me,Hameeda tazo sun gaisa sun Dade suna Hira dashi tambakar sun shekara da sanin juna, sunan mujiba ma ta shigo suka gaisa ba shi yabar Azare ba sai kusan magariba Dan ma Zahrar nata Masa magiyar ya tafi saboda rashin tsaro irin na kasar.
Tun daga lokacin hanya ta aure shi tsakanin kano da Azare. Mushahu na mutane ne kusan duk Wanda ya kwana ya tashi a Nan kukkuken unguwarsu Zahra yasa shi Koda kuwa ba gaisawa suke ba, wata kila ya taba yiwa wani alheri a cikin yaran gidanku Dan da gaske hannunsa a sake yake gurin Alkhairi.
Sunyi sabo sosai da jama'a a Nan har gurin malam Bukar Yana zuwa sauda dama idan ya shigo garin, wasu ma daga cikin samarin gidan malam din sunyi sabo sosai.
Lokacin da results dinsu Zahra ya fita Sam bataje ba Auncle Haisam ne yayi Mata komai Allah ya taimakeka ta fito da first class degree a akan anatomy.
Allah ya taikata da taimakon Ya Hassan aka kawota bauchi service, bayan zaman camp sukayi posting dinta Dr Sulaiman Adamu memorial college of Hygiene and Environmental health science Azare.
Ammah taji dadin hakan sosai haka shima Mushahun yaso hakan kwarai da gaske.
Zahrar najin dadin aikin sosai da sosai domin teaching Yana cikin hobbies dinta.
Bayan sun Gama ne da wata daya kamar yanda akayi Alkawari aka Fara kokarin Fara shidimar bikin ta dai dai lokacin Kuma akayiwa su Ummee rasuwa a saudiyya abinda ya Hana su zuwa kenan da har Ammah tace a daga bikin tunda rasuwar ta jikinsu ce kanin Baban Ummeen ne ya rasu,Amman sai sukace Dan me ayi idan komai ya lafa zasuzo suga daki kawaii.
A satin da za'a Fara bikin kusan Kullum Mushahu da Abokansa shakikai su Deeni da Aliyu Wanda Suke cussings suke ta zirga-zirgar ganin abubuwa sunyi yanda ake so duk wasu programs a nan za'ayi dinner ce kawai zasuyi a Kano, sun Kama dakuna uku a hotel idan zasu zauna har zuwa Daurin aure.
Saura kwana biyar Daurin auren ne wani abun al'ajabi ya faru da Hajiya Nafisa Maman Mushahu wadda suke Kira da Ammi.
Cikin dare tana barci ta farka a matukar razane saboda wani mugun mafarkin da tayi da Musbahun akan auren, addu'a tayi ta koma ta kwanta ai kamar jira ake barcin ya dauketa sai abunda ta gani a wannan mafarkin yafi wancen muni, wasa-wasa barci ya gagareta a wannan Daren kafin safe duk ta wani hargize ga wasu irin tunane tunane sun cika Mata zuciya na rashin kwanciyar hankali kafin yamma gaba daya ta Zama wata marar nutsuwa ba shiri ta Nemo kanwarta Aunty Jamila a waya Nan da Nan tazo tunda ba aure gareta ba, duk ta kwashe komai ta fada Mata akan Bata son auren Musbahun kwata kwata ita fa ko a cikin ranta ta tuna da zeyi aure ji take kamar zata zauce, da farko Aunty Jamilar ta dauki abun Wasa Amma ganin da gaske abin yake yasa ta Kira Babban yayansu Alhaji sulaiman da kanin Baban su Musbahun Alhaji isma'il, Suma da farko sunyi zaton na Wasa ne Amma da suka matsa akan ta Fadi dalilinta na Hana yuwuwar auren sai abun ya ta'azzara ya Zama kamar Mai tabin hankali, ganin abun Yana neman ya Zama wani iri ne yasa Alhaji sulaiman ya kirawo Aliyu tare da tambayar suna ina?.
Aliyun yace gasu Nan a hanya sunje Azare ne Amma har sun wuce wudil sun kusa kano ya fada Masa lallai direct su nufo sokoto road su duka.
Haka suka shigo suka tarar da wannan dambarwar ana ta fama da Ammi.
Ai tana arba da Mushahu ta Kara tuburewa tana fama fadar wallahi matukar ya kafe sai auri Zahra Bata yafe Masa nononta da yasha.
Su dai Basu ankara ba sai ganin Mushahu sukayi ya sulale ya zube a sume, da sauri Aliyu ya kawo ruwa aka zuba Masa Amma a banza ganin haka yasa suka nufi Asibitin Nasarawa dashi. Haka aka dunga juyawa da Ammi Amma ta kafe kamar kafiran farko duk Wanda ake tunanin ze kawo gyara a lamarin an fada Masa Kuma yayi bakin iyawarsa Amma ba wani ci gaba da aka nemi a Zafafa sai lamarin yaso ya koma Mata tabin hankali abinda daya tada hankalin Babarsu kenan Hajiya Yaya tace dole a hakura da auren tunda abin yazo da irin wannan lamarin marar Dadi daman tun farko ita bataso lamarin ba sai dai yaran yanzu ne baka hanasu abinda suke so, tunda Daman fa ance shine na uku a Wanda zasu auri yarinyar ana fasawa to shima gashi tun ba'aje ko Ina ba lamarin ya Zama haka.
Tashin hankali iya tashin hankali Musbahu ya shiga Dan dakyar aka Sami nutsuwarsa dan kwata kwata ya daina magana da kowa ya rufe duka wayoyinsa shima Deeni ganin kiran Zahra yasa ya rufe layin da suke wayar da ita, Aliyu ne kawai Bai rufe wayar ba Amma baya picking idan ta Kira a halin hake ne su Alhaji sulaiman sukaje Azaren da labari marar Dadi Wanda ya kawo karshen 'yar Wala walar da akeyi da Zahra akan aure ta kawo karshen duk wani makirci da bita da kulli da ake Mata na rushe aurenta idan ya taso abinda ya girgaiza duniyar Wanda suke fake suna tsula ta'addanci ta karkashin kasa.
✨
✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨
✨
MAMAN FATIMAH
Assalamu Alaikum warahamatullahi ta'ala wabarakatuhu. Dan Allah ayi hakuri da matsalar da aka samu gurin turo page fourteen sau biyu hakan ya faru ne saboda wasu dalilai Amma na karshen Wanda na turo shine cikakken fourteen din yanzu kuma na hade fifteen & sixteen guri daya na gode.
Page
Fifteen
&
Sixteen
📖🖋️
BACK TO STORY.
________ Gurin Zahra su Sajida suka shiga tana kwance a gado idanunta a rufe tayi zurfi cikin tunanin, Sam bataji shigowar su Sajida ba Saida mujiba ta Dan zungure ta bude ido ta yunkura ta tashi zaune tana dafe kanta dake Sara Mata.
Sajida ce ta zauna kusa da ita ta Kama hannun Zahrar tana fadin "bestie Dan Allah ki rage tunani kada wani ciwon ya kamaki, ki yawaita addu'a komai yayi zafi maganinsa Allah. Kuma wani hanin ga Allah baiwa ne, ke kanki Baki taba tunanin abun ze Zama haka ba, Kuma Allah ya juya lamarin yanda yaso, to saiki gode Masa bisa ni'imar da yayi miki, Kuma nifa mujiba Ina doubting akan wannan da aka daura musu aure, Kuma ki rubuta ki aje zakice na fada Miki kije kiga gidan da za'a Kai bestie, Kuma ki duba kiga irin kayan da aka kawo yanzu kinsan duk Wanda ya hadasu first class ne a gurin gayu wallahi komai bana banza Amma Kuma Wai almajiran malam ne gaskiya I doubt much".
Ta fada tana kallon mujibar.
Ita dai Zahra ta rasa inda zata Kama komai ya kwance Mata, su damuwarsu kaya da gida, ita Kuma tata damuwar ta yanda za'ayi zaman ne, har yanzu gani take kamar a mafarki Wai wannan karon ma Saida aka samu akasi,ta rasa daga Ina matsalar take, shi kuma auren da aka daura meye ze biyo baya tasan idan ba wani nufi ba na Allah shima sai an Sami wani kalubalen a cikinsa.
A hankali ta furta "Ya Salam! Allah ka shiga cikin lamarina, wallahi bestie komai ya kwance min bani da sauran dabara,kwakwalwata ta daina aiki yanda ya kamata kinsan Allah nifa kamar ma tsoronsa nakiyi Dan tunda na Fara ganinsa naji wani irin Abu a jikina wanda ban tabaji ba a kan ko wane namiji sai shi, Kuma yayi min abinda ya kamata na dauki mataki Mai karfi amman wallahi ko magana kasayi Masa nayi, yanzu kuma a haka zan rayu dashi? Ni wallahi bana sonsa Sam Kuma fa Shima yace baya son abin yake ba kawai dai baze iya watsawa su Abba kasa a ido bane". Ta karasa fada hawaye na zubo Mata a fauska.
Lallashinta sukayi da kyar tayi shiru kafin mujiba tace "haba Zahrar ki daina kuka idan kina daga hankalin ki na Ammah ma baze kwanta ba, Kinga irin haka ba Dadi duk da an aura miki Wanda babu soyayya da shakuwa a tsaninku, ita a hakan ma yayi Mata da ace wannan karon ma an fasa aure gara hakan tunda naga alama da ita ake fadan ke kin ratso ne kawai ake fakewa da lamarin ki Dan a Hana duniyar ta zaman lafiya da kwanciyar hànkali, Kuma Baki san dalilin da yasa Abba yayi hakan ba, kinsan dai Abba baze taba aura Miki baragurbi ba kedai kiyi ta addu'a muma muna tayaki, Bari na tambaye ki Mana idan kina addu'a bakya cewa Allah ya Baki miji na gari?"
Hannu tasa tana share guntun hayenta kafin ta harari mujibar tana fadin "Ina yi Mana kuma kawai saina yi sallah na kasa wannan addu'ar dan na Zama abinda na zama ko?"
"A'a ba haka nake nufi ba bayani zan miki shi yasa nayi Miki tambayar dai, Allah ya huci zuciyar Amarya".
"Kina jina mu 'yan adam muna rokon Allah ya zaba mana abinda yafi Mana Alkhairi Amma wani lokacin inda kake zaton alherin ne to sai kaga ba'a Nan yake ba, idan yazo ta inda baka zata ba tunda bakasan gaibu ba, sai kayi watsi dashi idan bakayi sa'a ba haka abun ze kwaranye baka mori komai ba, alhalin Kai ka roka aka baka sai kuma ka Raina abinda aka baka ba tare da kasan shine alherin ba. To Dan haka nake so ki yiwa Allah da manzonsa ki rike abinda Allah ya Baki tunda shi Kika roka Kuma ga abinda ya Baki sai kiyi ta Tahamidi ga Allah kawai, ki nemi Allah ya saka muku kaunar junanku da soyayya da jinkai. Dan kinsan dai idan ba wata kaddarar Ubangiji ba Babu abinda zesa ya rabu dake tunda ya karbi auren Nan wallahi ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba yana so, dan haka ki daure kiyi Masa biyayya shi arziki nufin Allah ne, naji ana ta 'yan kananun magamganu ki toshe kunnenki kada ki bada barakar da wani ze kushe Miki miji dan bashi da kudi, Allah ne Mai azurtawa lokacin daya so sai kiga wata Rana sai dai a tada labarin abun".
Sun Dade suna kawo Mata misalai da yawa na irin wannan auren nata daga baya Kuma ya Zama Alkhairi.
********** A matukar gajiye Mahmud ya shigo cikin gidan misalin karfe biyar na yamma tun safe ya kebe kansa a dakin daya Kama na hotel yake ta faman aiki yaso kwarai ya Gama da wuri kafin yamma amma abun ya gagara Dan da gaske aikin ya dauki hankalinsa sosai ga tafiyar dake gabansa Banda Allah yasa wasu abubuwan sun daidaita a jiya da dole tsakanin gobe da jibi dole yabar garin ko baya so. Amma cikin taimakon Ubangiji sai komai ya Fara daidaita, shi kanshi Yana Jin idan ya tsallake ya tafi daidaita wanna gabar Bai kyauta ba Sam, dan jama'a zasuga kamar ya gujewa auren gatan da akayi Masa ne ya watsa musu kasa a idon an Masa gata irin wannan sun dauki yarinyar su Mai tsada sun bashi ba tare da sun San ko waye shi ba, ko la'akari da karancin samunsa suka aura Masa.
Su Habib ya tarar a falon Yana karatun Alqur'ani, Abubakar Kuma Yana ta faman hada Nile sat.
Su duka suka amsa Masa sallamar Nan falon ya aje jakar laptop dinsa abinda bai taba kwatanta zuwa da ita ba kenan Dan duk aikin da zeyi sai dai yayi acan hotel din ya barota, amma yau dole tasa ya taho da ita nan saboda so yake ya raba dare Yana aiki shi yasa ma Kai tsaye ya nufo gidan da ita yasan bashi da matsala dasu duka biyun.
Abubakar ne ya tsaya da aikin Yana kallon Mahmud Yana fadin "Dan Allah Ina ka shiga Wai bakasan kana dagawa Baba malam hankali ba? shifa yafi son daya juya ya ganka, gashi ka Kama ka rufe wayar ana ta Kira a rufe".
Girarsa ta daman ya dan shafa kadan kafin ya zauna Yana fadin "cool down Mana my man Ina kake tunanin zan tafi? Wallahi aikine yayi yawa na wannan NGOs din bakaga har kayan aiki suka bani ba tun zuwan da sukayi wancan karon, yanzu haka ana koya min yanda zanyi amfani da ita laptop din ne yanda zanji dadin aikin, Bari nayi wanka sai muje gurin Baba malam din nayi Masa bayani yanda ze fashimta, sunce ma nan da sati daya ko biyu zasu kiramu zuwa babban taro da za'ayi".
Tunda ya Fara magana Habib ya dakata da karatun da yakeyi yana bin Mahmud da kallo haka nan kawai yaji Kamar ba gaskiya Mahmud din ya fada musu ba, Kamar yana boye wani Abu, shifa tun lokacin daurin aurensa ya lura da yanda Kamar yake baiwa Sameer umarni a wasu lokutan sai idan ya farga ne yakan yi maza ya canza taku, sannan a watannin baya ya taba jin yana waya a kusa da dakin da suke taron abinda ya shafi makaranta lokacin yana duba wasu sabbin forms da aka kawo na Enterprinuership da za'ay a gurin Sam baisan Yana ciki ba tunda kofar a rufe take ji yayi sosai Yana bada umarnin yanda abin ze kasance harda makudan kudin da za'a kashe gurin sawo kayan sana'ar da za'a koyar harda kudin da za'a participants din tunda program din harda matasan unguwa a cikinsa duk za'a Kuma bada kayan sana'ar da mutum ya koya kyauta, tun lokaci yayi masa alamar tambaya sai dai ba wata kafa daya Bari wadda za'a fashimci komai. Bai tabbatar da abinda yaji ba Saida akayi komai Kamar yanda ya bada umarnin, ga Kuma lokuta yawa sai yayi batan dabo ka nemeshi ka rasa Kuma har yanzu baisan takamaiamai Ina yake zuwa ba duk kuwa iya kwakwarsa.
Jakar ya dauka yayi gaba Yana fadin Bari na Dan watsa ruwa na fito. Da ido suka bishi har ya shige corridor din daze kaishi bedroom dinsu,kowa Yana ayyana wani Abu a zuciyarsa.
Ya dauki Kamar minti hamsin kafin ya fito cikin Riga da wando na shadda Fara tas, a gaggauce ya fito ganin lokacin sallar magriba ya kawo jiki.
***
Da dare Zahra tana dakin Ammah suna Hira da Inna maimuna tana Kara nusar da ita yanayin rayuwa Sajida ta shigo da waya a kunnenta ta gaishe da innar ta Mikawa Zahra wayar tana fadin "Baffan Rimi ne yake son magana dake"
Amsa tayi tare da sallama, cikin daki Inna ta nuna Mata da hannu ma'ana ta shiga ciki tayi wayar, Dan sajidar tana Mika Mata ta juya ta koma, haka Nan ta tashi duk da Bata San nufin innar na hanata waya a falon ba.
Gaishe da Baffan tayi tunda Daman ya Santa tun suna makarantar kazaure sunje masa ita da Sajida lokacin da Zahrar ta zauna a kano gidansu sajidar sanda akayi musu hutun midtrem break maimakon taje Azare sai umman sajidar ta nemi Alfarmar Ammah ta barta tayi hutun a gurinta,to kafin su koma ne sukaje Rimin sumailar gurin kakan sajidar, tun lokacin ya baiwa Zahra magunguna sosai yace tayi amfani dasu har Sajida na mita ita Bai Bata irin na Zahra ba, a lokacin murmushinsu manya yayi Yana fadin "yanda aka saka rayuwarta a gaba ke ba Wanda ya damu da taki rayuwar ita akwai tarnaki Mai yawa a kanta Kuma Naga jikin nata ba wani abun azo a gani na tsarin jiki.
Gaisuwar Baffa ya amsa Yana fadin "Ashe haka lamura sukayita faruwa ko Fadima? Dazu Babar taku tazo min da bayanin abinda ya ringa faruwa dake akan aurenki, yanzu haka tana Nan zata kwana saboda akwai abinda nasa ayi Miki gobe in sha Allah zatazo Miki dasu da yanda zakiyi amfani dasu in sha Allah ba abinda ze Kara faruwa dake, lallai akwai shedancin mutane akan lamarin Amma mu dauka Daman haka Allah yayi nufi, wanin Allah Bai Isa yayi maka komai ba face da izinin Ubangiji, ga Uwar taki ku gaisa".
Ya mikawa Maman Sajida wayar.
Bayan ta gaisheta ta Kara da yi Mata nasiha sosai itama, sannan ta fada mata gobe in Sha Allah daga Rimin Nan zasuyo ita da Babban danta Wanda some times shine direban ta idan zatayi doguwar tafiya, kafin sukayi sallama.
Dakin Ammah Zahra ta shiga ta fada Mata yanda sukayi da kakan Sajida, godiya sosai Ammah ta ringa yi tana Kara jinjina kaunar da bayin Allah nan.suke yiwa Zahra dalilin 'yarsu gashi saboda matsalar Zahrar zata taso tazo har Azare.
Washe gari tunda wuri Zahra da Sajida suka Gama gyaran dakin Ammah sukayi wanka sannan sukayi breakfast gurin karfe Sha daya Maman su Sajida da yayanta Ya Abba suka karaso murna gurin Sajida ba magana, dakin Ammah suka nufa da Maman Zahra tasonsu Fara shiga gurin Mama su gaisa Amma Sajida ta Hana tana fadin "A'a ki Bari mu shiga inda ya kamata idan min Gama abinda ya kawo ta sun gaisa da kowa so kike azo a zaune Mana a hana ruwa gudu".
Tarba ta girma Ammah tayiwa Maman Sajida itama ba wata babba bace Dan Bata Kai sa'ar Ammah ba, an sauki Ya Abba a dakin da suke sauke bakinsu yayin da magaji ya shiga shidima dashi.
Bayan Maman su sajidar ta Gama cin abubuwan da aka kawo Mata suka sake gaisawa dasu Ammah da Inna maimuna ta jajantawa Ammar abubuwan da suka ringa faruwa, ta Kuma Dora musu da bayanin da mahaifinta yayi Mata akan matsalar Zahrar inda ya bada tabbacin ko waye yake wannan shegantakar a kusa dasu yake sosai, Kuma dashi ake faduwa da tashi, kuma yace kada Wanda ya kawo wani Abu da sunan naci kona Sha yace a baiwa Zahra da sunan tsarin jiki ko na gyaran aure a barta taci sannan a kula da Koda abincin cikin gidan ne in dai ba ita Ammar ta dafa da hannunta ta Bata ba daga Nan har tabar gidan.
Wata babbar leda ta dauko wadda sukazo da ita ta bude ta Ciro jarka da ruwa a cikin Mai kalar yellow na za'afaran ta dauko wani garin magani Mai laushi ta hadasu da jarkar ta mikawa Inna maimuna tana fadar.
"Ga wanna ruwan addu'a ne da garin magarya zata dibi ruwan addu'ar ta zuba garin magaryar ta Sha ta shafe jikinta safe da yamma,wannan Kuma kafa da hannu kawai zata Riga turarawa sai Addu'oi da ya bada a Bata zata ringa karantawa safe da yamma".
Godiya sosai su Ammah suka shiga jerawa Maman Sajida Kamar ba gobe har sai da ta ringa fadin "Haba Hajiya meye amfanin taren abinda ya shafi Zahra ai ya shafi sajida wallahi shekaranjiya data Kira ta fada min hankalina ba karamin tashi yayi ba wallahi na dauka abin ya kwaranye tunda an dauki dogon lokaci kafin a Kara maganar Auren".
"Wallahi kuwa muma mun dauka na bayan da aka fasa ko matsalar namijin Aljani ne ya aureta Amma duk inda akaje da ita sai a ce ba wani iska a jikinta".
Inna maimuna ta fada.
Sun tattauna sosai da Maman Sajida Saida akayi sallar Azahar Sajida ta raka mamanta dakin Mama su gaisa, sun Sami kawar Mama Asabe sun hada Kai suna kus-kus bazaka taba cewa da mutane ba.
Sun gaisa sajida ta fadawa Mama mamanta ce, Basu jima ba suka fito Mama ta biyosu har kofar part dinta Nan godiyar ziyarar.
Sai kusan karfe uku su Maman Sajida suka juya Kano Sajida tace ita saita raka Zahra gidanta zata dawo.
Tun da Mahmud ya Kira Zahra sau daya Bai sake kiranta ba, yau yaji ya kamata ya Kira yaji lafiyar ta ko banza fa yanzu tana karkashin ikonsa ne cinta da Shanta da duk lamuranta suna wuyans Kuma ai Bai kyauta ba gaskiya ace yayi burus da lamarin ta abun sai yayi Mata yawa.
Sai gurin Tara na dare ya lalubo numbarta ya Kira, harta gama ringing ba'a dauka ba sai kawai ya share ya tura Mata text massage ya fada Mata Daman ya kirane yaji lafiyar ta.
Tun bayan tafiyar Maman Sajida Ammah da Inna maimuna suka shiga hasashen abinda kakan Sajida ya fada na hasashen Mai yiwa Zahra bita da Killin nan duk iya nazarain su Basu gano ba sai suka.barwa Allah amma dai innar ta soke kwanan Zahra a can gurinsu tace su dawo dayan bedroom din Ammah suna wanna ita da Sajida da ita innar ya ishesu ita ko katifa sai a saka Mata a kasa ta kwanta.
Hakan akayi su Zahrar suka tattaro suka duk wani Abu na amfaninsu suka dawo dakin.
Kafin su kwanta Saida Inna maimuna ta saka Zahra tayi amfani da duk magungunan da Maman Sajida ta kawo Mata, wanna ne dalilin dayasa innar tace su dawo nan tunda komai na duniya Yana son sirri, duk da Hameeda ce kawai ke kwana a tare dasu Zahra Dan Salma tunda suka dawo ma Bata taba kwana a part din nasu ba.
Tun Hameeda na jiransu Zahra su shigo har tayi barci.
Saida Zahra ta Gama amfani da duk abubuwan da aka kawo Mata sannan ta dauko wayarta rabon data dauko ta tun bayan sallar Azahar data hau online ta duba sakonnin whatapps.
Sajida da Inna maimuna Kuma sunta hirar duniya abunsu.
Missed calls ta gani har hudu uku na mujiba ne sai Kuma wani daya number ce amma kallo daya tayi Mata ta gane ta waye, ji tayi gabanta ya fadi to neman me yake Mata da wanna tsohon Daren haka kawai ya dagula Mata sauran lissafinta. Fita tayi daga call history din sai Kuma taga envelope alama massage ya shigo budewa tayi sakonsa ta gani a hankali ta furta ta "Ya salam".
Allah da gaske fa take jin wani irin lamari a tare da shi.
Da safe ma innar ta saka Zahrar gaba Saida tayi duk abinda ya kamata kafin ta fice tabar dakin dan tun kafin ta Fara Sajida tayi waje ta Basu guri. Saida tayi wanka kafin ta fito yin break bayan sun gama ne Ammah tace Zahra taje Abbansu na kira, gyalen rigar ta yafa a kanta ta nufi gurin Abban, lokacin data shiga ya Gama break Shima, guri ta Sami ta zauna kusa da kujerar da yake Kai tana fadin "Abbana Ina kwana?"
Jaridar dake hannunsa ya aje Yana fadin "lafiya kalau uwata, Ina fatan ba wata damuwa ko?"
Kai ta gyada kafin tace "ba komai"
"Masha Allah ya fada.
Kafin yayi gyaran murya ya Fara fadin "Uwa inaga in sha Allahu jibi da yamma Zaki tafi gidanki Dan dazu ne malam Bukar ya roki wannan alfarmar saboda shi Mahmud din ne zeje wani taron da kunyar da suke aiki dashi suka shirya to Kuma yace baya son ya tafi Baki tare acan gidan ba kada abin ya Zama na magana ace ko ya gudu ne ya barki a nan, to Nima din na karbi nasa hanzarin tunda Masha Allah jikin naki yayi sauki sosai Kuma Baki bani kunya ba kin kwantar da hankalinki".
"To Abba"abinda ta fada kenan tayi shiru, Mamace ta shigo dakin itama Tasha wanka sai baza kanshi take Kamar Kullum. Da barkwwnci ta shigo tana fadin "A'a bamu Gane ba, irin wannan kebewa tsakanin 'ya da uba mu ba'a neman ayi shawara damu".
Ta fada tana fadada murmushinta.
Gaisheta Zahra tayi kafin mamar ta gaisheta da Abban tunda ba itace da girki ba.
Bayan sun gaisa ne yake fadawa mamar "Ba wani shawara muke ba wadda Bata shafeku ba Ina fada Mata ne jibi in Sha Allah zata tafi dakinta tinda Allah yasa ta warrare Kuma shi mijin nata ne zeyi tafiya shi yasa nake son ta tafi dakinta".
Nisawa Mama tayi kafin tayi magana.
"Kamar Yaya zeyi tafiya daga Kai masa yarinya basai ya tafi da ita ba salon ya cuci yar mutane ya lallaba ya budu ya barta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 12 Chapter of 31