Kai ya girgiza yace " ba wai saboda shi bane, ni raine bazan iya gani a d'auka ba, Allah ne kadai ya isa yin wannan."
Cikin isa yazo ya wuce ta gun Abu Turab ko kallansa baiyi ba, shima Abu Turab ganin haka ya juya mai baya, Abdulmajid na zuwa ya bud'e had'adiyar motar Sarki wanda ya bada dan tafiyar Ango ya shiga.
Sannan ya kallu mai tukawar yace " mu tafi."
Kallansa yai yace " Ranka ya dade amma ai....."
Katseshi yai cikin fada yace " ina sasa dakai? Ko kanasan yanzu insa a kulleka?"
Da sauri ya shiga motar ya tada.
Yai gaba, Turab yana kallan sanda Abdulmajid ya shiga sai dai bai d'auka tafiya zaiyi ba.
Ganin sunyi gaba ya bi motar da kallo, lalai Abdulmajid, wannan kuma wani sabon wulakanci ne?"
Sabi'u ne ya kalleshi yace " kaga mai ya faru?"
Turab yamai alama da hannu yace " yai shiru kar aji, ba komai shi ya tafi a motar sa."
Sabi'u yai kwafa yace " amma wancan anyi mara mutunci wallahi."
Turab ya wuce ya shiga motarsa sukai gaba.
Tafiya suke sai dai gaba d'aya hankalinsa ya kasa kwanciya.
Me Magajiya take shirin yi? Yayi niyyar zuwa gunta kafin ya fito sai dai bangarenta taf yake da mutane.
Abdulmajid kam tafiya kawai sukeyi su biyu a mota, ya tabbatar duk wani abu da zatayi daga kan hanya zata yishi.
Sunyi nisa da tafiya wajen jeji kawai sukaga an tare gabansu.......
*TURAB😌*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*70*
Motar suka kalla da kyau da yanda aka nuna musu suka tabbatar itace, tsaida motar sukai ta hanyar tsayawa agaban titin tare da manyan sanduna da makamai.
Tsoro ne ya shiga jikin Abdulmajid l, shikansa driver din ya tsorata sosai.
Katon cikinsu ne ya bud'e motar ya cillo da driver din waje shikuma ya shige ciki.
Nan yaja motar sukai gaba, can cikin wani daji suka shiga dashi.
Abdulmajid ya kasa magana sai tsantsar fargaba dake damunsa, me ya kaishi? Amma dagaske su Umma abinda sukai shirin yima Abu Turab kenan? Lalai shikam yasan kwanansa ya kare, ashe bazasuyi sallama da Maironsa ba zai tafi kabari, dan tunda yaji wannan maganar a d'akin magajiya bai ko kara zuwa yaga Mairo ba.
Sai da sukai tafiya mai nisa sosai, wani gida ne kwaya d'aya a tsakiyar dajin, gida ne karami, mutumin ya tsaida mota ya bud'e bayar motar ya fizgo Abdulmajid.
Yana shiga ya cillashi ciki da karfi, jikake gum, ya buge, jikinsa ne ya shiga rawa ganin ba imani ko kadan a idan wannan mutumin, jawo kofa yai ya rufe, bai dade da fita ba yaji karar wata mota da alama ragowar ne suka iso dan ihu yaji sunayi kamar tab'abu.
Tsoro ne ya kara shigarsa, idanunsa sun firfito da tsananin tsoro.
Jiyai an banko kofa da karfi suka shigo.
Ogan cikinsu ne yazo inda yaje ya d'aga sanda ya makamai a kafa da karfinsa.
Wani mugun kara Abdulmajid ya saka wanda sai da dajin yai kara, tsananin azabar dayaji je yasa yasan anma kafarsa illa babba.
Zufa ta ko ina take ketomai, hawaye ne ke zubomai sosai saboda rad'adi so yake ma yace musu su kira wanda yasasu aikin dan ba shi bane amma ina...Azaba ta hanashi magana sam.
Murkususu yakeyi, ogan yasa dariya yace " ance mu wahalar dakai kafin mu shekaka bar zaho."
Suka tuntsire da dariya......
**********
A motar Abu Turab kuwa tafiya suke amma gaba d'aya hankalinsa ya kasa kwanciya, sai dayaga sun isa kano sannan yaji ya d'an samu sauki kadan a ransa.
Yana isa ya tadda masallacin masarautar nan taf take da jama'a, sai kiranshi ake suna gaisawa da mutane.
Har Saif ya gani a gun taron, sai dai kallo d'aya yamai ya d'auke kai yai kamar bai ganshi ba.
Yanda Hisham yai a sanda yaganshi yasa yasan da wani abu, kusa da Hisham ya karasa yace " Waziri lafiya?"
Shidai Hisham yana bayan motar sarki kadan, saboda dama anyi daga zarar motar ta fito tayi gaba sai ya bisu a baya, yana kallan aka cilar da driver din sannan wanj ya shiga yaja motar, sannan yayo gaba.
Kallan Turab yai a razane yace " motar Sarki ba a ciki ya kamata kazo ba?"
Turab yace " a ciki ne amma Abdulmajid.........."
Yanda yaga idanun Waziri sunyi ne yasa ma ya kasa karasawa, kallansa yai yace " ya akai kasan a motar sarki zanzo?"
Hisham kam baimasan me yake cewa ba shidai juyawa yai da sauri zai fita.
Turab yasa hannu da sauri ya riko rigarsa yace " ina Abdulmajid?"
Hisham ya gama rikicewa kai kawai yake girgizawa.
Turab yace " ina Abdulmajid?"
Hisham ya fizge rigarsa yai waje da gudu.
Sabi'u ya taba yace " yi sauri kabi Waziri kaga ina zaije." nan sabi'u yai waje.
Turab nan ya dunga kutsawa cikin mutane yana neman Abdulmajid sai dai bashi ba labarinsa.
An d'auran Auren Gimbiya Bilkisu da Yarima Abu Turab a ranar Asabar da misalin karfe goma sha d'aya na safe, a massalacin dake gidan sarki na kano.
Abu Turab kawai dai yake yakeyi amma gaba d'aya hankalinsa baya jikinsa, meke faruwa?
Hisham kam mota ya shiga ya dinga zabga gudu, sabi'u na bayansa yana ta binsa, a ransa yace " ko dai zariya zai koma?"
Har yai tunanin juyowa ganin suna ta tafiya ba tsayawa, gani yai ya gangara ya sauka daga kan titi ya nufi wani lungu cikin daji.
Tsayawa yai yana tunani kafin ya ajiye motar ya fito yabi bayansa cikin dajin, dan ya tabbatar inyashiga da mota hisham zai ganshi.
Hisham na isa wannan d'an gidan ko kofar motar bai rufe ba ya fito cikin hanzari.
Buga musu kofa yai tayi da karfi sai dai ba alamar kowa a ciki.
Ya gama rikicewa gaba d'aya dan ya gama sadaukarwa an gama kashe mishi d'a, zama yai a waje kawai yasa wani irin kuka.
Sabi'u ne ya karaso duk ya gama gajiya, hango gidan dayai ne yasa ya tsaya, Hisham ya gani a zaune yana baza wani irin kuka.
Boyewa yai jin shewar mutane, Hisham na jinsu ya taso a zabure ya cakumi wuyan ogan cikin su yace " ka kasheshi ko? Ka kashemin d'ana ko?"
Ogan ya kwace rigarsa yace " Malam me kenan? Kai kabamu kwangila sannan yanzu meye na zuwa mana da wannan zancen?"
Hisham cikin karaji yace " Abdulmajid kuka kama ba Abu Turab ba."
Kallansa sukai sukace " anma ai shine a cikin motar."
Hisham a rikice yace " bud'e min kofar, kun kasheshi ko?"
Bud'e kofar sukai, da sauri ya shiga ciki, yanda yaga Abdulmajid a yashe yasa ya gama rikicewa, cikin tsoro ya karasa gunsa, durkushewa yai a gub yana kuka sosai yace " najama kaina masifa, na kashe d'ana na cikina da kaina saboda wani buri nawa na shirme, nikam na shiga uku na...."
Oga ne ya matso yace " tab amma Allah ne ya kiyaye dan har naso mazgemai wuya nai tunanin barinsa zuwa anjima, ba shakka da anyi tsiya."
Hisham ya kalleshi a tsorace yace "kana nufin yanada rai"
Sosai ma sai dai kafarsa d'aya banaji zatai aiki.
Abdulmajid dake kwance yana fitar da numfashi sama sama kalaman Hisham suka daki kunuwansu, d'ansa?na cikinsa? Sai dai ba wani abu da zai iya yi dan ko magana ya kasa yi saboda dukan da sukai tamai da kafa.
Hisham ya d'ago Abdulmajid ganin yana numfashi yasa yace su taimaka mai ya sashi a mota.
Nan suka fito.
Ogan yace " Kayi hakuri yallabai, yanzu ya za'ai mu kama d'ayan?"
Hisham ya buga musu kallo yace " ku tabbatar kun bar garin nan kafin wani abu ya faru, ai dama na gama biyanku kudinku.
Nan ya shiga mota.
Sabi'u na kallansu, Abu Turab sukaso kamawa kenan su halaka? To ya akai Abdulmajid ya shiga motar? Da alama yasan da shirinsu kenan?
Lalai mutanen nan basuda imani.
Sai da Hisham yai gaba sannan shima ya fito, ya fita ya shiga mota, har zaiyi Zariya sai ya koma Kano.
Abu Turab yana cikin jama'a bayan an gama aka shiga cikin gida dan yin walima wacce yayun amarya suka shirya musu.
Suna gamawa ya fito kenan sai ga Sabi'u.
Da sauri ya matsa gunsa yace " ya ya?"
Sabi'u yace " Abdulmajid suka kama sun d'auka kaine, da alama Waziri ne yasa a kamaka."
Turab ya shaka fuskarsa da hannu biyu, ji yai idanunsa sun ciciko, mai yai wa mutanen nan, mai ya tsole musu a duniyar nan, duk abinda yaji game dasu, mahaifin Khadija? Magajiya? He will never forgive them, kallan Sabi'u yai yace " ya jikin Abdulmajid din?"
Sabi'u ya girgiza kai yace " da alama ba dadi abin dan naga kaishi mota akai."
Turab ya d'aga kansa sama saboda hawaye dake neman zubomai, sannan ya kalli Sabi'u yace " Da alama yasan abinda suke neman aikatawa, how can i forgive those people?"
Duk yanda yaso ya kore abin saj da hawaye ya zubomai ta kwaryar idanunsa, Sabi'u ya dafashi yace "Amma dama haka kake rayuwa cikinsu?"
Turab yai wani murmushin takaici sannan ya cije lab'ansa, wato su sukai su kasheshi sai su ba Basira magani suce hauka take saboda na mutu? Tabbas sai yanzu ya had'e puzzle din.
Hannunsa ya dunkule kai kace wani zai kaima naushi...........
Nikam ina ganin haka nai waje da gudu dan na d'auka ni za a make dan yanda naga idanun turab? Ba sauki......
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*71*
Magajiya kam tana zaune cikin mutane anata hidima, sai dai ta rasa gane kan dalilin dayasa akace mata wai Basira bata gidan, aikenta uku amma duk maganar d'ayace wai bata nan, ba haka taso ba lalai d'an iskan yaran can ne ya d'auke ta, to menene dalili? Inta tuna haka sai tai dariya tace " bakasan gani na karshe zaka mata ba.
Kowa yazo sai ya yaba kyan datai, saboda tsananin kyan datai, ga wani annashuwa da jin dadi dake fita daga fuskarta, tasha kwalliya, tasha lalle,hmmm abin ba a magana farinciki biyu take jira a kawo mata, na mutuwar Turab dana auran Abdulmajid da Gimbiya, taga uban da zai nemi kwace mulkin d'anta.
Aikowa akai akan Waziri nasan magana da ita, tace " a sanar dashi ina cikin taro, dan itakam ta san me zai sanar mata. Dama kuma abinda take jira kenan."
Sau biyu yana aikowa akan yana nemanta daga karshe tace " wai akan me tana cikin taron mutane zai dinga aikawa tazo?"
Murmushi tai a ranta tace " nafisan in zan fita anjima infita da kukan mutuwar d'ana Turab.
Jin haka ne yasa Waziri yaga in ya biyema jiran Magajiya d'ansa zai karasa, fitowa yai ya ja mota ya wuce asibitin ABU Gun abokin Mai Martaba.
Cikin tashin hankali da tausayawa aka shiga dashi cikin emergency.
*********
Tana zaune akan kujerarta
Sai da sukai ta sallama da mutane sannan aka barshi ya taho.
A hanya addu'a kawai yake akan Allah yasa ciwon Abdulmajid ba mai lahani bane, motar tasu tsit har suka isa kamar ba motar Ango.
Suna isa ya fito bai bi takan masu mai busa ba yai bangaren Magajiya.
Yana shiga aka fara gaisheshi, ganin gidan a cike taf yasa ya rasa yanda zaiyi, ga shi mata ne fal, juyawa yai ya fita tare da dafe kansa.
Kallan Sabi'u yai yace " muje gidansa, da alama ba nan yayo ba, dan ba alamar sun san wani abu."
Nan yai waje, sunje gidan Waziri tare da sanar da masu kula da kofa akan neman sa da suke yi, nan suka sanar dasu ai baizo ba.
Turab yace " muje gun Umma in sanar da ita sai mu shiga duba asibiti, dan na tabbatar tunda aka kaita wannan gidan a tsorace take."
Nan sukai gidan Mai martaba na cikin gari.
Mairo tana cire mata lalen data mata suna yar hirarsu sama sama, sukaji sallamar Turab.
Wani lallausan murmushi ne ya bayyana a fuskar Umma dan ba shakka zuciyarta a d'arare take, Mairo ma ta mike tare da d'auke robar lalen.
Turab ne ya shigo ya kalli Mairo cikin jin dadi yace " kanwata ina godiya sosai."
Murmushi tai tare da sunkuyar da kai.
Umma ta kalleshi tace " Alhamdulila, sai yanzu hankalina ya kwanta."
Turab ya zauna tare da cewa " umma ke sai yanzu kikai lalen bikin?" ya fada yana kallan Mairo ta gefe.
Fuska ta hade tace " itadai Umma lalle tai ba wai na biki ba, ko Umma?"
Basira ta d'aga kai tace " ina na isa yin lalle abikin Turab ai ni bikinki ne kadai zanyi Lalle Mairo."
Mairo tace " yauwa Umma." ta juya tai waje.
Turab ya kalli Umma yace " Umma kin tsorata ko?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace " Turab taya zan tsorata akan abinda nasan kana da dalili na aikata shi?"
Murmushi yai sannan yace " Umma da matsala Amma."
Tace " tame kenan?"
Mairo ce ta d'auko mai lemon zubo da tai tare da abinci, tana kokarin shiga taji yana cewa " Abdulmajid inaji yana asibiti."
Basira tace " mene?"
Turab ya kwashe komai ya sanar da ita.
Idanu ta runtse tashiga fadin Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.
Mairo kam jikinta ne ya shiga kakkarwa, daurewa tai tai sallama.
Turab ya amsa tare da juyowa.
Ajiye tiren tai ta mike zata fita.
Turab ya kalleta, yana kallanta ya fahimci taji me yace, nan yace mata "Abdulmajid na asibiti."
Kanta na kasa tace " Me ya dameni Yaya? Fatan sauki ne namai Allah ya bashi lafiya."
Mikewa tai ta fita.
Turab ya mike ya biyota tana kokarin shiga kitchen yace " kin tabbatar bai dameki ba?"
Kai ta d'aga mai sannan ta shiga ciki.
Kallan Umma yai wacce gaba d'aya komai ya mata zafi yace " Umma karki damu yanzu zanje mu duba inda yake."
Basira tace " ka cire babbar rigar."
Nan ya zareta sannan yasa akan kujera."
Tace " abincin fa?"
Kai ya girgiza yai waje.
A kofar kitchen din ya tsaya, Mairo ya kalla tana tsaye ta juya baya, ba abinda take a kitchen din, da alama tunani take.
Yace " Mairo zo ki rakani."
Kallansa tai tace " ina?"
Yace " neman Abdulmajid."
Tace "ni kuma meye nawa?"
Turab yai murmushi yace " wai dole ne sai an nunamin akwai dakakkiyar zuciya? Bayan ni ina ganin rauninta?"
Mairo ta juya kai, yace "wuce muje."
Fitowa tai tasa takalmi suka fita.
Sabi'u na cikin motar turab ya shiga gaba.
Ita kuma ta bud'e baya ta shiga.
Sabi'u ya kalli Turab ya kuma kalli Mairo ta madubi sai dai baice komai ba.
Turab yace " mu fara da asibiti babba ko?"
Sabi'u yace " ni nasan ma yana ABU dan shikadai ne asibitin da zasu(😂nace da wannan lokacin ne da bakace haka ba, yanda asibitoci sukai yawa.)"
Turab ya jinjina kai.
Sun isa asibitin ABU, suka nufi emergency, Mairo tana tsaye bakin kofar shiga, gabanta ne kawai ke faduwa, wanda ita kanta batasan dalili ba.
Can suka hango Hisham, Sabi'u ya taba Turab tare da nunamai Hisham.
Nan suka nufi gun.
A kwance yake kamar mai baccu sai kafarsa da aka gewaye da katako, kallo d'aya zaka ma gun ka fahimci karayace a gwiwarsa sannan ga bandage da aka nad'e kasan gwiwar dashi alamar ciwo, duk fuskarsa ma an masa dressing guri guri.
Hisham kam kallan Abdulmajid kawai yake ya baza tagumi.
Turab na isa gun ya kalli Hisham cikin b'acin rai.
Baimai magana ba ya kalli wani nurse dake gun yace " ya jikin shi?"
Yace "duk an gyara ciwokan da kuma karayar yanzu ma d'aki za'a maidashi dan neman samun sauki, saboda Director yace kar a barshi anan."
Turab yace " to."
Nan suka turo gadon.
Ta gabanta sukazo suka wuce, gaba d'aya jitai komai na jikinta ya dena aiki, kana kallansa kasan yana jin jiki sosai.
Binsu kawai take har suka isa d'akin, a baya ta tsaya ganin d'akin da suka shiga.
Hisham na kokarin shiga turab ya tare kofa tare da kallansa.
Yace " Waziri mai kake anan?"
Hisham ya bishi da kallan mamaki, wannan wace irin tambaya ce? Ya kawo yaro asibiti amma a tambayeshi me yakeyi anan?"
Turab ya kara cewa " waziri mai kake yi anan?"
Hisham yace " bam gane ba?"
Turab yace " saboda tsaro da kuma yin bincike na ke sanar dakai abu d'aya in har kanasan kaga Abdulmajid sai ka bi abinda nace."
Mamaki ya hana Hisham magana, Turab yai wani murmushi yace " ko kana tunanin bansan ni kukaso a ma illa ba?"
Gaban Hisham ya yanke ya fadi.
Turab yace " kaje gidanka yanzu, ka jirani zuwa gobe."
Hisham samun kansa yai da cewa to, ya juya yai gaba jikinsa a sanyaye, yanayi yana waiwayen kofar.
Kallan Abdulmajid Turab yai, ya dade yana kallansa, tsananin tausayinsa ne ke ratsashi gashi duk jikinsa ciwuka banda karaya, kamar ba shiba sam.
Turab ya kalli Sabi'u yace " zo muje gun likitan."
Sabi'u yace " karkuma abarshi shi kadai."
Kallan Mairo Turab yai da take rakube a gefe yace " akwai wanda ahi kansa mara lafiyar yafisan ya gani."
Bai fahimta ba sai dai ya gane akwai wanda zai zauna har suje su dawo.
Sai da sukazo inda taks Turab yace "ki shiga ki duba shi."
Sukai gaba.
Mairo a hankali ta tura kofar d'akin ta shiga.
Jikin gadon ta karasa sannan ta kalli fuskarsa, gaba d'aya an mata faci.
Fuskar ta kurama ido tana tuno abubuwan da suka dinga shiga tsakaninsu.
Sam bata san sanda hawaye suka ciciko a idanunta ba, a hankali wasu siraren hawaye suka gangaro kan fuskarsa.
Jin ruwa a fuskarsa ne yasa ya dan motsa idanunsa kadan, a hankali ya bud'e idanunsa da suka kumbura idanunta a rufe suke, yana kallanta ya maida idanunsa ya rufe.
Ina ya isa ya kalleta a cikin wannan halin? Ba ma wannan halin ba, ina ya isa yi mata magana bayan bai gama sanin wanene shi ba? Menene matsayinsa?
Idanunta ta bud'e a hankali sannan ta juya baya, tare da zama akan kujera, itadai so take ta karyata zuciyarta akan kukan nan tayine saboda tausayin d'an Adam ba wai saboda wani Abdulmajid ba.
Shikam ji yake inama ba wani babban sirri agabsa yaga Mairo tana nuna damuwa haka a gabansa? Meke shirin faruwa dashi?
Wasu zafafan hawayene suka gangaro ta gefe idanunsa.
********
A can kuwa Magajiya takaici ya isheta, har yanzu busa takeji da wasanni a gidan sarauta bata fara jin koke koke ba.
_TURAB_
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*72*
Turab ne ya kalli likitan sannan yace " kana nufin kafarsa bazata dawo dai dai ba?"
Kansa ya girgiza alamar a'a yace " ba wai bazata dawo daidai gaba d'aya ba, sai dai dawowarta daidai din abu ne mai wahala, a yanzu inya warke zamu had'ashi da sanduna dan taimaka masa gun tafiya, idan har Allah yayi sai kaga a hankali kafar ta warke in yana samun kulawa."
Turab yai godiya suka mike, kallan Sabi'u yai bayan sun fito yace " Sabi'u muje ka kaini gida, sai ka d'auko Khadija ka kawo asibitin ta zauna jinyarsa, ni akwai abinda zanyi."
Sabi'u yace " wacce muka kaifa?"
Turab yai murmushi yace " kana tunanin zai sake a gun yarinyar da yake so?"
Gaba yai daga fadar haka, mota suka shiga ya kaishi gida, akan inya d'auko Khadija sai ya maida Mairo.
Magajiya kam ana zaune a waje dan an fito waje wajen wani had'aden kwalliya ta sarauta da aka zagayen gun dashi, matane manya ke ta kid'an kwarya na ruwa, sai gaishe gaishe akeyi.
Turab yana shiga ya wuce bangarensa wanda yanzu komai nashi an kwashe daga bangaren, wanka yai sannan ya bud'e drawer da ya ajiye wata shadda a ciki dan dama ya ajiye ne saboda zuwa bangaren Amarya da ita, jawota yai tare da kallan d'ankwalin daya biyo bayan shaddar.
D'ankwalin Khadija ne, sawa yai a aljihunsa dan yau zai maida mata d'ankwalinta, inhar ya maida mata kuwa to yana nufin komai na alakar dake tsakaninsu ta tsaya kenan.
Fitowa yai daga bangaren, rawani yasa akamai, sannan yasa a d'aukomai dokin da Sarki ya bashi.
Had'aden dokin da mai martaba ya bashi ya hau, yasha ado na ban mamaki, Turab ya hau kai sannan ya nufi inda ake ta mai hawan dawakai.
Yana Isa masu busa suka canza salan busarsu aka saki wani kiraki.
Magajiya tana zaune labari ya iso mata na hawan da Ango yake yi.
Kallan yan aiken tai tace " Turab ne?"
Sukace sosai ma, duk da dai rawanun dayai bazai bari mu tabbatar shi bane amma ai kowa yasan Ango ne.
Tsaki tai a ranta tace " zancen banza kenan, Ango? Ai Abdulmajid ne angon."
Yana gama hawa dan ba dadewa yai ba ya nufi inda Magajiya take.
Aiko mata akai akan d'anta yazo kwasar gaisuwa.
Murmushi ta saki tace " ace ya shiga ciki ina shigowa."
Nan aka sanar ma Turab.
Ciki ya shiga ya samu guri ya zauna.
Magajiya ta mike cikin yauki ta nufi ciki.
Murd'a kofar tai ba tare da ta kula ba saboda bayansa ya juya tace " Ango kasha kamshi, dafatan yanzu ka hakura da aura........."
Juyowar da Turab yai tare da cuge rawanin ne yasa ta tsaya cak da maganar, jitai wani abu tundaga tsakiyar kanta har kafarta.
Turab ya tako cikin isa ya karaso inda take, hannu yasa ya tura kofar d'akin data rike da karfi bai cire hannunsa daga kai ba yace " Kina mamakin ganin wanda ya kamata ya mutu ne a tsaye a gabanki?"
Magajiya ta kakaro murmushi tace " me kake nufi? Kaine Angon mana, ko akwai wani aure da akai da ban sani ba?"
Turab ya girgiza kai yace " ina fa? Ai ni kadai ne a gidan nan aka d'aurama aure yau sannan aka Wani asibiti."
Magajiya tace "asibiti kuma? Me kake nufi?"
Turab idanunsa ne suka canza kala ya juyo ya kalleta yace " sa mayafi mu fita."
Tace " mene?"
Yace " abinda kikaji shi zakiyi."
Wata muguwar dariya ta saki tace " mene?kai harka isa ka sani nayi abinda banyi ra'ayi ba?"
Murmushi ya mata yace " daya wannan lokacin kuwa duk wani abu danai ra'ayi shi xakiyi."
Ranta ne ya baci matuka ta d'aga hannu zata wanka mai mari.
Jitai yace " Ya Abdulmajid zai ji in yasan kece kika sa aka kusa kashe shi?"
Hannunta ta tsayar kusa da fuskarsa, tace " Abdulmajid? Me ya sameshi?"
Turab yace " me ya sameshi? Yana kan gadon asibiti numfashi ma banaji yanayi, ko kin manta ke kika sa a kasheni? "
A rikice tace " to meya kawo Abdulmajid ciki?"
Turab yace " wannan kuma ke zan tambaya, ya zakiyi? D'an da kike gwagwarmaya a kansa gashican nufashinsa na neman d'aukewa."
Wani irin ihu ta saka ta kama kwalar rigar Turab tace " kana nufin d'an nawa ba ma tabbas ko yana da rai?"
Turab yace " ke nake jira muje ki ganshi kafin mu mikashi gidansa."
Wani irin ihu ta kara sakawa tace " kai har ka isa? Waye ya baka damar cewa d'ana numfashinsa na neman yankewa? Amma ban taba ganin mutum mara imani irinka ba, d'an nawa ka tura a ka kusa kashewa?"
Turab yai dariya yace " mara imani? Na tura? Magajiya na kasa fahimtar wa kikema inkiya a wannan maganar, ko kinaso kicemin Waziri shi kadai yai abin ba tare da kin sani ba?"
Magajiya ta kalleshi tace " Hisham? Eh shine yasa akai komai, ni meye nawa na neman ganin bayan rayuwarka?"
Turab yai wata dariya yace " dama ta ina zaki yadda kece sila bayan ni nasan wacce ke? Duk abinda Hisham ya miki kenan kanki kawai kika sani?"
Fuska ta had'e tace " bugar cikina kazoyi kenan?"
Turab ya bi kwayar idanunta da kallo, tace " me? Akwai
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 28 Chapter of 37