bud'e, kana kallan rubutun kaga rubutu ne na 'yan koyo, sai dai da yake bata iya karantawa ba yasa ta ajiye wasikar a tunaninta ba mai amfani bace.
Sai dai me? Kwana hudu kenan ana aiko mata da wannan wasikar sannan yaro ne yake kawowa kuma daga ya bada yake sa gudu yai waje, yau abin ya fara damunga dan da alama magana mai mahimmanci ake san sanar da ita.
Sawa tai a kira mata Rabi'a, bayan tazo sun gama gaisawa ta d'auko wasikar ta bata tace " Karantamin."
Rabi'a ta amsa tare da bud'e wa.
Na farko an rubuta "Hajiya d'anki na cikin matsala."
Na biyu " Hajiya ki yafemin sai dai ba yanda zanyi dolene na cigaba da zuba maganin nan inba haka ba Magajiya halakani zatai."
Na uku "Hajiya ki taimaken ki d'au mataki ko na samu zunubina ya tsaya anan."
Na hudu " Hajiya kiyi wani abu dan Allah."
Hajiya ta amshi takardar a taorace tace "Rabi'a kin tabbatar da abinda aka rubuta kenan?"
Rabi'a tace "Hajiya wlh abinda akace kenan amma me hakan yake nufi? Magajiya tana ba sarki magani? Akan me?"
Hajiya tace " jeki gida sannan maganar nan ta zama sirri tsakaninmu koda wani abu zai sameni kimin alkawarin bazaki taba fadan wata kalma ba."
Rabi'a tace "Na miki alkawari, nan ta mata sallama ta fita da tsananin mamaki, bazata taba iya ma Hajiya musu ba."
Tana fita Hajiya ta kona takardar sannan tai shiru tana tunani, ba wanda ta yarda dashi bare suyi maganar dashi, sannan batasan wacece tayo mata wasikar ba, gashi ita ta tsufa ba wani abu da zata iya yi.
Abu d'aya ne ya dace tai shine taje gun Magajiya dan nuna mata ba tsoronta ake ba sannan ga fadamata inhar bata daina ba zata sanarma Sarki.
Yau da safe tasa aka kira mata Magajiya, tun safe aka sanar da ita amma sai yamma liss sannan tazo.
Hajiya na zaune da charbi, zama tai akan kujera sannan tace" Hajiya kim wuni lafiya?"
Hajiya cikin takaici ta kalleta tace " me kike bawa d'ana?"
Magajiya ta kalleta cikin mamaki tace "me nake ba d'anki kamar ya kenan?"
Hajiya tace "Kamar yanda kikaji haka yake, wani tuggun kike dubgawa Abdussamad, nasan dai ba maganin mutuwa kike bashi ba tunda zamansa a mulki shine zamanki kema a mulki, sanar dani me kike masa?"
Dama Magajiya na tsananin jin haushin Hajiya dan tunda aka aureta tasan ba santa takeyi ba, fuska ta canza ta d'aure fuska tace " koma me nake bashi ai mijinane sannan bakida ikon shiga tsakanin mata da miji."
Ta mike zata fita, Hajiga abin ya bata mamaki tace " waye ya haifa miki har kika aura? Sannan ni dama tunda na fara ganinki wlh nasan ke ba alheri bace a gareshi ba kuma matar zama bace ta amana, ko kiyi gaggawar daina abinda kike bashi ko kuma wlh in sanar dashi, zakiyi mamaki inkika ganki a gidan yayanki da takardar saki, ba'a saki a gidan sarauta bari sakin uwargida wacce take sarauniya sai dai ina sanar miki za'a fara akanki."
Wata banzan dariya Magajiya tai tace " Me? Ni za'a saka?"
Hajiya ta kalleta sai dai yanda taga Magajiya tayi yasa tsoro ya d'arsu mata dana sani ya kamata me yasa bata fadama d'anta ba ta sanar ma Magajiya?"
Magajiya tazo kusa da ita ta sakar mata murmushi tace " ina jiran lokacin da za'a bani takarda, ki kuma tabbatar an bani, sannan maganar magani maganin hana d'aukan ciki ne ki tabbatar kin sanar dashi haka."
Ta juya ta fita, tana kallan Hajiya duk ta rikice jikinta ya d'auki rawa.
Bayan Magrib tanashan ruwa shikenan ta kasance ba lafiya tun daga wannan rana har yau ba baki ba zama bare tafiya."
}
Magajiya ta mike tazo saitin kunnen Hajiya tace " Kijira d'ana ya hau mulki in har kinada rai ni zan taimaka a fitar dake daga gidanan akaiki can bayan gari ki zauna kyafi jin dadin zaman duniyar, in kuma kinaso in hada da jikanki da kuma uwarsa Basira ku zauna tare acan."
Ta mike tai waje.
Tsayuwa tai a wajen gidan, me turab ya sani? Bataji akwai wanni babban sirri dazai tsoratata da ya wuce wad'an nan biyu, sauran duk sai dai tasa a aikata amma badai ita dakanta ba, inma zancen kashe yayan Basira ne ai ba ita bace tai Hisham ne.
Dolene ta nemi Turab ta kuma bihi cikinsa da jin sirrin da ya sani.
Turab zauna akan kujera yana d'an kada dan yatsansa d'aya tunani yakeyi wace hanya ce mafi sauki da kuma bakin ciki da zai sa Magajiya ta fita hayyacinta in taji Yayanta Hisham yaci amanar ta? Ya tabbata Hisham da Magajiya kowa amfani yake da dan uwansa.
Ita tana amfani dashi dan cikar burinta, shi kuma yana amfani da ita dan samun matsayin da zai wuceta nan gaba, murmushi yai yace " Badai tana tunanin in Abdulmajid ya hau mulki komai na burinta ya cika ba?"
Mikewa yai ya fito waje.
Hango Abdulmajid yai a zaune yana shan iska jiyai tausayinsa ya dan darsu mai, ya zaiji in yaji wannan sirrin? Yauce rana ta farko dayaji tausayin Abdulmajid ya kamashi.
Ya zaiyi ya sa Magajiya da Hisham su tunama junansu asiri da kansu?
Khadija!
Shiru yai jin sunan daya zo mai, tabbas itace a tsakanin mutanen biyu, ita da Abdulmajid, sai dai me? Zuciyarsa zata iya jure amfani da ita?
Juyawa yai ya koma ciki tare da furzar da iska mai zafi.......
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*58*
Duk yanda Magajiya tai akan samun mafita ta kasa, da sassafe kuwa ta aika akan a kira mata Hisham.
Ko gaisuwarsa bata amsa ba tace " Yaya inaji fa yaran can yasan wani abu namu."
Gabansa ne ya fad'i kallanta yai sannan ya tuna kawo Khadija gida da yai, ba dai wani abu ta fada mai ba?
Daurewa yai yace " bangane ba? Me ya sani?"
Ta girgiza kai tace ban sani ba sai dai daga yanda yazomin da kuma yanayin kalamansa inada tabbacin yasan wani abu wanda yafi fyaden da akama Basira."
Hisham ya sauke ajiyar zuciya jin da alama ba Khadija bace yace " amma kinsan yaran nan shegen yaro ne anya ba dan karkiyima Mahaifiyarsa wani abu bane?"
Magajiya ta girgiza kai cikin yanayin tunani tace " Yaya bakaga idanun yaran nan ba alokacin, sannan cemin fa yai in fara hada kayan lefensa yaban zuwa sati biyu, kamar ni dan karamin yaron da ko uwarsa na girma yazomin da zancen rainin hankali irin wannan?"
Hisham shi kansa yayi mamakin jin haka yace " da kuma bakinsa ya fad'a miki hakan?"
Tace " anan gun kuwa, sannan harda cemin in sa Abdulmajid ya janye auren Mairo, umarni fa yazo ya bani wanda ko ubansa bai taba ban umarni akan abinda yasan ina duk wani abu na ganin na hana wannan abun."
Hisham yace " da alama yasan wani abun to amma ta yaya?"
Magajiya ta juya kai tace " wannan shine abinda ke damuna."
Shiru sukai kafin can ta kalleshi tace " Yaya"
Kallanta yai yace " ya zakiyi?"
Murmushi ta saki tace " kamar ni? Abinda yafi damuna kenan dan jiya ko baccin kirki ban samu ba, kamar ni Magajiya ace wannan yaran zai kalla ya bani umarni?"
Hisham a ransa yace " an tabo Masifa."
Magajiya ta kalleshi cikin iza tace " zanyi abinda yace bayan na tabbatar da akwai sirri na a hannunsa, zanyi lefe zan kuma sa a sa rana, zan nuna ma jama'a Turab ma d'anane."
Hisham cikin tsananin tsoro ya kalleta dan ya tabbata wank mugun abun zata fada daga karshen abin arzikin datai, dan yasanta haka take in har aka bata mata rai sai ta nuna bakomai Sai kuma tayi abinda baki bazai fadu ba.
Magajiya ta kara wani murmushin jin dadi tace "Aure? Auren Bilkisu?" sai kuma ta sa dariya tace " lalai nayi gangancin barinka da rai."
Hisham ya kalleta yace " me kike tunanin yi?"
Kallansa tai sannan ta wani juya ido tace " sai muga ranar auransa waye zai je gun, mai makon kaga ai aure da shi a d'aura da Abdulmajid sannan su gama d'aura aure suzo su tadda angon da aka shirya za'ai dashi a kwance ba numfashi."
Hisham ya kalleta yace " ban fahimceki ba....."
Tace "Zaka fahimceni, dan kuwa kaine zakasa a kamashi a hanyarsa ta zuwa d'aurin auran, sannan musa abokinsa dole ya sanar akan bazai samu zuwa ba dan shi ba auran yake so ba, kaga ran Sarki zai b'aci matuka ya aura ma Abdulmajid Bilkisu sannan mai makon mu sakeshi lafiya sai mu juya abin a matsayin 'yan fashi ko kuma hatsarin mota, kaga mun jefi tsuntsu biyo da dutse d'aya."
Mamaki ya hana Hisham magana kawai kallanta yakeyi.
Kallansa tai tace " ya? Wasan nawa ya had'u?"
Idanunta ya kalla yace " Magajiya kenan, duk duniya Allah bai taba hadani da mai kaifin basira irinki ba, da ace Basirarki a abu mai kyau kike sa ta lalai da ancigaba a gidan nan."
Harara ta makamai tace " mai kake nufi?"
Jinjina ya mata da hannu yace " komai yayi nake nufi."
Tace " Uwata fa?"
Sai daya had'iyi yawo yace " tana gida ba lafiya."
Cikin kulawa tace " da alama sam yaya baka kula da Khadija, inaji zan dawo da ita gabana har tai aure, munyi magana da Mahaifin Saifullahi yace tunda yara sun daidaita zasu kawo kudi."
Hisham yai murmushi yace "Allah ya kaimu."
Kallansa ta kuma yi tace " Ya ake ciki a fada akan maganar auran Abdulmajid da wannan sakaryar?"
Hisham yai tsaki yace " kwana biyu dai anyi shiru da maganar dama Galadima ne uban san kawo maganar da Turaki."
Magajiya tai shiru kafin tace " Gun Abu Turab zani yanzun nan dan in tabbatar da abinda yake dashi."
Hisham ya kalleta yace " da kanki zaki? Ba gwara ki aika yazo ba?"
Murmushun jin dadi tai tace " ai tun yanzu za'a kulla abotar d'a da uwa saboda gudun zargi da zai biyu baya."
Kallanta yai sannan yai kasa dakai.
Mikewa tai ta fita sannan shima ya fito.
B'angaren Turab suka nufa, mai kula da kofarsa ne ya bud'e tsananin mamaki ya kamashi na ganin Magajiya.
Su kansu mutane duk wanda yazo wucewa alokacin sai dayai mamakin ganinsu.
Bud'e mata kofa yai tare da gaisheta.
Magajiya ta shiga tana kanta tsaye.
Garzali ne ga taho da sauri tare da gaishesu.
Magajiya ta kalleshi tace " Turab fa?"
Yace " yana d'aki."
Nan ya nuna mata hanyar falo ta shiga.
Tsayawa tai tana kallan bangaren, abinda ko bangaren Abdulmajid tunda ya tasa bata zuwa.
Garzali yai ciki dan kiran Turab.
Abu Turab ya gama sa kaya kenan yaji ana kwankwasawa, yace waye? Garzali yace "nine kayi baki ne."
Bai tambayi waye ba sai huka da ya saka ya sa turare ya fito.
A zaune ya ganta tayi zamanta na isa akan kujera.
Mamaki ne yasa ya ja ya tsaya tare da jingina kansa da bango, yace " Umma Magajiya da kanta?"
Alama tama bayin da su fita daga falon,saj da suka fita sannan ta kalleshi tace " tsayuwar anan ta menene? Abun mamaki ne in uwa tazo ganin d'anta?"
Kallanta yai sannan ya tako a hankali yana cewa " inafa abin mamaki, dama ai hakkinta ne na ta kula da d'anta."
Ya karasa maganar tare da zama.
Kallansa tai tace " nayi tunani akan maganar ka sai dai banaji kai ka isa ka bani umarni sai dai In zaka canza yanda kamin magana daga umarni zuwa roko."
Kallanta yakeyi har saida tazo karshe, gani tai ya sakar mata wani bazawarin murmushi yace " ko?"
Ranta ne ya d'an soso ta kalleshi.
Yace " kin fara had'a kayan? Ko dayake jiya mukai maganar bazai yiwu ace kin fara ba, amma ina sanar miki sati biyu na baki kacal in har kika wuce ina tausayin halin da zaki shiga dan banaji Sarki zai barki da ranki, in kuwa har ya barki to lalai a kurkuku zaki karasa rayuwa daga ke har yayanki."
Gabanta ne ya fadi, ta daure tare da kakaro dariya tace " inji wa kenan? Kai kana tunanin duk duniya akwai wanda ya isa ya hukuntani? Sarki? Hahah lalai yaro yaro ne."
Turab kallanta kawai yake, jin kalamanta yasa ya mike tsaye yace " Ba sarki bane zai hukuntaki Umma mantawa nai, nine nan d'anki wanda zai hukuntaki, ya kuma hukunta duk masu hannu a abinda kuka aikata."
"Ahhh, bansan me yasa nake tausayin mutanen da kukai amfani dasu gun cimma burinku ba, sai dai ina tunani anya zasu yafe muku? Sannan Hisham da kike takama dashi...."
Sai kuma yai shiru tare da yin kasa da kai yana dariya yace " ke kina tunanin zai cigaba da bin umarnin ki har sai sanda kika jefashi halaka?"
Kallansa tai cikin mamaki tace " mene?"
Kafada ya d'aga mata ya girgiza kai yace " Bansan komai ba."
Juyawa yai yace " in kin gama ganin gidan d'an naki kya rufomai kofa."
Ya juya yai ciki ransa a b'ace, wato bata d'auki Sarki da wani matsayi ba? Gani take tafi karfinsa.
Ba shakka ran Magajiga yakai gurin tunzura, lalai dole taga karshen yaron nan ita ganin sa ma ta tsani yi yanzu.
Haka ta fito rai a b'ace.
************
Abdulmajid kam yana tsaye a kofar gidansu Mairo sai data dade sosai dan sai da mahaifiyarsa ta tsawatar mata sannan ta fito.
Yana ganinta ya sauko yana washe baki.
Tsayawa tai tare da hard'e hannayenta ta juya mai baya a cikin soron.
Abdulmajid ya karaso ya kalleta ta baya sannan yace " Gimbiya irin wannan tsayuwa haka kamar mai shirin yin hoto?"
Juyowa tai ta kalleshi tace " Abdulmajid."
Da sauri yace " Naam."
Tace " dan Allah dan Annabi ka kyaleni, wlh wlh ni kam na gaji da wannam abun, ka sanni sarai banaso raina ya bace dan wlh xanyi abinda kaima sai kai dana sani."
Kalamanra ko a jikinsa yace " eh wlh, dan Allah Mairo kiyi abinda zanji jiki ni wlh so nake yi."
Wani banzan kallo tamai na takaici tace " wai kana d'an sarki me yasa kake abu kamar karamin yaro?"
Hannunta ya kamo, da sauri ta fizge tace " Wai Abdulmajid meke damunka ne? Na d'auka na sanar dakai banasan ka dinga tabani ko? Kaje can kun karuwan......."
Batai auni ba taji yasa hannu ya rufe bakinta.
Matsowa yai da sauri ta matsa jikin bango tana zare ido tace " meye hakan?"
Kallanta yai yace " Mairo me yasa kike tunani ni din dan iska ne?"
Harararsa tai batace komai ba.
Yace " nasan bazaki yarda da abinda zance ba amma wlh kinji na rantse ban taba sanin wata 'ya mace ba, ma sani sarai ina shafa bayin gidan mu dan jin dadi na sai dai ban taba bari abin yakai nan ba."
Kallansa tai tace " kana tunanin zina sai ka sadu da mace kawai take a matsayin zina?"
Kallanta yai yace " Mairo ni duk wannan ba sune a gabana ba, in kikace in daina taba mata zan daina nidak dan Allah ki auren, ko na aureki in kikaga dama kice sai kin amince zan kusanceki Wlh zam yarda ni dai dan Allah ki yarda ki auren, ina san......."
Katseshi tai tace " Ni dai dan Allah ka kyaleni na rokeka da Allah."
Murmushi ya sakar mata sannan yace" ma tafi yau, sai na dawo zuwa jibi."
Kafin tai magana har ya tafi, juyawa tai ta wuce gida.
*******
*TURAB*
🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)
*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*
*Wattpad :-AyusherMohd*
*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻♀*
*59*
Magajiya sam ta rasa yanda zatai, ganin ba mafita yasa ta nufi gun Sarki.
Yayi mamakin jin zuwanta bayan ta shigo ta zauna sannan ta gaidashi.
Kallanta yai tare da amsawa yace " Lafiya dai ko?" ya fada tare da d'aukan ruwan dake gabansa a kofi dan sha.
Fuskarta a sake kai kace cikin farin ciki take tace " dama maganar auren Turab ne, ina tunanin ya kamata in fara had'a lefe....."
Furzo da ruwan bakinsa yai tare da kwarewa, kallanta yai cikin tsananin mamaki yace " me? Me kika ce?"
Dariya tai na salo tace " me? Kana tunanin lokaci baiyi ba?"
Ido ya kura kura mata yace "Magajiya!"
Kallansa tai bata amsa ba, yace " kinsan me kike anan kuwa? Kin tabbatar a hankalinki kike ko kuwa wani tugun muguntar kika shiryo?"
Sansanyan murmushi ta sakar mai tace " ko d'aya na dai fahimci cewa aikinane wannan, sannan waye Turab? D'anka ne fa wanda daga shi baka kara samun wani ba, ta ya za'ai yara kwaya biyu ace mun kasa kula dasu? A wata masarautar sai kaga 'ya'yan sarki sunfi 30 amma mu a namu haryanzu biyu Allah ya bamu, me zaisa mu zauna muna samun sab'ani akan su?"
Wata banzar dariya yai dan ko magajiya zata dafa Al-qur'ani bayajin zai yadda da wad'annan kalaman nata, ya tabbatar da abinda take shiryawa.
Kallanta yai yace " yanzu me ake bukata?"
Nan ta fara mai bayani, yace zai bada kudi ayi komai cikin girmamawa da matsayi.
Tana fitowa yabi bayanta da kallo yana tunani, me ke faruwa? Ya tabbata Turab ko mai zai ce mata bazata taba yarda da zancen nan ba balle ma tasan sirrin mahaifiyarsa, me zai sa ta amince? Ya tabbatar akwai wani shirri da take yi.
*********
Turab zaune agun hutawar daya saba zama ya saka ledar maganin nan a gaba a hannunsa yana kallo cilla maganin yai sama kad'an sannan ya cafe yace " kai kuma aikin me kakeyi?"
Mikewa yai dan dole ne ya binciko maganin menene wannan.
Bangarensa ya nufa, yana shiga Garzali ya taso ya gaidashi sannan ya sanar dashi nemansa da mahaifiyarsa takeyi.
Mikamai maganin yai yace " so nake ka bincikomin maganin menene wannan yanzu, sannan ya zama sirri kar ka tambaya a gidan nan, kaje wajen gari"
Garzali yace " to" sannan yai waje.
Bangaren Mahaifiyarsa ya nufa, ta sa an shiryamai abinci, Turab ya zauna sannan ya gaisheta.
Kallansa tai cikin kulawa daga dawowarsa daga kano har ya d'an fada, Lantana ta kalla tace " Lantana zubamai abincin."
Turab ya kalli Lantana sannan yace " barshi zan zuba da kaina."
Nan ya jawo plate ya d'ebi fankaso guda biyu ya zuba miyar taushe wanda yaji kaza.
Hannunsa ya wanke sannan ya fara ci, sai da ya gama yasha zubo sannan ta kalleshi tace " ya kukai da Magajiyan?"
Murmushi yai mata sannan yace " karki damu Umma, sirrin nan sai dai ta tafi dashi har kabarinta badai ta sanarma wani ba."
Basira tace "me kake nufi? Kasan halin Magajiya fa?"
Yace " Nasani Umma sanin ne ma ya sani fad'in haka, sirrinki datake tunanin amfani dashi wajen hanani auren Bilkisu da kuma sa Mai Martaba yin murabus wannan sirrin ba wani abu bane akan sirrinta da nake rike dashi, ke dai kawai ki kula da lafiyar wannan shine kadai abinda nake nema daga gareki."
Kallansa tai cikin jin dadi da gamsuwa tace " maganar Mairo fa?"
Yana murmushi yace " Umman Mairo, wai ni Umma daga ni da alama ba wanda kikeso sai Mairo ko?"
Tace " Turab kenan, kasan yarinyar nan itace ta taimakeni har nakejin zaman gidan nan bai zaman min takura ba?itace ke d'ebe mana kewa daga ni har lantana, jinta nake kamar 'yata."
Turab ya jinjina kai yace " haka ne, shi yasa akoda yaushe nake godiya gareta, na sani ta kula dake wanda ni da nake d'anki ban baki wannan kulawar ba."
Basira ta kalleshi sai dai batai magana ba, sai dai yanayin kalamansa da yanda yake fitowa tasan magana ce wacce ke kwance a kasan zuciyarsa.
Turab ya d'ago sannan yace " karki damu Umma, Insha Allah ba abinda zai faru sai alheri."
Tace " Allah yasa."
Zama sukai shi da Lantana da Basira sukai hira sosai sai da yaji la'asar tayi sannan ya fito.
Yana shiga Garzali ya shigo falon, tare da mikamai maganin nan.
Turab ya kalleshi yace "Maganin menene?"
Garzali yai kasa dakai sannan yace " magani ne wanda zai halaka gab'obin jiki, ya hana mutum yin komai, ya kuma shanye mai b'arin jiki, a takaice dai guba ce mai illar gaske wanda samunta yake da matukar wahala."
Turab idanunsa ya runtse da karfin gaske dan ji yake gaba daya kamar an kwara mai ruwa.
Idanunsa a runtse yace " Ka yarda da sanin mai maganin daka tambaya?"
Garzali yace " kaf garin nan an san dashi dan nima kaini gunsa akai, shikansa yayi mamakin ganina da maganin, sannan ya sanar dani maganin a hankali yake lahanta mutum ba wai tashi d'aya ba."
Turab yace " jeka na gode."
Garzali ya mike yai waje.
Yafi minti goma idanunsa na runtse, wace irin matace wannan? Dan ya tabbatar itace tasa a ba Hajiya maganin nan, amma mahaifiyar mijinta? Wannan wace irin masifa ce?"
Jiyai kansa ya sara, ya mike yai sallah ya dade yana addu'oi kafin ya shiga bandaki ya sakar ma kansa ruwa.
Ruwa ne ke zuba a jikinsa hayi shiru yana tunani, ya dade sosai kafin ya fito.
Shiryawa yai sosai cikin wata dakakiyar shaddarsa ruwan madara, hula da takalmi ya saka sannan ua saka agoggo.
D'ankwalin khadija ya kalla ya dade yana kallan d'ankwalin kafin ya rufe kofar da karfi, takardar daya ajiye a gefen gado.
B'angaren Magajiya ya nufa yana tafe cikin isa.
Yayi sa'a Abdulmajid na zaune a gunta.
Tana jin ance yazo sai dataji gabanta ya fad'i, yauce rana ta farko data taba jin shakkar zuwan wani d'an adam gunta ba sai yau.
Ba shakka wannan abu ya kona mata rai.
Abdulmajid yace " ya shigo."
Turab ya shigo tare da sallama.
Abdulmajid ya bugamai banzan kallo yace "ina zakaje haka?"
Turab ya kalli Magajiya sannan ya kalli Abdulmajid yace " zance zanje."
Abdulmajid ya tab'e baki sai kuma ya zabura yace"badai gun Mairo ta ba ko?"
Turab ya kalleshi sannan ya maida idanunsa kan Magajiya datake kallansa yace" yau ba gunta zanje ba, gun Khadija zani."
Tashin hankalin daya bayyana a idanuwan Magajiya ba'a magana, Kallansa tai tace " me? Khadija? Ba dai Khadija wacce take 'ya ga yayana ba?"
Turab ya d'aga mata gira sannan yace " ya? Kin sanar ma Sarki akan maganar lefe na?"
Abdulmajid ya sheke da dariya yace "Lalai Turab amma kai ba karamin had'amamen mutum bane, kana tunanin soyayya da aure wata a lokaci d'aya?"
Turab yai murmushi yace " ba'ayi ne? Da farko dai ni d'in mijin mata hud'u ne banda kwarkwarori."
Abdulmajid yace " wannan damuwarka ce sai dai ka fita hanyar kanwata dan badai yar uwata ba kai ko kunya ma damu zaka had'a zuri'a?"
Magajiga kam kallansa take cikin idanunta da suka canza kala wanda bakin ciki ne karara ne d'auke a idanun.
Turab ya kalli Abdulmajid sannan ya kalli Magajiya tare da ciro ledar maganin nan. Ruwan dake gaban Andulmajid ya jawo ya zuba a kofi sannan ya zuba maganin nan.
Magajiya ta kalleshi tace " meye hakan kuma?"
Mika mata kofin yai yace " Umma sha."
Wani banzan kallo tamai tace " a gabana ka zuba magani kace insha? Nasan ko maganin halaka ne?"
Kai ya d'an langwab'e yace " kuma fa haka ne, kar in baki maganin dazai kwantar dake ya kashe miki gab'obin jiki sannan ya hanaki magana, ya kuma hana kwakwalwarki aiki yanda ya kamata."
Gabanta ne ya shiga fad'uwa, daurewa tai ta saki murmushi zatai magana Abdulmajid yace" ansha karya, yanzu kai kana tunanin akwau irin wannan maganin a duniya? Sannan in akwai ma mai zai sa ka saku?"
Turab ya kalli Abdulmajid yace " shine ai abin tambayar, Umma ya akai kika samu wannan maganin?"
Kallansa tai tare da fito da idanuwanta, daurewa tai tai wani dariya tace " Turab kenan, kanasan zolaya, yanzu ka shigo da magani kace ni na baka?"
Turab yace " kin manta? Ke kika bani a sanda muka had'u a b'angaren Hajiya?"
Magajiya tace " ni bansan wannan zancen ba, sannan mai zai sani in baka?"
Yace " shine abin tambayar? Mai zaisa ki bani? Sannan me na tare miki da zaki bani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 37