dakyau yaran yanasan yarinyar sannan Mahaifiyarsa ba so take ba, ko dan Magajiya taji ciwon bijire mata da d'anta yai ina tunanin Amincewa."
Basira tace " ba wai naki aminta da kai bane sai dai meyasa nakeji kamar kanasan had'a auren ne bawai dan farincikin d'anka ba ko dan karfafa zumunta da Barde ba, ya nakeji kamar dan cikar burinka na kuntatama Magajiya kake san had'a su?"
Sarki ya kalleta yace " wannan tunanin shine babban dalilin dayasa na dage akan auren Turab da Bilkisu."
Tace " bangane ba."
Yace " a masarauta dolene ka sadaukar da wani abu dan samun wani abun, bazai yiwu ka samu komai ba, inhar inaso Turab ya zama Sarkin da naso na zama dolene na samarmai mace jinin sarauta wacce tasan sadaukarwa."
Basira ta kalleshi tai murmushi dan ta fahimcu a fakaice magana ya gwab'a mata, tace " Allah ya baka hakuri."
Hannunta ya kamo duka biyun yace " inaso ki zama mai karfafamin gwiwa akan al'amurana, bawai dan Magajiya ba kawai nake san had'asu, inaji a jikina zata zama mata ta gari agareshi."
Shiru tai dan batasan me ma zatace ba, amma itakam dan ba yanda zatai ne, bataso Magajiya ta zama sirika a gun Mairo.
************
Yau kwanan Abdulmajid biyu kenan Magajiya bata kulashi, gaisuwarsa kawai take amsawa.
Yau dai abin ya dameshi bayan ya gaisheta yaki tashi.
Ya dade a zaune kafin yace "Umma nikam sai yaushe zaki huce ne?"
Bata kalleshi ba bare yasa ran amsawa, yace " kema kinsan ba ji nace ya kawomin abinci ba, sannan gani nai Kawu Hisham yaya yake a gunki kinga kuwa Uba yake a gurina......"
A gun wa yake uba?"
Kallan mamaki ya mata yace " Umma kinsan kwanan nan kin canza kuwa?"
Kallansa tai tace " na canza ko ka canza?"
Yace " Umma yanzu na kula kamar akwai abinda ke damunki, abinda bai kai ya kawoba sai inga kinji haushi, a da kuwa kina dadewa kafin inga b'acin ranki."
Shiru tai ita kanta tasan haka ta rasa me yasa takejin ta akoda yaushe kamar intai sake Abu Turab zai ruguza mata rayuwa.
Abdulmajid ya taso yazo gabanta yace " Umma meke damunki?"
Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace " Abdulmajid."
Naam Umma.
"inaso kamin alkawari a koda yaushe cikin ko wani hali zaka zama a bayana, bazaka taba juyamun baya ba."
Murmushi yai wanda sainda hakoransa suka bayyana yace " bakyasan indinga shiga jikin Kawu?"
Kai ta girgiza alamar a'a tace " kawai dai banasan inga wani yana neman janye min kai ne."
Yace " Umma kenan, wa ya isa ya janye miki d'anki? Nifa d'anki ne ba kuma wanda ya fimin ke duk duniyar nan."
Tace"ka tabbatar ka ajiye wannan kalmar a kasan zuciyarka."
Kallanta yai yace " Umma na kasa fahimtar dalilinki na yin hidimar bikin Turab, akan me wacce ta haifeshi bazatai ba sai ke?"
Magajiya tai shiru a ranta tace" kwalliya zata biya ai kud'in sabulu."
Amma a fili tace " karka damu nice uwargidan Sarki, hakkinane na kula da hidimar bikin 'ya'yansa."
Abdulmajid ya dai kalleta ne kawai amma zuciyarshi bata gamsu da wannan sharhin nata ba.
Haka ya taso ya fito.
Da yake juma'a ce massalaci ya wuce, bayan an idar da sallah Abu Turab na cikin mutane suna ta gaigaisawa ana tsokanarsa akan ya kusa zama ango.
Abdulmajid na zaune yana hangoshi, shi kansa Abu Turab baya minti biyu sai ya kalli inda Abdulmajid yake saboda yanasan ganin Hisham kusa dashi.
Abdulmajid ya miko yazo shima aka fara gaisawa dashi.
Hisham ne ya karaso gun, yana zuwa Abdulmajid na gaisheshi ya juya zai yi tafiyarsa.
Hisham ganin haka yabishi da sauri tare da kiransa, tsayawa yai tare da juyowa, Hisham ya iso yace " gida zaka?"
Abdulmajid ya kalleshi yace " eh, da wani abun ne?"
Zaiyi magana Abu Turab ya karaso yace " Abba barka da juma'a."
A tare suka juya suka kalleshi, Hisham yace " ni?"
Turab yace " Kai Abba, zumunci akeyi shine kuka taho gefe?"
Abdulmajid yace " a yaushe ya zama Abbanka?"
Turab ya kalli Hisham irin jin kunyar nan yace " Waziri baka sanae dashi ba?"
Hisham ya had'e rai yace " me zan sanar dashi?"
Turab yai murmushi yace " Abdulmajid ai munkusa zama surukai."
Kallan Hisham yai cikin mamaki, yace " me? Sirikai? Badai Khadija ba?"
Turab yai kasa dakai yace " da alama kuna bukatar keb'ewa ko kwa zanta na maganar, ko gun Khadijan zaka kaji komai?"
Abdulmajid ya cika yai fam, yace " Kawu me kenan?"
Hisham ya kasa magana.
Turab ya kalli Abdulmajid yace " ka tambayi kanwarka."
Ya juya yai gaba, sai dai hankalinsa na kansu.
Baisan me sukace ba sai dai yaga sun juya a tare sunyi hanyar fita.
Turab ya kalli Garzali yace " dubamin ko gida sukai."
Yace to.
Bai dade ba ya dawo yace " ya gansu sum shiga mota a tare."
Murmushi Turab yai yace " Bari muje muga Hajiya Umma Magajiya."
Yai gaba.
Tanaji an sanar da ita zuwan Turab sai da gabanta ya sake fad'uwa.
Mike wa tai ta shiga cikin d'aki, gyara kanta tai sosai, sannan ta fito.
A zaune ta ganshi yana cin ayaba.
Karasowa tai ta zauna, Turab ya kalleta yace " Umma barka da rana."
Ta amsa cikin izzarta sannan tace " banyi tsammanin ganinka ba."
Yace " nima bansan zanzo ba sai dai kinsan Juma'a dole ne d'a ya kwashi gaisuwar iyaye."
Baki tad'an tabe, jujuyawa yai kamar yana neman wani abu yace " Banga Abdulmajid da Waziri ba, na d'auka nan sukazo."
Kallansa tai tace " baka gansu ba anan kuma ka d'auka nan suka zo? Wace irim tambaya da amsa ce wannan?"
Turab yace " naga sun fita tare da aka idar da Sallah shiyasa na garzayo saboda ingaida Baban namu."
Shiru tai sun fita tare? Me kenan? Badai Hisham baiji fadanta ba?
Turab yace " Hala sun shiga garine zumunci, abinka da d'a da mahaifi."
A hankali ya karasa maganar.
Kallansa tai tace " me kace?"
Turab yace " me nace? Nikaina na manta."
Idanu ta kafa mai tace "kamar zance d'a da mahaifi kai...."
Dariya yasa yace " d'a da mahaifi kuma? Wa? Abdulmajid da Waziri? Ta yaya?"
Kallansa tai tsoro ya gama kamata, duk yanda taso ta b'oye sai da Turab ya gano hakan, yace " Umma?"
Kallansa tai tace " wani shirme kake fad'a, kai da Sarki nake magana ai."
Yace "Ahhh ni da Abba? Ko Abba da Abdulmajid?"
Magajiya ta makamai harara, yace "Au ashefa ni Abban nawa sun zama biyu tunda akwai Waziri."
Magajiya tai murmushi tace " Wai kana shirye shiryen bikin kuwa? Ko kuwa kana nan kana neman auren wacce ba baka za'ai ba?
Turab ya mike yace " Umma ki tabbatar komai na bikina ya tafi lafiya yanda ake so, in har kinaso bakina yai shiru kenan, sannan auran Khadija sai dai in ni ince bazanyi ba badai ku ba, daga ke har Wazirin saboda......."
Sai kuma yai wani murmushi yace " a bar dai maganar ko Umma? Banasan ciwo ya kamamin ke kafin bikin d'an naki."
Kallansa tai idanunta sun kasa d'aukewa daga kallansa tace " ko? Zamu gani ai."
Gira ya d'aga yace " ya kamata mu gani kam."
Ya juya yai waje.
Yana fita ta fara maimaita kalamansa, ta rasa me suke nufi, tabbas dole ne tasan me dan iskan yaran nan ya sani.
Mikewa tai tace "Hisham dani zakaja?"
A can gidan kuwa, sun isa gidan Waziri, khadija ta fito daga wanka kenan, mai kawai ta shafa ta saka doguwad riga ta zauna a bakin gado, ita yanzu komai ma baya mata dadi, in har ta tuno da kazanta da kuna rashin imanin da suka aikata.
Muryar Umma taji tana kiranta, fitowa tai tare da amsawa, ganin Umma tai bakinta yaki rufuwa saboda tsantan farinciki.
Umma tace mata " Khadija yarima ne yazo, yana nemanki."
Sam bata kawi Abdulmajid ba dan bai taba zuwa gidansu ba, ta d'auka masoyin ranta ne.
Da sauri ta koma d'aki ta shafa hoda da turare sannan ta yafa mayafi ta fito.
Sallama tai a falon, muryar data amsa ne yasa tasan ba muryar masoyin nata bane, bud'e labulen tai tare da cewa "Yaya?"
Abdulmajid ya kalleta sannan ya kallu Umma wacce ta taho rike da tire.
Matsa mata khadija tai Umma ta mikama Khadija tire mai dauke da lemon zobo, sannan tace " a kawo abinci?"
Khadija ta kalli Abdulmajid tace " Yaya wai a kawo abinci?"
Murmushi yai dan shi ya rasa me yasa Goggo take kunyarsa, sam Bata iya tsayawa suyi magana ko zuwa can tai, yace " na koshi khadija, zobon ya isa."
Umma ta juya, kallo d'aya zaka mata kasan tana cikin tsantsar farin ciki.
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*Na Ayusher Muhd🤸🏼*
*68*
Khadija ce ta karasa ciki ta zauna sannan ta gaisheshi.
Kallanta yai yace " Khadija meye tsakaninku da yaran can?"
Kallansa tai sannan tai kasa da kai.
Yace " Khadija me kike tunani? Kinaso kicemin yaran da na tsana shi kike so? A ma bar maganar so tunda nasan dama Kina sanshi amma me kike nufi da aurensa?"
Khadija a ranta tace " abinda nasan bazai taba yiwuwa ba kenan."
Amma a fili tace " Ya Abdulmajid."
Cikin fada yace " kinaso ki je gidan sarauta a matsayin kishiyar Gimbiya? Sannan a matsayin matar wancan yaran?"
Khadija ta kalleshi tace " Yaya wai me yasa ka tsaneshi da ya wa haka?bayan bai taba yima komai ba?"
Abdulmajid ya kalleta cikin b'acin rai yace " na tsaneshi, kallansa ma ba san yi nake ba, duk duniya shine mutum na farko dana tsana."
Khadija batasan sanda tace " bayan shine ya kamata ya maka wannan tsanar?"
Yace " mene?" khadija ta kalleshi tace "Yaya please ka dinga sa ruwan sanyi a ranka, in har wannan karamar maganar ta b'ata ma rai ya zakayi in babbar magana ta doki kunenka?"
Yace " babbar magana? Wacce iri kenan?"
Juya kai tai da sauri tace " ina dai fada ne saboda ni banga abin jin haushi a maganar ba."
Abdulmajid ya mike a zuciye yai waje ko zobon baisha ba.
Kanta ta dafe tare da rufe idanunta.
Hisham kam yana d'aki yana cire Babbar riga Umma ta shigo bakin nan nata a washe, tace "wai ya akai ya biyoka?"
Yace " sai ki rufe bakin ai, kin wani baje baki kamar yau kika taba ganinsa.
Kasa tai da kai tana murmushi.
Hisham ya shiga band'aku dan kama ruwa, yana fitowa yai falo inda Abdulmajid yake.
Me zai gani?"
Ba kowa a falon, da sauri ya fito yana kiran Khadija.
Fitowa tai daga d'aki tace " gani."
Cikin tsawa yace " ina Abdulmajid?"
Tace ya tafi.
Yace " ban gane ba?"
Shiru tai dan batasan me zata ce ba.
Waje yai da sauri cikin tashin hankali.
Umma ce ta karaso gunta tace " Me kika ce masa da har zai tafi ba ko sallama? Yanzu khadija bawan Allahn nan bai taba zuwa fa gidan nan ba sai yau, amma ki koreshi? Ta ya ya zaki......"
Kasa karasawa tai, Khadija cikin tausaya mata tace "kiyi hakuri Umma amma ba korarsa nai ba."
Umma tai shiru kafin tai ciki.
Khadija ta bita da kallo cikin tausayawa.
Abdulmajid yana fita yai gida.
Har zaiyi bangarensa aka sanar dashi kiran Magajiya.
Yana shiga ya taddata a tsaye da alama yawo take a tsakar falon.
Shiga yai ya kalleta yace "Umma ga......"
Wani wawan mari da ta sakar mai ne yasa ya kasa karasawa, tace " Uban me kaje yi gidan Waziri?"
Kasa magana yai sai kuncinsa kawai daya rike yana kallanta.
Magajiya ta kara hasala tace " wato bakajin maganata ko? Na d'auka na sanar dakai ba kai ba keb'ewa da yaya? Wato shine har da zuwa gidansa ko? Ka nunamin yafini matsayi a gunka ko?"
Abdulmajid yai shiru, tace " fitarmin daga falo, sannan wlh karka kuskura inkarama magana akan wannan zancen, na fadama."
Abdulmajid yai waje jiki a sanyaye, mota ya fada ya ja ta da gudu yai waje.
Abu Turab na kallan sanda ya fita, ba shakka yasan Magajiya ta haushi da fada ne, a fili yace " am sry, sai dai kaima kayi abubuwa marasa dacewa wanda dolene kaima kaji ba dadi."
Juyawa yai ya koma b'angaren sa.
Har zai zauna ya fito ya nufi bangaren Umma.
Tana zaune tana ta raba cingam ya shiga.
Yace " Umma amma dai harda 'yan katsina zaki aikama ko?"
Tace " kanaso kenan bikinka ya lalace daga biki zuwa gulma, gulmar da zata zama silar rugujewar komai."
Turab ya kalleta yace " Kina tunanin zasuyi zancen anan?"
Tace " Abu Turab kenan, bakasan mutane ba, kai a ido ne zaka ga kamar 'yan uwa ne amma a zahiri ba haka bane."
Kallanta yai sai dai baice komai ba, a kasan ransa shikansa yana san yaga 'yan uwansa.
Basira ta cigaba, kun had'u da Mai Martaba?
Yace " a'a."
Tace shikenan.
Kallanta yai cikin kulawa yace " lafiya dai ko?"
Tace bakomai.
********
Abdulmajid kam bai tsayar da motarsa ba sai a kofar gidansu Mairo, kallan kansa yai a madubi yace " baka da inda zaka sai nan?"
Kofar gidansu ya kalla sannan ya kwantar da kansa jikin sityarin motar ya dade a haka kafin ya tada motar yai gaba.
Yayanta ne ya shigo lokacin taba tsinke alayahu.
Yace " Yauma kin fita kikai?"
Mairo tace " infita zuwa ina?"
Harararta yai yace " wlh ki kiyayi kanki da wulakanta mutum, mutum ma irin Yarima wanda kalma d'aya zai iya sa rayuwar gidan nan ta ruguje, tun dazu bawan Allahn nan yake waje har ya gaji yai gaba."
Baki ta tabe tace " ni bai aikomin ba dan bansan yazo ba."
Ciki yai tare da yin kwafa.
Mairo ta cigaba da tsinke alayahunta, can tace " me ya kawoshi da ranar nan? Sannan bai aiko ba?" tsaki tai tace " damuwarsa ce."
************
Washegari kuwa Magajiya tasa aka kira mata Hisham, yana shiga ta rufeshi da fada kai kace itace uwarsa ba ma yayarsa ba balle kuma kanwa.
Ganin abin ya zo mai wuya yasa yace " Wai Magajiya inada tambaya."
Yaran nan da kike fada akansa na waye?"
Tashin hankalin da ba'a misaltawa.
Idanunta kadai sun isa su nuna maka tsantsan tashin hankalin da take ciki, tace " Yaya?"
Yace " kwarai ni yayanki ne, sai dai abun ya isa haka, akan yaran nan yaje gidana zaki sani a gaba da fada haka? Cinyeshi nai a gidan nawa ko me?"
Kallan mamaki takemai yanzu, yauce rana ta farko da Hisham yake maida mata murtani.
Tace " yaya ni kake fadawa magana?"
Yace " an fada miki d'in, duk yanda naso in kyautata miki na kula bakya gani, yanzu kwata kwata kin zama sai a hankali komai fada, ina Magajiyar da na sani wacce tsoro baya cikin zuciyarta?"
Tace " nikaina bansan meke damuna ba Yaya, sai dai tundaga sanda yaran can ya ce yasan sirrina nakejin kamar komai na rayuwata xai ruguje, yaya ka taimakeni ka kashe yaran nan da uwarsa, ni har itama banasan gani ba shi ba."
Hisham yace " in taimakeki? Duk abinda kike min?"
Tace " amma ai kai kasab burina ko? Dolene mu kawar da duk wata matsala da zata kawo mana kai akan nad'a yaran nan mulki."
Hisham ya kalleta a ransa yace "Magajiya kenan, zanyi duk abinda kikeso saboda d'ana, sai ya hau mulki in shekaki kema barzaho."
Hannu ya saka zai murd'a kofar shiga, abinda yaji ne yasa ya tsaya cak sai jikinsa da hau tsuma saboda tsananin tsoro da razana.
Magajiya ce ta katseshi tare da cewa " yaya."
Kallanta yai bai amsa ba.
Tace " na fasa kashe basira, mai kake gani in muka haukatata?"
Hisham yace " hauka?"
Tace kwarai " idan muka halaka Turab a ranar auransa ita kuma sai musa a haukatata kaga sai ace rashin d'anta ne yasata yin haukar."
Hisham ya sheke da dariya yace " gaskiya Magajiya ba digon imani a ranki, duk duniya kece mutum ta farko danasan yasan salan mugunta, ko shed'an sai dai ya sara miki."
Murmushi tai tace " ni dai yaya ka taimaken ka kyalemun yarona, wannan shi kadai ne abinda nakeson ka dashi, mu samu komai ya kammala, banasan wani abu ya tare mai hawa mulki."
Kafafunsa ne suka kasa d'aukansa da sauri ya dafa bango, dan gaba d'aya jikinsa kaurewa yake da rawa......
*Turab*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*69*
D'aki ya koma da sauri ya shige cikin d'aki shi kadai, labulayen d'akin ya rufe duka, ya shige lungun gado ya kankame kafafunsa.
Kalaman dayaji ne suke dawo masa, a haukata Basira? A kashe Turab ranar auransa?
Me ke faruwa? Me kunensa yakeji haka? Tsoro da fargaba sun hanashi fita, adaren ranar kuwa da zazzabi ya kwana.
Cikin dare kuwa yayi mafarkin wannan abu yakai sau nawa.
A zabure ya mike ya shiga cikin bargo, me Umma da kawu suke shirin yi? Kisa? Duk yanda yaso ya daure ko fitowa yai ya kasa.
Kwanan Abdulmajid biyu ko kofar gidansa bai fita ba, ya rasa menene abinyi dan abin duniya ya dameshi.
*****
Biki na ta matsowa, Gimbiya ansha gyara, gyaran da fadarsa ma bata lokaci ne, kullum Abu Turab na kiranta su gaisa.
Yau ma tsokanarta yai tayi a waya wai bata gajiya da killaceta da akai? Ba dama ko fita tai?
Sai dai tai murmushi tace " itakam bata ga wani abu ba."
Suna gama waya ya ajiye kan wayar sannan ya kalli Sabi'u yace " ya ya irin wannan sa ido haka? Ko kishi kake ne?"
Sabi'u yace " Gaskiya Turab da alama kanasan Gimbiya."
Turab yai murmushi yace " bai kamata in so ta ba?"
Sabi'u yace " ina na isa? Kawai dai da na d'auka kamar tursasa ma akai, amma yanzu naga kamar san ranka ne."
Turab yai murmushi tare da mikewa tsaye yace " Sabi'u kasan menene abinda ke halaka rayuwar zaman aure?"
"a'a."
Turab yace " nunama mace kiyayya."
Sabi'u ya kwashe da dariya yace " lalai Ango da alama ka fara shirye shiryen canza rayuwa."
Turab a ransa yace ina zaka gane abinda hakan ya jawo? Jiya da daddare ya dade yana tunanin wani abu, idan ya duba menene ya sa Magajiya ta zama tsantsar muguwa ba shakka rashin nuna mata damuwa da Sarki yai ne tun farko, wannan shine yasa take neman ta kwatarma kanta 'yanci na samun duk abinda takeso, tare da sashi ya so ta ya kuma kaskanta a gunta, wanda hakan ne ya jawo tai ta tafka kura kurai tare da kauce hanya, gashi yanzu tayi nisa wanda ta manta ma da dalilin dayasa ta cikin wannan halin tun farko.
Ajiyar zuciya yai tare da kallansa yace " Sabi'u kenan."
************
Gobe ne ake sa ran tafiya kano dan d'aurin auren Abu Turab, shirye shirye ake sosai da sosai, dan ma masu shirin suna Kano, masarautar kano kam ta cika ta batse da 'yan uwa na jini, na mulki da kuna na siyasa, Sarkin kano sosai yake cikin farinciki.
Dan ana sauran kwana hudu daurin aure yasa aka kiramai Turab ya kara bashi amanar 'yar tilon 'yar tasa da yake ji da ita kamar nama d'aya a cikin miya, yayyinta ma haka sukai ta bashi amanar ta, ba shakka ya fahimci tsantsar gata da ji da Gimbiya Bilkisu da akeyi, sai dai ko ina kalma d'aya yake fad'a _Baiyi alkawarin santa ba kamar yanda suke santa ba, sai dai ya musu alkawarin kula da ita, da kuma kaucema duk abinda zai sata dana sanin auransa._
Magajiya kuwa da Hisham sun gama shirinsu tsaf, ta rasa gane kan Abdulmajid dan sai yai kwana biyu kafin yazo gaisheta, inyazo kuwa gaisheta kawai yakeyi ya mike ya tafi, sai dai batasa wannan a ranta ba dan tana ta faman shirin yanda zasuyi gun halala Turab.
A ranar d'aurin auransa ne Abdulmajid sai zarya yake a d'aki, mai ya kamata yai?
Duk yanda yaso ya cire abin a ransa ya kasa, shi gani yake menene nashi a ciki? Sannan shima ai ba san Turab yake ba, sai dai gani yake kamar duk saboda shi Magajiya da Hisham suke neman halaka Turab, dan ya hau mulki ya kuma auri gimbiya, sannan su salwantar da mahaifiyarsa wanda take tushensa.
Har wajen karfe takwas yana ta zarya, gashi a lokacin mutane duk sun shirya ma sunyi gaba.
Magajiya ce ta aiko akan yai wanka yai shiri sosai na gani na fada.
Bai musa ba kuwa ya je yai wanka, kayan data aiko mai ya saka, kaya ne masu tsananin kyau da tsada, wanda ya tabbata ankashe kudi sosai a kansu.
Harya fita ya koma ciki tare da yanko yar takarda ya rubuta kamar haka _Ka tabbatar ka sanar ma mahaifiyarka kar taci komai yau, in har ba ita tai da kanta ba, kar kuma tasha komai._
Fitowa yai ya samu wata baiwarsa wacce take kurmiya, ya mika mata yace taje waje ta ba yaro ya kaima Abu Turab, sannan ta tabbatar bata fadama kowa ba wanda ya aikota sannan karta bari a ganta.
Hakan tayi kuwa, dan kurma Allah ya bashi iya rike sirri da kuma alkawari.
Turab yana zaune, Sabi'u na ta wani fesa mai turare kamar zai juyemai kulbar a jikinsa.
Turab yayi kyau na ban mamaki, Magajiya ta aikomai had'adun kaya sai dai bai sa ba, dan wannan Mahaifinsa ne ya aikomai.
Dole ne in ya wuce sai ka kalleshi saboda tsantsar kyan da yai, kwarjininsa da zatinsa kadai xai sa ka kalleshi ta baya.
Turab ya fizge turaren dake hannun Sabi'u yace " Ka bari in akazo naka auren sai ka fesa turare har a cikin bakinka ma, ba damuna zaiyi ba, amma ba ni ba."
Sabi'u yai dariya.
Shigowar Garzali ne yasa Turab ya kalleshi yace " Garzali ba na baka kaya nace ka saka ba?"
Kansa ya sunkuyar yace " Ranka ya dade kayan ai sunfi karfina."
Sabi'u ne yace " Gaskiya Turab ka d'au mataki da alama Garzali ya fara daina jin maganarka."
Da sauri Garzali yai kasa yace " Tuba nake ranka ya dade, yanzu zan saka."
Mikamai takarda yai yace " gashi inji wani yaro."
Turab ya amsa tare da bud'ewa.
Abinda ya ganine yatada masa hankali, yace " Garzali ina yaran yake?"
Yace " ya tafi."
Turab da sauri yai hanyar waje, dafashi Sabi'u yai yace " Lafiya?"
Turab yace " ina zuwa."
Waje yai da sauri sai dau ba yaran ba kuma alamunsa.
Fitowa yai ya nufi bangaren Mahaifiyarsa tana zaune kasanta mutane ne suna ta kukula Kayan robobi da su dubulan da zasu raba.
Mairo ya gani a gefenta, alama ya mata da hannu akan tazo.
Mairo ta mike ta fito.
Waje suka fita sannan ya kalleta yace " Mairo kina nan ai yau cir anan ko?"
Tace " a'a anjima nakesan tafiya."
Tai maganar fuskarta a had'e, irin wai kishin nan, balle yanda taga yasha kyau, haka kawai tana sanshi ba tun yanzu ba amma wata can a sama tazo zata aureshi...(😂nace Mairo ai dama haka rayuwa take, Matar mutum...Lol) dan itakam dan Basira ma ta aika tazone amma da bazata zo ba.
Turab ya mika mafa takardar nan, tana karantawa ta d'ago cikin tsananin tsoro tace "Yaya mekenan?"
Yace " ban san meke faruwa ba, sai dai na tabbatar akwai abinda ake shirin yi, ki tabbatar Umma bataci komai na gidan nan ba, ko ruwa in zatasha ki sa a kawo kara daga gidanku."
Tace " ko ruwa?"
Yace " bazai yiwu haka ba, yanzu bari nasa amaida ta kawai gidan Abba dake cikin gari, inaji hakan zaifi sauki."
Tace " mutanen da zasu nemeta fa?"
Kai ya dafa sannan yace " ko waye ma yazo nemanta ace batada lafiya tana asibiti."
Mairo tace "to."
Yace " ta fito yanzu ba sai kin fada mata ba, kawai kice wani guri nace a rakata ta gani, zan turo garzali, in yaso in kukaje gidan kya fada mata."
Tace to
Nan tai ciki, sai dayaga fitar Mahaifiyarsa sannan hankalinsa ya kwanta.
Haka suka kammala komai suka fito, sai dai jikinsa gaba daya yayi sanyi, inhar Magajiya zata cutar da Mahaifiyarsa ya tabbata ta kanshi zata fara, ya tabbatar akwai abinda take shirin yi masa.
Kansa ya dafe, da alama yayi sakaki da sharrin Magajiya, ya yi sake dayai tunanin bata isa yi masa komai yanzu ba.
Abdulmajid yana kallansa a tsaye, cikin mutane suna ta gaigaisawa, sai dai ya tabbatar shima abin na damunsa, dan murmushin da yakeyi inka kula da kyau iya l'abansa suke basu kai har zuciyarsa ba.
Ya tsani yaran can, amma me yasa yakeji bazai iya bari a kashe shi ba?
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 27 Chapter of 37