tunanin ni zan kai 'yata a ta biyu gidan wani? Sannan ni ban taba tunanin had'a zuri'a dakai ba kuma bazan yi ba har abada."
Turab yace "kumafa gaskiya ka fada, ni kaina bansan me yasa nazo ma da zancen ba, inaso ka sanar da 'yarka hukuncinka saboda mu hakura da juna."
Ya mike yamai sallama ya fito daga falon.
Yana fita yai wani murmushin gefe yace " nazo neman iri ne na auran 'yarka? Inji wa? Kai dai na tabbatar abinda na saka a kwakwalwarka ya shiga zai kuma fara aiki."
Ya juya, Karo suka kusa yi da Khadija wacce ta taho da tirw daga kitchen rike da tire wanda yake d'auke da juice.
Kaucewa tai saboda ganin zata bugeshi, garin kaucewa bata kula da kafarsa ba ta taka ta tafi kamar zata fadi, da sauri ya rikota ta baya.
Ajiyar zuciya tai da karfi dan tabbas ta d'auka fad'uwa zatai.
Juyowa tai a hankali, nan taga wanene idanunsu ne suka had'u da juna.
Sai da 'yan wasu dakiku suka wuce a haka kafin Turab ya daure yace " Baki bige ba?"
Gyara tsayuwarta tai sannan ta kalleshi, a hankali ta d'aga kai, kallanta ya sakeyi yaga ta rame, ita kuma tana san tambayarsa abinda ya kawoshi, a tare sukace "Nace me......"
Ganin yanda sukai maganar a tare basu san sanda sukai dariya ba, Turab yace " fara magana."
Kallansa tai tace " a'a ka fara." yana kokarin tambayarta yaji murya ance " Khadija me kikeyi anan baki kai ba?"
Juyowa tai ta kalli Ummanta tace " yanzu zan kai."
Kallan gun yai, mahaifiyarta ya gani, suna tsananin kama da Khadija sosai, da ace itace Abdulmajid to fa yasan tabbas zargi zai bayyana.
Gaisheta yai sannan ya fita, Hisham kam Turab na fita ya kumburo baki yana tunani, tabbas dolene ya fara jan d'ansa a jikinsa dan sai yanzu ya farga ya san Magajiya sarai tabbas gaba ma neman ma hanashi zuwa gidan zatai.
Ko tabin bayan Khadija data shigo baiyi ba ya shiga cikin d'aki.
**********
A can kano kuwa shiri sosai akeyi na auren Gimbiya, auren da babu kamarsa agunsu domin ita kadai ce 'yar sarki mace, shiri ake sosai wanda yasa kishiyoyin Fulani jin kishi dan komai ita keyi, Bilkisu kuwa an shiga gyara, dama ba zancen zance dan in suka fara gyaran jiki to ango bazai ga amarya ba saboda so ake inya tashi ganinta yaga kamar ba ita ba.
Turab kam na kiranta sosai suna waya.
Hisham ya gama tsarawa dan yau yana tashi daga fada ya nufi bangaren Abdulmajid........
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
_Sakon ta'aziyya gareki kawar arziki BillynAbdul Allah ubangiji ya jikan Mahaifinmu yasa Aljanna ce makomarsa.....(Ameen)_
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_Masu san karanta Matar Fayrouz na AsyKhaleel da sauran litattafanta su duba ta a wattpad @asykhaleel.😘😘_
*65*
Hisham yana fita yai bangaren Abdulmajid, baya nan ma sai ya zauna a falo ya aika a nemoshi, yace " in an ganshi kar acemai shine yake nemansa.
Abdulmajid ya fito daga bangaren Magajiya kenan aka sanar dashi yanada bako.
Yana shiga yaga Hisham, ya karasa ya zauna sannan ya gaidashi, Hisham ya washe baki yace " Abdulmajid sai ka ganni ko?"
Kallansa yai yace " Kawu me ya kawoka? Naga baka taba zuwa bangarena ba."
Hisham yai murmushi tare da kallansa yace " yauma wucewa nazoyi sai na fahimci ban taba shigowa ba."
Kai ya d'aga kawai baice komai ba, yau ce rana ta farko da suka kebe su biyu haka shiyasa yakejin abin wani banbarakwai kamar ba kawunsa ba.
Hisham ya kalleshi yace " ya maganar auren naka da Mairo? Har yanzu Magajiya bata sauko ba?"
Hisham ya kalleshi kallan mamaki, cikin rashin fahimta yace " eh kasan halin Umma ai "
Hisham yace " karka damu inaso kome ke damunka ka dinga sanar dani, ni zan yi iya kokarina wajen ganin na taimaka maka, Magajiya bazata taba bari ka auri yarinyar ba, sai dai ni zan san yanda zanyi in har kanasanta."
Ya kasa fahimtarsa, mamaki yake na yanda yake mai, Abdulmajid yace "Nagode, amma kana tunanin Umma zata yarda?"
Hisham yace " karka damu, kai daj ka yarda dani, duk wata matsala taka ka dinga zuwa kana sanar dani, ni zan taimakeka akan komenene, kawai dai ka dage kar ka taba bari Turab ya kwacema mulkinka."
Abdulmajid kallansa kawai yakeyi, Hisham ya matso yace " inaso a sati ka dinga zuwa gidana cikin gari, zansa Maman Khadija ta dinga shiryama duk abincin da kakeso, kaga sai kazo ayi hira, hakan zai ragema kewa ya kuma kara mana zumunci."
Shekarata nawa da haihuwa? Da can ba'ai zumuncin ba sai yanzu? Abinda ya fada kenan a ransa, sai dai a fili kallan Hisham yai kawai baice komai ba.
Hisham ganin yanda Abdulmajid yake yi yasa ya mike yace " ni zan koma sai mun ganka ko ran Juma'a ko asabar,sannan karka fadama Magajiya zuwana da zancen da mukai, ka santa."
Uhm hmm, kawai yace.
Hisham yai waje.
Kallansa Abdulmajid yai sannan ya mike yai ciki.
Hisham kuwa na fita ya jinjina kai yace " a hankali zan jawoka jikina, ai tsakanin Uba da d'a sai Allah."
Yana fitowa yai wuf yai kwana ya wuce, Abu Turab wanda yana shiga bangaren aka sanar dashi zuwansa ya fito dama yana jiran fitowarsa.
Yana hangoshi ya taho kamar irin bai ganshi ba d'in nan, Hisham na hangoshi ya tsaya tare da neman inda zai b'uya, dan dai girma ya kamashi ne amma da gudu zai saka, juyawa yai da sauri dama abinda yasa ya bi ta baya saboda bangaren Magajiya ne ta gaba, yana tsoron kar aganshi.
Abu Turab yana kallan ya juya yai wani murmushin jin dadi.
Hisham ya shiga bangaren Magajiya.
Tana kishingide ta bashi izinin shigowa.
Hisham ya shiga yana dariya yace " Magajiya ikon Allah hutawa kikeyi ne?"
Wani banzan kallo tamai hakan yasa yai shiru sannan yace " Magajiya barka da yamma."
Idanu ta d'an juya bata amsa ba, zama yai sannan yace " na lekone mu gaisa."
Tace " ka sandai muna da abinda ya kamata mu shirya na ranar auren yaran nan ko? Ga lokaci yana matsowa amma sam ka ki shigowa ayi magana."
Yace " haka ne, nima ai ba mantawa nai ba, yanzu ya kikeso ayi?"
Ta bud'e baki zatai magana aka sanar da ita zuwan Abu Turab.
Fuska ta canza tare da yin wata karamar kwafa, ba shakka itakam ta gaji da jin ko sunan yaran nan.
Shigowa yai ganin batada niyyar bashi izini.
Yana shigowa yace " Umma bakiji isowar d'anki bane?"
Murmushi ta saki sannan ta koma ta gyara zamanta tace " banyi tsamannin zuwan ka bane."
Zama yai sannan ya kalli Hisham yace " da alama sirri kukeyi da Kawun namu au ko ince Babana."
Magajiya ta had'e fuska, shima Hisham yaci mazu, Turab ya d'aga hannayensa yace " Tuba nake Babana kar in bata ma sirikin nawa rai kafin abani Khadija."
Magajiya ta kalleshi cikin takaici tace " kai dai ka nutsu akan auranka da Bilkisu ka daina wata banzan magana wacce bazata amfaneka ba."
Turab yace "Haka ne Umma, nayi..." yai alamar zip a bakinsa.
Kallan Hisham yai yace "Amma waziri kamar daga bangaren Abdulmajid na ganka ko?"
Hisham ya zaro ido, da sauri ya kauda kai gefe irin mara gaskiyar nan yace " a'a wucewa nai ba shiga nai ba."
Turab ya jinjina kai yace " kayi kokari sai naga kamar tacan yafi nisa."
Hisham yace "Hmm." da sauri ya kuma cewa " bari nikam na koma." ya fada dan kawar da zancen.
Turab yace " a'a bari ni na tafi da alama Umma akwai abinda zata cema, da na d'auka ma d'anka kazo ba gun Umma ba shiyasa na shigo."
A tare gabansu ya amsa da rass, Magajiya cikin tsananin tsoro tace " D'ansa?"
Hisham kam har zufa ta fara afko masa, Turab yasa dariya yace " menene hakan? Da ba d'ansa bane?"
Ai tuni Hisham kansa zuwa wuyansa ya cika da zufa, Magajiya kam a ranta tace "shikenan ta faru ta kare."
Turab ya karayin dariya yace " lalai Umma ba kara? Na d'auka d'anki a ka'ida d'an Waziri ne saboda jininku d'aya."
Bakin Hisham har rawa yake gurin cewa " sosai ma haka ne."
Magajiya kam idanu ta bud'e ta kurama Turab tana kokarin ganu abinda ke b'oye a ransa da gaske abinda yake nufi kenan?"
Turab ya kalleta yace " Umma lafiya? Naga kinata kallo na."
Idanu ta d'auke tare da cewa " ba komai, ya shirye shiryen biki?"
Yace "Thanks to you, komai na tafiya daidai."
Kai ta d'aga tace " yayi kyau."
Turab yace " Ayi hira lafiya."
Ya juya ya fita, yana fita ya kara kallan kofarsu ta gefe, "Haka ne nima ba mantawa nai ba, yanzu ya kikeso ayi?" kalaman Hisham da yaji sanda ya iso gun ne ya kara dawo mai, tabbas akwai wani mugun abu da suke kara shiryawa, ya tabbatar.
Juyawa yai ya fita.
Yana fita Hisham ya saki wata ajiyar zuciya ya kalli Basira yace " kinji hanjin cikina?"
Magajiya ta kurama kasa ido kafin tace " Inaji ya kamata mu maida Khadija kano."
Yace " Kano? Kamar ya?"
Tace "kasan Mahaifiyar Saifullahi ta kirani jiya da daddare tace wai Khadija tace ma Saif akwai wanda takeso, dolene mu maidata kano in taga bata gani yarancan sai ai auren, inba haka ba intaga mutuwarsa abin zai baci, ka san dagar da akai da ita sanda tana karama ma bare yanzu."
A ransa yace " ni da 'ya'yana sai dai a dinga sharada min abu, da girmana amma a dinga kaskantar dani"
A fili yace " hakan yayi."
Nan suka cigaba da tsarinsu.....
*********
Basira zaune a falonta, gabanta kuma leda ce irin mai karfin nan, da alama kaya ne a ciki.
Amsa sallamar Turab tai sannan ta kalli kofar da ganin shigowarsa.
Turab ha shigo sannan ya zauna yace "Umma gani."
Kallansa tai tace " Dama aikenka zanyi."
Kallanta yai sannan ya kalli ledar gabanta, sai kuma yar murmushi yace "Gun 'yarki?"
Tace " eh, Mairo zaka kaimawa, sa wa nai a d'inka mata na bikinka."
Murmushi yai yace "Umma kenan."
Kallansa tai tace " Amma baka tunanin hakan yazo da kamar wulakanci ko?"
Turab yace "wulakancin me?"
Tace " Na kaimata kayan da zata sa a bikinka bayan akwai wata a kasa."
Turab yace " Lalai Umma, ni bansan wannan ba ki tambayi Lanta....."
Da sauri yai shiru tare da kallanta, Kallansa tai itama tace " Turab har yanzu ba labarin inda Hajiya take? Bare Lantana?"
Kai ya d'aga alamar eh.
shiru sukai ganin haka yasa ya jawo ledar yace " Zanje in anyi Magrib."
*********
Garzali ne ya kaishi, yana cikin mota Garzali ya fito ya aika a kirata.
Ta gama kunce lale kenan wanda tayi a hannunta, aka sanar da ita zuwan Turab.
Wankewa tai dama ba sallah zatai ba ta saka hijab ta dan murza hoda sannan ta fito.
Tanaji 'yayan kishiyar babarsu na mata habaici, ko ta kansu bata biba tai waje.
A jikin soro ta tsaya dan bata fita waje zance, ka'idar gidansu ne haka.
Turab sai da ya hangota sannan ya bud'e motar ya fito, rike da ledar.
Tundaga nesa take murmushi har ya iso, Kallanta yai sannan ya karasa cikin soro yace " Hajiya Maryam an fito?"
Kallansa tai tace " Yaya ina wuni?"
Bai amsa ba sai cewa dayai " kwana dayawa?kin bata bat."
Fuska ta d'an rufe tace " wlh inasan zuwa gaida Umma magana ce banaso."
Leda ya mika mata yace " ga sakonki inji Ummanki."
Amsa tai tana murmushi tace " oh ni, me na samu?"
Yace " kayan bikin yayanki ta d'inka miki."
Gani yai ta d'ago da sauri, sannan yanayinta ya canza, yace " Badai Umma tayi lefi ba?"
Ya ke tai tace " a'a."
Kallanta yai zai yi magana aka dallesu da fitilar mota.
A tare suka kalli motar, Turab ya sa hannu ya rufe idanunsa dan sam bayasan a haskashi irin haka saboda idanunsa.
Mairo ta juya kai tare da jan tsaki.
Turab ta kalla ganin yanda ya rufe idanunsa yasa ta taho dan nufo mai motar.
Har ta iso sannan ya kashe, tare da fitowa daga motar.
Kallansa tai tace " Abdulmajid me ke nan?"
Kallanta yai fuskarsa a d'aure yace "me kike a can?"
Tace " ko ma me nakeyi banaji ya shafeka amma wannan dallenin da kai da fitila fa?"
Kallan inda Turab yake yai bai amsa mata ba taga ya nufi inda Turab yake.
Abdulmajid na zuwa ya d'aga hannu zai naushi Turab, Abu Turab ya sa hannu ya tareshi.
Kallo kallo sukai kafin turab ya sakar mai hannu sannan yace " ka kiyayi kanka da san duka, sannan ka kiyayi kanka da saurin hawa Da kuma kishi "
Abdulmajid yace " Kai waye da zaka bani shawara?"
Turab ya kalleshi ba shakka yana tausayamai alokacin da yasan sirrinsa shiyasa baya neman fada dashi a wannan lokacin.
Mairo ce ta karaso ta kalli Abdulmajid, zatai magana Turab yace " Bari na wuce."
Ya karasa maganar tare da wucewa ta gaban Abdulmajid.
Biyoshi tai tace"Yaya kama Umma godiya."
Juyowa yai ya kalleta sannan ya kalli Abdulmajid dake tsaye yace " Mairo."
Kallansa tai bata amsa ba, yace " karki dinga zafaffama Abdulmajid."
Tace " Yaya na fadamai ba so nake ba, na rasa dalilin takurar."
Shiru yai tare da cigaba da kallan Abdulmajid yace " ba yanda za'ai?"
Kallan mamaki tamai tace " yanda za'ai me?"
Kai ya girgiza da sauri yace "ba komai."
Ya karasa mota ya shiga.
Shiru tai tana kallansa har sukai gaba, ba yanda za'ai? Me yake nufi?"
Karasawa tai inda Abdulmajid yake.
Kallanta yai yace " Mairo mai ya kawoshi?"
Ledarta ta nuna mai tace " abu ya kawomin, ko da wani abun?"
Abdulmajid yai murmushi yace " Mairo lalen ki yayi kyau sai kika fito kamar amarya."
Harararsa tai tace " kamar Ango ne ba amarya ba."
Dariya yai yace " in kika zama kamar ni Angon ki ai ba wani abin bane."
Baki ta d'an murguda tace " Ka manta."
*********
Turab kam kansa ya kama a cikin mota wanda yaji yana sarawa, yace " Ya Allah! Ka kawo komai da sauki, kada ka bani ikon cutar da wanda bashida hakki akan al'amarin nan, ka bani ikon aiwatar da komai yanda ya kamata.
Nace Ameen
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_Haly(Mom Farhan) Allah ya kara lafiya yasa kaffara ne....Wish u quick recovery_
*66*
Abu Turab idanunsa ya bud'e a hankali ya shiga kallan d'akinsa kafin a hankali ya furzar da wata yar karamar iska daga bakinsa.
Sannan yasa hannu ya dafa gadon ya mike ya zauna, idanunsa ya rufe ya shiga karanto addu'oin safiya, kafin ya sauko daga kan gado.
Yau saura sati 3 bikinsa, dayake gidan maza ne ba wani abu special ake aikatawa ba, an dai kammala ginin bangaren da zasu zauna da gimbiya.
Saukowa yai daga kan gadon sannan ya nufi bandaki dan kama ruwa da yin alwala.
Bayan ya dawo daga masallaci ya zauna yai ta tilawar al-qur'ani har sai da gari yai haske, wannan al'adar haka yake yinta dan koyar wace ta ma'aiki S.A.W.
Sai wajen karfe goma yaci abincin safe sannan ya fito.
B'angaren Mahaifiyarsa yaje sukai 'yar hira kafin ya fito.
Yana kokarin komawa bangarensa ya hango Baiwar da take kula da bangaren Abdulmajid wanda ya shine ya sakata a bangaren dan kawomai rahoto akan Hisham.
Karasowa tai cikin hanzari sannan ta gaisheshi, tana yi tana kalle kalle.
Turab ya kalleta yace " lafiya da safen nan?"
Tace "banga d'an aike bane, dama Waziri ne ya zo yanzun nan, sannan rike yake da lefa katuwa, da ya shiga ciki na amshi laidar sai naga kula ce sannan ga kamshin abinci nan."
Turab yace " yayi kyau, koma bakin aikin ki."
Tace "Yarima Abdulmajid ya......"
Dakatar da ita yai yace " na tambayeki rayuwar Abdulmajid? Ko kuwa a sanda na baki aikin nan nace ki dinga kawon zancensa? A iya sanina ce miki nai kawai in Waziri yazo ki sanar dani."
Tace " Tuba nake ranka ya dade."
Turab ya sallameta sannan shikuma ya shiga ciki.
A bakin kofa ya tadda Garzali da alama fita zaiyi.
Turab ya kalleshi yace " in zaka fita ka biya bangaren Sarki gub Jakadiya."
Garzali ya kalleshi yace " Jakadiya?"
Turab yace " ka sanar da ita Hisham na bangaren Abdulmajid."
Garzali cikin rashin fahimta yace " to." dan bazai iya tambayarsa dakili ba.
Garzali ya garzaya yaba Jakadiya sako.
Ita kanta kallab Garzalin tai tace " abinda yace kawai ka fadamin kenan?"
"iya kacinsa kenan."
Ya juya.
Jakadiya tai shiru tana kara maimaita kalmar kafin daga baya ta fito.
Bangaren Magajiya ta nufa, Magajiya na karyawa ta shigo.
Sama sama ta amsa gaisuwarta tanayi kamar bataso.
Sannan tace " me ya kawoki?"
Jakadiya ta miko mata leda tace " maganine aka kawo na gyaran fata."
Magajiya ta kalli maganin dake cikin farar leda sannan ta kalleta tace " ni ce miki akai ko wani kare da doki ya bani magani amsa nake?"
Jakadiya tace "badai haryanzu baki hakura ba?haba Hajiya Magajiya, matar sarki, uwar sarki, kakar sarki."
Magajiya ta wani juya kai sannan tace " Me ya kawo ki? Dan na tabbata ba wannan bane kadai abinda ya kawoki."
Jakadiya ta dan shafi fuska sannan ta matso tace " hmm dama na kasa fahimtar wani abu ne, Na rasa me yasa nake ganin Waziri yanzu yana zirya bangaren yarima Abdulmajid."
Magajiya ta kalleta tace " ban gane ba.."
Jakadiya tace " Tuba nake Ranki ya dade amma nifa hankali ya kasa kwanciya da zuwansa."
Ruwan da ta gama sha ragowar cikin kofun tai kamar zata zubo mata har ta rufe idonta ta d'auka ita zata zuba ma.
Magajiya ta ajiye cup din sannan ta kalleta tace " najiki inaso kuma ki fita."
Jakadiya ta had'iyi yawu sannan ta mike tai waje.
Magajiya tai shiru tana tunani, dama kwanaki Turab ya sanar da ita ya ganshi amma shi ha musa, sannan an fada mata rannan an ganshi, sannan yau Jakadiya ta fada mata, me Hisham yake tunani? Tamai magana akan kai Khadija Kano ma ya mata burus sannan yanzu ya fara kewayewa yana zuwa gun D'anta?
Turab kam zama yai a falo yai zama cin abinci sannan ya rufe idanunsa, yana kada 'yan yatsun hannunsa, Magajiya! Ki jira juyawar bayan duk wani na kusa dake, a hankali zan ruguza miki duk wani abu da kike takama dashi....Slowly ya saki murmushi sannan ya bud'e idanunsa, ta ya zakuyi kisa ku cigaba da zama kamar wad'anda basuyi komai ba? Kun halaka rayuwar mutane dayawa amma ko tunawa bakwayi.
Hannunsa ya dunkuke sannan ya kalli bakin kofa cikin tsananin kunar rai.
********
Abdulmajid na mikewa daga kan gado aka sanar dashi zuwan Hisham, baiyi mamaki ba dan ya kula yanzu wata gulma ce take damunsa, inba haka ba da can me yasa bai mai haka?
Sai dayai wanka sannan ya fito.
Hisham ya sa an jeramai abincin dayasa matarsa tai, ita kuwa tanayi tana farinciki dan yauce rana ta farko da zatai abinci domin d'anta Shikadai.
Kallan abincin yai sannan ya karasa ya zauna, ya gaisheshi.
Hisham ya amsa fuskarsa a washe yace "Ashe bacci kake?"
Abdulmajid yace " eh wlh, kayi hakuri na barka kai kadai kawu."
Hisham yace ba komai, zauna kaci abinci, goggonka ce ta dafa ma.
Abdulmajid ya kalleshi sannan ya kalli abinci yace "Kawu me kakeso?"
Hisham yace " name kenan?"
"na tabbatar abu kakeso a gareni shiyasa kake nunamin kulawar da baka nunamin da, badai so kake in auri Khadija ba ko wani abun ba?"
Da sauri Hisham ya zaro ido yace "ka auri khadija kuma? Wannan wani irin shirmene? Auzubillah."
Abdulmajid yayi mamaki yanda yaga yayi, sai dai bai kawo wani abu ba yace " to inba shiba menene? Na tabbata akwai dalilinka na yin haka balle ma kace kar na dinga sanar da Umma zuwanka."
Hisham yai shiru yana tunani kafin yace " ko d'aya kawai dai ina ganin ya kamata mu saba da juna ne, na ga ko aboki baka dashi."
Abdulmajid ya kalleshi baice komai ba ya fara cin abincin.
*******
Magajiya kam Jakadiya na fita hankalinta ya kasa kwanciya, mikewa tai ta shirya ta fito ta nufi bangaren Abdulmajid.
Da yake ta baya ne bata wani dadeba ta isa.
Ana kokarin sanar da isowarta tace ayi shiru.
Kai tasa tare da tura kofar a hankali.
Hisham taji yana cewa " Na d'auka wancan sati zaka zo, sai naga baka zo ba."
Abdulmajid wanda ya gama cin abinci ya kalleshi tare da wanke hannu yace " ya su Umman da Khadija?"
Hisham yace " suna lafiya, zakazo ran juma'ar?"
"Yaje ina?" abinda sukaji kenan da ga bayansu.
A tsorace suka mike, Abdulmajid ya kalleta yace " Umma."
Kallansa tai sannan ta kalli abincin da ya gama ci tana gani tasan Hisham ne ya kawo dan ga kuka nan a gabasa, sannan ita ba irin abincin da aka kawo mata ba kenan.
Ba shakka ranta ya baci sosai, dan idanunsa sun canza fuskar nan tata ta had'e ta tamau.
Kallan Hisham tai tace " Yaje ina?"
Hisham ya kalleta sannan ya kallu Abdulmajid, kallan Abdulmajid tai tace " ina zaka?"
Abdulmajid yace " Umma."
Kallan abincin tai sannan ta kallu Hisham tace " me kenan? Waye ya baka ikon kawomai abinci?"
Hisham ya kalleta yace " dan na kawo mai abinci wani abin ne?"
Cikin d'aga murya wanda ni kaina sak dana razana tace " wani abin ne babba ma kuwa, yaya me ke damunka?"
Abdulmajid wanda ransa ya dan sosu ya daure yace " Umma dan ya kawomin abinci wani abun ne? Kawu nane fa na tabbata bazai cutar dani ba."
Kallan Abdulmajid tai tace " ta ya kasan bazai cutar dakai ba? Dan yana kawunka kawai?"
Hisham yace " mene? Kina nufin ni zan cutar dashi?"
Cikin bacin rai tace " yaya biyoni inasan magana dakai."
Tai gaba.
Abdulmajid ya dafa kai, sannan ya kalli Hisham wanda yama rasa mai zaiyi.
Yana kallan Hisham yai waje.
Komawa yai ya zauna jiki a sanyaye.
Ita kuma suna shiga d'akinta ta juyo cikin tsananin bacin rai zatai magana.
Hisham ne yai saurin cewa me kike nufi da zan cutar da abinda na haifa?
Wata irin dariya ta saki mai razanarwa, sannan ta tsuke bakinta lokacin d'aya ta matso kusa dashi tace " me? Abinda ka haifa? Inji wa kenan?"
Hisham yace " mene?"
Tace " ahhh dalilin kenan da yasa kake neman kula dashi yanzu? Saboda d'anka ne? Ko saboda kanasan amfani dashi nan gaba?"
Hisham yai kasa dakai.
Tace " idan har kana san kanka da arziki ka fita harkar d'ana, shine magajin sarki banasan wani abu ya faru har sai ya hau mulki, in kuma har kana tunanin wani abu kama daina dan zan iya sa Abdulmajid ya daina ko gaidaka ne kai kasani."
Kallanta kawai yake yama rasa mai zaice.
Hannu tasa ta shafi fuskarta sannan Tace " Yaya banaso muna fada akan abinda bai kai ya kawoba, ban hanaka kula Abdulmajid ba amma bance ka shishigemai ba, d'ana ne banasan wani abu na shakuwa ko sama da haka ya shiga tsakaninku."
Sam yama kasa magana, sai mamaki kawai da yake na kalamanta.
Magajiya tace " Yaya na aika da kayayyakin bikin Abdulmajid gida, sannan karka manta da shirin mu na ranar d'aurin aure, wannan shine abinda ya kamata muyi ba fada ba."
Ta karasa maganar tana murmushi kamar ba abinda ya faru.
Hisham " to." kawai yace ya mata sallama ya fita.
Tabbas daga Abu Turab sai ke zakisan ni kikama haka, ba uwa d'aya uba d'aya ba ko 'yatace ke wlh sai kinsan nikikama haka.
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
_I sincerely apologize to u 😌_
*67*
Basira ce ta kalli mai martaba tace " Barden ya amince ne?"
Takawa yai shiru alamar tunani sannan ya kalleta yace " Basira kiyi hakuri, nasan yanda kika d'auki Mairo na kuma san halin Abdulmajid, yanda Magajiya ta raineshi a haka yake, yaro ne wanda bai yarda da babu ba, sannan duk abinda yakeso gani yake dolene sai ya samu, hakan ne yasa nake nunamai ba haka ba, nake kuma janyeshi daga jikina saboda banaso yai tunanin komai nasa ne kamar yanda Uwarsa ke koyar dashi, sai dai nayi tunani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 37