fad'a ta Dan sakarwa kanta ruwa Bata jima ba ta fito Riga da Wanda na Pakistan ta saka tayi rolling da gyalen ta saka plat shoes na daki ta nufi falo Amma zuciyar ta tana ta dar- dar kada suyi arangama da Dodon nata, falon ta shigo shiru sai sanyin A/C da daddad'an kamshin da yake ga curtains din duk a sake ga fitilu masu qarancin haske a kunne saiya bada wani irin yanayi Mai saka nutsuwa.
Dan waige-waige ta Fara Kamar tana neman wani Abu gurin sai Kuma ta nufi gurin tv ta tsuguna tana hada socket din adapter din tv ta kunna ta kamo tashar Almajid, kokacin sun saka Qira'ar Muhammad Saddiqul minshawi a cikin suratul ISRA'I sai da ta dai daita volume din sannan ta nufi kitchen din a nutse da takunta Wanda da yawa suke ganin yangace da jiji da Kai alhalin ba haka bane naturally haka Allah yayi ta.
Kitchen din ta shiga Kusan shigowarta ta uku Kennan, lokar da taga kayayyakin aikin ta bude ta dauko roba mai Dan Fadi ta nufi store ta debo Irish ta fito wanke shi tayi ta fere ta zuba a tukunya ta kunna gas, sai kuma ta dauko kaza guda ta yanka ta wanke ta zuba seasoning da spices ta rufe, ta jona egg boiler ta zuba kwai hudu a ciki.
A gefe kuma ta dauko attarugu da Albasa ta yanka kananu ta aje a gefe Irish din ta Fara dubawa taga yayi ta sauke ta zuba a container Mai zurfi tasa fork ta murje ta dora frying pan ta zuba Mai kadan ta saya attarugu da albasar ta zuba a Kan irish din ta zuba magi da curry ta fasa ta yanka dafaffen kwan a ciki sannan ta fasa danye ta zuga ta juya ta aje ta duba kazar itama tayi Nan da Nan ta hada pepper chicken sannan ta jona tanda electric ta Fara zuba hadin Irish din Nan tana soyawa Kamar masa, tana gamawa tayi pepper chicken. Dora ruwa tayi a karamar tunya kafin ya tafasa ta dauko madara ta bude ta diba a wani bowl ta dama sannan ta dama corn flour a cup, jikin kitchen cabinets din ta tsaya tana bin karatun da yake shigowa daga parlour har sun kai suratul D'AHA.
Madarar ta zuba taci gaba da tafasa sannan ta zuba corn flour din ta daure da yayi dai dai yanda takeso ta sauke ta Kara Masa condensed milk a cikin ta juye, hadesu tayi a babban tray tayi ta nufi falon, Nan akan dining table ta jero komai sannan ta koma ta dauko sauran tarkacen su cups.
Kitchen din ta koma ta gyara gurin tas, sannan ta koma daki wanka ta shiga, tana fitowa ta shafa lotion dinta tayi simple makeup ta saka saka turarikanta na jiki dasu humra Nan da Nan jikinta ya shiga fitar da wani fitinan Nan kanshi, doguwar rigar Dubai Mai kananun stones pink mai duhu ta saka rolling tayi dan Vail din
rigar milk colour sai ta fito balarabiyarta sak Dan idan ba kaji tayi maka Hausa ba bazaka taba cewa tasan ko zo da Hausa ba, tayi kyau matuka yarintarta ta fito sosai idan ka kalli fuskarta very cute sai wani annuri take fitarwa.
Parlour ta fito gurin dining din ta nufa cikin takunta das das. Tana mamakin Ina ya shiga Dan ko motsinsa babu har yanzu ita kuma bazataje bedroom dinsa ba, idan ya gaji da zaman dakin ya tunda ba yaro bane yunwar cikinsa ta fito dashi. Kunun madarar ta zuba da masar Irish din kwara biyu kawai ta dawo main parlourn ta zauna tana ci tana sauraren karatun, sai da ta gama ta Kai kayan kitchen ta wanke sannan ta dauko Wanda ta zubawa baba Mai gadi ta nufi kofa a hankali take tafiya a cikin harabar gidan iskar bishiyoyin da sauran shuke shuken suna kadawa gwanin sanyi can gurin gate taga baba Mai gadin ya nufa da sauri da alama budewa zeyi.Dan tsayawa tayi daga gefe idonta Yana kan gate din Dan taji dirin mota zata shigo cikin kankanin lokaci motar ta shigo ido cikin ido sukayi da shi shine yake driving din gabanta ne ya bada ras ras Kuma ya kafeta da fitinannun idanunsa cikin gwaninta ya nufi parking lot, Sameer kuwa Kamar wani sakarai haka yake kallon zahrar Yana tsarkake suna Allah a zuciyarsa ya ganta har kusan hudu Amma da alama ganin tsoro yake Mata sai yau yaga zahirin zahrar, da sauri baba Mai gadin ya karaso yana gaisheta ta Mika Masa Dan Karamin basket din ta juya da sauri ta nufi kofar falon har Kamar tana dan sassarfa ta shige ciki, harta wuce idanun Mahmud suna binta Nan da Nan yayi kicin-kicin da fuska daman ga Sameer ya tabo shi ga itama da kalar nata shirmen, cikin zafin nama ya kashe motar ya Kama kofar ze bude Sameer ya kamo hannunsa ya rike Yana girgiza masa Kai kafin ya dungule dayan hannunsa irin na roko din nan yace.
"Pls Dan Allah cool your temper kada kaje mata a haka kayi Mata uzuri Batasan Kai ko waye ba, Kuma infact ma laifinka ne ka tafi ka barta a gida har zuwa wannan lokacin Kuma tana ganin hakan da tayi shine dai dai koni nayi supporting dinta hakan shine dai dai ta nuna maka tasan haqqin abinda ka bar mata amana" .
A Dan fusace ya kalli Sameer.
"Nine na Bata amanarsa da izuninwa ta fito nan wato. ya kalleta yanda yakeso ko? Matata take kaiwa Mai gadi abinci wannan wane irin zubewar aji ne a gurina? Dubi fa yanda ta fito? Ko baka gani ba?"
Ya fada yana kallon Sameer.
"Ni banga wani Abu na rashin kyautatawa ba a shigarta, kawai dai idonka wani Abu ya nuna maka na daban gaskiya".
Hannunsa ya zare daga cikin na Sameer din ya bude kofar a hankali ba Kamar dazu ba zagayowa Sameer yayi ya rufe motar yabi bayansa Dan Idan ya Bari ya shige irin na jiya ze masa ya ajeshi a waje, kofar ya bude wani sanyi da kanshin girki Dana turarikan daki sukayiwa Sameer sallama Bata Nan sai tv a kunne ana karatun har lokacin.
Direct gurin dining Sameer ya wuce yana fadin Bari na Fara da Nan Idan na gama ma gaisa tunda ba bako nake ba ya Fara budewa Yana kallon Mahmud Yana fadin.
"Tab da alama Allah ya tarfawa garinki nono irin wannan delicious".
Gaba Mahmud yayi Bai tanka Masa ba ya shige ciki.
Kofar bedroom dinta ya kalla har dariya take bashi bilhaqqi da gaske tsoransa takeji bare Kuma da jiya ya Dan motsa mata Jamiyya.
Ta Dan Dade a bedroom din nata daga baya ta bawa kanta kwarin Gwiwar ta fita ko banza bazata bada kofar da wani na waje ze gane da 'yar tsama a tsakaninsu ba Kar a Raina Mata wayo, fuskarta ta Dan Kara shafawa powder kadan ta Dan Kara fesa mouth freshner Mai kamshi apricot ta nufi kofa tana budewa saura kadan yau ma suyi karon, da sauri taja Baya. Shigar kananun Kaya yayi as usual dan zaman da sukayi ta fashimci kamat ya samu wani freedom ne na sakewa, trouser black da milk T-shirt ne a jikinsa hannunsa daure da agogo sai waya a hannunsa. Baya tayi da sauri tana Dan zare idanu Dan ba Karamin tsoro taji ba, Shima kallon ta yake Kamar ya rungumota ko yaji relief na abinda yakeji a zuciyarsa, amma sai ya share ya Mika hannunsa ya kamo nata ya natso da ita kusa dashi Sosai Yana Fadin "kin tashi lfy?".
Ya shafi gefen fuskantar, cikin siririyar murya tace masa
"Ina kwana? Shiru yayi Kamar beji ta ba, ya janyo ta suka Fara tafiya a cikin corridorn, sai da suka Fara gangara steps din taji yace waya Baki izinin fita gurin watchman din can?"
Ya Dan matse hannunta dake cikin nasa.
"Wash!!! Allah ta fad'a ba tare data shirya ba. Dan da gaske matsewar ta shigeta dago Kai tayi cikin narke fuska Kamar zatayi kuka dai dai lokacin Sameer ya dago Kansa daga daddana wayar da yakeyi Jin maganarta Sam beji tahowarsu ba wani irin perfect match couples ya gani sun masifar dacewa da juna ya Dade bega ma'auratan da suka burge shi kamar su ba, a zuciyarsa yake Fadin.
"Masha Allah".
Zahrar Tace masa.
"Ba kowa, Dan Allah ka sakar min hannu wlh zafi...."
Ta fada cikin shagwabar da Bata San tayi ba.
Murmushi Sameer yake ta saki daga inda yake Dan ba karya yasan muhmud yayi dacen da Basu zata ba abun kamar a film yake ganinsa. Dan lokacin da suka Fara ganinta da Kuma furucin da shi Mahmud din yayi ashe Allah ya karbi addu'ar.
Dan gyaran murya Sameer yayi Yana kallon Mahmud din tare da fadar.
"Yallabai a bar madam ta karaso mu gaisa Mana ni ba mazauni babe gaba nayi daga Nan"
Ya fada da sigar zolaya duk yaga har yanzu kamar Yana Jin zafinsa tun maganar da yayi masa na Safnah.
Sassauta rikon hannaun yayi suka ida gangarowa directly dining area ya nufa yana zuwa ya ja Mata kujera ya zaunar da ita sannan Shima ya janyo ya zauna.
Gurinsu Sameer ya karaso daga inda yake zaune Yana fadin.
"Madam barka da Asuba kingan ni sai yau ki?".
Ya fad'a yana Zama kusa da Mahmud.
A kunyace ta amsa da "lfy kalau Ya Sameer ya kaje gida? Ina madam?"
"Komai lfy ya hakuri damu?".
'yar dariya tayi kafin ta Mike ta Fara bude abincin Wani daddad'an kamshin ne ya doki hancin Mahmud har Saida ya lumshe idonsa, Dan kallonsa tayi sannan ta kalli Sameer tace "me za'a zuba?".
Kai Sameer ya girgaiza Yana fadin "ai ni na riga ku ci tun shigowarmu naji bazan iya jiran masu gidan ba saina shide Ina jin kamshin delicious Amma ace saina jira".
Ya fad'a Yana dariya.Dan murmushi Mahmud din yayi.
"Wato ko Ina saika nuna halinka ko?".
"Pls zuba min kawai".
Kallonsa tayi kasa-kasa, tace "Toh"
Masar dankwalin turawan ta zuba sannan ta zuba pepper chicken din ta tura Masa sannan ta zuba kunun Madarar sannan ta koma ta zauna a darare.
Wani cup din ya zuba kunun Madarar ya dauko da fork ya matso kusa da ita da plates din abincin yace.
"Oya saka hannu muci".
Ya wani hade gabas da yamma alamun ba wargi Kai ta shiga girgaizawa alamar ta koshi Shima ture abincin yayi Yana duban Sameer.
"Muje kawai"
Ya fad'a yan Jan kujerar baya.
"Zanci".
Ta fada a gajarce.
Komawa yayi ya zauna Yana fadin "fine tunda zakiçi gara Idan mutuwar zamuyi mu mutu tare Dan naga abinda Mata suke yayi kenan Idan aka Basu Wanda ba shine zabinsu ba su kashe shi su auri wanda sukeso".
Tunda ya Fara Kora bayani Zahra tayi masa kur da ido tana Mai maita.
Kai Sameer ya shiga girgaizawa Yana mamakin wani sabon hali da Mahmud din ya tsira, yaga alama nema yake ta Hana yarinyar Nan sakat.
Ita Kuma tunda ta furta zanci Bata Kara tofa ko kalma daya ba, sai kawai ta dauki fork ta cako Irish din ta Kai bakinta ta tauna ta hadiye, pepper chicken din ta dauka taci ta dauki kunun Madarar ma ta Sha duk Yana kallon ta shi kuwa Sameer Yi yayi Kamar Allah Bai halicce shi a gurina ba.
Tana gamawa ta tura kujerar da take Kai baya sannan ta dubi shi ido cikin ido tace.
"Gashi naci idan kana tunanin zan zuba maka poison a abinci kayi kuskure lalacewar tawa Bata Kai haka ba, Idan na kasheka wace riba zanci? wato ka tafi lahira free ko? duk lodin zunuban daka dauka niga sakarai na lodawa kaina, to Bari na fad'a maka ba saina aikata zunubi irin haka zan rabu da Kai ba A'a salin alin kowa ze kama gabansa ni da Kai tunda daman masu iya magana na cewa tsintacciyar magen Bata mage nasan komai Daren dadewa zaka koma inda ka fito".
Ta fad'a Tana wurga masa harara ta wuce ta kyalesu batabi ko takan Sameer da yake fadin "Allah ya huci zuciyar amaryarmu".
Da ido Mahmud yabi Zahra har ta bacewa ganinsa "Wai shi yarinya kamar wannan zata saka shi gaba ta fada Masa son ranta amma yayi shiru Yana kallon ta".
Sameer ne ya katse Masa tunanin da yake.
"Dan Allah kada ka koya matsa tsiwa wlh da gani Bata Saba ba, bakaga jikinta har rawa-rawa yake ba".
Ya fad'a Yana kallonsa.
"Jikinta na rawa kenan Kare mata kallo kayi har kaga jikinta na rawa ni ban gani ba?".
"Subhanallahi! Wace irin magana ce haka wlh ba haka nake nufi ba, Bari naje kawai sai munyi waya".
Ya Mike Yana aje rafar dari biyar guda biyu Yana fadin "A bawa madam ace Mata na wuce tunda ka Hana muyi sallama".
Ya biya Kan center table ya dauki keys dinsa yayi gaba tunda yasan ba magana Mahmud ze Masa ba Dan da gaske yazo wuya yanda yanayin fuskarsa ta nuna.
Bayan fitar Sameer, Mahmud kasa ko motsin kirki yayi wai shine tsintacciyar magen? Da gasken gaske maganar ta dokeshi kwafa yayi Yana fadin zakiga tsintacciyar mage iya ganinki sai kin gane bakin rijiya ba gurin wasan makaho babe".
Ji yayi kwata kwata abincin ya fice masa raga Rai duk yanda yake jin yunwa ture abincin yayi ya Mike ya nufi bedroom dinsa Bai jima ba ya fito cikin shigar yari filtex fari dinkin boda da farar hula a Kansa Yana baza qamshinsa na Ibada, yayi waje.
Tunda Zahra ta Fadi maganar dake ranta taji zuciyarta wasai, gefen bed dinta ta zauna tana mita.
"Haka kawai saika wani ringa sakarmin magana ba control duk abinda yazo bakinka saika fad'a mini, Wai na saka wani Abu girkinma ba saina Kara yo da Kai ba sannan na Zama suspect daman saboda A kashedin Ammah ne yasa nayi, kwana biyu amma kamar na shekara duk ka matsa min ka karbe min waya nayi Shiru na Zuba maka ido Naga gudun ruwanka, na fita mikawa bawan Allan Nan abinci kace da izininwa? Haka kawai ka zamar min karfen kafa".
Ta fad'a Tana kwafa.
Tunda gari ya waye Ammah Bata zauna ba shirye-shiryen tafiyar Inna maimuna take wadda zata tafi yau, cikin Shirin fita unguwa Mama ta shigo lokacin Ammar na zubawa innar kilishin da Abba yasa akayi Mata zaunawa tayi tana Fadin "Inna yau zakiyi Mana ta Baki wlh ba dadi".
"Kayya Hajiya Rabi banda abun yazo da sammazi Aida na jima da tafiya gida daga zuwa biki na share our na zauna kinsan da Ardo Yana Raye hakan ba zata faru ba yaushe ze Bari".
"Haka ne Kam Allah yayi musu Rahama".
"Amin" su Inna suka amsa.
Leda mamar ta aje kusa da innar tana Fadin.
"Gashi Inna ba yawa Allah ya kiyaye hanya ni fita zanyi unguwa nasan kafin na dawo kin tafi".
Gdy innar da Ammah sukayi Mata ta tashi tana yiwa innar fatan sauka lafiya.
Sai bayan ta wuce ne innar ke tambayar Ammah ina Hameeda ne Naga tun she jiya da safe bata qara ganinta ba.
"Jiya kina barci tazo Nan Wai ta tafi Jos gurin yayar mamansu larai".
"To ba laifi hakan ba laifi daman shekaranjiya ne da dare na fita zanje can inda na baza ganyen yandi Dana shanya naji uwar tana surfa Mata zagi ban dai San dalili ba Amma naji ita yayar tata tana Fadin sai kije kiba Zahra hakuri Mana tunda kanwar uwarta ce ni dai Nan na barsu Dana dauko shanya ta".
"Allah ya rufa asiri kowa yayi nagari Kansa ya yiwa kuma sharri Dan aike ne duk inda ka tura shi ze dawo, bansan abinda yarinyar Nan ta tsare musu ba, bana raba day biyu da abinda sukasa Hameedar tayi inaga daga baya ta gane Bata kyauta ba shine tayi magana uwar ke zaginta".
Sun Dade suna tattaunawa.
Gurin Sha Sha daya da rabi magaji yazo ya dauki Inna maimunar zuwa gidan Zahra.
Zahra na barci Dan batasan lokacin da barci yayi awon gaba da ita ba, cikin barcin taji alamar bell din kofa ta yunkura ta tashi ta yafa Veil din rigar saman gashinta.
Tana budewa taga Inna maimuna da magaji, jikin innar ta fada kawai sai ta saki kuka Wanda ita kanta bata San kona menene ba.
" Ke matsa can da Baki rabuwa da shiririta saboda Allah menene abin kuka magidanciya dake, Dan Allah duba min Nan Mai sunan malam wannan ai rashin wayo ne koba haka ba?"
Ta fad'a Tana kallon magaji, duriya yayi Yana fadin "kumfi kusa Inna na bankwana ne tunda Idan Kika shige wannan lungun Sai baba ta gani, ni Naga ma kinyi Rana gaskiya har yanzu Baki tafi ba".
"Ai a Gombe zanyi kwana biyu gidan Dan aminiyata da nayi rainonsa to nayi Masa Alkawarin zuwa idan zan tafi".
Ita dai Zahra tunda ta kwantar da kanta a cinyar Inna maimuna Bata Kara dagowa ba, jinta a jikin innar sai takejin wani sauki da nutsuwa suna saukar mata.
Gashin Kanta innar ta Dan shafa inda gashin ya fito tana Fadin shi dai wannan gashin baisan kitso ba Kullum Yana Nan a nannade kamar gammo".
Dan turo Baki tayi tana Fadin
"Ya zanyi kinsan ba kitsuwa yake ba ko anyi idan ya Dade kwana biyu ne kawai ga zafi".
"Allah ya kyauta kawai dai 'ya'yan zamani Amma har yaushe za'a yita Zama da Kai haka? Yau Wai uwar taku tace meya samu wayarki ko an Kira Bata shiga? tasan ba rashin caji bane tunda ance Kuna da wannan abar Mai amfani da hasken Rana"
Dan Jim Zahra tayi tace ya karbe wayar ai hakan be dace ba, Sai kawai tace.
"Nima bansan meye matsalar ba kawai rufewa tayi taqi kunnuwa".
Magaji ne Wanda yaketa faman cakular waya dago Yana fadin dauko mugani ko abun minor ne".
"Bata gurina tana gurinsa ban sani ba ko dubawa ze bada ayi".
"Shu wa?"
Ya fad'a da sigar zolaya, banza tayi masa kamar bataji ba.
Tashi daga jikin innar Zahra tayi tana Fadin Bari na dawo wlh murnar ganinki ta mantar Dani ko ruwa ban kawo Miki ba". Tayi gaba innar na Fadin "dawo Zahra'u nida ba bakuwa ba".
Gaba tayi abunta.
Saida ta ciko tray babba da dangin Zaki da sanyi har sauran pepper chicken din ta zubo musu, tunda ta aje innar ke binta da kallo tana jinjina abin wannan cimakar bata mai Karamin kafin bace ko ance gida tallafin qungiya ya samu har abinci ci susuka dauki nauyin bashi?"
Ita dai shiru tayi Bata tofa ba Amma a kasan zuciyarta da maganganu fal Wanda zasu tattaunawa da 'yarta.
Ware ciki magaji yayi ya kwashi gara har Inna na Masa Dan biki.
Wayarsa Zahra ta barba ta Kira Ammah ta gaisheta itama abinda ta fadawa innar ta fada Mata game da wayar lokacin data sauke wayar harda share 'yan hawayenta, magaji Yana Mata tsiyar shatwabarta tayi yawa ita Batasan ta kusa Zama uwa ba,Inna na Taya shi.
Sai da Innar ta Gama sannan ta tambayi Zahra.
"Wai Ina Mai gidan nawa ne banji motsinsa ba tunda nazo?"
Kafin Zahra ta lalubo abin fad'a magaji ya rigata Yana fadin.
"Ai kin baroshi can a unguwar mu gashi nan suna magana da Ya Abdul Hakeem a kusa da masallaci har suka daga Mana hannu".
"Awoh to ai kasan ban waye dashi ba sai a hankali".
Nasiha Sosai da ban baki Inna maimuna ta Kara yiwa Zahra tare da kara jaddada Mata mashinmancin biyayya ga miji.
Kaya Zahra ta zubawa inna a wata babbar leda harda atamfa dasu turaruka taba Magajin ya rike mata.
******
Tafiya ce miqqqqiya daga Azare zuwa Babban mutum ta Babura jihar jigawa, direban daya dauko Mama da Asabe ya Dan juyo yana kallon Asabe wadda ta maida hankali gurin cin doyarta da kwai da suka saya a kanya babba yace ",munzo Babban mutum fa Ina zamuyi kinyi shiru alhalin kece idona tunda wannan ba yanyata bace".
"To na manta wallahi kasan da Dan Habu muke zuwa na zata shine ita dai Mama Bata cewa komai Dan niqab nema a fuskarta badan ta matsu da son ganin malam na bande din ba da ba yanda za'ayi tayi wannan kasadar Dan yanda ta fadawa Abban Itas/gadau zasu wata dubiya Alhajin yaso Bala direba ya Kaita ta nuna Masa da kawarta matar tshon Ambassador zasuyi tafiyar abinda ya Hana Bala direba kaita kenan, hanyar tinkin ta nuna Masa alamar Niger zasu shiga.
"Yanzu ke Asabe a she Niger zamu shiga shi ne kikace min kauyen Babban mutum wlh da bani da takardar ecowas da Saida na zubeku ku nemi wadda zata karasa daku kinsan kuwa yanda suke da doka da order?".
Tafiya ce miqqqqiya daga Babban mutum zuwa bande, sun Sami tarba Mai kyau daga yaran malam na ciki suna fitowa su Asabe suka shiga malam din yana zaune akan buzu da wani zabgegen carbi a hannunsa ya amsa musu sallamar su suka zauna suna gaishe shi.
Asabe ya dago kai kalla.
"Baki fad'awa Hajiya sakona ba?"
"Allah ya taimaki malam na fad'a Mata cewa tayi na kawota gurinka tazo taji Koda yanda za'ayi lamuran ne suke neman canza fasali".
Carbinsa ya Fara ja yana girgiza Kai yayi hakan kusan say uku kafi ya sauke wani dogon numfashi yana Kara girgiza Kai.
Mama cikin kidimewa ta furta.
"Da matsala ko malam?".
"To da matsalar Amma Abu mafi ban mamaki shi yaron har yanzu bana ganin komai akan Lamarinsa kwata-kwata sai yau Naga wasu mutane a Kan lamarinsa da Kuma itama yarinyar an tasa ta gaba da dafa'i shiri Kuma na gasken gaske sai dai naga wata tafiya a gaban mijin nata da alama Kuma tafiyar da Alkhairi q a cikinta sai dai idan dauke hankalinsa za'ayi daga garin kwata kwata, idan ya tafi ya kasa ko tunanin garin bare ya dawo, idan ba haka akayi musu ba ba makawa sai kin Zama 'yar kallo a gidan dan duk yaran gidan Mata ba wadda tauraruwarta ta kama kafar tata da gaske haka Allah ya yita da madaukakin Alkhairi".
Zuru Mana tayi ta kasa magana, maganar dai ita kenan Zahra tafi nata 'ya'yan.
"Malam ayi duk abinda ya Kanata inda hali ma ya rattaba Mata saki kafin yabar garin".
""Abinda ban gani ba kenan a cikin auren nasu Dan Idan shi ne ze saketa to inaga sai dai ta mutu da auren Dan Banga hakan ba a tare dashi,ni a yanda na gani a istiharata ma ya Santa batun a Nan garin naku ba Kuma da soyayyar ta Mai karfi a zuciyarsa wadda har abada baze iya rabuwa da ita ba, ayi dai hakan yanda Idan iyayenta suka gaji da jiran dawowarsa Bai dawo ba su raba auren da Kansu". Bayanin ya kwantawa da Mama hankali, ya kawo abubuwa ya bata har Wanda za'a hada da tuaren wuta a bawa zahrar Idan harta turara Mahmud ya shaqa shida Azare har abada.
Kudi masu kauri Mama t✨✨
✨✨
💎 AUREN HUCE HAUSHI 💎
✨✨
✨✨
MAMAN FATEEMAH
PAGE TWENTY FOUR (24)
_____ Tun bayan tafiyarsu Inna da magaji sai gidan ya zamar Mata shiru Bata Dade a parlourn ba ta koma ciki, da taga tunani yana neman ya dameta saita dauko qur'an dinta ta Fara karatu Saida taji Kiran sallah ta aje taje tayo alwala.
Bayan ta gama sallar ta Haye gado ta Kara A/C tayi kwanciyar ta ba tafi minti talatin da kewnciya ba taji alamar Baki ana Danna bell, tashi tayi ta nufi kofar da gaske dai bazata samu barcin na kirki ba,Kofar ta bude a hankali su Amatu ita da Aunty safiyya ne guri daya suka zauna a Dr sulaimanu Adamu model school of Hygiene inda tayi service, su Kuma permanent lecturers, rabon ta da Amatu tun ranar daurin aurenta dan lokacin da zata wuce jama'are garinsu Bata biyo ta gidan Ammah ba daga gidan Aunty Hasana ta wuce kawai. Cikin nuna tsantsar farin ciki Zahra ta rike hannun Amatu tana fadin "wlh nayi fushi Amah Ina nan Ina jama'are? Amma kikaqi dawowa ni Aunty safiyya zanyi welcoming kawai Amma ke kam dai sai a hankali kawai, Aunty sannu da zuwa". Ta fad'a Tana Basu hanya tare da karbar yaron Aunty safiyya dake hannun Amatun.
"Hakan ma na gode tunda an karbi Auntyn ai shike nan tunda ita ta gari batayi laifi ba saini da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 31