hannunta na rawa, ta daure ta kalli Jakadiya tace " bani guri."
Nan Jakadiya tai wuf tai waje kai kace dama jira take ace ta fita.
Tana fita Magajiya ta dafa kanta, tabbas yasan sirrin nan, garin yaya? Dolene ta b'olo da hanyar da zatasa ya kasa fadan komai, amma Basira ta sani ai, tabbas sai tayi dogon nazari.
**********
Sai daya cire kaya ya gama wankan sannan ya tuna ba towel a cikin toilet din.
Tsayawa yai, yai shiru yana tunanin mafita.
Ita kuwa Bilkisu ta shirya tsaf cikin wani had'ad'en leshi mai kyau, peach colour tayi kyau sosai, tana kokarin kame kanta da ribbon ne taji alamar kwankwasa kofa, kallan band'akin
tai tana mamaki, sannan ta mike tazo kusa da toilet din tace " Daga nan ne?"
Turab yai gyaran murya, tace " wani abu kake so?"
Iska ya furzar sannan a ransa yace sai ince bani towel?
Itace ta katseshi da cewa " Yarima?"
Turab yace " towel zaki d'an bani."
Idanu ta zaro sannan tace " to."
BJuyawa tai ta d'auko sabon towel ta kwamkwasa a hankali ya d'an bud'e kofar tare da zuro hannu, ita kuma ta juya kanta tana ta mikamai, yana kokarin kamo towel ya kamo hannunta, shiru ne ya biyu baya batare da ya sake ta ba, a hankali ya shafa zuwa kasan hannunta ya ja towel din.
Itakam gaba d'aya jikinta yayi sanyi tanaji ya turo kofar band'akin ya rufe.
Juyowa tai ta kalli toilet din sannan ta murmusa.
Turab kam shima a ciki yana rufewa yai murmushi sannan ya sa towel din, tana jin alamun zai fito ta fita falo.
Sai da ya shirya tsaf sannan ya fito falon, tana zaune kan kujera, kasan carpet din an jera musu kayan abinci kala kala, kamshin turarensa ne yasa tasan ya fito.
A hankali ta lumshe idanunta.
Kallanta yai yace " Amarya kin tashi lafiya?"
Murmushi tai tace " ina kwana? Kaga ka sa ban gaisheka ba sai daka fara tambaya ta ya na tashi?"
Yace " daga masallaci na biya wani guri ne."
Tace " ayya! Kaci abincin sai muje gaisuwa."
Gaisuwa?
Tace " eh, zaka kaini in gaida matan Sarki."
Yace " ohh lalai, to sauka muci abincin."
Tace "nasha madarar shanu ni sai anjima zanci."
Bai ce komai ba ya zauna a kasan carpet din, yana kokarin bud'e kula ta sauko tare da d'aukan plate ta zuba mai.
Kallanta yai fuskarsa d'auke da murmushi yace " masu aiki nawa kikeso a turo nan bangaren?"
Tace " amin uzuri da masu aikin nan, tun ina karama komai sai dai amin banasan a gidan mijina ya zamana komai sai dai amin, ni ba abinci na iya ba ba shara na iya ba balle wanke wanke, banaso akawo mutanen da zasusa ya zamana kula da kaina da mijina sai dai amin."
Kallanta yai cikin jin dadi yace " Kina tunanin zaki iya?"
Tace "ummm"
Yace " shikenan zan sanar ma Umma."
Ya gama cin abinci sannan suka nufi bangaren Matar sarki ta biyu, sai da suka gaisa sannan sukaje gun ta uku, duk inda sukaje sai kowa yai mamakin tsananin kyau irin na Gimbiya, sannan suka nufi bangaren Magajiya.
Tasa an had'a abincin sha da kayan marmari an jera a falon ta dan dama tasan da zuwansu, taci kwalliya na gani na fada kai kace wani had'ad'en taro zata hallarta.
Sai da suka zauna sannan ta fito cikin isa da izzarta.
Gimbiya tayi zama irin na 'ya'yan mulki a gaban iyayensu Kanta na kasa ta shigo.
Magajiya ta zauna tare da kallansu, Turab yace "Umma Magajiya Barka da Safiya."
Tace " Ango na d'auka zaka bari sai zuwa jibi, irin wannan wahalar da amarya haka?"
Ta fada tana kallan Bilkisu.
A hankali ta d'ago ta kalli Magajiya, idanunsu ne suka had'u, Bilkisu ta sakar mata wani sansanyan murmushi tace " Barka da Safiya."
Magajiya idanunta na kanta tace " Amarya barka da shigowa masarautar Zazzau, dafatan zaki samu kwanciyar hankali kamar yanda kike samu a can."
Tace " Karki damu indai farin ciki ne Umma dan na tabbata d'anki zai kula da ni sosai."
Ta rasa meyasa taji zafin kalamanta, bayan ba wani abun ta fada ba, amma me yasa takeji kamar magana ta fada mata?
Daurewa tai tace " Haka akeso, ai Turab yaro ne na gari."
Bilkisu tace "Godiya muke, dan yabonki yana nuna hakan take a gun al'uma."
Magajiya ta kara kallanta, me yasa yanzuma taji maganar ta bata mata rai?
Turab kam murmushi yai yace " na d'auka kina gun Abdulmajid."
Tace " dama ku nake jira mu gaisa sai in fita."
Yace " ohh amma da sai naji kamar kince da mun bari sai nan da kwana uku."
Ta kalli Bilkisu tace " hmm ai da dai ka barta ta huta d'in."
Bilkisu tace "godiya nake da kulawa, amma Umma duk wani hakkina ina ganin gwara nayishi lokacin daya dace."
Tace "haka ne."
Turab kallan Magajiya yake yana mamakin yanda take amsawa Bilkisu duk da dai yasan da bakunta amma yasan dukda haka wannan ba style dinta bane.
Basu wani dade ba suka fito, har ya kai falo tace " Turab."
Dawowa yai ya shigo d'akin, kallansa tai tace "Magana nakesan muyi."
Yace " banaji akwai wata magana data rage a tsakaninmu a wannan lokacin, sannan asibiti nakeso na tafi dan kuwa naji labarin Abdulmajid ya farfado inada bukatar jin wanene a kuma garin ya ya aka aikata mai hakan."
Magajiya zatai magana yai gaba.
Yana fita ta mike tare da matse hannayenta, Abdulmajid?
Yana fita itama ta mike ta sanar da masu kula da ita akan zuwa asibiti.
********
Hisham ya gama galabaita gaba d'aya ya wuce asibiti dan ganin Abdulmajid da jikinsa, yana zuwa ya tadda khadija a zaune ta had'a gwiwarta da kanta a kan sallaya.
Yana shiga ya tafi da sauri inda take ya rike hannayenta ya d'agota yace " Khadija!"
D'agowa tai sannan ta kura mai idanunta da suka kumbura, wanda har fuskarta itama ta kumbura.
Muryar Abdulmajid yaji yace " Khadija zaki iya komawa gida da kanki?"
Kallansa tai batace komai ba, yace " kije gida ki jira Waziri, ko kuma kije waje ki jirashi yazo kuje gida, magana zamuyi."
Mikewa tai kamar wacce ba tada laka a jiki tai waje ko kara kallan Mahaifinta batai ba.
Tana fita Hisham ya matso yace " Abdulmajid yaushe ta dawo....?"
"Ba wannan bane abinda yasa nace zamuyi magana, tambayarka nakesanyi."
Hisham ya kalleshi gabansa na faduwa.
Abdulmajid yace " menene tsakanina dakai?"
Hisham ya had'iyi yawo yace " naam?"
Abdulmajid yace " ni d'anka ne?"
Hisham kallansa kawai yake dan bashida amsar da zai bashi.
Abdulmajid yace " inaso daga rana irinta yau ka cire batun nan a ranka dan bazanci amanar Umma ba, ban damu da wanene ya haifeni ba wacce ta raineni itace Uwa a gareni, akan Umma zan iya juya ma baya zan kuma iya tozartaka, kaine ka d'aukeni ka bata dan haka babu damuwata akan duk wani abu da zai shafeka."
Hisham bai taba tunanin abinda zaiji daga gareshi ba kenan, yace " Abdulmajid kanaso kace ni dana haifeka banida matsayi a gunka?"
Yace " matsayi? Kai kasan wannan, sannan ka gaggauta maida Khadija kano inhar kanasan rayuwarta ta daidaita, sannan in har kanaso in d'inga ganin kimarka da darajarka a matsayin wanda ya haifeni ti ka tabbatar ka fita hanyar Umma ta, sannan ko da wasa naji labarin ka aikata abu irin kwatankwacin abinda ka min banaji zan iya yafe maka."
Hisham da sauri ya d'ago ya kalleshi yace " naji bazan aikata ba ko kadan amma laifin dana aikata a baya fa?"
Abdulmajid ya ce " au akwai abinda ka aikata irin wannan a baya? To a wannan d'akin inaso ku warware a lakar dake tsakaninmu."
Hisham ya matso da sauri yace " Abdulmajid kayi hakuri wlh....."
Idanu ya runtse sannan yace " naji amma kada ka kuskura abinda ka aikata ya fito fili dan bazan iya kallan mutane ba in har abinda ka aikata ya fito fili, ciki kuwa harda abinda kamin."
Hisham da sauri yace " naji, naji."
Abdulmajid yace "kaje gun Khadija, ba dadi take ji ba."
Nan yai waje.
Yana fita ya kalli kofa sannan yai ajiyar zuciya, yace " anya Turab wannan hanyar zata bule?"
Tunowa yai da kadan daga cikin kalaman Turab dayace " ka tabbatar ka nunama Waziri kai a bayan Magajiya kake sannan ka nuna masa in har ya amsa laifinsa to lalai kai dashi har abada........"
Tunowa da ragowar kalaman yai a ransa sannan yace a fili " Turab kenan, wato in Waziri ya ki amincewa da laifinsa sannan ya fahimci ni a bayan Magajiya nake lokacin ne kishi zai afko a tsakani, ita zataji haushin kin amsa laifinsa wanda za'ai ta bincike gun gano gaskiya, sannan shi kuma zaiji takaicin bijerewata zuwa gun magajiya, idan ya raba tsakaninsu sai ya sani nasa Umma ta fadi laifukanta da kanta cikin ruwan sanyi ba tare da tasan abinda takeyi ba, saboda yardarta gareni ganin na ki mahaifina saboda mulki............"
Murmushi yake yai ganin ya fara hada kan puzzle din da Turab ya bashi, a fili yace " daidai nake aikatawa??????"
Nikam da sauri nace " Kwarai😄😂"
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*78*
Hankalin Hisham yayi tsananin tashi yana fita jiyai jiri na neman d'aukansa sai daya dafa bango.
Daga nesa ya hango Khadija a zaune a jikin bango tana bin mutane da kallo, tsananin tausayinta ne ya kara ratsashi, shi dai bai ga ranar da wannan buri nasa ya masa ba, ina amfani gaba d'aya ya tarwatsa rayuwar 'ya'yansa?
Kusa da ita yaje yace "Khadija "
Kallansa tai sai dai ba magana, yace " tashi muje."
Mikewa tajeyi da yake batada karfi tai kamar zata fadi, da sauri yasa hannu ya rikota yace "yi a hankali."
Hannunta ta fizge sannan tai gaba.
Kallabta yai jiki a sanyaye suka shiga mota, ya ja sukai gida.
Har suka isa ba wanda yai magana a cikin motar, tana shiga gida ta wuce d'aki ta sauko da akwatinta ta shiga had'a kayanta.
Umma ce ta shigo cikin kulawa tace "Khadija ya jikin Yari......"
Ganin tana had'a kaya yasa maganarta ta tsaya, kallanta tai tace " Khadija me kenan?"
D'agowa tai ta kalleta sai dai bazata iya cewa komai ba dan ta tabbata tana magana kuka ne zai zo mata, kurama Umma ido tai a ranta tace " me yasa kikai haka Umma? Me yasa baki hana Abba aikata munanan aiyukan nan ba?"
Kallanta Umma tai tace " Khadija lafiya?"
Khadija ta maida kanta kan kayan ta cigaba da shiryawa, ganin batada niyyar magana yasa ta fito.
Hisham ta tarar a d'aki ya baza uban tagumi, ko sallamar da tai bai amsa ba, tace " Baban Khadija me ke faruwa?"
Kallanta yai shima sororo, tace " ba shiru zakai ba me ke faruwa naga Khadija duk ta canza sannan tana ta faman hada kaya? Sannan ni bakacemin komai game da ciwon Yarima ba kadai cemib kawai bayajin dadi ne......"
Ya isheni haka nan, ki barni da abinda ke damuna dan Allah, haba! Kinsan ya nakeji a zuciyata a wannan lokacin? Komai na neman rugujewa a rayuwata, d'an da nake tunkaho zai ramamin rashin mutunci da cin zarafin da Magajiya tamib yanzu ya rikide yace shi ba wani abu tsakanina dashi, itace uwarsa, sannan Khadija ko kallona basan yi take ba ke kuma zakizo ki sani a gaba kamar wanda ya amshi bashinki?"
Umma tace " ban gane me kake nuf......"
"ba sai kin gane ba, dama ina kanki zai yi aiki? Kwakwalwace dama kamar ta kifi?"
Umma ta juya jiki a sanyaye tai waje, dakin Khadija ta koma ta tsaya kawai tana kallan ikon Allah.
Khadija kam dama tun jiya idanunta biyu taji sanda Turab yace ta koma kano, sannan dama itama bataji zata iya cigaba da zama a wannan garin, Umma ta kalla tanasan mata magana sai dai ta kasa.
Umma idanunta duk sun ciko dan itakam kalaman Hisham sun kona mata rai, inda sabi yaci ace ta saba amma duk sanda ya mata sai ta dingajin ba dadi.
Hanyar band'aki ta nufa bayan ta dau zanin wanka, ta daure tace " kano zan koma."
Ta shige ban d'akin, kallan kofar Umma tai jiki a sanyaye sannan ta mike hartaje zata shiga d'akinsu kuma ta fasa saboda takaici, juyawa tai ta koma d'akin khadija ta zauna.
**********
A bangaren Basira kuwa su Gimbiya anata kunyar suruka, Umma sosai ta yaba da hankalinta, nan tasa aka kawo mata abincin safe jin Turab yace bataci abinci ba, duk da bataso ci ba sai da Umma tasata taci, sun dade kafin Garzali ya turo a sanar da Turab akan zata fita.
Abinda kawai aka ce kenan shiyasa Basira bata fahimcesu ba, Gimbiya kuwa kallansa tai sai dai bata tambayeshi ba, ya kalleta yace " in barki anan ko in maidake can kafin in dawo?"
Tace " ina nan."
Yace " ok, ba dadewa zanyi ba."
Umma ta kallesu tai murmushin jin dadi.
Turab ya juya ya fita, Garzali ya tarar a waje yace " ta fito?"
Yace " yanzun nan."
Turab yace " muje, ka tura a sanar mai?"
Garzali yace " eh Ranka ya dade."
Mota suka shiga suka tafi asibitin, suna kallan motarta daga gaba su kuma suna baya, har suka isa.
Magajiya ta fito ta nufi d'akin da aka kwantar da Abdulmajid.
Turab yana kallanta ta shiga shikuma ya tsaya a bakin kofa.
Tana shiga aka ajiye kayayyakin data kawo, kallan danta tai cikin jin dadi ta matso tace " Abdulmajid? Idanunka biyu?"
Kallanta yai sai dai baice komai ba.
Magajiya ta zauna kusa dashi cikin jin dadi tace " na sani ai, nasan d'ana ta ina magajin sarki zai kwanta kamar bara numfashi?"
Abdulmajid ya murmusa yace " Umma kiyi hakuri na saki damuwa."
Kanta ta girgiza tace " wa ke wannan zancen? Ai farfad'owarka shine komai nawa."
Kallanta yai sannan yace " Umma kinsan Kawu yanada hannu akan abinda aka min?"
Idanu ta zaro sannan tasa hannu a kirji tace " mene?kanaso kace shiya ja maka wannan abun?"
Turab ya murmusa yace " GOOD JOB ABDUL"
Abdulmajid yai kasa dakai cikin rashin jin dadi, Magajiya tace " karka damu ba yayana ba ko Sarki ne ya kuskura ya tab'amin kai bazan taba yafemai ba."
Abdulmajid ya kalleta yace " na sani dama........"
Turo kofar da akai ne yasa shi yin shiru, Turab ne ya shigo tare da sallama.
Bata juyaba amma tanajin sallamarsa sai da gabanta ya fadi, me ya kawoshi?
Turab ya matso yana cewa "Umma ashe kin garzayo."
Juyowa tai ta kalleshi tace " Au Turab kaine?"
Yace "ni ne, kinsan dolene nazo duba Abdulmajid tunda ni aka je halakawa tsautsayi.........."
Katsesh tai da sauri cikin tsoro tace " ina amaryar? Badai barinta kai ba?"
Yace " ya zanyi? Dolece ta sani zuwa ai, naje gunki akan zamu gun Mai Martaba dan yin wata magana ashe ke kina nan?"
Idanunta ne suka fito, duk yanda taso b'oye tsoronta sai da ya nuna tace " ban gane ba?"
Turab ya matso yace " magana ce wacce ya dace ayi gani gaki ga Abdulmajid sannan ga Waziri."
A rikice ta d'ago ta kalleshi sannan ta kalli Abdulmajid tace "Turab wai kwanan nan meke damunka ne? Wuce muje gida mayi maganar a can."
Murmushi yai sannan yace " Bakyaso muyi a nan?"
Hararsa tai tace " muje ko?"
Ta na kokarin mikewa Zagi ya sanar da isowar Mai Martaba.
Kallan Turab tai dan tabbas tasan yasan da zuwansa, murmushi ya mata sannan ya d'an d'aga gira kadan ya juya kai.
Sarki ne ya fara shigowa bayansa kuma Waziri ne ya shigo.
Abdulmajid ya kalli Turab dan baisan me yake shirin aikatawa Ba.
Sarki ya nemi fadawa daau fita dan zai duba d'ansa.
Nan kowa yai waje, kallan Abdulmajid yai cikin tausayawa yace " Ya jikin naka?"
Abdulmajid ya dan sunkuyar dakai yace"Barka da war haka Takawa."
Kallansa sarki yai sannan ya kalli Turab wanda ya rusuna tare da gaidashi, Magajiya ma tace " Barkanka da war haka."
Sarki ya kalli Turab bayan ya zauna yace " me kakeyi anan kabar yar mutane ita kadai, ba kayi dubiyar ba?"
Yace " yanzu nake kokarin tafiya dama inasan zuwa gunka ne nida Umma."
Magajiya ta kalleshi sai dai kafin tai magana yace " Dama wani abu nake san......"
Katseshi magajiya tai da sauri tace "Ya kamata ka koma gida ko? Ba dadi ango daga aure ace yana waje."
Turab ya kalleta sannan ya kalli Hisham wanda yai tsuru tsuru yace " Magana ce akan Abdulmajid."
Yanda gaban Magajiya ya ke faduwa zata iya cewa wannan shine rana ta farko da takejin faduwar gaba haka ba kakkautawa dan tabbas tasan so yake ya sanar da tsakaninta da Abdulmajid......
Meye mafita?
Kafin kwakwalwarta tai aiki muryar Turab taji yace "Umma maganar da mukace zamuyi da Abba akan abinda ya samu Abdulmajid, ina ganin dolene ga Waziri anan wanda nake tunanin yafi kowa sanin abinda ke faruwa."
Wata irin ajiyar zuciya ta saki wanda sai da kowa ya kalleta.
Kallan Hisham tai sannan ta kalli Turab a ranta tace " tanan ka b'ulo?"
Hisham kam gaba d'aya ya rasa abinda ke mai dadi, ga Abdulmajid yace karya kuskura ya aminta akan shine sila.
Magajiya ta kalli Turab sannan ta kalli Sarki tace " haka ne Turab sai dai ina ganin abari yaji sauki tukunna kafin ai wannan maganar."
Turab ya kalleta yace " haka ne amma bakya tunanin kafin nan wanda ya aikata laifi ya kamata shima ya fuskanci, ba dai saboda zargin da akema yayanki bane yasa kike......"
Wani mugun murmushi tai tace " Kana tunanin in har Waziri nada hannu a ciki zan nemi birne laifinsa?"
Turab zaiyi magana sarki yace " ya isa haka, ina kuma tunanin tunda naji maganar na kuma sam mai ya faru yanzu dolene ayi bincike a fada, gunda alkalai suke."
Hisham! Kaine ka aikata?"
Hisham ya kalli Abdulmajid sannan ya kalli Magajiya tunowa yai da Khadija wacce ta fito da akwatinta a gida tana jira ta tafi aka aiko yazo shine yace ta jira ya dawo.
Ina zai sa kansa?
Magajiya tsoro take kar magana ta shiga fada dan tabbas in ta shiga daga bincike sai ance meye dalilinsa na aikata hakan, daga nan kuma tana tsoron kalaman da zasu fito daga bakin Hisham in yaji ana tsananta bincike a kansa.
***********
Turab ne ya kalli Magajiya wacce fuskarta yau ta bayyana da shakka karara, murmushi taga ya sakar mata a ransa yace " are u scared?"
"In kika tsorata tun yanzu the game will not be fun."
Idanun Turab kawai take kallo..........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*79*
Mikewa tai tace " Turab me yasa kuke san bud'e abu cikin bainar jama'a? Me zai hana........"ganin irin kallan da Turab, Sarki da Abdulmajid suke mata ne yasa ta fahimci tana neman kauce hanya, daurewa tai sannan tai wani murmushi tare da komawa ta zauna tace " Yaya! Abu d'aya zan tambayeka kafin in cigaba da magana, da gaske kaine ka nemi halaka Abdulmajid?"
Hisham ya kalleta cikin mamaki dan shi gaba d'aya ya rasa ma mai zaice, Abdulmajid ya kalla wanda shima kallanaa yakeyi.
Turab ya kallesu sannan yace " Abba da alama ya kamata kaba Umma lawyer cikin gida."
Kallansa tai tace " mene?"
Turab yai dan dariya yace " menene na tada hankali Umma? Naga kamar kina neman d'aurama Waziri laifin da ba lalai shine ya aikata ba."
Bakinta ta dan motsa sannan tace " me kakeso kace a takaice?"
Sarki ya kalleshi sannan ya kalli Hisham yace " Waziri!"
Hisham ya rusuna da sauri, takawa yana kallansa yace " me zaka iya cewa game da abinda ke faruwa a d'akin nan?"
Hisham yai kasa dakai cikin tashin hankali, Sarki yace " jeka jirani a fada in har bakada abin cewa anan, to lalai zaka samu abin cewa a can, saboda dolene ka sanar damu dalilin dayasa ake zarginka."
Hisham yace "Tuba nake ranka ya dade amma ni kaina bansan dalilin dayasa akemin wannan zargin ba."
Turab yace " gaskiya ne, nima kaina ban fahimci me yasa ake ma wannan zargin ba, me ka aikata takamaima? Shi yasa nake ganin gwara aje fada yanda za'a tabbatar da zargin da akema ba gaskiya bane."
Abdulmajid yace " Haka ne, nima ina tunanin hakan yafi Umma."
Magajiya ta kalleshi gabanta na faduwa sai dai jin wata dabara ta fad'o mata yasa ta murmusa tace " hakan yayi, sai yaushe yanzu za'ai zaman?"
Turab ya kalleta, kamar wanda ya shiga ranta sai jitai yace " Abba gani nake yanzu in har ba abinda zakai gwara ai shari'ar nan yanzu, in ba haka ba shi kansa Waziri banaji zai samu kwanciyar hankali."
Takawa yai gyaran murya sannan yace " hakan yayi, ina neman Waziri da Turab a fada nan da minti talatin."
Abdulmajid yace "Abba nima ina neman alfarma dan hallarta."
Sarki ya kalleshi yace " karka damu, kai dai ka kula da kanka."
Abdulmajid kasa yai da kai dan shi kam yafisan yasan kome ke faruwa a idanunsa.
Turab ya fahimci haka sai yace " Abba zaman asibiti ba dadi mai zai hana mu nemi sallama, in yaso saboda kafarsa sai a dinga turashi a kujera?"
Sarki yace " a'a ku barshi anan dan samun lafiyarsa."
Magajiya kam kamar wanda aka nausa a ciki haka taji ta, tsananin tashin hankalin data shiga, dolene a cikin minti talatin d'in nan tai tunanin abinda zata tsarama Hisham dan fad'a a fada dan in batai da gaske ba lalai asirinta zai tuno, ita tsoronta ma wannan munafikin yaran dazai kasance a gun.
Sarki ne ya mike sannan yai waje.
Yana fita Turab ya mike shima yai waje dan ya tabbatar Magajiya tana bukatar kadaicewa da yayanta.
Abdulmajid ta kalla sannan tace " Abdulmajid bari in raka Yaya tunda fada zai wuce."
Kai kawai ya d'aga.
Suna fita ta mai alama daya biyota, sai da sukai tafiya sosai gun da ba mutane sosai, yau ko tafiyar kasaitar ma batai ba, suna shiga gun daba mutane ta juyo tace "Yaya ya zamuyi?"
Hisham yace "game da me kenan?"
Tace " ina tsoron kar muje akwai wata shaida da wannan yaran yake dashi na kana da hannu akai, dan yanda yake magana na tabbata akwai wani abu a kasa."
Hisham ya kalleta yace "ni ba wannan ne a gabana ba Khadija na gida tana jirana."
Kallansa tai tace " Waziri!"
Kallanta yai dan yanda ta kira sunan alamace ta ranta ya baci, Magajiya ta had'e rai tace " me kake san kace? Ba damuwarka bane ko me ya faru?"
Ya kalleta yace " ba haka nake nu......"
Tace " ko ma menene ba damuwa ta bace, abu d'aya na sani idan har ka kuskura ka bari sunana ko alamun sunana ya fito daga cikin wannan abu to ba shakka zan iya yada kai, kafi kowa sanin wacece ni, akan kaina ba abinda bazan iya aikatawa ba."
Ta juya ta fara tafiya, idanu ya runtse dan yama rasa ya zaiyi, da girmansa da komai amma yana cikin halin tsoro na jin kunyar duniya, juyowa tai ta kalleshi tace " ahhhh na manta ka kiyayi bakinka tun kafin 'ya'yanka susan kisan kan daka aikata."
Ta juya tai gaba.
Hannayensa yasa ya shafi fuskarsa sannan ya kalli sama, a hankali ya juya yai waje.
Gida ya nufa.
Khadija na kwance akan gado kalaman da taji tsakanin Magajiya da Hisham ne suke mata yawo a kwakwalwar, kalaman da bata taba jin mugayen kalamai irinsu ba, filo tasaka ta rufe kanta wasu zafaffan hawayene suka shiga zubo mata.
Mahaifiyarta ce ta shigo ta kalleta, jikinta ne yai mugun sanyi ta karasa gunta tare da d'aga filon, Khadija ta gani tana hawaye hannunta ta rike tare da cewa tashi khadija.
Khadija ta mike a hankali ta zauna, hannu tasa kan goshinta saboda taji zafi sosai sanda ta rike hannunta.
Jin yanda kanta ya d'au zafi yasa ta kalleta tace " Khadija meke damunki? Meke damunki da kike san tafiya ki bar mahaifanki?"
Khadija a hankali ta kwantar da kanta kan cinyar mahaifiyarta wasu zafaffan hawayene suka zubo mata a hankali tace " Umma mecece rayuwar nan? Me cece a ciki da har mutane ke jefa
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 31 Chapter of 37