Share this page
akwai matsala,nan da nan zube kasa tafara musu kuka sosai tana yarfa hannu gwanin ban tausayi. kirjinta dake mata zafi ta dafe tana cewa noo noo noo this cannot happen to me, yau fa rana ne, im suppose to be engaged, tanata kuka Kowa nata jin tausayinta.. Daga waje kuwa dukansu sun kasa yanke hukuncin shigowa ciki sai musu akeyi akan Ahmed tsakanin anty ramotu da hajya khadija,ita dai tasan danta baijin magana amma aynzu so take tasan ko yana lpya dan hanklinta bai kwanta da fitar da yay acikin gaggawa kamar yadda mai gadi ya fada ba. Kafayat na ciki tana mai tsananta kukan datakeyi duk ta birkito kasa ana rirriketa, jin karar horn din mota a bakin gate tin daga waje yasaka ta birkita ta miƙe tsaye tanamai cewa "is that Ahmed?..dat must be Ahmed..bari naje na duba shi..tin kafin su anty nurat su rikota a guje tayo wufff tayo waje da tunanin Ahmed zata gani nn su anty moju duk suka biyota abaya. Tana isowa farfajiyan gida ta samu kowa hanklinsa ya koma ga bakin gate dan kaf tunani dayane ke yawo a mind dinsu kowa na fama da fargaba da bugun zuciya. Mai gadi yaja gate tun bai gama budewa ba hajya fatihat adetunji ta waina babban jeep dinta na prado tayo cikin gidan a mugun zafafe kafin kace kobo harta kashe motar agabansu. Evrything happen so sudenly dan A karkace ma tay parking motar tata tsabar dirin masifa ta sauko daga cikin jeep din babu ko talkami a kafarta a mugun masife ta taho tanamai cewa "kiloshele gon gon? Kini? What is happening here kafayat...? Wani Turus kafayat din ta tsaya cak batako motsi a tsakiyar su hajiya khadija dan tun dataga motar mahaiyarta ne ya shigo gidan bana Ahmed ba sai tafarajin kanta na juyawa sosai tafarajin jiri jiri.. "Are u ppl daft? Nace menene ya faru? Why is my doter in tears.. Anty ramotou da su anty mojushola sukai shiru kowa ya tsime yana kyabe bakinsa cikin rashin sanin abun cewa Babu zato Ta wani finciko kafayat din tajawo ta tsakiyarsu snn ta matse mata hannunta sosai tanamai dubanta da fuskan rashin imani da tausayi,girarta na sama a dage tace" meye faru? Why are u in tears, _kini aṣiṣe? Kafayat kilode ti o fi wa ni omije?._ .answer me. What is it... Kuka mai tsuma ne ya kufcewa kafayat din tausayi yasaka hajya khadija karasowa wajenta tana isowa ta kwaco hannun kafayat din ana mahaifyarta tadan jawota jikinta sigar lallami snn ta rungumeta akafadunta ayayinda take kukan sosai. Wani irin shewar baqar kishi dana kashe aure hjya fatihat tayi snn tace " i dont understand oo..inata magana anmin shiru.. Ahmed ya mutu ne? Is damilare dead..dat boy shud better be dead so that my doter will not be crying like this .... A mugun tsawace Anty ramoutou tace Ah, ah, how dare u fatihat... _oya werey?back to sender u evil woman.._ Hjya fatihat tabita da muguwar harara Rai abace Anty moju tace..thunder fire dat your evil maught...idiot woman, shegiyar mata marar respect. Ido bushe hjy fatihat ta hararesu snn tace And who shud i respect here?ehhhh..kufadamin? Meya same yata take kuka shine kawai damuwa na ko acikinku babu isashen da zai iya min bayani ne. Anty adizat ta harzuka harzata cakka mata baqar magana Cikin katseta Hajya khadija tace pls relax, ayi abu cikin hankli, hjy fatihat Duk da kika ganmu anan hanklimmu atashe yake cikin sanyin murya sosai tace "My son is missing" muma nemansa mukeyi bamu gansa ba, munxo tare dashi har nan amma kuma har yanzu bamu san inda yake ba. Hjya fatihat taja tsaki adan kunyace alaman bataso jin haka ba dan a tunaninta Ahmed din ya walakanta mata yarta ne ko har ya furta cewa bazai aureta agaban familynsa ba.. Ta tura bakinta gaba tana kikkifta ido ahankli snn tace ohhhh,mtsss, ashe ma bacewa yay?arggh, Toh Shikenan kuma dan Dami ya bata sai akace ataru ayita kuka akansa kamar ana gidan mutuwa ..in mutuwan yay kuma yaya kenan.. Sosai ransu anty ramoutou yake harzuka da maganganun matar amma basuce mata komi ba sabida basa son su tada wani magana since hajy khadija tay kkrin sassaita maganan cikin hikima ta hanyar cewa bata Ahmed yay.. atleast sunsan ko itama kafayat din zataji dama dama aranta akan da ace guduwa yay. A zafafe kafayat din ta dago kai tana kuka sosai ranta abace tace mum why now? Wai Meyasa kike kiran kalman mutuwa ne wa damilare and in front of his family too pls how is dis fair. A masife cikin katseta tace "nothing is fair here musamn ma dakika maida kanki jaka marar kwakwala agaban wayn mutanen, Ni banma yadda dacewa bacewa dansu yay ba, arent u planning a suprise engagemnt for him? Toh Wayasan ma guduwa yay yabarki munafukan dake zagaye dake kuma sukace miki batawa yayi. Cike da dakatarwa kafayat tace Mum pls, karki sake cewa familyna munafukai saidan kece babban munafuka if not a ina kikaji zancen engagemnt dina da damilare? Furucin sosai yaci ma hjy fatihat rai amma ta tsime tace "oh mamaki ma kike sha ? Toh Ai maganan duniya bata boyuwa.. hmmm okay ohhh, to barikiji The same way i heard it kidauka aranka cewa haka nan ma Damilare zaiji zancen cewa zakimasa surprise engagement and dats why he will run away and leave u.. Cikin karayar zuciya da kufcewar kuka kafayat tace mum ya isa haka Ance miki bata yayi..we wll find him am sure Hajy khadija ta katse su da sauri tanamai cewa yes. Zamu nemoshi and Pls hajya fatihat leave evrything to us..zamu nemosa snn za'ayi engagement din nan ayau..in ma bamu same shi yau ba duk inda yaje ya dawo nayi alkwari he wll engage kafayat agabana. Hjiya fatihata ta bushe da dariya snn tace "Iya dami? Ki tabbata geskiya kike fada min ooo cos if not..,if not...wallh, tallahi, kinji na rantse miki da Allah kece zaki fi kowa shiga uku awajena.. i wll make ur life soo terible and miserable the same way ur son is taking advantage of my doter. Hajiya khadija batace mata komi ba tajanye hannun kafayat suka koma cikin gidan aka barta da su anty ramoutou suna cecekuce kamar zasu tada gidan haka suka kaure da masifa.. Da sauran dirin masifan suka dawo cikin gidan dukansu bayan tafiyar hajya fatihat, nan suka samu lokacin har hjya khadijat tay nasara wajen rarrashin xcyar kafayat da kalamai masu dadi da kwantar da hankali akan da cewa zasu hadakai ne sunemo Ahmed duk inda yake a afadin garin Abuja. Anty mojushola da tsananin fushi ya rufe mata ido tana shigowa tahau dakawa hjya khdijatu tsawa tanamai dora mata laifin komi . Kowa cewa yake laifinta ne da Ahmed ya zamo marar tarbiya wanda baijin maganan manya Anty moju Sai diri take tana kumfar baki anty ramoutou na rirrikota at same time tana mai tayata. Surutu suke ma hjy khadijatu a masife suna hargagi tamkar zasu bugeta .. Sai cewa suke ajininta na hausawa Ahmed ya debo rashin sanin darajar mace shiyasa ya iya walakanta matar da zai aura tun yanzu.. Sosai Kafayat ta rude a tsakaninsu duk sai tarasa maganan waye zata ji guda daya. Su anty temi sunce da gangan Ahmed ya gudu bayan hjya khadija tace mata bacewa Ahmed yay Anty ramoutu Tace iya dami kece xaki biya yarinyar nan kudinta data kashe, dan kece kika lalata yaronki ya zama wawa, Uve encourage your son to be soo irresponsible duk da kokrin da mukeyi akansa. Anty moju ta dafe kirjinta tana sumbatu cikin jin takaici da yarensu tana cewa _gbogbo rẹ ni nitori ọmọ rẹ pe obinrin yii ṣe ẹlẹya idile mi?_(duk akan danki ne akazo har gidana aka cimin mutunci?) _Ọlọrun mi yoo ṣe idajọ rẹ_ (Allah ya isa..Allah zaimin sakayya *anyone) Tun Bata kammala rufe bakinta sai wayar hjya khadijatun yay kara da alaman shigowar wata sako.. Anty moju ta dube hjya khadija snn tace mata" _tani iyẹn? Ṣe o jẹ ọmọ aṣiwere rẹ?_ kallonta kawai hjy khadija tayi, Sai can da ta tuna cewa bata jin yaren su snn tace "i said, Who is that? Is it your foolish son..) Hajy khadijatu bata kulasu ba tsabar ranta ya baci sosai, tana dubawa kuwa taga sunan Ahmd saidai sakon nasa ta voicemail ne ya aiko, hamdala tay cikin ranta snn tace musu Its my son Ahmed, tana fadin hakan kowa ya miƙe tsaye, sauri take tana kkrin ta bude sakon taji meyene aciki nan taji an fauce wayar a hannunta tana daga ido taga wayar a hannun anty ramoutou tana mai kkrin budewa cikin sauri, galala da baki tay tana kallonsu. Hannun Anty ramoutun har rawa yakeyi tanamai cewa "Bazamu yarda ki cigaba da yaudarar yar mutane ba, in ma hada baki kukayi da danki ai zan playing sakon kowa yajishi a fili.. Lokaci guda falon ya dau shiru kowa ya kasa kunne can saiga muryan Ahmed ya soma fitowa cikin nitsuwa. Yace mammy Dan Allah kiyi hakuri kiyafeni, i wanted to tell u dat im out of town, zan danyi kwana biu awani waje. im really sory maaa, i just cant wait, sabida inda zanjen ne yanada mtkr muhimmanci agareni, And pls tell the rest of the family that im sorry, idan na dawo zanzo in kawo musu wanda zan aura din..am really sorry for dissapoiting evryone. Anty moju ta saka ihu tanamai cewa Haaaaaaa so Damilare has dis bold guts? har nine zan kirashi gidana snn ya shareni yay tafyarsa wani waje? I swear to oludumare am going to deal with dami, ahhhhh..zan nuna masa cewa na riga ubansa bello zuwa duniyan nan.. how useless can he be, imagine the audacity!!!!! Da karfin huci ta furta maganan Out of strong frustration and anger dan ta tsani raini sosai anty ramoutu ne agabanta tanakan bata hakuri Hajy khadija batace musu uffan ba ta amshe wayarta a hannun anty ramotun ta kara sauraran sakon ,jiki a ragwabe kafayat ta koma kasa a sulale tay zaman turus hawaye na sauka zurrrrr daga cikin idanunta. Magangnun mahaifyarta sune suka shiga mata yawo a kwakwalarta musammn ma datake ce mata itace kadai ce take acting desperate akan batun auren ta da ahmd, itace kadai take son shi dayawa, itace kadai take wahalar, snn shi baisan darajarta ba. Masifar da su anty sukeyi yasaka kafayat ta kara shigewa cikin rudani musmmn ganin yadda suka taru sukama Hjy khadijatu chaaaa akai sai duk ta dauka ko dagaske ne kawai dama deceiving dinta hajya khadijatun take sonyi shiyasa take son ta rudeta ta rufawa danta asiri akan laifin dayay. But she just cant forgive Ahmed soo easily a wann karon, taya ma zai gudu ranar engmnt dinsu witout consiidering her feelings, why? Tana cikin zantar da hakan aranta ta fashe da wani irin kuka mai kara. Atare duka suka taru sunata rarrashinta. After a while kura ya lafa saidai kowa yanayinsa babu dadi dan kowa sai dirin masifa yakeyi ata cikin zuciyarsa sun zauna kowa ya daure fuskarsa yana diri. Hajya khadija ce kawai tare da kafayat a daki ta kwanta akan cinyarta tanata mata kuka sosai. Babu kalar hakuri da lallamin da hajya khadijatu batay wa kafayat ba amma haryanzu zafin abun da rudanin sata shiga bai dena damunta aranta ba. Daga yanayin tambayoyin da kafayat take mata acikin kuka yasa jikin hjya khadija ya soma bata cewa kafayat is already doubting her akan behvrs din Ahmed. Tausayin yarinyar ya dameta duk sai Ta rasa yadda zatay ta fahimtar da kafayat din cewa ita bata san komi gameda tafiyarsan nan ba. Tasan kuma inta kyaleta anan gidan su anty ramoutou zasu iya kara hura mata wutar shakku da rudani acikin zucyarta game dasu dan haka ta umarce kafayat din akan cewa ta shirya kayanta suje gidanta su jira dawowar Ahmed din acan atare. Dake ita ta raine su tasan duk wani luggansu acikin sauki ta shawo kan kafayat din ta hanya nuna mata cewa tana tare da ita yau sosai. Immidiety bayan sallahn zuhr suka bar gidan, ko wani sallaman kirki su anty moju basuyi mata ba dan ko kadan basuji dadin tafiya da kafayat gidanta da tay ba. Koda suka isa gidan ma lallaminta ta dingayi tana mai shagwabata tamkar itace ta tsuguna ta haifeta, ganin kafayat din ta damu sosai yasa tay mata alkwarin cewa muddin Ahmed ya dawo zata sakashi ya bata hakuri with an engagement ring kmr yadda take so din. Sosai kuwa duk wata lugga da salon rarrashin hjya khadijatu yy tasiri acikin zucyar kafayat dan dama can bata taɓa furta mata hakan ba, she is sumhow realived dataji yau hajy khadijatu da bakinta tace zata tursasashi ya aureta inya dawo dan bata taba furta mata hakan ba sai yau. Rarrashi da kalaman hjya kahdijatu shine ya dawo da kafayat daidai tadan sake jikinta kadan.. ****** *10.30 am* _margaret ekpo intnl Airpot calabar, cross rivers state nigeria._ A daidai wann lokacin jirginsu Ahmed ya kammala sauƙesu yana isowa arrivals already uber driver dinsa na nan jiransa agaban space na parking with a broad and warm welcoming smiles. Gaishe sa yay baima amsa shi ba. madaidaicin troley dinsa drivern ya amsa ya saka masa a booth sann ya taho a guje ya bude masa murfin motar agidan baya ya zauna after some few min drive suka iso transcorps hotels dan shine convenient location din dake kurkusa da aiport din. Tun akan hanyar yaketa nazari a brain dinsa na yadda zai bullowa dan uwansa brother hamzat dimeji da wann maganan cos he really need his support fiyeda da yadda ake tunani. Tunani yay Kodai ya aiki Banji ne tunda su suna abuja ynxu akanda yaje ya samesa ya masa bayanin komi kafin lkcin shi ya samu nitsuwa saisu tattauna? that seems like a prety good idea dan Yasan abokinsa banji duk ya fisu nitsuwa da iya magana cikin girmamawa da manya. A hadadden suit din daya kama daki mai lamba 105 ya zauna ya soma hutawa kadan snn ya jawo system dinsa ya fara duba abubuwan dake gabansa dan karya manta da wasu. Already shida abokinsa banji sunyi kyakkwan bincike game da festivals din da za'a gudanar a garin wanda anan ne yake saka ran zaigana da fuskar yarinyar dayazo nema, a cikin nitsuwa yake scrolling files dinsa da cursor har ya iso kan wani file da aka rubuta _leboku_ Wato festivals. Acikin wann document din ne aka turo masa dukkan wani bayani hade da locations na wajajen da zaije domin cimma abunda ya kawosa garin cikin sauki. Bude files din yay ya soma karantawa daga farko dan yay refeshing memorynsa. _Leboku_ kalma ne dake nufin festival da yare, awajen mutanen wann gari na calabar babban festival dinsu bai wuce annual new yam festivals da suka shafi shekaru aru aru sunayi ba, shi new yam festival din ansamo shine daga mutanen yankin _yakaa_ masu speaking yaren su na _yakuur_, ana taruwar gangamin celebrating wann gagarumin festival din ne a south south ko east region na cross rivers state, inda ya haɗa da dukan Comunities da yarukan dake karkashin mutanen _yakaa_ wato yankunan ugep, idomi, ekori,mkpani and nko. sai kuma international celebration na new yam festival dake ayinsa ne sau daya a shekara acikin yankin ugep inda kasashen duniya daban daban suke tahowa domin halattar wann gagarumin festiva kamr irinsu jamaica, lebenon, sierreleone da kuma yan cameron. Shiyasa ake ambatar festival din a matsayin the biggest african street party . Musmn ma da garin calabar ya riga ya shahara da cinikayya na siye da siyarwan kaya tsakanin yan kasa da yan kasashen waje, duk wata harkan comercials activites dinsu ya bunkasa ne tun acan zamanin slave trade a 18th century. Cross river calabar wajene daya tara rabe raben harshuna kamr irin Yaren dayafi yin karfi awajen wato yaren EFIK duk dama anfi regarding din region din as an IGBO LAND. Sakamakon transition din da aka samu na cigaba a duniya yasaka duk wani harkan kasuwancin dake yankin cross river suka bar zancen saida bayi suka dawo siyarda manja, da sauran ma'adanai kamr su ivory, red wood, rubber, barwood. Cinikayyar su tafi karfine da mutanem portugal, da kuma french,dutch da america. Yaren Efik ya kashune izuwa "seven sister clans" most of them suna tsakanin cross river ne da akwa ibom. Yanki ne da gabaki dayanta take zama a karkashin _ibibio tribe_ Sabida ibibio tribe din dadaddiyar yare ce datake in existance tun kafin a samo kasa me suna nigeria, ibibio land is known as the mother eastern region of nigeria as a whole. Shine yankin da ya hada zuriarsa da yakunan mutanen Efik( sune northen ibibios) annang(sune westen ibibios), oron niger in niger delta state, eket(sune southen ibibioa), sai kuma ogoja disrict inda yawancin babban kasuwar su ta festival yake, Wanda ahalin ayanzu duka wayann yarukan sune aka fi saninsu da yankin _Biafra_ (bight of biafra) East, and South eastern nigeria. During civil war ne aka raba sashunan suka dawo su uku ,wato south east,(cross river,calabar) south west(akwa ibom izuwa yankin boarder nigeria da cameron) sai northwest (adamawa, da taraba) some are in delta states some in abia, umahia and equtorial guinea. Mutanen dake wayann yankunan sunfi ta allaka ne akan addinin su ta gargajiya gadon kaka da kakanni wato addinin nan bautar spirits din magabatansu. Shiyasa yankin easten nigeria gabaki dayansu suna under two dimensions ne wato suna kiran spirit din magabatansu da Allolin su ta hanyar" offering din "secrifices,consultations na bokaye, chief priest incantations, worships of sprits, communicating with the death,da yin muamala da mutattu, Sunada shahararrun Alloli kamar irinsu _God of nature_ (Wann din shine Allahn yanayi) wanda idan yace kai mai arzikine toh ta zauna akanka kenan, hakama idan yace kai din matsiyaci ne tsiya tazauna akanka kenan bamai iya zanca maka yanayinka._sai God of destiny_ Wann Allahn nasu shikuma shine wanda idan wani abu mummuna na kaddara ya afku akan mutum akanje ne a rokesa akan yay reversing din abun ko kuma ya canza shi mai gabaki daya, misali" kamr idan mutum mai kudi ko mai ilmi ya mutu accidently, toh familyn mamacin zasu iya consulting diviners na Allolinsu sai agaya musu abinda yasaka dan uwansu ya mutu,snn abasu sharudan da zasu bi suyi reversing destiny dinsa dan ya dawo rayayye, wann Allah nasu shine yake basu, snn inhar sukabi sharudansa strickly to tabbas komi zai kasance musu daidai. Akwai wasu ire iren su kamar God of heaven, god of earth snn kowa da aikinsa Sann akowani division na yarukan akwai sacred lands(akai) wato forest, _akai_ shine baqqar jejin da suke aikata duk wani tsafe tsafensu, ana kiran wajen _Akai_ ne sabida babu wani halittar da aka halatta masa yin noma ko yin gini ko kasuwanci aciki ajejin gabaki dayanta. Wajene da ake binne gawawwaki, ake gina manyan shrines, da kuma hazikan secret societies masu tuamali da manyan Allolinsu, da cult grps kamr irinsu Akpo onyoho, ekpe, idiong, ekoong and obon da sauransu sune acikin jejin saboda they are consider as sacred. Inhar kai baka kasance member na wani cult acikin wayn ba toh shiga cikin jejin ya haramce ka kenan har abada hakama bazaka dauki koda itace ko tsinke daga jejin ba, bare ajega deban ganye ko hunting animals, koko kace kaje debo dodon kodi ko kuma itacen girki. All these things are highly prohibted in the sacared land or forest. Snn dukan yankunan sunada wani al'ada da ake cewa _"the soul and life after death_ Duka yankunan earsten nigeria suna kasa rabe raben soul din mu a gidaje guda hudune ..acewarsu soul dinmu na farkon shine "gangar jiki"wato (etherel body) Na biyun kuma shine asalin "ruhi"(soul) na ukun shine fatalwa (spirit)na hudun shine suke cewa (over-soul). Acewarsu shi Over-soul din ba ajikin dan adam yake ba dan ahade yake da spirit din jikinsu..they believe that over soul shine gangan jikin dan adam dayake zama acan duniyar mutattu. A cikin wann sashen ne ake gane masu animal soul, water soul, ko shadow. Misali akwai souls din su dayake rayuwa a matsayin maciji, ko kura ko zaki ko duji ko tsuntsu ko wani wild animal ko forest beast. saidai most time akan iya shiryawa mutum mugunta idan aka gano inda nashi over soul foarm din yake, misali in nashi soul din na water body ne, wani zai iya striking din ruwan daga inda yake sai kuma mutumun ya mutu a dik inda yake, hakama idan inuwa ne evil spirit zasuyi saurin kamawa su daureshi, in dabbane za'a iya harbesa da kifiya ko bindiga ya mutu. Snn sun yarda da cewa idan mutum ya mutu a duniyan nan rayuwarsa ta duniyan shine zaije yay acan lahira. Misali, idan ka mutu a matsayin manomi anasu tunanin a sama ma matsayin manomin zaka taso, hakama idan kamutu a mai arziki da arzikinka zaka tashi, snn inka mutu mashayin giya hakanam zaka tashi dashi kacigaba da rayuwarka bayan mutuwa. Shiyasa kafin nan akaika kabari sai an maka guzirin abubuwan amfani kamr su abinci tukunya, kayan sawa da abubuwan bukata dan a tunanin su ko daga wani irin yanki ka fito daga zarar ka mutu a cikin zuriarka ta duniya zaka tashi. AHMED saida yaja wata iriyar doguwar numfashi mai tsayi bayan ya kammala karance brief files na tarihin al'adan su na da can da yadda suke muamalarsu da mutane a al'adance yanzu har izuwa yadda suke yin al'adun su na aure da biyan sadakinsu. Kafin nan ya kammala nazari akan komi har lokacin azhr ya tunkaro dan haka ya sauƙa daga kan gadon ya rage kayan jikinshi ya faɗa toilet yay wanka yay alwala snn ya taho yay sallah, bai iya shirin gaggawa ba dan haka ya fasa fita batare da yaci abinci ba. Oder abincin kawai yay ta telephone din dake room din aka kawo masa hadadden rice and lamp stew with couslow ya zauna ya ci sosai ya koshi snn ya soma yin shirin zuwa filin da za'aci taron,nan ya bude trolly dinsa ya fidda wata hadaddiyar casual wear mai fitinannen kyau snn ya shiga shirya kansa acikin nitsuwa... #surayyahms 08060712446 chats only [5/28, 9:20 AM] SURAYYAHMS: *KISHIYAR ƘABILAH..8* BY SURAYYAHMS. CALABAR INT'L TRADE FAIR (C.I.T.F). Wajajen karfe 2:00 na rana Ahmed ya kammala shirinsa izuwan wajen taron, yau yasaka wata hadaddiyar golden colour raymond shirt ne akan wata dark brown pants da cooperate duster coat mai open breast wanda kallo daya kamasa akaro na farko zakace shidin wani kazamin dan mai kudi ne dan gatan hajiya dan bakaramin kyau yay ba, kan nan tashi tasha gyara kamar a sace shi, duk inda ya ratsa sai an juya an kalleshi sabida banbancin yanayinsa da mutanen wajen gawata mayyar qamshin turaren regenedes dake bibiyar duk wata salon tafiya da kuma motsawar jikinshi mai tafiyarwa. Kwanaki 32 ake deba na musmamn domin yin shahararren festival din wanda aynzu haka baifi saura kwanaki sha hudu a kammala festival din gabaki daya ba.. Shi damacan ba wai damuwarsa bane yazo yaga wasannin al'adansu yazone dan ya same abun daya kawo shi a garin. Dan zaman da yay a garin during disease reaseach dinsa yasaka yadan sassan wajaje da dan dama acikin gari shiyasa ma bai damu da neman location din hidiman awajen kowa ba. Kai tsaye ya wuce wajen sanin cewa yana da valid i.d card dinsa ajikinshi wanda yasan duk inda yaje ya nuna zai zamu masa free pass tunda shaida ne nasanin cewa shima babban likitane. Daga cikin hidimomin da suka rage baifi hidima hudu zuwa biyar bane akarkare dan duk sauran shirmen festivals dinsu sunyishi ne a baya tun kafin ya iso. Wanda suka ragen sune Hiv/aids walk and conference, sai canirval queen peagent (beauty contex), sai musical displays da ekpo session wanda shine akeyinshi karshe wanda ake yinshi tare da bokaye da dodonni. Yaune za'ayi business and street walk tun daga hall din tinapa business resort, dats bayan an kammala yin taron da zasuyishi na HIV/AIDS conference sun danyi walk to honour the occasion,a daren yau dinne kuma za'ayi beauty contest at the same hall na hotel din for calabar carnival queen peagent. Tun karfe 12.00 na rana aka fara taronsu na hiv/Aids conference inda likitocin turawa da kuma manyan masana kiwon lpya da wasu daga cikin ministers na kasa da sauran masu hannu da shuni aka taru aka tattauna akan wann cuta. Ahmed bai wani jima acikin hall din ba aka kammala taron kowa ya fito waje domin yin street walk din, yana fitowa ya fara haduwa da mutanen da yadan sassani just few mutanen da suka sanshi sosai awajen sukayi recongnising dinsa suka tsaya suka dan gaggaisa dashi duk basu

Chapter 7 of 19