zamu tafi bamu gaishe da Aunty Zahra ba?".
Mahmud ne yace "Faruq Auntyn barci take sai dai zuwa anjima sai ku dawo kaji".
***
Cikin damuwa da matsanancin tashin hankali Mama ta tashi, tunda garin Allah ya waye ta tasa kayan da Hameeda ta shigo dasu jiya a leda da envelope din kudin da mijin Zahra ya Basu a gaba ko bakasan kayan kwalliyar Mata ba kaga wadan Nan kasan ba Karabiti bane ga uwa uba kudin daya lafta musu ita abin har ya Fara Bata tsoro, dan a zahiri kowa yasan fakiri ne wanda Bai ajeba bai bada ajiya ba amma a badini abubuwan da yakeyi suna da ban mamaki.
Wayar ta ta dauko tayi dealing din wata number ba'a Dade ba aka daga Bata koyi sallama ba ta Fara magana "Asabe kome kike kizo anjima da matsala babba komai Yana neman ya dagule fa kizo kiga abinda wancan tsintacciyar magen ya baiwa su Hameeda jiya harda fadin magana dan Hameeda ta fadin maganganun danace ta fada wallahi Ina kokonto akan lamarin yaron nan Dan jiya da dare Dana Kira malam na BANDE cewa yayi Wai mun kuskure wani abu shi yasa har Alhajin ya iya daura mata auren Kuma yayi duk iya yinsa ya kasa ganin komai akan mijin nata sai wani haske kawai yake gani".
Daga can taji magansr mamar ta amsa da "hakane ba damuwa sai kinzo din ta aje wayar tana jan karamin tsaki ta tashi ta shiga toilet.
A bangaren Ammah kuwa bayan Sajida da zulai sun Gama aikin break fast din da aka Kai gidan zahra, sajidar wanka tayi ta Shirya kafin ta fito falo su karya, bayan sun Gama ne ta kalli Ammah tana fadin "Ammah in Sha Allah yau an tafi gida Ina son na wuce school ne daman na jira ne saina raka Zahra gidanta tun last week muka Fara lactures".
Ta fada a ladabce.
"To Babu laifi hakan Allah yayi Albarka, sai Magaji ko Malam Bala wani ya Kai ki mun gode madallah, kunyi sallama da mutuniyar tun jiya kenan!" Ta tambaye ta.
Kai ta girgaiza tana fadar "A'a sai anjima zan shiga muyi sallamar".
___
Zahra Bata tashi ba sai wurin takwas da rabi tayi Mika gami da salati tana Kara ware idanu tana kallon dakin da alama kamar ma ta manta inda take Sai a hankali ta dawo cikin nutsuwarta "ya Salam".
Ta furta hankali tana ware sexy eyes dinta, wallahi Sam ta Manta da waifa a dakin gidan aurenta take ba a dakin Ammah ba, tashi tayi zaune kan sallayar tana Kara kallon Kanta har lokacin hijabin da tayi sallar ne a jikinta.
Toilet ta shiga duk jikinta ya Mata wani irin nauyi Sam Bata jin dadin jikin nata ruwa Mai dumi ta hada ta shige ciki tayi kwance tana shakar kamshin turen wanka data zuba ta jima sosai a cikin ruwan kafin tayi wanka ta fito sabon towel ta dauko mai kalar purple Babba ta daura ta fito gurin mirror taje lotion ta dauko ta shafa a jikinta, tashi tayi ta nufi gurin wata jaka kayan gyarab gashinta ta dauko, zuwa tayi ta zubesu yanzu da a gida ne da Ammah ce zata gyara Mata tsab ta hade shi guri daya, tana kiciniyar daureshi taji alamun bude kofa da sauri ta kalli gurin, Mahmud ne cikin shigar kananan Kaya yayi wani irin fitinannan kyau, hannunsa ya nade a kirji ya jingina da kofar ya zuba Mata idon dake figitata, shi be shigo ba shi be koma ba ya kafeta da idanunsa.
Tunda suka hada ido dashi tayi saurin sunkuyar da Kanta jikinta na wata irin rawa duk ji tayi ta rasa yanda zatayi daga ita sai towel din Nan a jikinta, gashin ta saki ya bazu har gadon bayanta ta matse hannunta a kijinta, sun Kai kamar minti uku a haka Yana Kare Mata kallo son ransa a cikin zuciyar sa Yana tsarkake sunayen Allah da yayi Masa kyautar bazata da wannan kyakykyawar halittar dake gabansa a matsayin matarsa ta sunna halaliyarsa wadda ba wani shamaki a tsakanin su.
Cikin takunsa Mai Cike da karsashi Amma a nutse, ya doso inda take tsaye Yana zuwa ba zato ba tsammani taji ya saka hannu Yana tattaro gashin daya bazu a kafadarta yana fadar "Bari na gyara Miki tunda Naga yana neman gagararki".
Bata iya ce Masa komai sai jikinta daya cigaba da tsuma, tsab ya hade ya saka ribom din daya gani a kusa mayukan gashin brush comb ya saka ya Kara gyara shi sannan yayi baya a hankali ya zauna akan sofa Yana fadar "ki shirya kizo muje ki bamu break fast gashi can Ammah ta aiko tun wurin 7:30 su Musaddiq suka kawo".
Bata amsa ba Kuma ta dago kalle shi ba, d'an gunguni ta fara kasa kasa "kawai ka zauna mun a daki kana kalleni kaki fita a gabanka kake son na saka kayan ko me?".
Yana kallonta gefen ido tana magana a ciki baya raba daya biyu yasan complain take akan zamansa. Tashi yayi Yana fadin "idan kin Gama kiyi min magana Ina aiki ne".
Ya juya ya fice.
Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadar "innalillahi ni Fatima Naga ta kaina Wai shi wannan waye shi? Nifa wallahi lamarinsa sun fara bani tsoro gaskiya" ta fada tana cuno Baki, sai Kuma tayi sauri har towel din jikinta na neman faduwa key ta sawa kofar, a gurguje ta saka doguwar rigar lace peach colour Mai touching din flowers green Bata daura Dan kwalin kayan ba saita rufa gyale green,Sam batayi wani make up ba powder kawai ta shafa sai lips glow turarenta ta fesa ta nufi kofa ta bude ta fice tsaye tayi a cikin corridor din saita rasa a wane bedroom din yake.
Ta jima a tsaye tana saka yanda zata tunkari dakinsa Kai tsaye, cikin yin shahada ta nufi inda take zaton nan ne bedroom din nasa a hankali ta murda handle din ta tura kamar wadda za'a cewa ket ta ruga, wani sanyi da kamshin turensa Dana freshner ya shiga hancinta dakin ba wadataccen haske duk curtains din windows a sake suke can kan sofa ta hango shi da laptop a gefen sa yana ta faman daddanabawa tsaye tayi ita Bata shiga ba ita Bata koma ba, yana kallonta ta gefen ido Amma sai ya basar kamar bai ganta ba.
"Assalamu Alaikum".
Ta fada a darare, Bai kalleta ba Amma ya amsa sallamar.
Dan Jim tayi kafin tayi karfin halin cewa "na gama shiryawar".
Kansa ya dago ya kafeta da idanunsa da yake razanata dasu kafin yace "idan bazaki shigo kije kawai an fada min Ina cinye mutane ne da Kika tsaye a nan".
Dan cuno Baki tayi ta saki handle din ta shigo a nutse Amma fa Babu nutsuwa Kota sisin kwabo a zuciyarta ta ayyana "waya sani ko mayen ne tunda abune a duhu".
A tsakiyar dakin ta zauna an carpet Kanta na kallon tace Masa "barka da Asuba".
Shiru yayi kamar Bai jiba Saida ya Mula dan kansa yace "Lafiya ya kwanan bakunta I hope ba wani damuwa ko?".
Kai ta gyada masa alamar eh.
Yace "good Bari na karasa wani dan aiki muje muyi break ko?"
Ya fada Yana kallonta.
Ganin tayi shiru yasa yaci gaba da aikinsa ita Kuma tana zaune duk sanyin dakinsa ya Mata yawa, tana son sanyi amma sai taji na dakin yana neman ya sakata rawar jiki.
Baifi minti biyar ba ya rufe laptop din ya Miki, gurin da take zaune ya nufo yana zuwa ya Dan tsuguna kusa da ita Yana fadin "taso muje kada nabar 'yar amanata da yunwa na amsa query a gurin su bestie ko?"
Ya fada Yana murmushi.
Hannunta ya kama ya dagota tsaye suna shakar numfashin juna Amma ita kanta yana duban kasa, dayan Hannun yasa ya dago fuskarta as usual yanda ya saba.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali Amma bata rufe idon ba kamar yanda ya hanata a jiya Bata manta ba amma ta kauda Kai gefe dan da gaske Bata iya had a ido dashi.
Dan kwanto da ita yayi jikinsa Yana juyo da fuskarta yana fadin.
"Wallahi kada ki rusa min budget dina kisa na kwashe kunyar nan daga idanunki tun banyi niyya ba matukar zakici gaba da irin wannan dabi'ar".
Das das girjinta ya kara bugawa akan wadda yake, tana fadin "oh ni Zahra tawa ta sameni shi Wai wane iri ne haka? sai yayi ta sakin magana ko kunya babu".
Saida ya matsa mata taci abincin kirki bayan sun Gama ne suka dawo parlor suka zauna Sam Babu sabo ko kalilan a tsakaninsu kallo ya kunna a Nile sat ya kamo super support suna kwallo live.
Ganin ita ba wani gane kan ball din take ba yasa ta Mike zata koma daki ta kira Sajida taji ya maganar tafiyar Dan tun jiya da Abba yace a jiya zata tafi gidanta sajidar tace itama sai gida ta.
Takunta biyu taji ya janyo ta ta fada jikinsa ba Shiri ta zaro ido waje hura kata iskar bakinsa yayi a fuskarta dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace "Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama yasa naki fita ko ina".
✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
💎 PAGE TWENTY 💎(20)
_______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a fuskarta, yasa hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very cute da ita, shifa baya gajiya da kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa buwayi Gagara misali daya mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata yarda sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba.
Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft kiss ya yiwa gefen wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!".
A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi kofa, Bata jira taga waye ba tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari.
Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda tasha gudu, jin alamun bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon qurillah irin wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?".
Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana fadar "Wai meye Kika wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls".
Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki kuwa just one day Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo na sameki haka kin wani Kara Zama fresh dake".
"Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?"
Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya Kinga ai dole na fada ko?".
"To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?"
Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci karatun ko tunda na samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da amfani dasu dazuma munyi waya da safe yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata na a fada Miki kada wani ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya".
Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata bada wasa ba.
Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa Zahra nasiha akan ta rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a tare dashi tun ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa heart beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?"
Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada".
"Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata baby amman Kamar an dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani azababben kwarjini da yayi min harda fadar na ringa kula kada nayi musu asara'.
Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar.
"Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki alhakina gurin hanani kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa bane za'a aje masa mace kamar ke ya iya kauda Kai gaskiya"
Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?.
Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... "
Sai tayi shiru.
Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale kowa duk wanda ze raina Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman Kara shiga jikin ki da wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki kada ki bada damar hakan".
In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada
"Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba Zahra ce Mike tana fadin "ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke kamar matar liman a daki na da Bata ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta gani Yana tsaye ya canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza kanshi sa na ibada.
Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi fuskarta kadan sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana "Wai meye ne yake faman shafa mata fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani rike mata gyale ta wani barta tsurarta".
Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa nayi muyi sallama naji Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko".
Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar.
",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta fine".
"To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata dauki nauyin zuwan mu Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa qasa.
Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka za'ayi".
Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri tayi baya tana turo Baki yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya bazan canza ba sai dai idan bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam".
A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy".
"Amin to bestie sai munzo ko".
Bai jira abinda zata ce ba yayi ficewarsa.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana Zama kusa da Sajida Mika Mata envelope din tayi tana fadin "yaushe ya Baki kikace bakya so?".
"Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta rokeshi, yanzu Dan Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan ma nace bana so su rike".
Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai gashi nan tunda a gaban ki ya bayar saiki karba".
"Bude mu gani to"
Sajidar ta fada.
Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin Sajida tace wallahi bestie akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya Miki Kama da Wanda baida abinyi ko wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi muhallin daya ajeki, ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan ki kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi Masa akayi? Ki tuna Nan fa ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali idan ya tuna hankali ze yarda da hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan wani Abu a tare dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma yanda na fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan tun sanda kuka hadu ba tare da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai kwanan Nan labarin ze sauya irinsu basayi da wasa fa".
Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa.
Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa Zahra kafin ta daga.
"To"
Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin.
"To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na dauka da Wasa yake lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai kawai yace su Bari Shima Yana son yaje kanon Sai ya tafi Dani".
Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya Abdul Hakeem Yana dama dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga target dinsa kenan yau yake son ya yad'a manufarsa shi yasa yayi Riga malam masallaci yace Wai daman kanon zaya".
Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya kankama ne ban sani ba Ina shirme?".
Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin "To bestie sai gani na gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da hankalin ki zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah".
Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka lfy. Amsa tayi tana Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta gani a mota a zaune cikin mamaki tace.
"Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?".
Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk zuciyarta ba Dadi Kamar ta Hana sajidar tafiya amma ba hali.
*********
Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya kwana, tun jiya daya karba da yamma Bai koma unguwar ba.
Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin. "magulmaci kawai".
Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya ya tambaya Ina Habib yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan sarki.
Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana shigowa da sallama mlm din yace.
"Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da wasu ayyuka gasu nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?"
Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" .
"Masha Allah. Allah yayi Albarka"
Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting.
Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya koma sun bin tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita hotel din suka nufa a hanya Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka komai an sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da ita tunda zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin ze iya Zama na surutu ko ace ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?".
Dan Jim yayi kafin yace.
Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene ni Nan nace Lagos zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's educated, zatayi saurin gane komai ni kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?".
Kai ya gyada Masa alamar eh.
Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda za'a kashe a makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya dauko kayan ya Kira Sameer ya fada Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake, Sameer din ne ya shiga gaba direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din.
Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki hatta nama da kifi daga can aka kawo kayane masu matukar yawa.
Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a tsaitsaye suka gaisa yayi gaba zuwa bedroom dinsa.
Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka Fara shigon kayan masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga dasu store din kayan abincin suka hada da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan gara su gireba dasu dublan da alkaki.
Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida aka Fara shigo dasu Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu ba amma yasan kima sun San kayan na manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta Amma bata furta ba.
Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin.
✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
✨✨
💎 PAGE TWENTY ONE 💎 (21)
...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan suka gyara parlourn,lokacin da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta cire bedsheet din ta zubo da pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa Mai nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta "lfy me kike nema ne haka Kika birkita gurin haka?".
Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta".
Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba Kuma Baki nema ba sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?".
"Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar ta ko Baki ne 'yan ganin daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai dayan tunda ba a ciki take ba.
Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana mamakin sa ita tunda take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane take gani.
Kamar
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 31