hannun yaro, amincin ta da Sajida ya Kara karfi tamkar uwa daya uba daya suke, Dan lokacin da sukaje hutu sajidar har Azare taje ta gaishe da Ammah ta karbowa Zahra sako.
Duk lokacin da za'a yaye dalibai makarantar tana hada gagarimin taro tana baiwa best student na kowane department award.
A karshe semester din ne aka hada taron Wanda ya Tara al'umma daban daban daga kasashen duniya masu Taya 'ya'yan su da 'yan uwa murnar gama karatu, celebration ne ake na gasken gaske, su zahra dai suna kallon abubuwan tunda wannan shine na farko da akayi suna Nan lokacin da akazo bada award ne ba zato ba tsammani aka Kira zahra Muhammad sani daga Nigeria aka Bata award na overall a department dinsu akan kowane subject.
Wayyo murna gurinsu ba'a magana Dan Zahra kuwa har mukan Dadi tayi data duba taga yawan daliban da suke a department din nasu Amma ace ita ta karbi best ai abin murna ne Kam. Sun Sha hotuna da mutanen mu na africa more especially 'yan Nigeria.
A ranar Zahra tayi takaicin karatun nesa da ace a gida ne da Abbanta ko Ammah ko wani daga cikin yayinta zata danqawa kyautar su sharing happiness din tare Amma Nan kuwa fa sai da friends da wasu tsirarun mutane Wanda ma ba saninsu tayi ba sukayi farin cikin, ga Uncle Haisam ma a matarsa da yaran duka sun tafi turkey.
Sai ta waya sukayi murnarsu da jama'ar gida ta tura musu hoton award din ta waya hotunan da suka dauka.
-----------------
AZAREN KATAGUM
Alhaji Jafar ne da Malam Bukar sai Habibu dan kanwar malam Bukar dake aure a suleja malam din yake rikonsa tun yana karami mahaifinsa ya rabu da mahaifiyar sa acan gida Yobe da tayi auren a suleja din ne baban Habibun yace baza'a tafi Masa da yaro gidan wani ba yayi agolanci, rigima sosai aka kwasa da shi saboda itama tace bazata bar danta a inda za'a kashe Mata shi ba. Shine mafarin malam din ya dauko shi tunda ba wasu 'ya'ya yake dasu da yawa ba, a hannun malam ya girma shi yayi karatun boko har matakin HND.
Jikamshi malumfashj zasuje Daurin Auren 'yar abokin Alhaji Jafar din sannan zasu shiga Jikamshi dubiyar malamin malam Bukar din daya kwanta kwanakin baya a Asibitin Ibadan nisa yasa shi majiyyacin ya Hana masu zuwa dubiya sai yanzu daya dawo gida ne malam zeyi amfani da wannan damar yaje dubiyar.
Tafiya ce mikakkiya Dan tsakanin Azare da malumfashi tafiya ce ba kadan ba Dan haka sukayi sakko Habibun ne ze tukasu malam Bala anyi Masa Rashi acen garinsu Itas gadau Yana can.
Cikin ikon Allah Basu rasa Daurin auren ba Dan Sha buying Mai kyau suna cikin garin malumfashin.
Basu Bata lokaci ba suka dauko hanya sun biya jikamshin sun duba malamin Alhaji yayi masa kyau ta girma.
Suka dauki hanya sosai Alhaji Jafar ya yaba da tukin Habib Dan baiyi zaton ya kware irin haka ba.
Sunzo kachako lokacin sallar la'asar yayi guri suka Sami inda akayi wani Dan masallaci dan matafiya.
Suka firfito Dan gabatar da sallar, malam ne ya Fara gewayawa yayi dahara sannan Shima Alhajin yayo sukayi alwala suka shiga sallah Saida suka Gama suka fito sannan Habib Shima ya nufi gurin you daharar Amma shi saiya nufi wani bangaren daban, Bai jima da tafiya ba sai gashi da sauri Yana Kiran" Baba malam! Kuzo ku gani". Da sauri suka nufi inda yake harma da wani mutum da suka Sami a gurin Kamar Mai kula da gurin ne Dan daga gefe da 'yar tiredar shi suka rankaya Habib na gaba suna bin shi tun kafin su karasa suka hango mutum a kwance Kamar marar Rai.
"Subhanallahi "abinda suka gada kenan suna karasawa kusa dashi sai da suka matsa sosai suka Gane da ransa Amma Yana cikin wani yanayi, dako dako sukayi aka rasa ya za'ayi dashi matashi ne ba zefi sana'an Habibun ba saidai a yanayin yanda jikinsa yake ba alamar wahala a tare dashi. Habib ne ya matsa kusa dashi sosai ya tsuguna Yana dudduba jikinsa ko akwai alamun duka ko makamancinsa amma babu komai, shawara sukayi su daukeshi kodan ceton Rai su tafi dashi idan yaso sai su dauki hotonsa a Dora a social media wata kila a Dace.
Lokacin da suka shigo Azare ana sallar insha'i directly asibiti suka nufa dashi ma'aikatan nan da Nan suka duqufa a kansa, sai gurin Sha daya Allah ya taimaka ya kawa kwakwkwaran numfashi.
Sai lokacin suka nufi gida malam ya turo dalibansa guda biyu ya fada musu dakin da aka kwantar da Wanda suka tsinta din, ya basu kudi saboda abun bukata.
Haka su Abubakar suka kwana da shi sai gurin hudu da rabi na Asuba ya bude idanunsa Yana kallon bakon gurin da yake ciki ga bakin mutane a gurinsa, yukurawa yayi ze tashi yqji ya kasa kansa Kamar an Dora Masa dutse, bakinsa ya bude zeyi magana yaji kwata kwata ya kasa yayi yayi Amma Sam maganar taki yuwuwa sai hakuri yayi ya zuwa bawa sarautar Allah ido.
,💋❤️
💋❤️
AUREN HUCE HAUSHIN
💋❤️
💋❤️
✨ MAMAN FATIMAH ✨
✨PAGE THIRTEEN ✨(13)
__________Washe gari daga gidan Alhaji Jafar Abdul Hakeem da magaji suka kawowa su Abubakar abinci Asibiti, sun tausaya bawan Allah nan sosai Dan zuwa lokacin sun fuskanci baya magana Kuma jikin ma baya motsuwa yanda ya kamata, toilet ma sai da sukayi Kama Kama suka kaishi, a haka su malam suka shigo Asibitin tare dasu Malam Mudi, Basu Dade da zuwa ba likitoci suka shigo round sun tambayi menene Asalin ciwon to su dai sun fada musu Yan suka hadu dashi Dan Basu da masaniyar komai akai.
Gwaje -gwaje suka rubuta ayi Masa Dan binciken lafiyarsa.
Basu Dade ba suka koma gida saboda a ranar Alhaji Jafar ze shiga Bauchi suna da meeting da gwamna Amma ya bar kudade a hannun Abubakar saboda magani da sauran hidimar Asibitin.
Da yamma Habib ma ya shigo ya duba marar lafiyar nasu, Wanda har lokacin baya magana.
Likitoci sunyi iya nasu binciken basuga komai ba a tare dashi, sai dai rashin maganar kawai Amma Kuma Yana Jin komai da ake fada.
Bayan sun Gama bashi taimakon daya kamata suyi Masa suka sallame shi, Magaji ne ya dawo dasu gidan malam, Nan dakin malam na waje aka ajeshi tunda aka dawo dashi gida malam ya dukufa da Yi Masa addu'a Dan yayi bincike akan lamarin ya fashimci inda matsalar take, har Taraba ya tafi gurin malaminsa da yayi karatu a gurinsa ya fada Masa matsalar yaron, kwanansa biyu ya dawo Azare aka dukufa da rokon Allah da maganin hausa, haka zalika Alhaji Jafar ma Yana taho Masa dashi daga wani Islamic chemist da yayi musu bayanin matsalar yaron a can Abuja.
Cikin ikon Allah ba'a rufe wata hudu ba ya Fara magana sai dai idan yayi sau daya sai a wuni bai sake wata ba.
A haka aka dunga bashi taimakon har Allah yasa ya dawo normal Yana magana. A lokacin ne malam ya zauna dashi da Habib suka fada Masa inda suka same shi da halin da yake ciki a lokacin shiru yayi kafin yace musu shi dai yasan wata Rana Yana gida ciwon Kai ya takura masa har ya kasa fita, jzuwa dare yasha magani ya kwanta, to tun daga lokacin bazece ga yanda akayi ba shi dai ya farka ne ya ganshi a Asibiti tare dasu a hankali Kuma ya Gane a wani garin ma yake daban ba garinsu ba. Lokacin da Alhaji Jafar yazo garin malam ya fada Masa komai yanda sukayi da Mahmud din, Alhajin yasa aka Kira shi ya Kara jajanta Masa sannan ya nemi ya fadi garin nasu a mayar dashi Dan da gani Dan manyan mutanene.
Nan fa ake yinta Dan kekashe kasa yayi yace shifa ya manta sunan garin nasu akayi juyin duniya yace sai dai ko Nan gaba idan Allah ya nufa ya tuna, abinda ya tuna ma daga baya tunanin yazo Masa, haka suka hakura badan sun amince ba bayan ya tafi sun tattauna da Malam din akan lamarin inda Suke hasashen ko bacin Raine ya baro shi da gidan ya gwwmmace yayi zaman sa a Nan kafin ya huce ya nemi komawa gidan.
Nan yaci bada da Zama da Malam Yana kwasar ilimi kala kala.
Nan da Nan ya Zama Dan gida suka dinke da Habib duk da ze iya girmar Habib din da Kamar shekara biyu dan yayi Kamar sa'an Abdul Hakeem.
Bai cika wata shida ba Allah ya kawo aikin NGOs din Nan Wanda aka sakewa makarantar fasali da tsari suka sayi wani katon fili na makudan da sunan makarantar akayi gine ginen hostel din Yara suka dauki ma'aikata suka gyara tsarin karatun saboda kwazon Mahmud har co-ordinator din Shirin Muhammad Sameer ya dauke shi aika a shiyyar Katagum local government din ya Zama shine idon su a Nan, tunda ya iya rubutu da karatu. Habib ma Yana bada gudunmawa sosai a aikin duk da Shima nasa aikin da ma'aikatar ruwa ta Nan local government din tasu.
Wannan kenan.
____
Syprus.
Zuwa lokacin su zahra karatu ya Mika, tun tana saka Rai da zuwa Nigeria har ta hakura Kuma abinda ya Kara Bata mamaki sau biyu Abba da Abdul Hakeem suna zuwa ganinta idan harkar kasuwanci ya kawo sun Istanbul.Amma Koda wasa Basu taba ce Mata ga lokacin da zataje gida hutu ba.
A haka har suka hada shekara biyu a kasar, da gaske gida take son zuwa shi yasa lokacin da hutunsu ya gabato batayi shawara da kowa ba ta kama shirin barin qasar, online tayi komai Kamar su Sajida sai da komai ya Zama daidai sannan ta fadawa Uncle Haisam Shima bai hanata ba yasan tayi hakuri, Mama Hanifa ma ta waya ta fada Mata Nigeria zata wuce kawai, haka Ummee ma ta wayar itama ta fada Mata taso ta hanata Amma sai tayi wani tunani kawai tayi shiru kudade dai to tura Mata masu yawa Wanda har saida Zahrar ta Kara kiranta tana tambayar kudin ma meye haka da yawa? Tace ta turo Mata ne kawai ko idan take zatayi wani abun, godiya tayi Mata sosai hakan Kuma dabi'ar Zahrar ne komai kankantar Abu idan akayi Mata alherinsa zatayi godiya Kuma ko waye ta Bata Bata duba ai iyayene.
Kwana biyu suka Kara da akayi hutun shima visa din su Khadijah ne Bata Zama ready ba.
Lokacin da jirginsu ya dauka a Aminu Kano international airport taji ta sauko ta shaqi iskar Nigeria ji taji Kamar a Aljanna take lallai kowa yabar gida gida ya bar shi, saukar safe sukayi wurin karfe Sha daya ba yanda su zahra da Khadijah Basu da zahra ba akan ta zauna ta Dan huta kona awa daya ne a gurin sajida Amma tace A'a Azare tayi Kira su Anisa ne da Fatima suka bi Sajida Su dan huta kafin driver dinsu ya karaso tunda ba nisa tsakanin kazaure da kano, Kuma Gwammaja kan hanya ne.
Shatar taxi Zahra ta dauka ta kaita Kano line Dan direban taxi din ta tambaya Ina zata samu motar zuwa Azare ya fada Mata akwai gurare Amma ita Kano line yafi Mata kusa.
Har cikin Tasha Mai taxi din ya shiga da ita gurin motocin arear Bauchi, tayi Masa godiya sosai ta kuma Kara Masa kudi akan yanda ya bukata.
Away biyu da rabi Mai kyau matarsu zahra ta shiga Azare tun shigowa su ta Fara ganin 'yan canje canje a garin Kamar sabbin titina street light na solar sai gine gine masu kyau. Masha Allah ya dunga fada a zuciyar ta, Mai adai daita ta Sami ta fada Masa inda ze kaita, tunda suka tinkaro unguwar naji want irin nishadi ya mamaye ilahirin zuciyar ta, unguwar tasu ma an Sami cigqba sosai ga wasu gine gine sabbi masu kamar makarantar kwana har da gate a gurin gidan malam Baba gidansu ma gaba daya ya canza anyi Masa mahaukacin gyara tamkar sake sabo akayi.
Lokacin da Mai adaidatan ya sauke ta dai dai lokacin ya Hamza ya fito da alama wani gurinzeje Nan kusa.
Da madaukakin mamaki yake kallon zahrar shi dai Koda Wasa baiji ance zatazo ba Kuma yasan da ansan da zuwanta ai Bala driver ko su suje su daukota a kanon. Da sauri ya karasa Yana Mata sannu da hanya ita Kuma tana gaishe shi, shi ya biya Mai Dan sahun yace ta shiga ciki za'a shigo mata da kayan.
Tunda ta shigo gate din tasan eh lallai gidan ya lashe makudan kudin Dan gaba daya an canza fasalin gidan, tunda ta shigo gidan Mai gadin ke kallon zahra Dan shi dai sabo ne Bai Dade ba ta dai gaishe shi tayi gaba Nan ma wani mamakin ya rufe shi Jin tayi hausa radau Dan shi dai ze iya rantsuwa da abinda ze kashe shi wannan ko zo Bata sani ba da Hausa.
Ai mamakinta Bai karu ba Saida ta shiga cikin Nan dai ko rantsuwa tayi ba kaffara sabbin gine gine ne dam kwata kwata inda parts din su na da yake gurin ba komai sai filing da shuke shuken flowers.
Lokacin data shigo gidan ba motsin kowa kamar ba mutane a gidan kowa ne kofar part Yana rufe Ido ta lumshe tana shakar iska Mai Dadi ta gidan. Idonta na nufen Nan tana tsaye Dan ita batasan wane dakin zata nufa ba tunda da gaske ta Zama bakuwa a gidan, maganar Ibrahim taji Mai bin magaji Yana fadar "kai!" Da karfi ya juya a guje Yana fadin Ammah! Ammah! Kizo ga Aunty Zahra a tsaye a kofar part din Mama".
Magaji ne dake zaune a falon yana kallon wani series na 'yan Lebanon ya dago Kai da sauri daga kallon T.V Yana tsaki Yana fadin Amma Kai ba karamin soko bane dallah Banda tsabar hauka zaka wani ware murya Kama kwala Mata akan shashancin Kawai Wai zahra A'a wat......"
Maganar ce ta makale Masa lokacin da zahrar ta kunno Kai ciki da sallama a bakinta, dan a bude yabar kofar saboda zumudin ya kawo labari.
Ammah ce ta fito da sauri tana fadin Wai Kai har abada Ibrahim bazaka giirm..."
Idonta ya sauka akan Zahra wadda tayi tsaye ta langabar da Kai tana kallonsu,kafin Ammah ta dawo daga duniyar mamaki sai Jin zahrar tayi ta rugumeta ta saki shashhshekar Kuka.
"Ikon Allah!" "Ikon Allah!"
Abinda bakin Ammah ke fada kenan, ita Kuma zahra ta riketa kamar zata bace Mata.
Mamace ta shigo dakin da sauri tana fadin "Ina zahrar yanzu sahura ta shiga ta fada min taga Zahra ta shigo yanzu".
Ta fada tana kokarin Zama idanunta suna kan Zahrar.
"Wallahi kuwa Mama kin ganta Nan yanzu Ina daki Ibrahim ya shigo a guje Yana fadin gata Nan a waje nayi zaton shashancinsa ne Saida na fito na ganta kwatsam ba zato ba tsammani ba wani bayani".
Ammar ta saki da Dago kanta tana goge hawayenta tana fadin. "Haba Ammah an kaini wata uwa duniya an manta Dani idan nace zanzo ace A'a ni Kuma wallahi na gaji gida nake so shi yasa naki fadawa kowa na tasho kawai na gaji da ganinku a waya ni zahiri nakeso". Ta fada tana maida kanta jikin kafadar Ammar.
Tunda ta Fara magana Mama ta kureta da ido dan wani irin mahaukacin kyau taga Zahrar ta kara, ga wata irin gogewa da wayewa tamkar ba Zahrar data sani ba komai nata ya canza har ma salon yanda take magana.
"Ai kodai ki daina irin wannan kasadar ta tahowa daga uwa duniya irin wannan ke kadai sai ki fada ko addu'a ayi Miki sannan aje a daukoki daga Kano, Amma fa Ina tunanin a motar haya kikazo garin Nan ko?" Mama ta fada.
Kai Zahra ta gyada alamar eh, dai dai lokacin Yara suka shigo da jakunkuna ta guda biyu.
zaunawa tayi tana gaishe dasu Ammah, sannan magaji yayi Mata sannu da hanya Yana fadin "irin wannan surprised haka uktiy? kin ganki kuwa kin juye Balarabiyar ki sak kodan kina cikin 'yan uwa dangi farare irinki"
Dariya Zahra tayi Masa kawai.
Ibrahim ne ya shigarwa da Zahra jakunkunan ta dayan bed room din Ammah, ya fito ya nufi kitchen ya kawo Mata ruwa da lemo, ya koma ya dauko warmmers din abinci sai Ina yaka saka yake da zahra har Mama na Masa Dan biki.
Saida tayi wanka taci abinci sannan suka zauna da Ammah bayan sallar insha'i, hira sosai Suke Amma duk yawanci korafin Zahra ne na hanata zuwa.da Ammah tayi, a haka Abdul Hakeem ya samesu Shima yayi mamakin ganin.zahra kamar a mafarki Dan lokacin da ta dawo baya nan yaje Darazo ganin ganin wasu gonaki da Ya Hassan ya saya a can.
Sun raba dare suna Hira da 'yan uwanta a falon Mama sunyi waya ma da Abban tunda lokacin Yana aAbuja, Shima yayi fada sosai lokacin da Ammah ta Kira shi ta fada Masa ga zahra tazo.
Sai da ta kwana biyu tana huce gajiyarta, tana jikin Ammah kullum kamar kamar wata 'yar yaye, duk 'yan uwan kowa nan nan yake da ita, kowa kokarin kyautata Mata yake yi.
Sunyi waya da Aunty Hasana tace Mata tana nan tafe Jos zatayi Mata sati Amma sai Abba ya dawo, haka kusan Kullum sai sunyi waya da Hameeda.
Ranar data kwana biyar ne Ammah ta takura Mata akan ta leka makwabta ta gaishe wasu da yawansu sun shigo, wasu Kuma sun turo yaransu suyi Mata sannu da zuwa harda abin hassafinsu.
A waya Zahra ta Kira mujiba akan ta Shirya ta rakata Nan gidajen su shishhiga a gaisa.
Doguwar Riga ta saka kirar Dubai blue black Mai duwatsu tun daga sama har kasa ta saka plat she dinta fari tas ba wani makeup da tayi powder kawai ta saka sai lipsglow turarenta na Alkawari ta fesa Mai sanyi kamshi, Kota sa ko Bata Saba komai na sutarata kamshin yake.
Ta fito Kamar wani dawisu Dan da gaske zahra mai kyauce komai nata Kamar ita ta zabarma kanta. Tunda ta shiga bedroom din Ammah ke kallonta data ita sai halicinta suka San abinda zuciyar ta ke ayyana Mata a fili Kuma sai tace "Masha Allah! Har kin shirya?"
Kai ta gyada Mata tare da fadin "Eh Allah Dan dai kin matsabe Ammah Allah da Babu inda zani sai nayi sati biyu ko gate ba leka ba".
Wata leda Ammah ta Miko Mata tasa hannu ta karba tana tambayar "na waye?"
" Idan kunje gaida Baba malam saiki bashi tasa tsarabar turarika ne".
Murmushi Zahra tayi har fararen hakoranta suka bayyana tana fadar "wace irin tsaraba Kuma Ammah nida ba Hajji naje ko Umara ba daga makaranta fa na dawo hutu".
"To Miko min kije hannu sake ki gaisa ki taso tunda Zama da turawa ze saka ki koyi rowa" ta Mika Mata hannu alamum ta Bata ledar.
Dariya tayi Zahrar tana fadin "Allah ya Baki hakuri Ammah Ina ni Ina koyo rowa a garin wasu alhalin na gaji kyauta gaba da baya Allah qara lfy". Ta nufi kofa tana fadin "saina dawo"
"Allah ya tsare Kya gaishe da Malam din.
Gidan su mujibar Zahra ta Fara shiga suka gaisa da Mamanta sannan suka shishhiga gidajen suka gaisa, gidan Malam ne na karshe, a hanya Zahra ke tambayar Mujiba ginin da taga anyiwa Almajiran Baba Malam? nan ta fada Mata iya abinda ta sani akai.
A cikin rumfar canopy din da Malam yake bada karatu Zahra suka tarar da Malam din suna magana da wani matashi sukayi sallama a bakin rumfar a tare malam da Wanda Suke magana suka amsa sallamar, Yana fadin Bari naje na karbo yanzu in Sha Allah. Juyowar da zeyi sukayi ido hudu da Zahra wallahi ita dai batasan lokacin data rufe idanunta ba Dan wallahi wani Abu ta gani a idonsa Wanda Bata taba gani a idon kowa ba take zuciyarta ta wani harba a cikin girjinta. Ga wani mayen kamshi daya cika Mata hanci ita dai Bata San ya wuce ba Saida Mujiba ta tabata tana fadin ki bude idonki "Zahra menene?".
Ajiyar zuciya tayi a hankali tace "ba komai muje"
Cikin rumfar suka shiga suka zauna daga gefe suna gaida malam din.
Amsawa yayi Yana fadin Masha Allah da bakin turai ne Fatimah yaushe Kika shigo ban sani ba kodon Alhaji Yana Abuje shi yasa bani da labari".
Sunkuyar da Kai zahra tayi tana fadin.
"Ban Dade ba Baba Malam yau kwanana biyar da dawowa, Saida na huta nace Bari nazo na gaisheka"
"To Masha Allah! Allah yayi Albarka ya bada sa'ar abinda akaje nema, ai ba'a Gama karatun ba ko?".
"Eh da sauran shekara daya karatun ne da banbanci da namu na nan tunda su basa yajin aiki".
"Wannan haka yake, Allah yayi jagora ya bada sa'a"
"Amin" suka amsa tashi zahrar tayi ta karasa gaban malam din ta aje Masa ledar turarikan dake hannunta tana fadin "gashi Baba ba yawa"
Godiya yayi sosai kafin yace "ku shiga ku gaisa da zainabu batajin Dadi tana fama da masassara tun jiya".
"Allah ya sauwake"suka fada suna fita faga cikin rumfar.
Tunda suka shigo gidan suka sallama Amman gidan shiru a falon ma ba kowa uwar dakin Zahrar ta nufa tunda gidan ba bakonta bane, can tsakiyar gado ta hango Iya Abun jikinta yana ta kadawa tana ta rawar sanyi da sauri Zahra ta karasa kusa da ita tana Mata sannu Amman Sam ta kasa amsawa hannunta Zahrar ta Mika ta taba jikinta sai taji Kamar wuta.
"Ya Salam".
Ta fada tana nufar falon inda tabar mujiba tana fadar "Bari na fadawa Baba Malam jikin Kamar ya matsa gaskiya". Tayi waje ba tare data jira taji abinda mujibar zatace ba.
Tafiya take cikin sauri burinta ta Isa gurin malam ta fada Masa abinda kenan.
Ita dai Batasan yanda akayi ba sai ji tayi ta bugi kirjin mutum da kanta abinda yayi sanadiyyar ta tafi taga -taga zata Fadi taji an fusgota da Dan qarfi kafin ta Kai kasa sai ganin ta tayi rungume kane kane a jikin koma wannene an saka hannu biyu an zagaye bayanta.
Kici kicin kwace jikinta ta shiga yi data Samu ta Sami kanta coming fishing ta daga ido taga wane Mai tarar aradu da fadin Kaine ya kwakumeta haka da yammcin Allah wata'ala ta sauke Masa zallar rashin mutunci duk da ba halinta bane, tana daga Kai sukayi arba dashi ya kafeta da idanunsa masu wani irin kaifi da mugun kwarjini a cikin nata idanuwan Wanda a ganinta dashi na farko ya yamutsa duniyar ta
.AUREN HUCE HAUSHI
MAMAN FATIMAH
Page Fourteen 14.
-----------kusa da ita ya matso sosai Kamar ze Kara rungumo ta, da sauri tayi baya tare da rufe idanunta ruf zuciyarta na Kara speed, a hankali yayi magana saitin kunnanta "ki rinqa duba gabanki idan kina tafiya Mana kada kiyi Mana asara pls".
Ya fuske yayi wucewarsa ciki Bai Kara bi ta kanta ba. Nan inda ya barta Bata iya motsawa ba, wani Abu ilahirin jikinta keyi itafa ji take kamar kafarta bazata iya daukar ta ba wallahi,.shi Kuma wanene wannan a tare da malam haka? A Ina ya Samo shi Dan a gaskiya baiyi Kama da kolo ba Sam to waye shi?". Tambayoyin dake Mata Kai kawo kenan a kwakwalwarta daga ganin mutum haka kawai ze nemi yayi Mata shiga hanci da qudundune,ga wani irin kwarjini a cikin idanunsa da Bata taba gani a gurin wani namiji ba. Bata ankara ba taji maganar malam Baba Yana fadin " A'a Fatimah ya Kika tsaya a Nan ko wani Abu kike jira?"
Da sauri ta bude idanun tana kallon malam da wani yana binsa a bayan.
"A'a ba komai Daman gurinka zani jikin Iya Abun ne Naga kamar ya Dan matsa tana ta rawar sanyi".
Ta fadan kanta na kallon kasa kamar marar gaskiya, dan ji take kamar malam din Yana Jin mayen kamshin turarensa da ilahirin jikinta keyi.
"To Babu laifi muje ciki, yanzu Mahmud yaje ya dauko abokinsa don ya kara dubata tunda jiya sunje Asibiti da Halima matar malam Mudi ance zazzabin typoid ne yake damunta, to da jikin yaki Dadi ne za'a Kara bincike ko na cizon sauro ne zazzabin".. suka wuce ciki sannan zahrar tabi bayansu zuwa falon Iya Abun Kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki. Yana tsaye daga bakin kofar ta waje ya harde hannuwansa a kirji kamar Mai tunanin.
Ganin malam din da salahuddeen sun shigo ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 10 Chapter of 31