*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*33*
Hisham ya iso Zariya cikin tashin hankali, ana magrib yana shiga bangaren Magajiya.
Zaune take gefenta kuma Khadija ce tana duba mata wasu kayayyaki, Abdulmajid kuma na gefenta na hago.
Hira sukeyi da Abdulmajid sama sama, itakam Khadija bata sa musu baki a zaune kawai take tana aikin da aka sata.
Can cikin hirar tasu ne Abdulmajid ya kalli Khadija yace " ke dama inada magana dake."
Kallansa tai batace komai ba.
Fuskarsa a had'e yace " haryanzu baki daina zuwa b'angaren Abu Turab ba ko? Kina mace ko kunya."
Magajiya ce ta kalleta tace " Khadija me kenan?"
Kanta ta maida kan kayan tace " meye amfanin ma in naje tunda ba kulani yake ba?"
Dariya Abdulmajid yasa yace " kinji kunya wlh, kina mace kina bin namijin da baya sanki."
Zatai magana Hisham ya banko kofa cikin hanzari.
Jin yanda a ka bugo kofar yasa duk su ukun suka maida ha kalinsu kan kofar.
Hisham na shigowa ya kalli Khadija yace " bamu guri."
Mikewa tai tsam dan dama ba san zaman takeyi ba sai dai jikinta ya bata ba maganar arziki zasuyi ba.
Tana fita ta tsaya a jikin kofar d'akin.
Hisham ya kalli Magajiya cikin tashin hankali yace " Magajiya!"
Ita kanta hankalinta ya tashi ganin ita data aikashi maganar aure kano? Ya dawo mata a haka?"
Kallansa tai tare da tattara hankalinta kansa.
Yawo ya had'iya sannan yace " yaran nan yana gani Magajiya."
"Yaro? Wani yaro kake nufi kenan?"
Yace " yaron nan mana da baya gani."
Idanu tad'an juya tace "wai wani yaran kake nufi? Nibansan wani yaro ba."
Abdulmajid ma yace " wani yaro kake nufi Kawu?"
Hisham yace " Yarancan Abu Turab."
Dariya Magajiya tai tace " Waziri? Ko dai gajiya ta fara ratsaka ne? Me kake san fada takamaimai?"
Hisham ya kallesu cikin wani yanayi yace " Wlh da gaske nakeyi, yarancan Abu Turab idanunsa garau suke."
Abdulmajid ya mike tsaye yace " ni wlh na dauka maganar arziki zaka fada ashe tsokana kazo da ita, ni nayi masallaci."
Hisham ya kalli Magajiya yace " Magajiya na taba miki karya akan harkar dana san bazata amfanemu ba?"
Wannan lokacin kam ta kalleshi kallan nutsuwa, Abdulmajid ma ya ja ya tsaya.
Khadija kam da baya da baya ta juya tai waje cikin tashin hankali, me kenan?
Hisham ya kalli Magajiya sannan ya kalli Abdulmajid yace " dayaje kano a garau yaje musu."
Magajiya ta kanne idanuwanta tace " ban fahimta ba."
Nan Hisham ya zayane mata kaf abinda ya faru na zuwansa.
Tashin hankali karara ne ya bayyana a idanun Magajiya, kallansu tai cikin tashin hankali tace " ku bani guri."
Nan suka mike suka fita.
Abdulmajid ma bangarensa ya wuce cikin d'emuwa da rashin sanin abinda zaiyi.
Shi kuma Hisham yai waje.
Magajiya ta kasa zaune ta kasa tsaye ba shakka in har hakan ne lalai kaf duniya ba wanda ya taba rainamin hankali irin yaran nan.
Kwallawa wata mai kula da ita tai, cikin hanzari ta iso.
Bata ko juyo ta kalleta ba tace " kiramin Abu Turab."
To tace kawai tai waje itama.
Abu turab yana zaune kan sallaya tilawa yakeyi cikin daddadan muryarsa, yau ko masallaci bai je ba dan bayasan ganin kowa.
Garzali ya mai sallama, sai daya kai aya sannan ya amsa mai.
Garzali ya matso ya tsugunna sannan ya sanar dashi sakon Magajiya.
Ya dade kafin yace " ace mata ina zuwa."
Nan yai waje.
Sai dayai sallar isha'i sannan ya mike ya fito, Garzali ya mikamai Sandarsa wacce Lantana ta kawo.
Amsa yai sannan yai gaba Garzali yabi bayansa.
Bayan an mai iso ya zauna a kilisarta sannan ta shigo cikin takamarta.
Idanu ta kafa mai har ta zauna shikam fuskarsa a had'e take yana zaune kansa a kasa.
Bayan ta zauna ne ta kalleshi tace " Abu Turab ka iso?"
"Barkanki da warhaka Umma Babba."
Murmushi ta sakarmai sannan bata amsa ba tace " kiranka nai in baka wani labari."
Shima bai amsa mata ba dan lalai ji yake bazai iya kallanta ba saboda tsananin tsana.
Magajiya tacigaba " Wani dan tsakone kurma ya taso karkashin kulawar kura, ita kurar dama tanada nata d'an hakan yasa ta had'asu duka ta rike, a kwana a tashi sai kurar nan ta tsufa, ta fahimci dole tana bukatar barma d'anta mukaminta a daji.
Kasan abin mamaki?"
Abu Turab ya d'ago suka had'a ido, bai d'auke idanunsa daga cikin nata ba yace " bazai wuce wannan d'an tsakon kurma yace shi yake san aba wannan mukamin ba."
Ta kuramai ido itama tace "Haka! Ashe ka harbo jirgin, sai dai kasan wani abun tsoro a labarin?"
Kallan ban fahimceki ba ya mata tace " Tun daga sanda Kurar nan ta fahimci kudurin wannan d'an tsakon har yau ba wanda yasan inda wannan d'an tsakon yake."
Wani lalausan murmushi ne ya bayyana a fuskar Abu Turab yace " sai dai ban fahimci abu d'aya ba a labarin, d'an tsakon dama can kurma ne ko kuwa yayi hakan ne da saninsa ya noke bakinsa?"
Idanun Magajiya ne suka d'an canza sai dai da sauri ta maida fuskarta cikin yanayin hankali a kwance tace " hmm wannan shine abinda ya sa kurar nan dana sani."
Gani tai ya saki wata yar karamar dariya har hakwaransa suka bayyana ya kalleta yace " Tuba nake Umma Magajiya, na saki a duhu danai na nuna miki nidin bana gani."
Wannan karan kam duk yanda taso ta b'oye bacin ranta ta kasa, karara ya nuna a fuskarta.
Abu Turab ya rangwadar da kai yace " umm ya zamuyi yanzu?"
Tace da me kenan?
Yace " dan banaji zan iya yafemiki."
Kallo tamai cikin mamaki tace " bakaji xaka iya yafemin kamar ya kenan?"
Fuskarsa ce ta canza idanunsa sukai jaa, ya kalleta yace " bazan taba yafe miki ba daga ke har yayanki, abinda yama yayan mahaifiyata da matarsa da ke da kika umarceshi a sanadiyar kokarin rabani da duniya da kukai kuka jamusu mutuwa, ni Abu Turab in har Basira da Abdussamad sune suka haifeni sai na sa an muku hukunci daidai da laifinku."
Wata muguwar dariya ta saki, wanda ya sashi tsayawa yana kallanta tace " kai a suwa kenan?"
Yace " a wanda yake da damar zama Sarki."
Ta ja tsaki tace " Shekaruna d'aya da mahaifinka, hakan na nuna nid'in batayau bace, ba kai ba hatta mahaifinka bai isa yaja dani ba."
Abu Turab ya d'an juya bakinsa sannan ya had'a lab'ansa yace " well, shi daban nid'in daban, mu zuba mu gani."
Tace " shikenan mu zuba mu gani, na baka sati biyu kacal, ina zaune anan zakazo gwiwowinka biyu ka nemi gafarata."
Yace " ina fatan hakan ta kasance."
Kallan juna sukai, kansa ya saukar kasa ya juya kansa gefe tare da d'aukan sandarsa yace " Umma Babba nagode ni zan wuce, ki huta lafiya."
Kallan mamaki tamai, gani tai ya sa sanda a gaba kamar makaho.
Idanu ta kuramai har ya fita, ta murmusa tace " hmm a kashi 100 na baka 40, ba laifi ka iya b'oye fuskarka da abinda ke ranka, ko dayake d'an Abdussamad ne."
Fuskarta ta kuma had'ewa tace " kai har ka isa? Kamar ni? Kamar ni Magajiya ka rainan hankali?"
Kwafa ta saki.
Abu Turab kam na fita ya juyo ya kalli bangarenta sannan ya juya ransa a b'ace.
*********
Itakam Khadija ta shige d'aki ta kwanta akan gado, me ke faruwa? Ya Turab yana gani? Anya kuwa? Ta yaya? Yaushe?
Itakam ta kasa yarda da abinda taji, ba dai wani sharrin zasu kullama bawan Allah ba?
Da sauri ta mike zaune tace " dole in fadama Yaya gobe akan abinda sukace."
*TEAM ABU TURAB🤝🏻*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*34*
Washegari.
Da safe zaune yake a gaban Mai Martaba a cikin Turakarsa.
Mahaifinsa ya kalleshi cikin kulawa yace "Turab me yasa ka dawo tun jiya? Sannan tundaka dawo baka zo ba."
Fuskarsa a d'aure take dan sam ba fara'a a cikinta kallansa yai yace " Dama zuwa nai na sanar dakai zan auri Bilkisu yar gidan Sarkin kano."
" Alhamdulilah nagode kwarai na kuma ji dadi daka fahimceni."
"Bayan umarnin auranta daka bani a yanzu auranta yana tattare da amintata, a da auranta zanyi saboda umarninka, sai dai yanzu zan aureta ne dan kaina."
Fuskar mai martaba ta kara fadada da farinciki yace "naji dadi yanda kuka fahimci juna."
Kallan Mahaifinsa yai yanajin wani radadin takaici a ransa, yace " zan koma."
"Abu Turab!"
Komawa yai ya zauna sannan ya kalli Mahaifinsa dan yanda yaji ya kira sunansa yasan yana bukatar nutsuwarsa.
Mai Martaba ka kalleshi cikin kulawa yace " Abu Turab me yasa kake so ka b'oyemin abinda ke ranka? Me yasa bakasan mudinga raba damuwar dake zuciyoyinmu?"
Shiru yai sai dai zuciyarsa tadan raunana.
Sarki yace " Meke damunka?"
Shiru ya kuma yi sai dai a wannan karan ya d'ago ya kalli mahaifinsa da idanunsa da suka canza launi.
Sarki ya cigaba" Shikenan mubar maganar inhar zuciyarka bata san inji."
Abu Turab yace " zan koma Abba."
Mai Martaba ya murmusa yace " to Turab."
Mikewa yai ya fito daga bangaren mahaifinsa, ba shakka yanasan ya sanar dashi damuwarsa da kuma neman shawararsa sai dai ba yanda zaiyi domin kafin ya kasance mahaifinsa sarki ne shi a wannan garin dole kuma yai abinda ya dace a matsayinsa na sarkin garin.
Bangarensa ya nufa rike da sandarsa yana gana Garzali da wani na gefensa.
Sunsha kwanar da zata kaisu bangarensa yaji muryar Khadija tace " Ya Turab."
Haka kawai ta samu kansa da kin tsayawa dan abinda Mahaifinta sukamai bayaji ko ganin Khadija yana kaunar yi a wannan lokacin.
Ganin bai tsaya ba yasa ta kara sauri, har tazo inda suke, tace "Ya Turab."
Tsayawa yai sai dai bai juyo ba.
Gabansa ta dawo ta kalli Garzali tace " dan Allah kudan matsa kadan zanma Ya Turab magana."
Nan suka gaisheta suka matsa.
Kallansa tai tace " Yaya."
Bai kalleta ba sai dai yace " ya akai?"
Tace " yaya kana ganina?"
"Me kike nufi da hakan?"
Ta kara matsows tace " Yaya ninasan baka ganina, sai dai na rasa dalilin Abba na na zuwa ya fadama Magajiya wai kana gani."
Kallanta yai, ta kalleshi hakan yasa ya kauda idanunsa, tace " Yaya Please ka kula da su wlh sam hankalina ya kasa kwanciya dasu, na tabbata da abinda suke shiryama."
Jitai yace " yanzu kinaso ki cemin zuwa kikai kiban shawara akan kula da Mahaifinki? Ko kuwa zuwa kikai ki sanar dani Mahaifinki zai cutar dani?"
Cikin rashin fahimtar kalamansa tace " Ban fahimceka ba..
.."
" in mahaifinki zai cutar dani tayaya nake da tabbas din ke bazaki cutar dani ba?"
Kallansa tai a zabure cikin tsananin mamaki tace " Yaya."
Yace " da mahaifinki da ni wanene mafi kusanci dake? Wanene wanda yake jininki? Tayaya zan yarda zaki juya ma mahaifinki baya akan wani makaho wanda bakuda hadi dashi?"
Gaba daya ta ma kasa magana dan batada amsar da zata bashi, tana neman amsar da zata bashi taga ya fara tafiya.
Idanunta ne suka ciciko a hankali wasu zafaffan hawaye suka xubo mata, me yaya yake nufi?
Gani tai ya tsaya a jikin kofar bangaren Mahaifiyarsa da alama magana yake da wani, gani tai ya saki fuska ba kamar yanda ya cukule mata ba.
A hankali ta tako har gefen da suke.
Mairo ta gani a tsaye a gun rike da kula suna magana, juyawa tai zuciyarta sam ba dadi.
A bangaren sa kuwa, bayan ya taho daga gun Khadija zai wuce yaji tace " Ya Ina Kwana?"
Juyowa yai ya kalleta yace " Mairo kece?"
Tace " nice, Umma ce ta sani in kawo mata abu yau da safe."
Murmushi yai yace " Mairo kinaji da Umman nan."
Ta kalleshi tace " Da cemaka akai Ummanka ce kai kadai?"
Kallanta yai yace " Yar gidan Umma ce ke dama ai."
Zatai magana yace " ki gaisheta."
Tace " bazaka shiga ba?"
Kallanta yai fuska a sake yace " Later."
Daga nan yai gaba.
Kallansa tai cikin mamaki dan taga ba haka suka saba ba.
************
Abdulmajid ne zaune gun Magajiya yace " Umma ya kukai Jiyan? An bincika yana ganin?"
Magajiya ta kalleshi tace " Abdulmajid, ka nutsu sosai kaji abinda zan fada ma."
Kallanta yai sannan yace " inaji."
" Ka shiga hankalin sosai da Abu Turab ka daina masa kallan wanda bashida wayau ko bai san komai ba, wlh wnnan yaran hmmmm"
Tai shiru sannan tacigaba " kadai bi a hankali karka kuskura ka fada tarkwansa."
Abdulmajid ya dan tabe baki yace " ni Umma har wannan yaran ya kai in shiga hankalina a kansa?"
Ta kalleshi cikin isarta sannan ta ce " Abdulmajid kenan."
Kara tabe baki yai yace " ni Umma dama maganar aurena nazo muyi, nace tunda dai Bilkisu an riga an hadata da Turab mai zai hana mu juya akalar auran kan Mairo."
Ya karasa maganar yana dan sosai keya.
Kallansa tai tace " Mairo? Wacece hakan?"
Yadanyi kasa dakai yace " Mairo 'yar gidan Barde."
Barde?bakada hankali ne?"
Yace " Umma to...."
Katseshi tai cikin fada tace " nimeyasa baka tunani ne a al'amuranka? Abu Turab zai auri Gimbiya Bilkisu kai kuma dan hauka kacemin wata Mairo? Me yasa ne bazaka dinga abu da tunani ba?"
Fuska ya hade dan maganar ta batamai rai, Magajiya ta cigaba " kada ka kuskura ka karamin wannan banzan zancen."
Tana kaiwa nan ta maike tai ciki.
Kallo ya bita dashi da alama zai je gun Sarki ya fadamai kuwa dan shi kam Mairo yakesan aura ko ta wani haline kuwa, dan kwanan nan har mafarkinta yake wai sunyi aure.
🤣
**************
Kwana biyar da dawowarsu kuwa Mai Martaba Sarki Shu'aib mahaifin Bilkisu ya aiko mutane daga Masarauta akan amincewa da aure da sukai.
Wannan labari ya tadama Khadija hankali, sai dai duk yanda taso ganin Abu Turab abin ya faskara, itadai ba dama ta shiga bangarensa dan ya bada umarnin hana kowa shiga bayan Mahaifiyarsa, sannan ko a waje tadaina ganinsa.
Mairo ma wannan labarin ya d'aga mata hankali, sai dai ba yanda zatai dan dama ta riga tasan komai.
Yau ta gama aikin gida kenan tana 'yan kukuninta na takaicin abinda ake sata yi, wani yaro ne yazo ya sanar da ita ana san ganinta a waje.
Hijab dinta ta ja ta saka dan bata kawo saurayi bane ko wani na kunya ba.
Mamaki ya kamata kwarai ganin Abdulmajid a tsaye a jikin soron gidansu.
Kallansa tai cikin mamaki sannan ta karasa gunsa tace " Malam lafiya?"
Abdulmajid ya kallesta kalleta yace" Mairo ina kika shiga ne? Sam na daina ganinki dole kika sani na zaro jiki na fito."
Kallan sa tai tace " ban fahimci inda ka dosa ba."
Yace " Kin manta me nacemiki ne? Na dauka na sanar dake kedin matata ce."
Dariya ta saki tace " Matarka? A yaushe kenan akai hakan? A iya tunanina ban amshi sadakin ka ba."
Idanu yadan rage yace " An kusa ai indai wannan ne, inkuma kinaso in baki yanzu to."
Ka bani yanzu? Da alama tunanin ka ya fara tafiya ko?
Matsowa yai a zuciye hakan yasa ta matsa da sauri sannan ta nunashi da hannu tace " Stop Malam! Tsaya anan karka kuskura ka tabani."
Kallanta yai rai a bace yace " Mairo."
Tace " kwarai kuwa sunana Maryam wacce ake cewa Mairo yar gidan Barde kanada magana ne?"
Kwafa yai sannan yai murmushin mugunta yace " ina tausaya miki yarinya randa kika zo hannu."
Baki ta murguda tace kafa zanzo ba hannu ba.
Ta juya tai ciki ranta a bace.
Murmushi ya sakeyi sannan ya juya.
*TEAM ABU TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*35*
Wata yarinyace wacce bata wuce shekara goma sha hudu ba ta, kana ganinta kasan yarinyace da take aiki a gidan duba da yanayin kayan jikinta.
kwankwasa kofar tai mai kula da kofarsa ya bude tare da tambayar ta me ya kawo ta.
Yarinyar mai sanyi ce kana ganinta kuma kaga shiru shiru, kanta a sunkuye tace " Yarima Turab ne ya umarceni da inzo."
Yace " to, shiga."
Nan ta wuce ta shiga, yanata mamakin abinda ya kawota da magrib din nan.
Ka idar rayuwar Abu Turab in yai sallar Magrib to sai yayi Isha'i yake tashi, sannan kwanan nan saboda bayasan haduwa da kowa yasa ko masallaci ma ba zuwa yake ba, sai dai yai sallah a gida yai tilawarsa.
Yarinyar nan tana shiga ta zauna a cikin falon da ba kowa sai shi dake zaune daga can gefe kan sallaya yana karatu.
Falon ba wani haske gareshi ba, in ba gabansa dake d'auke da fitila kusa da al_qur'anin sa ba, ya kashe fitilun ne saboda kar a fahimci idanunsa yana gani, sannan karatun ma bada karfi yake yi ba.
Yarinyar tana zaune a bakin kofa har sai dataji kiraye kirayen sallar isha'i sannan ta mike ta fito, sam Abu Turab bai ma san da zuwanta ba, balle fitarta.
Haka yarinyarnan ta d'au kwana hud'u tana wannan zuwan, kullum kuwa ana magrib take zuwa.
Mai gadi kofar kam kullum yana mamakin wannan abu, sai dai bashida ta cewa dan da Abu Turab bai yarda da zuwanta ba tabbas da ya haneshi da barinta ta shigo sannan da ita kanta ya koro ta.
Yau ne kwanan ta na hud'u da fara zuwan, kamar yanda tasaba zama a kofar yau ma haka tai, sai dataga an dade da sallar magrib sai ta tsiri rage kayayyakin jikinta.
Ta rage daga ita sai wata yar bes sai zanin dake jikinta, kara ta saka tare da fad'uwa kasa.
Abu Turab dake karatu ya mike da sauri tare da tahowa inda yaji karar, ganin mace yai a kwance tanamurkususu sam bai kula da jikinta ba ganin yanayin da take ciki, da sauri ya karaso ya d'agota yana tambayarta abinda ke damunta, juyi kawai take tana wash wash.
Masu kula da bangarensa kuwa suna zaune suna hira sukaji wannan karar nan suka taso da sauri.
Shigowa sukai ganin duhu yasa Garzali ya kuna fitila dan sun dauka wata matsalarce ta faru jin yanda Abu Turab ke cewa lafiya? Ita kuma tana kiran wash.
Haske ne ya bayyana a d'akin me zasu gani? Abu Turab ne rike da yarinya, gashi cikin duhun nan yarinyar tai amfani da damar ta ballemai botira guda biyu na saman rigarsa.
Gaba d'aya turus suka tsaya cikin tashin hankali me zasu gani? Meke faruwa?
Abu Turab ne ya kallesu sannan ya kalli yarinyar dan sai a lokacin ya kare mata kallo.
Sai kuma a lokacin ya fahimci sharri ne akazo a kula mai.
Mikewa yai tare da hankad'e yarinyar, ita kuma ta hade kafafuwanta tasa kanta a ciki tasa wani irin kuka.
Zaiyi magana sukaga an bud'o kofa.
Abdulmajid ne, gefensa kuma Galadima.
Kallan sa Galadima ya shiga yi cikin mamaki da tsana yace " ashe dama abinda ake fadamin da gaske ne? Lalai ka zubar da mutuncin masarautarmu."
Abu Turab ya kalli Abdulmajid wanda yad'an juya yana dan murmushin mugunta.
Galadima ne yacigaba da cewa " Yanzu Ka kyautama mahaifinka da mahaifiyarka? Kana makaho? Ace har da neman mata? Wa'iyazubillah, dolene gobe a zauna saboda kai, ko kuma yanzu ka wuce muje gun Mai Martaba tun kafin magana ta fita."
Abu Turab ya jujuya sannan yace " Galadima?"
Inajinka.
Abu Turab yace " ina neman alfarma."
Tame kenan?
"Inaso ka taimaka muje gun Mai Martaba a wannan lokacin, sannan mu tafi da yarinyarnan, a kuma taimaka a kira mahaifiyata da kuma Umma Magajiya dan su zama shaidar abinda zai faru."
Galadima yace " dama ai canzamu yanzu, ya kalli Garzali yace " jeka kira Magajiya da Mamansa."
Nan yai waje.
Galadima yace " muje."
Haka suka isa gun Mai Martaba lokacin yana zaune bayan ya dawo daga masallaci.
Bayan Zagi ya nemarmusu uzuri sun shiga.
Mai Martaba ya kalli galadima yace " Galadima lafiya?"
Kallan Abu Turab yai sannan yace " ba lafiya ba sai dai muna jiran isowar shaidu kafin a fara shari'a."
Sun dan dade a zaune kafin Basira ta fara isowa sannan Magajiya wacce hankalinta kwance ta iso dan dama jiran kiran take in kuma ba'a kirata ba tana jiran labarin korar Abu Turab ko kuma killaceshi da hanashi fita daga bangarensa, a kuma hana kowa ganinsa.
Bayan kowa ya hallara Galadima ya sanar da duk abinda ya faru ga Mai Martaba.
Tashin hankali ne karara ya bayyana a fuskar Basira.
Magajiya ta kalli Galadima tace " Galadima me kake san kafad'a? Kana tunanin Abu Turab keta mata hadi yai ko me? Na san halin Turab bazai yiwu ba abinda ka fada sannan ta ina ma zai fara yin lalata bayan idanunsa ba gani suke ba?"
Abu Turab ya saki wani murmushi yace " Haka ne Umma Babba ba gani nake ba tayaya zan kama yarinya ta karfi in keta mata hadi?"
Abdulmajid ya kalleshi yace " bayan kamaka da mukai?"
Abu Turab yace " ina yarinyar?"
Nan Galadima ya kirata.
A jikin bango ta takure kana ganinta a ido kaga salaha.
Abu Turab yace " ba gani nake ba sai dai ina fatan yarinyar tana nan?"
Sarki yace " tananan me zaka ce mata? "
Abu Turab yai kasa dakai yace " Tuba nake ranka ya dade sai dai ina bukatar yi mata tambayoyi."
Nan Sarki ya bashi dama.
Abu Turab yace " baiwar Allah ya sunan ki?"
Tace " Zulaika."
Yace " Zulaika kin san ni?"
"Eh yarima Turab sunanka."
" Me yake kawoki bangarena?"
Kuka ta saka tace "kaine ka ce indinga zuwa duk bayan magrib."
Abu Turab yace " gaskiya ne, amma a ina muka hadu na fada miki haka?"
Tace " a waje ranar ka fito."
Allah sarki me nake miki in kinzo?
Kuka ta saka hakan yasa Sarki yace " karki damu sanar dani duk abinda yake miki.
Tana kuka tace " tatabani yakeyi ya cire min....
."kuka ne yaci karfinta hakan yasa tai shiru.
Abu Turab yace "Galadima a ina kaga yarinyar nan da ni?"
Galadima yace " a falon ka mana."
Abu Turab yace " waya taba neman mata na lalata a sarari? To ko mata tace ya kamata a ganni da ita a falo?"
Galadima yai shiru, Sarki ya katseshi da cewa " in idanun ka ya rufe da alfasha fa?"
Kai ya jinjina yace " haka ne sai dai inada tambaya ga yarinyar, ni ba gani nake ba wanda kowa yasan da haka, ta ina zan iya janyota? Ko ince ta ina zan iya mata karfi?"
Sarki ya kalli yarinyar yace " bashi amsa."
Tana kuka tace " kirana yake yi."
Abu Turab ya ce " Umma babba yi mana shari'a aa nan an ganmu a farko farko gaba da kofa kadan sannan tace kiranta nakeyi me zakice?"
Magajiya wacce tunda ya fara tambayoyinan ranta yake a b'ace tsananin mamakin rainin hankalin dayake musu yasa tama kasa magana, makaho? Wanda kowa yasan da hakan? Kallansa tai jin tambayar daya mata tace " gaskiya ne wannan abin dubawa ne galadima."
Abu Turab yace " Umma babba dan Allah inada tambaya, in har yarinyar nan ta karfi nake mata me yasa ba'a taba jin kararta ba sai yau?"
Magajiya ta kalleshi zuciyarta fal bakin ciki amma a fili tai murmushi tace " Gaskiya ne Turab wannan ma abin dubawa ne."
A ransa yace "Hajiyar Poker Face."
Abu Turab yace "Galadima in har lalata nake da yarinyar nan ta yaya za'a ganta a nuste ina nufin kayanta da kuma d'an
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 37