Share this page
ba dake sun santa da son aiki hala har ta wuce gidansu anty mojushola tayasu shirye shiryen bidiri. A ta fannin Adiaha kuwa daren gaba daya bata samu runtsawa ba dan duk hanklinta atashe yake da furucin Ahmed akan abunda kakarta tace akansa. Ta tura masa tex na ban hakuri yafi a kirga baiyi replyn ko daya ba, tana kiran layinsa kuma zataji akashe kusan kwana tay tana cikin damuwa akansa sosai. Washe gari da kyar ta tashi zatay sallah dake bata wani iya sosai ba saida ta danne zuciyar ta taje sashen hjy hajarat. A zaune ta sameta akan daddurma tanajan charbi Kallo daya tay mata ta dauke fuskarta dan bakaramin takaicinta takeji aranta ba. Ganin yanayin kakar tata ya sakata jin bata kyauta mata ba, dake tana da tausashiyar zuciya hakanan ta zauna kasa kusa da ita tafara bata hakuri akan rashin kunyar datayi mata jiya agaban mijinta. Hjy hajara taso ta karayi ma Adiaha magana akan Ahmed koda zata shiga hayyacinta a fasa auren nan amma yanayin Adiahan yasaka ta kasa iya ce mata komi. Cikin sauke nannauayr ajiyar zuciya Tace mata ai komi ya wuce Snn ta amince mata tay aurenta da duk wanda take so tunda Abunda ta zaɓa ma kanta kenan.. Adiaha ta y murmushi tace ta gode,hjy hajara bata karace mata uffan ba harsaida ta kammala guiding dinta tay sallan safiya kafin suka zaune take ce mata Alhaj Aliyu zai kira Ahmed din ya bashi hakuri. Snn za'a daura auren ne da misalin karfe 2 da rabi na rana dan sunce yau zasu koma Abuja tareda ita. Nasiha na zaman aure ta dinga mata, dana hkrin zama acikin dangin miji da iyayen mijin gabaki daya musmmn ma da dukansu suka kasance kabilu, tanayi tana jefa mata hannunka mai sanda acikin zantukan nata wai koda zata dan fahimceta tay makanta karatun ta nitsu amma ina Adiaha tay mugun nisa a son Ahmed bata gane komi idan ana fadin laifinsa agabanta. Sassafe Alhaj aliyu ya danne zuciyarsa ya nemi Ahmed awaya privately ya masa magana man to man akan abunda ake ciki, Abun yadan ba Ahmed mamaki amma dake abokinshi banji ya riga ya bashi hakuri sai ya bawa alhaj aliyun hakuri kawai yace masa ayi masa afuwa lkcin datazo masa da maganan ranshi a bace yake shima badon ransa yaso yagaya mata hakan ba. Tunda sukadan samu fahimtar juna da Ahmed shikenan kowa hankalin sa ya kwanta aka dawo ana jiran lokacin daurin aure. Iya bakin kkri alhaj aliyu da hjya hajara sunakan yi wajen hidiman abincin da za'ai awajen daurin aure kominsu dan daidai gwargwado. Banji ne aka aiko da safe yazo gidan ya kawo ma Adiaha kudi kimanin dubu dari biyu akan ta siya kayayyakin da zata saka da duk wani irin kwalliyar datake so tay na daurin aurenta ayau. Tun da safen suka shiga kasuwa da kudin ita da kakarta hajya hajarat dan adan kimtsata tay kyau tunda yau ranar aurenta ne. Bangaren su hajiya khadijatu kuwa tun asubahin fari da suka idar da sallah suka dokawa brother kazim kira atunanin su gara ayi maganan tun yanzu kafin ashiga hidiman waliman komawar sabuwar gida. Suna kiranshi kuwa ya dauka sai yace musu bari ya fita a office dinshi zai kirasu dan lokacin mun ba daya bane dana can, yace zaiy connecting da brother hamzat sabida maganan babba ne. Duk hanklinsu a tashe ya barsu yaukam ma sama sama sukayi break fast hanklinsu nakan waya suna jiran kiransa, da safe ne amma sosai gidan yay shiru duk anje gidansu anty mojushola dan anan ne za'ayi duk wata shirin hidima. 8clk dot saiga kirar brother kazim ya shigo. Suna dauka sai brother hamzat shima yay kira daga yola sai suka hadu akan screen na computern mahaifinsu. Sunkai minti biyar suna gaishe da iyayen nasu cikin nitsuwa da nuna girmamawa sosai. Kafin nan sufara tattaunawa akan Ahmed a farko ma saida brother kazim ya musu albishir da sabuwar mota jeep high lander ta tayi yar 20 million daya siya musu na gida yace kyautarsa kenan dazai basu na murnan komawa sabon gida, brother hamzat kuma ya dauki nauyin cewa shine zaina ciyar dasu agidan daga yanzu. Murnan jin hakan yasaka har iyayen nasu har suka mance da damuwarsu akan Ahmed na lkcin sukadinga saka musu albarka suna musu fatan Alheri a rayuwarsu dukansu biyu har suna hawayen murna. Each time suka shirya kawo maganan auren Ahmed sai sundan yi wasa da emotions dinsu Koda sukaga sun yi sanyi suna cikin tsananin jin dadi da farinciki anan ne suka dawo a siyasance suka kama kan Maganan rayuwar Ahmed. Lokaci guda kowa ya nitsu. Tiryan tiryan Brother hamzat ya fara magana yanamai basu labarin duk wani abunda ake ciki da batun Ahmed da Adiaha yanayi brother kazim din kuma yanamai kara yima abun kwalliya sosai yadda zai saka sunajin tausayin yarinyar sosai. Abu dayane basu gaya musu ba shine zancen zuwan Ahmed garin calabar akan Adiaha. Kawai dai sun killace labarin ne ta hnyar nuna musu cewa poor Adiaha ta hadu da Ahmed ne during his reaserch kuma gashi harta sadaukar da komi nata sabida shi, yace "iyayenta, addininta da kabilarta, duk ta aje akan dan uwansu Ahmed kuma tunda Ahmed din yace musu hanklinsa ya kwanta da ita su sun yanke shawarar kawai ayi hakuri kawai abashi ita inyaso daga baya asasanta da kafayat. Da mamakinsu kuwa Alhaj belllo ne ya fara amincewa da maganan dan bakaramin tausayin Adiahan yaji aransa ba duk dama bawai sun gaya masa asalin labarin ayadda yake azahiri bane. Saidai jin cewa ta sadaukar da komi nata harta gudo yola domin Ahmed yasan cewa tabbas yarinyar tanason dansa sosai, brother hamzat yace musu yay bincike akanta sosai kuma ya hadu da kakarta a yola sunce in Ahmed din ya shirya zasu bashi auren yarinyar. Daga hajy kahdijatun har alhaj bellon mamakin yayansun suka dinga sha jin sunyi komi aboye batare da sanninsu ba. Sun dade suna tattaunawa akan lamarin har dai brother kazim ya fito musu sarari yace yana son aje adaura auren Ahmed din yau domin akawo yarinyar Abuja cos she dont have anyone anymore face Dan uwansu AHMED. Iyayen sunso suja maganan amma hakanan yayunsa suka cinye su da kalamai masu dadi, duk inda aka bullo saisun toshe. Brother kazim yace zai turo musu harda files na private investigation akan familyn Adiaha inma suna son suga shaida akan komi domin hanklinsu ya kwanta. Alhaj bello da hjy khadija still basu amince da zancen auren kai tsaye ba saidai sunce sudai bazasu hana auren ba amma maganan ayishi yau yau sai sunyi shawara atsakaninsu tukuna, Sukace a basu nan da karfe 10 na safe zasu nemesu suji. Bayan sun kammala wayar suka zauna tsakaninsu suka dan tattauna Akan lamarin Kadan kafin kowa ya koma sashensa domin yin cikakken tunani. Banda tausayin Adiaha babu abunda ya cikama alhaj bello jimada kai. Shikansa gani yake kmr tabbas koba dan komi ba iyakar jihadin zanca addini da Yarinyar tayi ta baro iyayenta akan dansa kodan wnn zai bari Ahmed din ya aureta dan su samu ladan shahada dukansu. Ata fannin hajya khadijatu kuwa kanta sosai ta kulle tsakanin labarin Adiaha da kuma lamarin kafayat da already take zarginta da juya mata baya. Wani bangaren na zuciyarta na gaya mata cewa idan sukayi hakan basuma kafayat Adalci ba duba da irin jiran Ahmed datay tun tsawon lokcin yaranatar su,awani bangaren kuma inta tuno da labarin adiaha sai taji aranta cewa babu yadda zasuyi su watsa ma yarinyar nan kasa a ido musammn ma data sadaukar da komi nata domin Ahmed. Jin cewa kamr bata da alqibla yasaka ta kira sister ta hjy maimunatu, Taci sa'a kuwa dan a aiport take zatazo south africa cikin birnun johannesburg domin tattaunawa da shugaban kasarsu tacan. Nan ta gaya mata abunda ake ciki dan sosai ta rasa bayan wanda zatabi. Bugu daya kuwa hjy maimunatu ta zaɓar ma Ahmed auren Adiaha, ta fito fili ta gaya ma hjy kahdijatu cewa yan uwan mijinta sun anty mojushola sunaso suyi amfani da kafayat din ne dansu mallake gidan ta batare da tasani ba,sann tace mata tunda Allah ya kawo mata babban mafita tayi marmaza kawai tay grabbing din shi, wann din wani oppurtunityne babba, tace mata tabi bayan danta Ahmed kawai akan abunda ya zaba makansa karta sake tay sanya akan ra'ayin kowa cos evryone is selfish about his son. Yau har fada tay mata sosai akan nunawa datakeyi wai tanajin tausayin Kafayat tace mata duk layinsu dayane Zatazo ne ta mallake mata danta bawai dan tazauna da su lpya ba. Dake bata da wani lokci sosai maganan a tsaye sukayishi tace inhar ta kammala meeting dinta a south africa da wuri zatazo nigeria sama sama taga me ake ciki dan bazata taɓa kyalewa ayi ma yar uwanta taron dangi ba. Bayan nan suka kammala wayar. Ajiyar zuciya hajiy khadijatu ta sauke dan kuwa tabbas tasan babu yadda zatayi face tabi shawarar yar uwarta tabi bayan danta akan abunda yake so din. Ta tuna jiya jiyan nan ma saida kazim yay musu irin wnn nasiha akan batun cusawa ahmed ra'ayi na daban. Zancen depression din da akace ya shiga ciki akansu sosai ya dameta dan tasan danta yanasonta sosai dolene yasaka abubuwa aranshi muddin zata juya masa bata. Zama tay tanamai dogon nazari kafin nan ta tashi ta sake yin wanka ta saka wani irin cool royal blue ceibo lace dayaji wani irin aikin stones na alfarma, sosai tay kwalliyarta sama sama mai fidda kwalisa tay kyau ta fetsa turarenta masu qamshi snn ta dawo sashen mijinta ta sameshi yana kan danna wayarsa shikadai Sau biyu ya kalleta sai yaji yakasa dauke idonsa akanta yafara mata murmushi hartazo ta zauna kusa dashi duk ya rude yana kallonta kmr sabon maye sabida hjy khadijatu kyakkwar bafulatana ce fara sol mai yellowish skin colour tana da tsiririn hanci zar kamr pencil, dirinta na zamani nne irin wanda tsufa baiya nunawa sosai ajikinsu din nan. Har saida tay murmushi mai sanyi tare da lumshe ido tanamai kwantowa ajikinshi kafin nan ya dawo hayyacinshi sosai yasaka hannunshi slowly ya rungumota jikinshi sosai yanamai shunshuna qamshin turarenta mai dadi da shiga jiki, har wani lullumshe ido yake alaman dadin qamshin yana bugar dashi sosai. Kaunarta ya dingaji aransa yanamai ratsashi sabida yanason mace irinta yar kwalisa da zata rika waiwayo masa da zamanin kuruciyarsa dan ya dingajin kanshi kamr matashi ba tsoho dan sittin ba. Kisses masu zafi zafi yake sakar mata akan labbanta da goshinta Ahankli har abun ya fara yin nisa sukaje dakinshi atare suka biyama junansu bukata cike da shaukin juna kamr ba atare suka kwana jiyan ba. Bayan kura ya lafa kanta na bisa kan kirjinshi ya rungumota yana shafata kadan suka fara hirar lamarin dansu Ahmed, tunda ta fito fili tace masa itadai inhar Ahmed ya amince itama ta amince dan bata son tayima Ahmed dole a batun rayuwanshi amma zataso idan ya samu nitsuwa yay considering din auren kafayat din itama. Alhaj bello dake cikin shaukin soyayya yace mata shima ya amince, amma inhar Ahmed baida ra'ayin auren mata biyu kwata kwata bazai sake takura mashi akan aure ba..yace mata duk sakacinsu ne ya jawo Ahmed ya tsallakesu da damuwarsa yakai kukan sa wajen yayunsa. Haj khadija tace hakane Sunyi kuskure ahaka amma komi zai gyaru. Daga nan ta rungume mijinta gam gam ajikinta tanamai yaba mashi sosai akan irin hadin kan yayansa da hallacinsu saijin kanshi yake acan sama yana kara huruwa sama sama tsabar dadi. Kamar jiki baisha ruwa ba haka ya sake komawa duniyar soyayya da matarsa dake ita kadaice matarsa daya auro mai karancin shekaru snn yayi tarawar aure da ita a matsayinta na budurwa wanda bata taba saduwa da kowani namiji ba saishi shiyasa haryau yake mugun ji da ita a harkan kwnciyar gadon aure. Saida suka murza junansu akan gadon suka gaji snn suka shirya suka fito cike da shaukin soyayyarsu su mai dadi. 10.30 am suka kira Brother hamzat shikuma yay connecting da brother kazim suka basu go Ahead akan ayi komi daya dace akan batun ahmed din, hjy kahdija ma tace ta amince musu dan tasan hakan datayin ma zai saka dadarta taji dadi sosai ..tsabar alhaj bello ya yadda da yaransa bai wani ja ba da sukace karfe biyu zasu daura auren yace musu suyi komi zai aiko da kudi shima tare da wasu yan uwansu a matsayin magabantan ahmed din daga nan abuja, yace su tabbata bayan an daura auren zasu tura masa file din information familyn Adiaha zai duba izuwa yamma idan an kammala walima zaije ya sanar dasu anty mojushola komi kuma yasan suma bazasuki ba. Komi ya kammala Alhamdullhi aka watse kowa na farinciki aransa. Daga nan iyayen nasu suka shiga bidirin walima tare da family members aka fara hidima na komawa sabuwar gida, hjy khdija da mijinta yau wani sabuwar soyayya suka bude kowa yanata kallonsu yadda suke makale da juna kusan kowani lokaci. Bakaramin haushin hakan su anty mojushola sukeji aransu ba, kafayat is no where to be found, sai can har an kammala kawo duk wasu nau ikan abinci sann ta kirasu awaya tace musu taje wajen mum dinta for an emergency signature akan wasu document na babanta dayabar mata amma zata dawo sharp sharp kafin yamma dan bazatayi missing wann ranar ba. Duk basu saka komi aransu game da kafayat ba nan aka cigaba da hidima anata bidiri ana shashewa sabida kaf yan uwan da abokan arziki sun halacci waliman an cika gidansun bana wasa ba dan har ankon leshuna farare saida akayi mata da maza. A fannin kafayat kuwa tun yau da safe take rikici da mahafiyarta da kuma kawartan da suka kawo mata wani irin maganan banza akan waisuna son ta aure mahaifin Ahmed. Tsabar takaici Kafayat saida tay kamar zata fasa musu kai da kwalba. Yadda ranta ya mugun baci da suka ambace hakan yasaka sukayi saurince mata wasa suke mata amma har acikin ransu dagske sukeyi domin kuwa plan dinsu kenan sun fada ne dansukaga reaction dinta Da kyar kafayat tay hakuri tabar maganan ya wuce dan awajen kamar zaginta akayi da akace ta aure tsoho dan shekaru sitttin da wani abu bayan ga Dan autarsa Ahmed nan dan talatin da biyu maijini ajika. Waima Me zatay da tsoho a duniyan nan? Kai ko brother kaxim ne akace ta aura batajin zata aure shi bare kuma babanshi..sosai maganan ta ƙona mata rai duk dama awasa suka mata shi. Bangaren su Ahmed kuwa shikansa saida yasha mamaki matuka dayaji irin amincewar da iyayensa sukayi afarat daya cikin gaggawa. Wanda aransa yasan cewa badon brother kazim ya hada musu harda siyasa ba da abunnan bazai taba yuwa acikin sauki ba. Lokaci guda suka inviting dayan abokinsu bankole Cos They plan the weding to be secret, shikam bankole akan abun munafurci dama yafi kauri dan ya fara tsanar halin kafayat tun ranar ta taɓa nunamishi cewa batason tarayyarsa da AHMED akan dan yana harka da yan mata. Dukansu atare suka taso tun suna yara amma banji ne kawai yakeson Ahmed da kafayat, banky baison lamarin aransa ko kadan. 11.am ya iso yola ya same su a hotel, suna da ankonsu na kece raini da sukayi dayawa dan haka samun kayan sakawa baizamo musu tashin hnkli ba. Ahmed ne kawai aka kawo masa sabon kaya daga Abuja. Brown Shadda ce mai tsada da mahaifinsa ya aiko dashi tare da mutanen da ya aiko su suzo ayi dauren auren dasu. Basu iso yola basai bayan zuhr prayer,.. Su kusan su bakwai alhaj bello jimada ya turo yolan duk yan uwansane da abokan arziki wanda shekarunsu ya danja sosai. Nan da nan su banji suka taya Ahmed shiryawa, kayan kuwa bakaramin kyau tayi masa ba duk dama baiji aransa kamar aure zaiyi yau ba. Bangaren adiaha ma sosai aka shiryata awani beauty lounge dake babu lokacin dinka mata kayan aure haka sukayi odering bridal ready made lace flowing gown mai kyau dark green and gold in colour Da duk wani abu na kwalliyar Amarya. Da kayar da accessories dinta duk saida suka cinye duba dari da sittin dake set biyu ne aka siyo mata harda mayafai da jewries masu kyau da kayan kwalliya. Kafin 2pm na rana yayi Adiaha was already looking breathlesslessly beautiful irin kyan da bata tabayiwa kanta ba Koda kakarta da sauran mutanen da suka danzo suka soma yaba kyaun datayi sai kuma taji kuka da damuwa mai tsanani yana gumeta taciki. She become sooo emotional and weak tayaya ne ma har zatay aure babu iyayenta aganganta? she tried to call them ta waya amma taji layinsu kaf baya shiga harda na yar uwarta ekaete. Duk sonta da daurewa bata iyayi ba saida tay kukan jin tsananin kewar familynta ayau din sosai. She wish and wish suna nan sukagan irin kyan datayi aranar aurenta. Da kyar aka kwantar mata da hankli da aka nuna mata hoton a Ahmed awajeb daurin aure taga yadda yay kyau shima tare da friends dinsa hakan yasaka taji sanyi ranta kadan. 2 .30pm na ranar asabar din aka taru a masallacin kofar gidan Alhaj aliyu mutanen Ahmed suka bazama wajen cikin shigarsu ta kece raini da motocinsu masu daukar numfashi. Batare da wani bata lokaci ba akayi duk wata abunda ya dace snn aka daura auren "Ahmed damilare bello jimada, da matarsa miss Reema bassey. Bayan ankamala komi cikin mutuntawa akayi pictures Dr banky dayaga Adiaha ta fito saiyaji jininsa ya hadu da ita sosai, haka ya dinga yabonta yana cewa ahmed tafi kafayat tsari da hankli nesa ba kusa ba. In no time suka dawo tamkar abokanta suna sakata jin dadi aranta sosai musmm ma banji dayasan komi akanta sosai, Adiaha tana bashi tausayi inya tuna cewa Ahmed only married her out of pity and no way out compulsion badon soyayya ba. Ciwo kan kafayat ya dingayi mai tsanani da kyar ta shirya kanta tsaf taci ado da yamma ta kamo hanyar dawowa Abuja domin tazo a karashe hidiman da ita snn ta zubawa su anty mojushola final drop na maganin acikin abinci suma ta gama da su. Ciwon kan data dingaji yasaka bata iso Abuja ba sai wajajen karfe shida na yamma saura tazo ta samu angama taro anata daukar hotuna. Kawai sai ta shiga rubibi akay hotunan tare da ita Ta zuba drink da magani ta kawo masu anty mojushola ta basu suka sha tasaka su a gaba tana basu labarin tafiyarta na karya. Ta lura kamr hanklinsu baiya jikinsu dan sama sama suke bata kulawa duk idonsu na waje guda musmmn ma da sukaga kamr alhaj bello da haj khadijatu sun hada kansu yau da alama suna boye musu wani abu. Harsaida aka daura auren Ahmed kafin nan brother hamzat ya hadasu dashi a video call yay magana da iyayensa suka saka masa albarka sosai. Alhaj aliyu daya kasance kamar shine waliyyin auren ta ln shima saida aka hadasu sukayi magana da alhj bello jimada da hjya khadijatu aka dan gaggaisa. saida ya dawo cikin gidansa snn yadan fayyace ma hjy hajara yanayin iyayen Ahmed din sai asann tafara jin sanyi sanyi a zcyarta. Da yamma lis akazo daukar adiaha dan karfe biyar da rabi jirginsu zai tashi izuwa abuja in less than 40 minutes zasu iso Abuja inda za'a kawota family house ta zauna awajensu anty moju shola. Shiyasa yau din suka daga batun komawa cikin sabon gidan nasu duk dama anyi waliman an kammala Saukin abun shine brother kazim da brother hamzat duk sun gayawa matayensu dawuri akansu shirya tarban amaryan Ahmed, tare da warning dinsu akan cewa karsu gayawa kowa news din auren sai sun iso da amaryan Abuja. Anata hidiman waliman nan suna nasu shirin suma agefe duk dama gulman abun na ciccinsu agindinsu musmmn ma anty nuratu. Duk sunsan masu anty mojushola ake boyewa komi dan ba'ason atada rikici acikin mutane mutuncin familynsu yaje ya zuba. Suna son suyi gulman amma suna mugun jin shakka da tsoron mazajensu Wajajen karfe biyar na yamma aka kammala shirya Adiaha da wani brown bridal gown na atampa wanda shima siyenshi a dinken sukayi aka rufa mata hadadden mayafi mai kyau akanta golden colour kalar jakarta da hadadden takalminta, duk ta rude ta makale sosai ajikin hajy hajara tanata kuka ayayinda take kan mata nasiha tanamai dada ja mata kunne akan zaman aure. lokacin har Ahmed ya sauya kayansa na auren izuwa wata simple yadi fari kal dashi yolo yolo datay masa kyau sosai amma baiko saka hula ba acewarsa kayan auren sunmasa nauyi ajiki. Biyar na cikawa sukazo gidan domin su dauketa nan ne hjy hajara ta kira Ahmed gefe ta masa nasiha tare da bashi amanan Adiaha harta so ta bashi tausayi duk dama ya lura kamr batason auren aranta itama. 5.30 aka kammala musu nasiha atare snn aka rako adiaha cikin mota tanata kuka Ahmed baice mata uffan ba har suka kai airpot abokansa ne kawai suketa lallashinta hartayi shiru. Koda suka iso Abuja ana kkrin shiga magrib agidan banji suka sauka tare da ita, after sallahn isha'i ne suka dauko hanya daga ita sai Ahmed din a mota har suka iso family house dinsun kamar yadda iyayensa suka umarcesa. Tun ahanya yafara fayyace mata cewa wasu daga cikin manya a familynsa basusan da zancen auren ba so she wll have to bear with their first shock and unruly coments. Akaci sa'a kuwa Lokacin kafayat bata gidan har ta sabule ta wuce gidansu sabida haryanzu maganan brother kazim yana taba mata zuciya sai taji batajin sha'awar kwana agidan kuma. Karfe 8 na dare daidai Ahmed suka iso kofar gidan aka bude musu gate suka shigo ciki saida ya kashe motarsa snn ya samu nitsuwa ya fara mata bayanin yadda zatay gaisuwa da sauransu. Duk sai taji ta rude ganin komi ya mata na daban da yadda ta saba gani arayuwarta. Tun tana cikin motar take karewa gidan kallo ganin gidan babbane ba laifi. Ahmed yace mata ta zauna acikin motarsan tukuna shi zai je ciki ya dawo kafin azo a dauketa saisu shiga ciki atare. Har ya bar wajen kallonsa takeyi tsabar yadda kirjinta yake bugawa da sauri da sauri. Daga ta cikin gidan kuwa Babu wani mahalukin da ba'a kirashi a falon yau ba. Duk wani mai amsa sunan jimada ya hallara su anty moju kansu ya bala'in daurewa tunda sukaga an kirawo meeting din gaggawa nabazata. Yaransu ne kawai basa wajen amma tunda ga kan brother hamzat da aunty nurat, aunty adizat da any zainab da su manyan gidan kowa ya halacci taron, sai brother kazim daya kira a video call dan ayi komi dashi. Tun kafin zuwan su Ahmed gidan anty mojushola ta matsa sai dai agaya mata dalilin taron nan dan ta matsu taji meyene, nan alhaj bello jimada ya nitsu bai boye mata komi ba ya fara musu da bayanin yadda aka ciki da batun Adiaha snn yace musu dansa Ahmed ne suka yiwa aure yaudin zasuyi introducing matarsa wa duka family. Anty moju tay ihu tace karya suke yi batasan da wann zancen ba, tun tunin nan wa ita kawai akeyiwa bayani amma shock din data shiga ciki najin cewa har anma Ahmed aure yasaka ta dawo musu tamkar wacce bata fahimtar mesuke cewa harsanda akace ga Ahmed din ya iso da matar da ya aura. Kowa awajen jikinshi yay sanyi dasukaji ance ga labarin Adiaha amma banda su anty moju Babban damuwarsu shine da ba'anemi shawarsu tun farko ba akayi komi da hjy khadijatu. Gani suke an raina musu wayo snn dan uwansu ya kaskantar dasu sosai, ya dora matarsa a sama da matsayin dayake basu na respect aransa. Brother hamzat yace ma su aunty nurat akan da suje waje ita da anty adizat su shigo ciki da Adiahan kowa ma ya ganta, caraf anty ramatou ta tashi tabi bayansu cos she just cant wait for this bomb blast gani take kamar karya ake musu. Lkcin Ahmed yana sauri dan ya shigo ciki sai gasunan suna fitowa suma, a kofa suka hadu ya tsaya cak dan gani yay kowa na kallonsa kamar basu taba ganinsa a rayuwarsu ba, ko ajikinsa ya tsime snn ya wuce ciki dan ko gaishe su baiyi ba ya haɗe ransa sosai. Anty ramatou ce ta tsaya dagata kofa bata karasa can din ba ta zuba ido tanata kallonsu, kirjin Adiaha bakaramin bugawa yakeyi ba musammn dataga manyan mata subiyu sun doso ta inda take, da wuri ta ja mayafi ta rufe fuskanta da mayafin mai gabaki daya. Anty nurat ce ta bude kofar motar tsabar gulma saida ta yaye fuskan adiahar duka suka kunna hasken bulb din motar suka mata kallon tsaf tsaf dasukaga bata da aufi nan suka buga wata shewa tareda rangwada mata guda a kunne. _Iyawo wa_ "Ure welcome our bride" Lokcin Kirjin Adiaha

Chapter 18 of 19