Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Wasa da gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin. "Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba.. "Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba, duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta. Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita" "Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon ba". Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara". ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI Strory & Written By Maman Fateemah Page 29 📖🖋️ _____ Sun jima a haka Yana lallashinta kafin ya dagota su tashi tsaye tare " me za'a bani nayi guzuri dashi?" Ya tambaye ta, shiru tayi kafin ta Dan watsa hannu tana Dan kallonsa ta gefen ido. "Ai kaga bamu kwana a gidan ba bare nayi maka wani Abu Saida idan biscuits din Nan Zan dauko maka sai ka tafi dasu na bada a sawo min wani". Dariya abin ya bashi ita bilhaqqi da gaske take fada Wai biscuits kamar wani yaro. "A'a niba shi nake so ba tsarabar da zan rike Ina tunawa da ita har na dawo". "Me Kenan?" Ta tambaye shi cikin nuna rashin sani. Jikinta ya matso sosai ya riko ta Yana kallonta da wani yanayi mai wuyar fassarawa, Bakinsa ya Kai Kan nata Dan bakin yasa Hannun ya talkafo kanta batayi zato ba tsammani taji harshensa na yawo cikin bakinta ya lalubo nata harshen cikin gentle yake tafiyar da ita ba kamar ranar nan ba, sun dauko Kusan minti biyar Yana Abu daya ji tayi kafafunta na neman gagarar daukar ta, jin jikinta na rawa yasa ya Kara mannata da jikinsa wani Nishi tayi ba Halin magana, kokarin yanye harshenta take daga Bakinsa Kai ya girgaiza Mata sai da yayi mai isarsa ya saurara Mata Kan gadonsa ta zube da gaske ya kashe Mata jiki ji take idan ta taka kafarta faduwa zatayi. Dan rankwafawa yayi saitin fuskar ta "Haba 'yan Mata be strong Mana me akayi da maza inji karya, taso muje ki rakani idan na biye Miki labarin salo ze canza". Ya kamo hannunta ya mikar da ita, jakar laptop dinsa kawai taga ya dauka, gyalenta wanda yake yashe a kasa ya tsuguna ya dauko Mata Yana rufa Mata a kanta. "Zaki bani Aron motar ki naje Kano da ita? amma fa saina dawo na dawo Miki da ita a airport Zan bada ajiyarta yanda idan muka dawo saina karba kawai". Kai ta gyada Masa alamar Eh. *A'a magana zakiyi idan kin amince to idan Baki amince ba na nemi hanyar Tasha kawai". "Ka dauka kaje da itan koka dawo ma na bar maka za'a kawo min wata ba kaji Abba ya fada ba". "Ke! Kinsan kudin ta kuwa zakice kin barmin Dan ki hau Abba ya saya Miki, Aron ma Ina laifi". Yaja hannun ta suka nufi kofar a falo ya tsaya Yana wasu 'yan dube duben da Batasan Kona menene ba sannan suka nufi harabar gidan, kasa hakuri tayi ta jefa Masa tambayar. "Wai haka zaka tafi ba kayan sakawa da takalma da sauran abun bukatu ne?" Dan shafa gefen fuskar sa yayi ya Dan furzar da iska daga Bakinsa. "Bana tafiya da Kaya ai wahala ce nasan duk inda zani akwai na sayarwa na saya kawai, aikin gane?"kallonsa kawai batace Masa komai ba. Saida yaje gurin Mai gadi ya bashi wata envelope sukayi maganganu sannan ya dawo gurin da take tsaye. "Zan tafi sai Allah ya dawo Dani, ki kula da kanki bana son yawo Amma idan gidan Ammah ne ko Aunty Hasana idan Bata koma Jos ba kina iya Zuwa". "To na gode, Allah ya tsare hanya ya bada sa'ar abinda akaje nema". "Allahumma Amin. Allah ya tsare min ke daga sharrin mutum da Aljani da dukkan abinda yake cutarwa, ya Ubangiji na bar maka amanar iyalina ka Zama gatan mu". Ya fada yana nufar motar, a hankali ta biyo shi ya bude ze shiga ta riko hannunsa ta Manna masa kiss a tsakiyar hannun. "Safe journey" ta fada da wata murya Mai rauni da gudu ta juya idonta fal hawaye. Tsaye yayi Yana kallon ta har ta shige ciki, ajiyar zuciya ya sauke kafin ya shiga ya tada motar jikin window ta tsaya har Saida ya fice daga gidan. ________________________ Tunda Mahmud ya bar cikin gari ya saki motar, rabon da yayi tuqi irin wannan har ya manta, kyakykyawar awa daya da minti arba'in da Tara ta kawo shi Kano, daga Hotoro NNPC sai ya shiga ta ring road ya fita 'yan kaba haka ya dunga yayyankewa har Zuwa round about na sani Baban kwari Sannan ya nufi Malam Aminu Kano international airport,Yana daf da shiga gate din ya saka face mask da glass sannan ya shiga, wayar Sameer ya Kira tana daf da katsewa ya daga. "Kana Ina? Na shigo yanzu ina fatan komai ya dai-daita?". Dan Jim ya yi yana sauraren sa. "Ok kazo ina parking lot inda ake bada ajiyar motoci". Ya sauke wayar Yana kalon masu Kai da kawowa. Yana Nan tsaye har sameer din ya karaso ya gaishe da Mahmud cikin girmamawa, jakar laptop din Sameer ya karba da key din motar ya nufi inda suke da alhakin karbar ajiyar, shi Kuma Mahmud ya nufi reception din. Sameer Bai jima ba ya dawo da takarda shedar bada ajiya, sun Dan tattauna kafin lokacin tashinsu yayi, zasu shiga screening ne Mahmud ya Kira wayar zahra, tana kwance a gado rungume da pillow bayan tayi kukanta Mai isarta ta lallashi kanta tunda Babu Mai lallashin gani takeyi shima kamar ya tafi kenan. Ringing din waya taji da sauri ta tashi Dan ita Sam tama manta da wata waya tunda ya Bata Bata karabi takanta ba, da sauri ta dauko tana duba waye ya Kira MM DANGE ta gani wani sanyi taji ya saukar mata, Picking tayi tare da sallama, sai kuma tayi shiru. "Zamu tafi ne nace bari na kira na fada Miki, ko zamu sake waya ze iya kaiwa jibi kada hankalinki ya tashi idan komai ya dai-daita Zan kiraki in Sha Allah". "Tom Allah ya saukeku lfy". "Allahumma Amin my precious, please take care bye". Ya katse Kiran yasan idan yaci gaba kuka zata saka Masa ya rasa wane irin idanu gareta masu saurin kuka. Sha biyu da rabi jirginsu na kamfanin air Max ya daga. Wayar tabi da kallo kafin ta aje kusa da ita, sai Kuma ta tashi kamar wadda aka zabura. Wayar ta dauko dubawa tayi wata baguwar number ta gani batayi kasa a gwiwa ba tabi Kiran Dan missed call ne tunna jiya. Cikin kankanin lokaci Kiran ya shiga Bata jima Tana ringing ba aka daga muryar matashiyar macece daga ji tana ji da ajinta sallama Zahra tayi Mata suka gaisa sannan zahrar tace Mata taga missed call dinta ne a wayar ta. "Missed call Dina gaskiya bani na Kira ba Amma Dan Allah wacece ke?. Yar dariya Zahra tayi kafin tace "sunana Fatima Zahra Muhd sani Ni mazauniyar Azare ce ta jihar Bauchi". Kit ta kashe wayar ta yunkura ta tashi, ta nufi kofa tana daf da fita taji wayar ta Kara daukar Kara ta dawo number dazu ce yi tayi kamar zata share sai Kuma ta dauka taji me zata fada Mata. Sallama tayi daga can ta amsa sannan ta Dora da fadin "Dan Allah kiyi hakuri da farko ban ganeki bane sai da Kika fada min sunan ki wlh nice na Kira bansan yanda akayi banyi saving number din ba matar oga Mahmud ko?" "Eh nice ke wacece?" "Sunana Fateeha matar Sameer Babban yaron oga jiya ne ya bani number yace na kiraki na gaisheka nayi Miki Allah Sanya Alkhairi sai Kuma ba'a daga ba, an Sha sauga bamuzo mukaga daki ba gashi har sun wuce China, amma in sha Allah idan suka dawo zamuzo indai ban haihu ba har lokacin" "Nagode kwarai da gaske,Amma naji kince China ba UK zasu Fara Zuwa ba? To can din zasu tunda kune masu tafiyar Amma na dauka da China zasu Fara tunda canne aka samu matsala sai Kuma Dubai, kinsan ogan naki ne kamar computer yake baya gajiya da aiki danma yayi wannan hutun Mai yawa sai Habibi ne yake wasu ayyukan". "Hakane kam aiya huta yanzu sai a Dora daga inda aka tsaya". "Ai gaskiya samun kamar oga Mahmud sai an tona". Basu jima ba sukayi sallama. Ta Dade a zaune tana jujjuya hirar su da matar Sameer, zamewa tayi ta kwanta tana duban sama a hankali ta furta. "Ubangji ga baiwar Mai rauni ka jibinci lamarina Kasan ko waye ka hadani dashi ka Kuma sakamin nutsu a tare dashi ban tabaji bana sonsa ba Amma lamarinsa Yana bani tsora na rasa alkiblar daya duba, Allah ka Zama gata na ka jibinci dukkan lamurana Dan Isar Manzon Allah s .a.w.w. Tashi tayi ta fita dakin nasa ta koma dauko tray din da Takai Masa break fast, duk wani Abu daya danganci kayan electronic sai ta kashe sannan ta fito tana gangarowa daga steps din corridor ne taji door bell din tana Kara alamar anyi Baki, a Kan dining table ta aje kayan ta gyara gyalenta ta nufi kofar. Budewa tayi sai sukayi arba da zilai Mai aiki da 'yar jakar kayanta. Cikin farin ciki Zahra ta karbi jikar kayan tana fadin "sannu da zuwa anti zilai".. Suka shige ciki murnar Zahra taki boyuwa itama zilan ba Karamin murna tayi ba lokacin da Ammah ta fada Mata zata zo ta Taya Zahrar Zama. Nan suka shantake suna Hira har Kusan karfe dayan Rana kafin Zahra ta raka zilai dayan dakin da ba cikinsa take ba ta aje kayan ta. Tambayar Zahra zilan tayi me zata dafa musu, "Ki dafa komai na ni harna manta wlh ashe ko break banyi ba, ga sandwich can ki dauka kada ya lalace, Zan shiga na Dan kwanta kafin karfe biyu" "To Allah kaimu" zahra tace "Amin"harta fara tafiya zilan Kira sunan ta tsayawa tayi har zilan ta karaso. "Uwar dakina Naga kamar wani mutum mun gaisa dashi ko Mai gadi kuka canza". ,"Eh Mai gidan ne ya canza shi wlh jiya lfy muka fita Amma yau muna dawowa ya sallame shi, wani ya Kira ya zauna Dani kafin ya dawo. "Wani Kuma daga Ina,?. "Nima ban san daga Ina yazo ba" Tab Allah kyauta ya kamata asan asalinsa gaskiya zamanin ne yazo da wata irin rayuwa sai godiyar Allah". "Wannan gaskiya ne". zahrar ta fad'a. Ita nufi bed room ita kuma zilan tana nufar kitchen. ✨✨✨ ✨✨✨ AUREN HUCE HAUSHI. Story & Written By Maman Fateemah. This page is deducte to the Family of late Alhaji Isah Musa bakin kasuwa kazaure. Innalilllahi wa Inna ilaihi raji'un! Ina Mika sakon jaje da ta'aziyya ga jama'ar garin MAJIA TAURA LG bisa ibtila'in daya samesu na gobara Mai Muni sakamakon faduwar tankar man petrol, Wanda yayi sanadiyyar rasa daruruwan rayuka Allah ya jikan wadanda suka rasu,wadanda Kuma suke gadajen Asibiti Allah ya tashi kafadunsu ya Basu lafiya yasa ya zamar musu kaffara ya kiyaye faruwar haka a gaba dan darajar manzon Allah s.a.w.w Page 30 _______Misalin karfe daya da rabi Mai a dai daita sahu ya sauke Asabe a bakin gate din gidan Zahra Dan yauma Saida taje can kauyen jama'are gurin wani mutum da wata kawarta ta tab'a fada mata shi, Nan ma ta karbo abubuwa Wanda za'a binna a gidan Wanda har abada Mahmud baze kara waiwayo garin Azare ba ko sunan jihar Bauchi ma Sai yaji ya tsane shi. Cikin karfin gwiwa ta karaso bayan ta sallami Mai Dan sahun tunda tasan Mai gadin Dan hannu ne dubu biyu ta Isa tasa yayi musu kowa ne irin aiki ne, iyakar ta tace masa na tsarin gida ne ze binna Mata saboda yau da gobe. Knocking tayi da Dan karfi tana mazurai ita ga uwar matar gida. Cikin takunsa na kakkarfa ya bude kofar gate Dan da hanzari tayi baya Dan ji yayi Kamar ze bangaje ta, kallo daya yayi Mata ya gane face din Dan hoton da oga ya nuna Masa yafi bada mahimmanci akanta Dan ita ce suspect dinsa ta farko, yasan da ita za'a yi amfani gurin isar da ko wane irin sako ne. Da hargagi Zayyan ya tunkaro ta. "Wa kike nema?" Duk daburcewa tayi nan da Nan jikinta ya dauki rawa. A'a Daman gurin matar gidan nazo munzo jiya ne basa Nan shine na dawo yau". Ta fada tana rawar murya. "Kama gabanki Nan ba wata mace a ciki gidan maza ne, idan Kuma Zaki shiga Bismillah tsuntsu daga sama gasashshe, Dan muna da kudajen da basa haram akan duk Mai tsautsayi, idan na Kara ganin giccinki a wurin Nan saina hadaki da karena yayi min fata-fata dake, wuceeee min daga nan" yayo kanta,da gudu ta kwasa ko waiwaye babu. "Stupid! Da gani wannan tsohuwar kwarkwar ce wlh Banda oga ya hana da kinci na jaki banza wato kin samu oga a araha shine kuka Neman zaku masa shegantaka akan matarsa ni na rasa yanda akayi ma oga ya Fado garin Nan,? Kuma har ya iya Zama a haka ba wani damuwa, ko Dan meze dameshi Yana tare da wannan danyan gold din". Ya fada Yana komawa bakin aikinsa Amma zuciyarsa fal tunanin abinda ogan nasa ya sani game da wannan matan daya turo Masa hutunan su ya Kuma shata musu dogon layi. Asabe Bata samu zarafin tsayawa ba Saida ta dangana da wani gurin me suyar kifi a bakin titi shima gani tayi gurin da jama'a ko cimmata yayi za'a ceceta, gefe ta koma tana mayar da numfashi sai lokacin ta dubi hanyar data fito ko Mai Kama dashi Babu. Gefen wani dutse ta zauna tana tunanin to koba gidan da sukaje jiyan bane tunda ba wannan basamuden suka tarar ba Amma daga Daren jiya Zuwa yau har lamarin ya canza ita damuwarta daya shin sakon da suka bayar ya sameta ko kuma na jiyan ba shine asalin Mai gadin ba yayi musu ta 'yan duniya ya barbe kayan da kudin ya wuce nasa gurin. Tashi tayi Kamar wadda aka tsikara ta dauki 'yar ledar data sawowa Mai gadin Dan abun tohiyyar Baki sai Kuma labarin ya canza salo. Harta dauko wayar ta Sai ta mayar idan tayi gigin fadawa Mama kwabarta zatayi ruwa Dan a yauma Saida Mana ta karo kudi masu nauyi tace a bawa Mai gadin yanda duk abinda za'a saka shi yaji baze iya gardama ba, to idan ta koma Mata da wannan labarin amshe kudin zatayi tasan halinta kayan ta, data Bata naira dubu gara ta bawa Dan tsubbu dubu hamsin, Sam Bata karuwa da ita saita wadannan hanyoyin idan ta aiketa tunda itace amintacciyarta ta Nan takeyin nata duk rintsi bazata so ta rasa wannan mafakar ba Dan Kusan da ita ta dogara gurin kwaramniyar yau da Kullum nata. ******* Saida Zahra tayi barci Mai isarta sannan ta farka lokacin biyu har da minti ashirin da hudu, da sauri ta Mike tana addu'ar tashi daga barci tayi mamaki ita fa gani tayi kamar barcin minti goma Sha biyar tayi Ashe lokacin ya ja haka, alwala tayi tazo ta Fara sallah bayan ta idar wayar ta da dauko Ummee ta Kira cikin shauki tun dazu ta nemeta network din na garin ba kyau sai hakura tayi, Bata jima ba tana ringing aka daga ba Ummeen bace wata ce ta daga tana ta yi Mata larabcin gargal ita kuwa zahrar na language yafi kwarewa a Dan daburce tayi Mata bayini ta gane Ummeen ta fita masallacin Annabi sallah tunda har lokacin suna Madina basu tafi ba Kuma a yanda sukayi daga Saudi Arabia Nigeria zasuyo gurinta, sallama tayi wa matar ta kashe. Number sajida ta lalubo ta syprus tasan zata Sha mita tun ranar da sukayi ways da wayar Amatu tayi Mata buyagi ta kashe Basu Kara waya ba, har tayi ringing ta katse Bata dauka ba, Bata hakura ba wani Kiran ta karayi shima Yana daf da ze katse aka daga. "Haba bestie Ina ta kira kin shareni ko har yanzu fishin ne?" Mai makon taji bestien sai muryar Fatima taji tana kwallawa Sajidar kira tana fadin "ku taho ga Amarya Zahra! Zahra" ta kirata da karfi tana murna kamar zata tsaga wayar, daya bayan daya suka dunga gaisawa suna ta korafin amarci Dadi ta Kama waya ta rufe wato Bata so a shigar musu rayuwa ko? Hakuri ta Basu tare da fada musu tayi missing din waccen wayar ne har sim din, sai daga karshe sajida ta karbi wayar. "'yar duniya wato kinji dadin lamarin ko Kika wani shareni, ni yanzu ai yallabai Mahmud ya fiki kirki kinsan ya kirani Kusan sau uku? Daman ko Baki kirani ba Zan kiraki dazu wurin Sha daya ya kirani Wai na kiraki na lallasheki yayi tafiya ya baroki kina kuka?". Ya fada tana kunshe dariyar ta. "Malama ki fito kiyi dariyar ki sosai kada ta kume Miki a ciki,da kike wani kunsheta". Dariyar tayi da gasken sai tayi Mai isarta tace. "Dan Allah bestie mekika bawa wannan guy din Kinga yanda yayi masifar macewa a Kanki? Wlh har tausayi yake bani Ni har mamaki nake idan ya kirani Yana min maganarki ranar Nan fa cewa yayi na bashi labarin zamanki a Nan syprus din wlh nayi zaton da Wasa yaki tunda nasan ba Karamin cajin kudi za'ayi ba. Amma haka na ware na rinka bashi labarin har na Gama ko a jikinsa, yanzu Ina aka tsaya da fatan komai ya dai daita? Dan nafi son dai dai lokacin ganawarmu muyi murna biyu graduation da naming ceremony". "Wlh Zan kashe yaushe Kika zama haka Mai bin kwakwkwafin jama'a? to bazakiji ba an fada Miki kowa ma irinki ne ai wlh ya Abdul Hakeem ya debo ruwan dafa kansa Dan nasan Dan bawan Allah saiya rinqa guduwa daga gidan" Wata irin dariya ta saki tana fadin "billahil Azeem gara wata wainar data wake yarinya gyara zancen ki idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma idan ana sallah ba'a magana". "Wlh sharri zakiyi Masa Amma shi dai salihi ne". "A inda salihai sukayi karanci ba". "Mubar zance kawai tunda abun ya Zama haka". Zahra ta fada tana cire hijabinta daga jikinta vest ce Fara Kal sai wando shima fari ai pink din kananun flowers gashin tayi parking a tsakiyar Kan ta kashe da band shima pink, sai fito baby sak. Gyara kwanciya tayi, tayi ringinnine da wayar a kunnenta Hira sukaci gaba da sajida yawanci duk akan auren zahrar ne. Sun dauki lokaci Mai Dan tsawo suna tattaunawa akan bututuwa da dama kafin suyi sallama, ta nufi toilet wanka take son yi kafin ta fita cin abinci. ******** Jirginsu Mahmud a Addis Ababa Bole international airport yayi landing, daki biyu Sameer ya kama musu Nan kusa da airport din tunda a kalla zasuyi Kusan three hours. Saida ya kaiwa Mahmud jakar laptop dinsa sannan ya nufi nasa dakin, bayan fitar Sameer Mahmud wanka yayi sannan yayi sallah maimakon ya kwanta ya Dan huta sai kawai ya bude wayarsa so yake ya ganta duk wani matsi da yayi tana manne da zuciyarsa so yake ya ganta kafin ya kirata. CCTV ya shiga ta wayarsa duk abinda akeyi ya rinka bi Yana gani yasha dariyar karon Zayyan da wannan matar wadda ko sunanta Bai sani ba, shi yasa ya dauko shi yasan shi kadai ne cikin amuntattunsa Wanda ze Masa wanna aikin ba tare da an samu matsala ba. Saida ya gama kallon ko ina na gidan yaga ba wata matsala, sannan yayi zooming din cikin bed room dinta daga ita sai vest purple da wando skintight kanta tayi parking da purple din band sai tayi wani irin kyau na musamman, kura Mata ido yayi Kamar ya warto ta yakeji, turare ta dauko tana fesawa a jikinta. Nan ya shiriri ce Yana kallonta knocking din da akayi Masa ya katse Masa abinda yakeyi, umarni ya bada a shigo Sameer ne sai ma'aikaciyar hotel din dauke da tray na abinci sai karairaya take shi har dariya abin nata ya bashi, me Kamar zahra yaushe irin wadannan zasu burge shi, bayan ta wuce ne ya dago ya dubi Sameer "kada ka qara zuwar min da irin wannan a rinqa bawa maza suna kawo min kawai". "Noted sir" Ledar dake hannunsa ya Mika Masa Mai tambarin wani boutique ne, sannan ya aje Laptop dinsa a kusa dashi Yana nuna masa wasu ayyukan da ya Gama yanzu, sun jima suna aikin kafin sameer ya fita saboda lokacin tashinsu ya kusa cika shi kuma Mahmud ya ciro kayan da nufin sakawa. Saida Zahra ta Gama feffesa turarenta sannan ta dauko after dress ta zura ta yane kanta da gyalen sannan ta nufo parlour, zalai ta samu tana 'yan goge goge duk da ba wani datti a gurin, gaishe da zilan tayi tana Mata sannu, ajiye mofar tayi "Allah ya taimaki uwar dakina ga abincin can nayi Miki abinda kikeso faten dankalin turawa da pepper soup din kifi" Zama Zahra tayi tana fadin "Kai Amma wlh na gode kwarai da gaske shi yasa nake yinki kinsa favorite Dina wlh". "Ai shi yasa na cewa Ammah kada a wani dauko yarinya tun daga Mubi Nima na isa na zauna dake saina kirawo Kanwata Alawiyya ta cigaba da yiwa Ammar kafin Allah yasa yallaban ya dawo, ai ni har zaman wanka ni zanyi Miki Koda kuwa bakwa garin Nan ne". Dan smile tayi kawai bata ce komai ba saima ta canza akalar zancen. "Ni Kuma Aunty zilai kin mikawa mutumin Nan abinci kuwa?". "Ai tunda na Gama na zuba na hada harda ruwa da lemo na mika Masa. Naga Dan gayu ne beyi kalar masu gadi ba". Dariya zahra tayi tana fadin "Aunty zilai kenan shi Mai gadi har Kama gareshi". Yana da kama Mana Wai Kinga wannan din?" Na ga wani dai dazu ban sani ko shine Wanda aka Kira jiya cikin dare". " Cikin dare Kuma?" Kai ta gyada "Mata kusan Hakan tunda Sha biyu ta wuce ya kirawo wani kawai umarni ya bashi yazo garin Nan da safe kinsan bakwai a Nan tayi mass nifa mutumin Nan wlh tsoro yake bani na kasa gane kansa". Dan murmushi zilan tayi tana kallon Zahra "kiyi hakuri uwar dakina a hankali Zaki San komai a kansa badai Kuna tare ba da sannu Zaki gane shi din waye, kici abincin sai muci gaba da hirar idan kin gwma". Bata k'i Shawarar zilan ba ta tashi ta nufi dining ita Kuma zilan ta nufi dauko Mata ruwa da mutuniyarta farm fresh, sai da ta Gama cin abincin sannan ta dawo parlourn gurin da tabar

Chapter 21 of 31