a duk inda yake fadin duniyar nan na kawo miki shi gabanki,
Ammi ina son ki cire dukkanin damuwa da quncin dayake ranki sbd lafiyarki,
Ammi…….
Hannunta ta Dora a bakinsa cikin nutsuwa kafin ta rungumesa tana kwantawa gefen kafadarsa ta bude Baki tace
‘Zan bika duk inda zaka tafi dani HAYATEEM,
Bazan iya rayuwa ba idan Ka tafi Ka sake barina,
Zuciyana bazata iya sake daukan rayuwa babuka ba HAYATEEM,
Karka banni Ka tafi dani ko ina ne zan bika na rayu tareda Kai sanyin idaniyata….
Yanda take maganar ya sake Sosa zuciyarsa fiyeda yanda zai iya boye wa dan haka hannuwansa suka dan ringa rawa ya rungumeta sbd akwai alaman rashin lafiyan jiki da tinina sosai a bayyane da sautin maganarta.
Maganganu ya bude Baki yafara jero mata masu nutsuwa da samar da nutsuwa a kwakwalwanta yana bayyanar mata babu abinda zai qara rabasu sai mutuwa dan haka ta kwantar da hankalinta ta cire damuwan komai dan babu inda zashi batareda ita ba.
A daidai wannan lokacin aiki akeyi gadan gadan a bangaren me girma LEUL din Yaransa suna tsaye qyam Akan aikin Wanda take aleey yayi ordern wasu manyan Kayan da abubuwan da suke buqata na ubangidansu daga wajen masarautar kuma aka kawo cikin gaggawa suka duqufa sbd kafin ya gamo ganawa da mahaifiyarsa suke buqatan komai na bangaren ya kammala daidai da hutawarsa,
Acan bangaren wishmah dinma Maa sakinah ce a tsaye tareda masu aiki da bayi Ana aikin abinci na musamman me tsari da tsaftar gaske tareda lafiya daidai da taste dinsa tin na yarinta duk da sunsan ya sauya tako ina amma dai sunsan zai kaunaci komai da zaayi masa sbd kewansu da kewan kulawansu akansa da girkinsu.
Maa tenya kuwa take qwanjinta da kuzarinta harma da walwalanta ta dawo a lokaci daya Jin kanta takeyi tenya dinta ta baya da zata iya tsayuwa ako ina dan bawa NUAB da Ayanah kariya da duk abinda sukeso dan haka take ta bada umarnin a tara bayin da zasu ringa hidimar bangaren LEUL boyem da kanta zata zabesu ta basu training me karfi da kyau dan kuwa karfinsu ya dawo fiyeda ma Wanda suke dashi a baya dan kuwa a bay suna shakkar a cutatar musu da NUAB suna basa kariya amma a yanzu shine Wanda zai basa kariya a karkashin iko da karfinsa.
#MAMUH
HAYATEEM
by
Mamuhgee
700
0022419171 AccessBank Maraym Sani gummi
09033181070
Yan Nijar kuma
89825722
Depot my nita
Nissaiba laouali
[09/12, 10:47 am] Asia ahmd: *_HAYATEEM_*
Mamuhgee
54
Tin asubar da sautin karar dawowan LEUL BOYEM ta shiga kunnuwan duk wani babba me matsayin dayake masarautar a tsaye suke suna kaida kawo cikin mamaki me girma da shakka tareda tinani kala kala Wanda rashin tinanin kamawa ma yafi yawa a cikin kwakwalwansu sbd a tsawon shekarun nan sun manta sun shafe magana da tarihin LEUL boyem daga masarautar babu Wanda ko a maida zance ya kuma tada maganarsa kaman yanda sukaga sultan bai taba maganarsa ba saisu ma suka watsar dashi da zancensa kaman yanda aka rufe babin mahaifiyarsa kwata kwata baa ma sakota a lissafin matan sultan kokuma wanzuwarta ako wace hidimar masarautar da ake buqatan halartar matan sultan din dan duk inda akace matan sultan to su uku ne keda cikakken ikon sunan sbd zamantowanta wishmah duka ya Halarta mata wannan suna da matsayin,
Ayau Asuba tsaka kawai cikin bacci da rashin tsammani ko a mafarki sukaji sautin sanarwar dawowansa batareda aiko da sakon dawowan tasa ba kaman yanda yake tilas kawai suka samu dirarsa a masarautar,
Babban abinda ya girgiza kaf manyan fadar masarautar shine a bayan ASIM ALMAZZ suke sun shirya tsaf sun yanke kuma sun kudirta shine sultan na boyem dan kuwa daga ranar da aka wayi gari babu sultan bazaa qara awa biyu ba batareda sun nada ASIM ALMAZZ ba wannan Alkawari ne da burin da kowannensu yake dashi.
Dan hakanne dawowan LEUL BOYEM ta girgiza su jijjiga me karfi sbd basu taba saka ran dawowansa ba
Sun shirya goge sunansa da uwarsa a cikin tarihin boyem daga ranar da sultan YASAR yabar duniya hakama sun saka rai sun kwanta da tinanin koda zai dawo qasar to sanar da daya daga cikin iyayensa sun mutu.
Meya dawo dashi kwatsam haka babu zata ba tsammani?
Menene dalilinsa na dawowa Bayan shekaru masu tsayi?
Idan ma yana tinanin ya dawo ne karban matsayinsa to tabbas ya makaro dan bazasu taba Bari ba korasa zasu sake yi inda ya fito wannan Karan ma shi da uwarsa kila dan haka a shirye suke dashi zasu nuna masa karfin matsayin da suke dashi Wanda sunada ikon zartarwa,
ASIM ALMAZZ ne sultan na gaba Wanda da karfi zasu tabbatar masa da hakan ya tattara ya koma Gagarin dayake yi bada gatan masarauta ba hakama dole zai amsa kiran shugabannin Masarauta ya fuskanci hukuncin dokar daya taka ta masarauta ta zuwansa batareda ya aiko manzon aike ba da wannan zasu hukuntasa ya koma inda ya fito.
Hakan ya saka kusan dukkanin manyan suke a cikin tinani daya da shiga tsananin son ganinsa da isar dayake ji da ita dan haka suke a cikin shirin isa fada da gaggawa sbd ko sultan dole yana can cikin bacin rai da fushin abinda LEUL din yayi.
Koda karfe goma na safe ta buga duk Wanda yake masarautar ya samu cikakken labarin isowan sa,
Hakama waje da garuruwan dake qasar sun fara samun labarin dawowan LEUL BOYEM,
Yan jaridu ma da television tini suka fara yada Labaran Wanda Aleey ne da kansa ya basu cikakken bayanan ta waya sbd qasar BOYEM ta shedar da zuwan magajinta koda kuwa ziyace kadai ya kawo ba zama Yazo yiba,
Yanda zancen ya ringa yaduwa da shiga koina ya saka mutane dama yan jaridu fara jefa maganganun to a yanzu waye asalin magajin da zai mulki BOYEM,
Waye asalin me BOYEM a cikin magajin guda biyu da ake dasu,
Waye sultan zai zaba bawa mulkin da kansa kokuwa jira zaiyi saiya bar duniya Allah ya bawa me rabo saa?
Wannan maganganun ne suka fara daga hankalin wainda sai daga baya labarin dawowan LEUL BOYEM din ta samesu maana ASIM ALMAZZ kenan da HAILE wadda ta tabbatarda NUAB ALMAZZ dinne ya dawo da gasken gaske kenan.
Gabaki dayanta da yayanta a Zaune suke babban palonta na hutawa sunyi shiru kowa da abinda yake ransa idanunwansu jajir babu Wanda jininsa baya tafasa yana hawa sbd tsagwaron zallan baqin ciki bawai dan suna tsoron sa ba sbd basa tinanin yanada abinda zai sakasu tsoron sa ko shakkarsa kawai dai sultan da suka gama samun cikakken kansa Akan tinanin yama gama Dora ASIM ALMAZZ a mulkin BOYEM yanzu kuma wannan ya dawo zai rikitar musu da tinani da raayin sultan dan haka suke cikin baqin ciki me tsanani amma Bayan hakan Sam sunsan tako ina babu inda zai kamo kafar ASIM a komai dan haka sukai shiru cikin takaici da baqin ciki,
ASIM ALMAZZ dayake Zaune a kujeran datake ta Mutum daya idanuwansa a dan rufe yayi shiru da zurfafa a tinani bude idanuwansa yayi ahankali ya sauke Akan mahaifiyarsa kafin ya bude Baki cikin tasa Izzar da Wani irin yanayin dayake ji a ransa na babu Wanda ya isa ya rabasa da matsayinsa dayake Kai da Wanda yakeso a duniyar nan batareda ta aikasa inda ya kamacesa ba yace
‘Mamee babu abinda zai faru ki kwantar da hankalinki kokarinki na shekaru bazai taba tafiya a banza ba zan tabbatarda da hakan,
Indai ba nine magajin karagar mulkin BOYEM ba to tabbas BOYEM zata rasa magaji da sultan din da zata kira nata,
Kawai dai a yanzu ku Bari wannan dan gudun hijirar daya dawo ya gama abinda ya kawosa ya tattara mistress din mahaifinsa ya qara gaba da ita zuwa yawon bin yan taaddan da akace yanayi.’
Karban zancen HAILE tayi cikin wani irin radadin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 28