tunda tsintacciyar mage ai Bata mage, gaskiya Abban Yara ka tsaya ka duba lamarin nan Mana kada fa azo ana Dana sani kaga masu iya magana na cewa keyace".
Abban ne yace "ba abinda ze faru sai Alkhairi Amma Jibi da izinin Allah uwata zata tafi dakinta, tashi kije Uwata Allah yayi Miki Albarka yanda Kika yi min biyayya Ubangiji ya Baki 'ya 'yan da zasu yi Miki biyayya kema".
A zuciyarta ta amsa da "Amin"
Saida Abbai yaga ta fice gaba daya sannan ya dawo da dubansa gurin Mama yace "haba Rabi'a har yaushe Zaki dinga magama irin wannan a gaban kankanuwar yarinya Kamar Zahra ai Bai kamata ba ki duba kiga yanda aka dunga walagigi akan auren yarinyar nan a baya yanzu Kuma anyi aure Zaki ringa fito da maganganun da zasu iya sakata a wani Hali ai kwantar da hankali uwata take bukata ba irin haka ba, mu bita da addu'a in sha Allahu Alkhairi na hada Wanda a gaba duka sai sun gode min koda kuwa bana duniyar ne".
Tunda Zahra ta shigo ta kwanta a kan sofa a nan falon Ammah na kallonta tasan kan zance dan tunda Abba ya dawo daga masallaci ya fada Mata, zancen da suke da Inna ma kenan ta shigo suka bar zancen.
Da hantsin Ammah ta Kira Aunty Hasana ta fada mata.
Zuwa Sha biyu tana gidan suna zaune a falon Ammah Mama ta shigo ita da kawarta ta amana Asabe wadda kwanan Nan ta mayar da gidan gurin zuwanta sabanin baya da sai a share watanni Bata zoba, Nan suka zauna akaci gaba da tattaunawa akan tarewar Zahra har Asabe ke fadin zata saka wata 'yar gusau da suke makwaftaka ta yiwa Zahra hadin kazar amare da daka shine nata Gudunmawar.
Da yamma Aunty Hasana ta umarci Sajida da Hameeda da zilai Mai aiki suzo suje gidan Zahrar a gyara abinda ya kamata tunda jeren ya dan jima da yi.
Sun fito zasu tafi ne Abdul Hakeem ya tsayar da Auntyn Yana fadin "sai Ina Kuma Aunty mu?"
"Gidan Zahra zamuje a Dan Kara gyarawa jibi Abba yace za'a kaita kaga kuwa ai dole a shiga a duba ayi abinda ya kamata".
Komai tsab suka sameshi da gani ana gyarawa Kullum dan har wani hadaddan kamshin freshner ke tashi a falon haka bedroom din Shima komai neat yake a toilet ne abin ya bawa Aunty Hasana mamaki an zuba kayan wanka masu azabar tsaba Bata Kara tsinkewa da ta janyo locker ta jikin mirror taga wasu designers din turaruka na Mata Kuma da yawa na kamfanin Al -haramain ne harda irin Wanda Zahra take amfani dasu.
Ita dai Hameeda Yar kauye ta Zama a gidan Dan ko a mafarki Bata taba kawo Wanda aka aurawa Zahra, ze Kama hayar gida irin wannan aljannar duniya haka ba.
A kitchen ma Nan Hameeda da zulai suka lalace komai na gurin saiya burge mutum, Nan ma Saida Auntyn taga wani fregde ash colour a cikin Dan ack din jikin kitchen din irin Mai kofa Kamar ta wadroof ko ba'a fada ba kasan kudi sunyi kuka a gurin.
Burner Auntyn tasa aka jona aka zuba turarikan wuta Wanda aka hadowa Zahra daga Saudi Arabia tun wancen lokacin tunda basa komai saima Kara kamshi. Basu baro gidan ba sai kusan magariba.
Aunty Hasana taso ta wuce da Zahra gidanta amman Ammah tace A'a ba inda zata so suke ace Mata tsohuwar banza idan so suke su tafi to ita zahrar ta Kira ta fadawa mijinta idan ya amince ita nata Mai sauki ne ita kuma Zahra tace lahlah a barshi kawai.
Wajen goma saura aunty Hasana ta dauki yaranta suka wuce gida. Da safe Saiga Asabe da dahuwar kazar amare da jarkar zumar Mata da ta tsimi tayiwa gidan tsinke, part din Ammah ta shigo direct, bayan sun gaisa ne ta mikiwa Ammah babbar ledar data zubo kayan tana fadin "Ina Amarya tazo gashi na cika Alkawari tazo ta cinye ta bani kashin tace a koma Mata dashi zata hada Mata wani Abu dashi. Inna maimuna ce tace "ai kuwa yanzu taci abinci ta shga daki saidai a aje zuwa anjima sai taci ko gida ne sai a aika Miki da Qashin, mun gode kwarai madallah Allah yabar zaman tare". Asaben ta amsa da "Amin ai bama sai an tashi mutum ya kaiba Nima saina jira taci din ko Nan da yamma ne" ta fada tana mikewa tayi musu sallama ta nufi dakin Mama.
Bayan fitarta ne Ammah ta dubi Inna maimuna tana fadin "nifa jikina Bai bani ba akan taci wanna abun Dan ni tunda ta fada jiya naji abin Bai kwanta min ba,mutuniyar da gaisawa ma sai ta kure akeyi da ita Amma fa ki duba sai wani rawar jiki take akan abinda Bai shafe ta ba ko alama, Kuma kar nice wani abun arziku sukeyi da zahrar Dan ko gaisawa saita kure, Amman ki duba ki gani yanzu sai haba haba take da Zahra.
Dakin Ammah aka shiga da kayan ammar tace zata cire tsokar tabar musu kashin, hakan ne ya kasance tayi komai ta baiwa auta ya kaiwa Asaben dakin Mamar.
Saida Asaben ta tabbatar auta ya fito ta kwashe da dariya tana fadin "wallahi Maman yara kinsan ta kan mugumta, yarinya har yarinya amma ta Kare a auren marar asali Wanda ko danginsa ba'a sani ba"
Kwafa Maman tayi "barni kawai Asabe wallahi tun lokacin da aka dauko yarinyar nan hankalina ya kasa kwanciya, saboda babu ta inda Allah ya rageta duk abinda ake so jikin 'ya mace to Allah yayi Mata ga uwa uba yanda mazan zamanin nan suka jarabtu da son Mata irinta nasan ba karamin mutum ne ze dauke taba Ina zaune sai dai na Zama 'yar kallo ga nawa 'ya'yan a gabana, wallahi baze yuwu ba ai hankalina Bai Kara tashi ba Saida na raka Aunty Ladi gurin wani Mutum a can jos nayi Masa maganar Asma'u to cikin binciken ne maganar yarinyar ya Fado yake fada min na kyale maganar Asma'u don ba yanda zanyi da ita jikinta a shirye yake haka Shima Alhajin ba abinda zeyi tasirin da ze rabashi da ita, Amma ga wata yarinya Nan duk gidan ba 'yar da zata wuceta a sa'ar rayuwa a gurin aure Dan mijin da zata aura ba karamin mutum bane Kuma dai..... Sai kawai bawan Allahn Nan yayi shiru da bakinsa nayi nacin duniyar nan Amman yaki karasa mana zance, haka muka tasho Aunty Ladi nata zugani kada na kuskura na Bari ta auri Mai maiko duk yanda zanyi nayi Naga hakan Bata faru ba. Nayi ta fama duk Wanda zezo gidan Nan gurin yarinyar nan zezo duk kuwa da Fadi tashin da nake akan su Salma amman a banza, maganar dai daya ce Zahra, ni Kuma nayi Alkawarin badai Zahra tayi aure ta barmin Yara a gida ba,Kuma badai ta auri Mai rufin asiri ba, gashi kuwa ta Kare a Wanda ko asalin kirki bashi dashi Abu daya ya tsaya min a Rai yanda Naga gidan da zata zauna da abin yaso razani sosai Dan ba haka na zata ba, amman duk da hakan ma yayi tunda ai gidan ma Malaminsa ne ya bashi aro su zauna, Kinga kuwa karshe sai dai a Kare a yawon haya cikin Yama yamar matan alarammomi, Kuma wannan kayan da ake qafafar an saka a gidan karshen wasu kayan saidai a sayar Dan Babu abinda za'aci dasu Dan an sawo da zimmar su tafi Abuja sai gasu sun Kare a gidan Alaramma".
Ta fada cikin izgilanci.
**
Duk yanda Zahra taso ta kwantar da hankalinta abin ya faskara dan da gaske zulumi takeyi na yanda zata fuskanci wannan sauyin da yazo Mata a bazata Wanda Bata tab'a tunanin hakan ba ko cikin mafarki, lallai tayi zaton daga kan Mushahu komai ya kwaranye Amma sai wata matsalar ta taso wadda tafi ta baya.
A kwance ta wuni duk ta tsangwami kanta Sajida sai tausarta take duk da itama tata zuciyar a kusa take Dan da gaske tana tausayin zahrar ba kadan ba.
Gurin karfe biyu ne sukaji alamar Kamar anyi Baki a gidan da alama ma da dan damarsu.
Sajida ce ta fito ta gaishesu zata koma cikin ne Ammah tace taje ta Kira Mama tace tazo su gaisa da Baki Iyayen Musbahu ne daga kano.
Ta fita tana mamakin to meya kawo su Kuma.
Tare suka shigo da mamar Dan sajidar na fada Mata ta nufo dakin cikin rawar jiki.
Ciki Sajida ta wuce yayin da mamar ta zauna tana gaishe da bakin nasu Kafin Inna maimuna ta Fara Mata bayanin Maman Musbahu ce tazo da 'yan uwanta ta bada hakurin abinda ya faru Wanda ita kanta Bata San yanda akayi ba sai daga baya ake fada Mata shine tazo taji ko da yanda za'ayi a gyara matsalar tunda ta dawo hayyacinta take cikin damuwa domin kwata kwata Musbahun baya cikin nutsuwarsa tun bayan samun labarin an Aurar da zahrar, ganin lamarin nasa ba sauki ne yasa suka nufo nan Ashe har da yaron sukazo sun jima a gurin Alhaji ma kafin su shigo nan din, hakuri kawai ya basu akan aikin Gama ya Gama tunda yanzu matar wani ce ita.
Kallonsu Mama ta karayi tana tambayar "Ina mamar tasa take"
Hajiya Nafisa kanwarta ita ta nuna Maman Musbahun tana fadin "gata nan"
"Ayya Allah sarki Hajiya sai hakuri Allah Bai nufa matarsa bace ba sai dai yazo ya duba wata tunda da sauran yaran a gidan".
Mama ta fada tana kafe Hajiyar da ido.
"Kayya a yanzu dai bana tunanin haka zata yuwu sai ko a gaba tunda ban taba ganin abinda Musbahu ya kwallafawa Rai ba Kamar auren yarinyar nan tunda kuwa ya rasa ta bansan Kuma lokacin da ze Kara maganar wani auren ba".
Sun Dan Jima kafin Ammah ta tashi ta shiga gurin su zahra tace ta fito su gaisa da Baki zasu tafi.
Jiki ba kwari ta nufo kofa doguwa rigace a jikinta kirar Bahrain Mai duwatsu har kasa blue black gyqlenta kwai ta Dora a kanta Dan Sam Zahra Bata fiye son saka hula ba a kanta Dan Sam santsin gashinta baya Bari hular ta zauna ta dunga zamewa kenan.
Cikin takunta na nutsuwa ta shigo falon hade da sallama Kanta na kallon kasa ta karaso cikin nutsuwa ta zauna gefen Ammah a kasa kan carpet, tunda ta shigo suka bita da idanun kowa da abinda yake ayyanawa a zuciyarsa.
"Masha Allah! tubarakallah 'yata matso kusa dani dole my son yayi kamar ya zauce da labarin rasaki ya riskeshi" abinda Aunty Nafisa ta fada kenan tana nunawa Zahra kusa da ida, jiki ba kwari ta karaso ta zauna tana gaishesu.
Suka amsa jiki a sanyaye su kansu sun San dansu yayi wani babban rashin da maida shi sai nufin Allah, tunda Daman shiya hada shi da Zahrar kuma shiya raba lokacin daya so.
Nan sukayi sallama suka fita cikin matukar jimami Dan da gaske sunyi rashin sirika.
A daki Zahra kwanciya bayi ta rufe fuskarta da hannu biyu Batasan lokacin da hawaye ya zubo Mata ba, Wai shike nan komai ya Zama past tsakaninta da Musbahu duniya ba tabbas. sajida na kallonta Bata hanata ba Dan itama Saida ta matse, lokacin zahra na falo Mushahun ya Kira wayar ta, sajidar ta dauka yanda taji maganarsa ko rantsuwa tayi bazatayi kaffara ba kuka yake shima da idanunsa Dan abinda ya fada kawai ya karya Mata zuciya, kalamai ne na bankwana ga masoyi da da given off akan Abu, da kyar ta iya fada Masa ba zahra bace itace magiya yayi Mata dan Allah ta fito Masa da zahra yayi Mata sallamar karshe Amma hakuri kawai ta bashi tunda yanzu Zahra matar aure ce bashi da hurumin yin magana da ita.
Sun Dade a haka kowa da abinda yake sakawa a zuciyarsa nkafin su jiyo maganar Magaji Yana fadin "Ammah ga Ya Mushahu zaku gaisa yazu tafi ne".
Su biyu suka shigo suka gaishe dasu Ammah a nan Inna maimuna ke fadin "kayi hakuri da hukuncin Allah kaji kada kayi fushi da mahaifiyar ka itama bayin kanta bane duk uwa bataqi ace danta yafi kowa sa'ar abokiyar Zama ba, irin wannan matsalar ta Jima tana bibiyar yarinyar Nan to munyi zaton daga kanka abun ya Kare sai Kuma ya canza salo akan mahaifiyar ka, kayi hakuri ka fawwalawa Allah komai shi ze baka wadda tafi Zahra daman Allah hukunta kai ba mijinta bane ayi hakuri".
Kansa Yana kasa tunda ta Fara maganar wani Abu ya tsaya masa a makogwaro yaji Sam ya kasa magana sai Aliyu ne ya amasa da "ba komai Mama haka Allah ya nufa, Allah ya Basu zaman lafiya mu zamu koma".
"To Allah ya tsare ya baka mace ta gari wadda zata maye maka gurbin Zahara'u" Inna ta fada ita kuwa Ammah kasa magana tayi dan da gaske yaran tausayi suke Bata sun kwallafa Rai da juna Amma akayi musu karan tsaye, a zuciyarta ta ayyana "Allah ka biwa yaran Nan hakkinsu duk Mai hannu a cikin Bata lamarin Nan kayi Mana sakayya da gaggawa Dan isar Annabin Rahama Muhammad s.a.w.w."
Ta window zahra ta leka lokacin da suka fito daga falon kamar ance ya juyo sai ganin zahrar yayi tana kallonsa da sauri ta juya ta rufe fuskarta da hannu ta saki wani marayan kuka ta zube a gado. Su Kuma suka fita zuciyarsa Kamar zata Kama wuta dan ganinta ba karamin fami ya zamar Masa ba, har ji yayi Yana wani layi Kamar ze fadi.
Magaji ne ya shigo falon Yana fadin "Sun tafi, wallahi Ammah naji tausayin Ya Musbahu sosai kinsan har gurin Baba malam yaje Amma magana daya dai kowa yake fada masa yayi hakuri, bayan mun fito ne yace na nuna Masa mijin Aunty zahrar na fada Masa ai shine suka Fara gaisawa dashi bayan sun gaisa da malam, shiru yayi sai kawai Naga ya dafe kansa Yana girgizawa, yace na hakura da zahra nasan wannan baze taba sakin zahra ba. wallahi Ammah sai Naga yana goge hawaye gaskiya Allah saiya saka musu wannan ai zalunci ne Kullum idan Aunty zahra ta samu miji sai an samu matsala".
Ya fada Yana Jan tsakin takaicin.
"To magaji babu yanda za'ayi haka Allah ya hukunta sai hakuri".
Bayan tafiyarsu da Kamar awa daya Abdul Hakeem ya shigo ya fadawa Ammah tazo Abba Yana kiranta.
A bedroom dinsa ta sameshi Yana tsaye ya goya hannunsa a baya Yana Dan Kai kawo a tsakar dakin.
Sallam tayi Masa ya amsa sannan ya sauke hannunsa ya nufi gefen gadon inda Ammah ta zauna tana tambayar "Lafiya kuwa Abba meya faru Naganka a haka?"
Ajiyar zuciya ya sauke Yana fadin.
"Da matsala gaskiya yaron nan ne yazo a rikice yana kuka Kamar yaro karami da kyar muka lallashe shi nida Abdul Hakeem ga mahaifiyarsa da 'yan uwanta kingansu dai nasan mazan ne suka ce ba ruwansu shine ita da kanta ta taso tazo wallahi hawaye bibiyu ta rinka yi min akan na rufa Mata asiri na warware wancan auren a maida kan Musbahu abin har abin tausayin wallahi, shi yasa na turosu cikin Dan ku Basu hakuri tunda wancen zance ya wuce Kuma ji nayi da nauyi na Kira malam wallahi tunda ganin Mahmud nake Kamar Dan cikinsa Kinga na Kira shi akan maganar ai Bai kyautu ba, to bayan sun tafi ne Abdul Hakeem ya Kira Hassan ya fada masa shine ya kirani Yana min magiyar Dan Allah a rakata dakinta yau basai gobe ba da tun farko ma ankaita da hakan Bata faru ba yasan wasu ne daga nan zasu Gaya Masa tunda Yana da mutane sosai suce ai tana gida ma yayi bata tare ba suyi tunanin ko Babu auren ne, Dan haka Nima nayi na'am da maganar tasa, kuje kuyi duk abinda ya kamata da magariba zan mikata dakinta da kaina in Sha Allah, na Kira malam ma na fada masa."
"To hakan yayi duk abinda ka yanke dai dai ne Allah ya nuna Mana lokacin".
"Amin ya amsa"....
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
✨✨
❤️❤️
❤️❤️
💋💋
💋💋
MAMAN FATIMAH.
PAGE SEVENTEEN (17)
_________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai Zahra a ciki daga bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa umarninsa,suka dira kofar gate din gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San Alhajin farin sani yayi sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka zagaya Gurin da Abban yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai tashin kamshi take Mai Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana bedroom dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same shi a can gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa.
Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya mikawa Abdul Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya umarci Mahmud daya zauna kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu, Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki shiru, gyaran murya Abban yayi kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a sun shafa Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya baka ni nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda yanayin rayuwa ya kaiku na baka ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a tare da kai, kullum addu'ata Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma Alhamdulillahi na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan iyayenta duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya Mata saboda Mai rauni ce, ka zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin Dana baka aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya kawo maka mafita a bisa lamuranka".
Suka amsa da "Amin"
Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa abinda Bai sabawa Allah ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas iyayensa da 'yan uwansa lokacin da Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta kewarku ki saka hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki komai Kika gani rubutacce ne daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take, ko shi mijin naki idan yayi nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake, to Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da iyaka ikon Allah ne kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske".
Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa aka.
Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa Kuma amana na karba na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu Albarka"
"To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata ki daina kukan Nan haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi Miki Albarka, ga makullin motarki wadda mukazo da ita takice na sai miki, kudin dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da ita nace ya juya Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati Mai zuwa za'a kawo Miki dayar ma".
Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan ya dawo ciki, a inda ya bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan hawaye suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya saka hankici Yana share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk ilahirin jikinta Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai sauke ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa sannan ya saketa Yana fadin " sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa na karamin yaro ne".
Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu da suke mallakinta, Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer"
Ya fice Yana ja mata kofa.
Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade a jikinta, doguwar rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan toilet ne, lokacin data shiga abin ya girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace tasan ba kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata tambaya? ta Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin.
Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen sofa taga wani stool kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara sallah.
Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta tashi ta fito har lokacin tana share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin data fada jikin Sajida ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya.
Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina kukan Nan ba da bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo Miki ba? ki Kuma godewa Allah a kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin taho kina kuka duk kin dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata fashe Dan ba haka suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya"
Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin mutum.
Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu tana fadin "wallahi bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min Sam duniyar bata mun dadi".
"Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 31